The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined variable $postsdone - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Trying to access array offset on value of type null - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 28488 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 28489 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 28490 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 28491 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 28492 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 28488 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 28489 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 28490 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 28491 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 28492 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 880 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 880 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 880 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 880 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $multipage - Line: 33 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 33 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $multipage - Line: 65 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 65 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
BARIKI NA FITO*BY* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA**(Maryam Obam)
#4
*PAGE 15*
Bariki direct u/kanawa ta koma, har takai gida Yarima bai zoba, dan haka taita zaman jiranshi, tayi wajan 30mnt din sai gashi ya kirata akan ta fito yana kofar gida.....
Tashi tayi ta fita inda ta sameshi cikin mota....
Gaidashi tayi cikin kulawa tare da fad'in ya aiki??
Mai yakon ya bata amsa saiya kafeta da ido, ba komai yake tunawa ba sai kalaman mahaifin nashi, inda yace karya K'ara mishi maganan auran da yake son k'arawa ..... Ido ya lumshe yana tunanin abubuwa da dama, ya tabbata bazai iya juran rashin Zainab ba, amma ya, ya iya tunda mahaifin nashi haka ya bashi umarni.... Tunda yake abbanshi bai taba cewa Kar yayi abu ba ya ketare, yana ji a jikinshi bazai iya juran a hanashi auran Zainab ba......
Jin yayi banza da ita yasa ta d'ago taga ita yake kallo da sauri tayi k'asa dakai tare da fad'in Yarima lafiya kuwa??
Murmushi yayi tare da fad'in lafiya, kawai I miss you ne...
Murmushi tayi tace kullum fa saika ganni jiya ne kawai baka ganni ba....
Yace hakane, jiyan kawai da ban ganki ba, yasa naji kaman Nayi shekara ban ganki ba
Dariya tayi mara sauti domin taji dad'in maganan da yayi.......
Sun d'an taba fira, sannan ya mata sallama ya wuce.....
Bayan Yarima ya koma Gida direct wajan mum dinshi ya nufa, bayan ya gaidata ya zauna kusa da ita tare da fad'in mum plz ina son magana dake which maganan ya shafi rayuwana.....
Gaba d'aya hankalin mum din yayi kan Yarima wanda magananshi ya bata tsoro, musamman daya ce maganan dazai Mata ya shafi rayuwanshi..... Tace Yarima Mai ya faru?? Maiya sameka? Wani abu ne?
Yace mum akan maganan k'arin auren da nake son yine. Plz mum Ina son yarinyar Sosai, mum Bari kiji tun a mafarki na Fara ganinta........
Mum tace mafarki??
Yace eh, tare da bata labarin abunda yake faruwa... Ya d'aura da fad'in mum had'uwa na da yarinyar had'in Allah ne, ina matukar sonta, mum Idan aka hanani auranta ban iya j......
Da sauri mum tace ya isa haka, jikinta a sanyaye tace Yarima zanyi magana damai martaba, Kaje ka huta dan naga alaman kaman yanzu ka dawo.....
Yace eh mum, tare da tashi ya fita.....
Mum shuru tayi tana nazari, lallai ya kamata abar Yarima yayi wannan auran, tunda har Ya iya cire kunya ya Mata bayani irin haka..... Tashi tayi ta nufi gefen mijin nata , toko ci Sa'a shi d'aya ne, zama tayi tare da fad'in Barka da yamma.
Mai martaba Ya amsa da yauwa, yana ga kaman kina cikin damuwa? Domin Fuskanki ya nuna hakan.
Tace inada magana ne akan Yarima.
Da sauri mai martaba yace maiya sami Yarima din??
Tace babu komai magana ne akan auranshi da yake son karawa....
Mai martaba yace ba jiya nace abar wannan maganan ba, sai nan gaba
Tace hakane, amma ina son fad'a maka Yarima yanzu yabar wajena, akan maganan auran nashi, labarin yanda sukai da Yarima ta fad'a mishi harda mafarkin da Yarima yakeyi, sannan tace ina son in baka shawara ,tunda muke da Yarima bamu taba cewa yabar Abu ba, sannan daka baya ya dawo da maganan......
Mai martaba ya dakatar da ita da fad'in, lallai wannan babban magana ne, Yarima yana mana biyayya a matsayin mu na iyaye..... Tunda har na hanashi maganan ya kara taso da ita bai kamata in hanashi ba, domin hanashi zai iya sawa ya bijire mana, domin shi SO daban yake, sannan muma ya kamata mu masa adalci mu amince da duk wata bukatarshi Indai bai sabama Shari'a ba..... Yau na fahimta abunda ya dad'e yana damuwa, lallai iyaye k'alu bale garemu Idan d'anka ko y'arka suna maka biyayya tare dajin duk wata magana taku, Indai yaron ya Kawo muku abu kuka nuna bakwa so, Indai ya dage Toh ku tayashi son Abun tare da mishi fatan alkhairi..... Sau da yawa wasu iyayen suke saka yaransu suke bijire musu Bayan yaran suke da gskya amma iyayen Suki yarda da kudiran yaran, in ba'a sami Mai hakuri ba saiya bijire musu, yaka mata iyaye su dinga Lura da miye yaransu suke so tare da abunda suke bukata.... Kar matsayinku na iyaye yasa ku manta hakkin yaranku akanku...... Haka zalika Kuma yaran Kar soyayya yasa ku bijire ma iyayenku ,domin Kaf duniya babu mai muku son gskya kaman iyayenku....... Akwai wani labari da naji na wani yaro da yake son auran wata yarinya....... Yarinyar kowa yasan bata ji, Ma'ana dai y'ar iska ce yarinyar, lokacin da yaron Ya fad'ama ma iyayenshi sai suka k'i yarda suka ce ya nemi wata, shiko yaron yace Wlh ita yake so, aka buga aka raya, Baban yaron yace sam bai yarda Yaronshi ya auro yarinyar ba domin y'ar iska ce....... Ganin yanda babanshi ya dage, sai yaron Ya daina musu komai dama iyayen ba masu karfi bane, yaron ke musu komai tunda yana aiki,...... Toh Kunga irin matsalolin dake faruwa, a sanda naji wannan labarin Nayi takaici Sosai, ai iyaye iyaye ne, yaka mata mu dinga hakuri dasu, mu muna ganin mune akan dai dai, haka suma suke gani sune akan dai dai, in kayi hakuri kabi umarnin su, kasan kwana nawa za suyi a duniyar?? Koko saika rasa su zaka Fara kuka dayin dana sani?? Wlh baka taba sanin muhimmancin iyaye sai basa raye, sai munyi hakuri da iyayenmu sau da yawa kana ganin abunda yake dai dai kuma kowa yasan dai dai ne amma su sai suce sam, in mutum ya duba Aida basa haka, yanzu harda girma daya kamasu sai yasa suke irin haka, Idan mutum yana girma tunaninshi yana kara canzawa...... Idan har yaro yana tuna haka ya kamata ya dinga hakuri da iyayenshi, sannan abunda kama iyayenka kaima haka naka za suyi maka shairi ko khairan, sannan Indai kai burinka kuntata ma iyaye bazaka taba ganin haske ba a rayuwa..
Mum tace hakane, Allah yasa mu dace
Mai martaba ya amsa da Ameen, tare da fad'in zan tura aje a nema masa auran yarinyar cikin satin nan insha Allah, saiku Fara shiri
Mum tayi y'ar murmushi tare da fad'in Allah ya bada Sa'a zamma Yarima albishir
Dariya Mai martaba yayi tare da fad'in dan nema ba, Ashe tun a mafarki yake ganin yarinyar ikon Allah.
Mum tace Wlh nima nayi mamaki, Allah dai yasa abokiyar zama ce.
Mai martaba yace lallai soyayyarsu had'in Allah ne, duk Wanda yace zai shiga tsakani akwai matsala
Mum tace hakane, tayu rabo ne na kusa tsakani sai yasa ya kasa hakuri, kuma rabo na kisa
Mai martaba yace hakane, Allah ya shige mana gaba.....
Mai martaba yasa an tura gidansu bariki, inda su waziri suka je, kuma babu laifi su waziri Sun yaba da irin gidan tarbiyan da bariki ta fito, domin tunda Yarima ya fad'a mata ranan da za suzo bariki ta hayo wasu mutum biyu Sunan sune y'an uwan mahaifinta, sannan duk ta tsara musu yanda za suyi.
Koda waziri yayi maganan sadaki akan nawa zasu yanke
D'aya daka cikin kawun Bariki na karya yace dubu hamsin ya isa, domin karancin sadaki shine albarkan aure,
Waziri yaji dad'i Sosai domin ya gano gidan mutunci Yarima yake neman aure sannan ba masu kwadayin abun duniya bane, duk da ya gansu talakawa kuma ko yanzu a sauron gidan suke zaune, Ma'ana a zaure.
Nan take Waliyan Yarima suka biya sadaki, dubu hamsin tare da K'ara million d'aya suka ce wannan kaman matsayin kyautatawa ne, tunda iya abunda suka yanke shine na sadakin,
Dakyar iyayen bariki suka amshi kud'in, domin cikin mutanan Yarima sunce gidan sarauta in sun bada Abu dole ake amsa, ba'a miyar musu. Sannan an tsaida rana nan da wata biyu
Nan dai akayi addu'a tare da tashi kowa Ya wuce.....
Cikin Wanda sukazo daka gefen Yarima harda Mai Anguwa, ma'ana sarkin u/kanawa, wanda Kafin su zo shine aka bama damar yin bincike akan gidansu yarinyar da irin tarbiyanta, kuma yace babu wani matsala gidan tarbiya yarinyar take Yadai yi magana Mai Kyau akan gidansu bariki ? ko Mai yasa yayi haka?? Bayan yasan yanda sarauta take?? Sannan hausawa na cewa shidai ramin karya kurarre ne, koma dai miye dalili za muji zamu gani....
Koda su waziri suka koma, sunyi ma Mai martaba bayanin irin gidansu bariki, Sun fad'a mishi gidan mutunci Yarima yake neman aure, sannan suka kara da fad'amai sai dai talakawa ne Sosai ba masu karfi bane, domin yana yin gidansu ya nuna hakan, kuma kaman gidan Haya suke, waziri ya kara da fad'in sai dai abunda ya kara burgeni duk da irin talaucin su , suna da wadatar zuci, basu da kwadayin abun duniya
Mai martaba yaji dad'i Sosai, tare da fad'in ina son Kafin Ayi bikin a nema musu Gida su koma, wannan kyauta ce daka gareni
Waziri yace an gama godiya suke .
Bariki bayan magabatan Yarima sun tafi, ta fito ta sami babanta na Bariki da sauran mutanan, nan suka bata kud'in, sannan ta sallami mutum biyu din akan saita kara nemansu. Tafiya sukayi suna godiya.
Kallon abbanta na Bariki tayi tace gskya aiki yayi kyau
Yace Sosai kuwa, sai naji dama auran nan da iyayenki na gskya kika had'asu, ina tsoran ranan da asiri zai tonu
Bariki tace karka damu, komai a tsari nake tafiyar dashi.
Yace dakyau tare da fad'in ni kam inda mmnki zata yarda Aida munyi aure
Bariki tace dagaske kakeyi?
Yace dagaske nake Wlh
Bariki tace Aikam zan mata magana sannan ni zan biya sadaki, da kayan lefe akwati guda biyu ai zan had'a maka Indai dagaske ne wlh, nima na samu lada
Yace ina godiya Kinga gwara Ayi auran, tunda nida ita Kar tasan Kar ne
Dariya bariki tayi tare da fad'in wannan haka yake.
Yarima Aliyu yana barin asibiti ,direct wajan bariki ya nufa, inda bata ma San da zuwanshi ba, saida ya kirata yace ta fito yana waje, Dan haka ta tashi ta fita ta sameshi a mota
Yarima kallonta yayi cikin jin dad'i tare da fad'in amaryata
Murmushi tayi cikin jin kunya tare da gaidashi
Amsawa yayi tare daja mata hanci, yace am so happy today
Kallonshi tayi tare da fad'in happy for wht?
Yace soon zaki zama tawa ..... Oh na manta kin ma riga kin zama, Ashe an bani ke har an biya sadaki...
Murmushi kawai tayi
Yarima yace yaushe za muje kiga gininki?
Tace a'a basai Naje ba,
Yace toh ni ina son kije ki gani , ya za'ayi kenan??
Tace zan tambayi Umma inta amince sai muje
Murmushi yayi kawai tare da kawar da maganan yace, Mai kike bukata Ayi da bikin mu??
Tace kaman me??
Yace event din da za'ayi
Shuru tayi tana nazari inta yarda Ayi event Kar a wajan event taga Wanda ta sani, Kar su fad'ama Yarima gskya Kafin ita ta fad'amai, kai gskya a'a.. Kallon Yarima tayi wanda shima ita yake kallo tace Yarima inaga Kar Ayi wani bidi'a.....
Kamo hannunta yayi tare da fad'in, a'a ya kamata muyi koda Abu d'aya ne, muyi dinner, inaga zaifi
Tace toh amma fah badan taso ba, ta dai amince ne dan Kar yaga kaman ta'ki yarda da maganansa.....
Kallonta yayi yace tunda an gama maganan event saura na akwati zan baki kud'i Kisai irin kayan da kike so, duk da za'a kawo miki daka gidanmu, wannan wanda zan baki akwai wanda nake bukata ki siya wanda only me zan dinga ganinki dashi, saiki K'ara da irin naki choice din .
Bariki ido ta rufe ciki jin kunyan maganan Yarima, ta rasa mai yasa Idan yayi mata wata maganan take jin kunya Bayan tasan ita bata jin kunyan magana gaban kowa, kodan Yarima badan iska bane sai yasa nake jin kunyan shi? Tabbas hakane domin duk Wanda kuka ga yana maganan banza gaban wani in kuka duba za kuga shiya bada dama Ayi mishi.
Sunyi fira akan in zai dawo zai Kawo Mata kud'i cash ta siya abunda take so sannan ya Mata sallama ya tafi ..... Toh andai ce duk abunda akace an yishi had'e da karya komai daren dad'ewa gskya zata bayyana, zamu gani asiri zai tonu Kafin biki ko sai Bayan biki muje zuwa........
~MARYAM OBAM~


*PAGE 16*
Bariki gida tayi, tana shiga ta doka ma habib kira akan yazo, kallon uwarta ta bariki tayi tace Umma.....
Amsawa tayi da fad'in ya akayi? Yau dai Kedai shar
Bariki tayi dariya, tare da fad'in ina son miki magana Allah yasa zaki amince....
Umma din tace name fah.?
Bariki tace akan abbana, Mai zai hana kuyi aure, inaga zaifi muku.
Umma tace aure? Dawa Rufamin asiri, barni inyi abunda ya kawo ni.
Bariki tace kin fiso ki zauna babu aure??
Tace a'a ina so inyi mana inna samu dai dai ni
Bariki tace gashi kin samu
Dariya tayi tare da fad'in shiya ce miki zai aureni? Ko Kece kike son had'awa??
Bariki tace shiya Aiko ni inyi miki magana, kuma naga Wlh auran shiya dace daku.
Tace hakane, Allah ya tabbatar mana da alkhairi, saiki fad'a mishi na amince
Bariki tace Alhmdlh, amma dan Allah Ayi bikin Kafin aurena..... Nan dai sukai ta tattaunawa suna cikin fira habib ya fad'o kaman an jefoshi
Bariki tace miye haka ko sallama babu
Tsaki yayi tare da fita ya tsaya a kofar d'aki yana gafaranku dai masu d'aki, tare da kuso Kai.....
Bariki tace wannan ne sallama??? Ai b....
Yace dakata Mlm, nifa ban gane miki ba, tunda Yarima ya fara soyayya dake kika koma wata iri iri, in ke kin zama ustaziya ni barni yanda nake.....
Bariki tace Allah ya shirya, ni bama wannan ba zauna kaji.....
Kallon tara saura kwata ya watsa ma bariki, sannan yace wlh Ina gab da in Tsiga miki rashin mutunci, Idan kina kaini jinsin da ba nawa ba.....
Tace Allah ya baki hakuri, zauna dan Allah
Zama yayi yana bud'e hanci wai shi a dole ranshi a bace yake
Bariki tace iyayen Yarima sun Aiko har Sun tafi
Yace haba dan Allah?? Gud'a ya saki tare da fad'in inama inada duwawu babba dana tashi nayi rawa da duwaiya guda d'aya....
Bariki dariya tayi tare da fad'a ma habib yanda aka yanke bikin nan da wata biyu
Habib yace Wlh bariki ban San mai yasa ba, ina sonki da Yarima,...
Bariki tayi dariya tace ngd kawata, nan suka shiga tsara yanda za'a gudanar da bikin da yanda za'a samo kawayen Haya duk habib yace abar komai a wajanshi......
Sannan maganan gyaran jiki irinsu dilka, maganin Mata bariki tace y'ar Maiduguri take So,da yar Sokoto
Suma habib yace duk zai Kawo, cikin satin nan dan a Fara , sunyi magana Sosai inda tabi habib suka je maraban jos domin ta Fara had'a kayanta wanda take bukata wanda bata so kuma ta bayar.....
Koda suka je sunga haulat ita da Hjy babba suna magana, ganin bariki yasa haulat ta nufi bariki Tana fad'in Indai za'aga wannan kina wajan.....
Habib yace Wlh Haulat zan miki bura uba, ban so
Tabe baki Haulat tayi tana bashi hakuri,
bariki kam wajan hjy babba ta nufa tana fad'in haka hjyta har yanzu fushin ake dani?.
Hjy babba yace kyaji dashi, ni Kinga karki batamin rai yanzu da yamman nan
Bariki tace haba hjyta kiyi hakuri mana
Hjy babba yace Wlh bariki kina bani mamaki, da kyanki da kuruciyarki da lafiyanki, amma kice zaki aure, keda ake rububinki haba bariki
Bariki tace hjyta adai yi hakuri
Hjy babba yace ya wuce yana tabe baki
Bariki tace godiya nake tare dayin gaba ta nufi d'akinta.....
Tana cikin had'a kaya haulat tazo, ganin bariki nata aikin had'a kaya yasa haulat tace badai bikin yazo ba??
Bariki tace eh Wlh, Kinga wata biyu aka sa, gwara in fara had'a kaya, in kyautar dana kyautar wa inbar na Bari
Haulat tace hakane, ni har yanzu ba'a fad'amin dan wani gari bane ko sunanshi
Bariki tace saurin Mai kike ki jira koma Waye zaki gansa in lokaci yayi
Haulat tace Allah ya kaimu, nan ta Fara taya bariki had'a kaya, haulat ta d'auko wata Leda nan kayan suka zube dan ledan ya fashe, Aiko ayabar roba suka fito...... Haulat d'auka ta farayi taga har guda biyar tace bariki dama kina dasu?? Ah ba banza ba kika daina harka da maza ba, ashe kina da abunda yake d'ibe miki sha'awa
Bariki kai ta girgiza tare da cema haulat ki d'auka duka na baki, ni ban taba amfani dashi ba, yanda aka bansu haka na ajiyesu dan banda abunda za suyi min
Haulat ta dinga godiya tare da fad'in amma wanda ya baki yasan kina son babban ayaba tunda harya baki....
Bariki tace Alh madu Yaban dan iskan tsoho, ci gaba da had'a kayanta tayi harta gama taba haulat kyautan kayanta da yawa.
Haulat tana ta mata godiya duk yanda haulat taso bariki ta fad'a mata wa zata aura amma bariki ta'ki Tadai fad'a mata dan gidan sarauta ne, abunda kawai bariki ta fad'a mata kenan..........
A kwana a tashi babu wuya wajan uban giji, bariki ta gama istabra'i, sannan iyayenta sunyi aure, mai martaba ya siya musu Gida Mai kyau 4bedroom a u/kanawa inda anan iyayen nata na Bariki suka tare, sannan bariki tace ta bar musu gidan halak malak, domin suna Mata aiki yanda ya dace, bariki ta K'ara kyau da haske domin ana mata gyaran jiki Sosai.....
Yau bikin bariki da Yarima baifi kwana Goma ba, Yarima yanzu ba kullum yake zuwa wajanta ba, domin aiki sunyi mishi yawa, ga hidiman biki, gana asibiti ga fitinar zinatu, abubuwa sunyi mishi yawa Sosai..... Yana office ya Gama duba patient yaji yana bukatar ganin Zainab dinshi dan haka ya tashi ya nufi gidansu, wanda yanzu in yazo ciki yake shiga dan akwai falon ba'ki a gidan, kiran Zainab din yayi yace ta sameshi a waje basai y'a shigo ba.
Fita tayi inda ta sameshi a mota ta bud'e ta shiga tare da gaidashi
Mai makon ya amsa sai yace Kai my princess Kinga yanda kike K'ara kyau kuwa?? Gskya ana gyaramin ke dakyau,
Murmushi tayi cikin jin kunya sannan tace Kai Yarima wani kyau nake karawa?? Tayi maganan a shagwabance
Yace Zona nuna miki tare da janyota jikinshi, wani irin kamshi ne ya daki hancinshi Wanda tunda ta shigo yake ji, amma daya janyota jikinshi sai yaji kamshin ya fito Sosai, gaba d'aya yaji jikinshi ya fara weak domin kamshin turaren yasa jikinshi ya fara yin sanyi..... Itama ta gefenta wani iri take ji domin maganin da ake bata ya tsumata Tana matukar bukatar namiji amma babu yanda ta iya dole sai mijinta Bayan tayi aure, gashi yanzu Yarima yana son tada mata bala'i.... Yarima Aliyu hura mata iska yayi a fuska da sauri ta d'ago suka had'a ido peck yakai mata a goshi tare da furta I love you my princess
Da sauri ta lumshe ido
Ganin haka yasa Yarima ya kura mata ido yana kallonta tare dajin wani irin mugun sonta na K'ara shiganshi.... Jin shuru yasa ta bud'e ido a hankali idonta ya sauka cikin kwayar idonshi da yake kallon nata idon..... Dukansu wani irin yanayi mai wuyan misaltuwa suka shiga....... Karan wayar Yarima yasa ya saketa ta tashi da sauri daka jikin nashi ta koma ta zauna dakyau..... Daukan wayan yayi ya duba, ganin mai kiran yasa bai d'auka ba, zinatu ce......
Bariki kam gaba d'aya ta birkice, dan dan tabata dinnan da Yarima yayi har tana jin zuban ruwa a cikin pant dinta, lallai ya kamata Yarima ya rage zuwa, ko kuma ya daina tabata.... Domin Indai hakan zaici gaba da faruwa zata sha wuya, ido ta lumshe tasan ba komai yake sata yawan sha'awa ba sai maganin da take sha, wacce y'ar Sokoto take bata.....
Yarima ne ya Katse Mata tunani da fad'in, my princess zan gudu, bata sim yayi guda d'aya tare da cewa ta cire nata, baya son ta kara amfani dashi.....
Amsa tayi, tace toh dama tun tuni take da burin canza layi, amma tana tsoran Kar Yarima yace Mai yasa, yanzu tunda ya kawo mata, hankali kwance, sannan ya bata check na 3mil yace a K'ara gyaran jiki domin naga suna gyaramin ke dakyau......
Tace Yarima kafa ban kud'i cikin kwanakin nan, kaban a kalla wajan 7mil kace in siya kayan akwati, kuma gashi kace May be gidanku su Kawo nasu gobe ko jibi, kai kamin gashi gidanku zasu kawo, ga kud'i kuma kana karamin, gskya abun yayi yawa, ka barshi.....
Bata fuska yayi tare da fad'in in kin ciro kud'in ki zubar a bola tare da ajiye mata check din a jiki.....
Ganin yanda ya bata fuska, yasa tace Yarima kayi hakuri, wlh ba haka bane, naga hidimar tayi yawa ne Sosai, Kaga y......
Yace enough, komai na miki, kin can Canta inyi miki shi, and karki manta am your husband to be, waya kamata inyi ma Abu Inba keba?? In my life ban taba kyauta ko wani abuba a nuna ba'a soba sai ke..
Da sauri tace kayi hakuri plz na tuba, ngd Allah ya saka da alkhairi....
Jin ta fad'i haka yasa yaji dad'i..... Ba komai yasa Yarima ya bata wannan kud'in ba, sai sanin da yayi ba masu hali bane su, and y'an uwanshi zasu Kawo akwati, ance ana bada kud'i, sai yasa ya bata wannan kud'in dan iyayenta su bada tukwici... Ajiyan zuciya yayi tare da fad'in zan tafi sai munyi waya,
Tace OK
Yace kin dai ki zuwa kiga gidanki koh?
Tace Yarima saurin Mai kakeyi?? Ka Bari har a kaini mana
Murmushi yayi domin kin amincewanta yasa ya kara yarda damai tarbiya da kuma kamun kai zai aura, sabanin matan yanzu da suka lalace suke ganin haka shine wayewa, tab kunji Yarima shi'a dole zai aura ustaziya?
Sallama ya Mata sannan ya wuce......
Bariki gida ta shiga jiki a sanyaye lallai Yarima yana matukar sonta da yawa, hawaye ne ya gangaro daka idonta, tare da tausayin kanta yanda zai dauketa in yasan ko ita wacece......
Anata shirin biki musamman ta gefen ango, domin dai ita amarya rufa rufa take ma auran ba kowa bane ya sani, sai dai zargi da wasu sukeyi......
Ranan da za'a kawo akwati saida bariki da habib sukai hayan mata guda biyar, An kawo akwati guda ishirin da hud'u, dozen biyu kenan, kaya ne makil na Kece raini masu tsadan gaske..... Ganin yawan kayan yasa umman bariki taga 1mil yayi kad'an dan haka ta sami bariki dake boye cikin wani d'aki, tace ya kamata a K'ara kud'in nan Kinga uban kayan kuwa? Bariki kara 1mil tayi ya zama 2mil, nan aka basu kud'in tukwici, tare da abun ciye ciye da aka tanadar musu, bayan sun fito sis din Yarima Fatima tace Kai ance yarinyar talakawa ne amma har da bata 2mil, Aini ban d'auka zasu bada koda dubu d'ari ba, dariya sukayi sannan aka canza firan,
Bayan sun tafi bariki ta fito tana kallon kayan, itama Abun ya bata mamaki ganin kaya masu uban yawa da tsadan gaske, yanzu ga akwati ishirin da hudu, gashi kudin da Yarima ya bata itama ta siya guda sha biyu, duka talatin da shida.....
Ummanta ta bariki tace Kai gskya ki gode Allah y'ar nan, Yaron nan yana sonki Sosai, ji uban kaya sannan kayan d'aki yace baya bukatar komai, kai Kinji dad'i wlh
Bariki murmushi kawai tayi jiki a sanyaye, domin sai yanzu ta Fara jin tsoran abunda take kullawa na auren bariki, da tana ganin abun kaman wasa, amma tunda har taga akwati yau an kawo ta tabbatar Abun dagaske ne, d'aki tayi ta Fara rusgan kuka tare da fargaban abunda zai biyo baya..... Hmmm Allah ya kyauta dai zan iya cewa
Biki ya kan Kama amma amarya bata cikin nutsuwa kullum tana cikin fargaba, harta rame saboda damuwa, kullum bata da wani aiki sai kuka tare da K'ara tsanar rayuwar bariki........ Tana cikin wannan kukan Yarima ya kirata, da sauri ta seta kanta dan Kar ya gane sannan ta d'auka...
Gaidashi tayi
Amsawa yayi tare da fad'in ya naji muryanki haka??
Da sauri tace mura nakeyi Yarima
Yace toh fah, Allah ya sawake zan Aiko miki da magani.
Tace nasha tun dazu
Yace OK, toh ya shirye shirye?
Tace Alhamdullilah
Yace za'a Aiko miki da kayan da zaki saka a dinner sannan masu makeup za suzo suyi miki ranan, lil sis taban sa'ko in fad'a miki
Bariki tace ok Allah ya kaimu
Ya amsa da Ameen, sun d'an taba fira Kafin sukai sallama.....
Yana ajiye wayar gimbiya zinatu ta shigo, Tana fad'in yanzu Yarima saboda cin fuska a cikin gidan nawa kake waya da wacce zaka aura??? Kuka ta fashe dashi tare da fad'in haba Yarima Wlh kana cimin fuska da yawa maina maka haka da kake Yimin wannan abun??
Ganin yanda take kuka sai yaji ta bashi tausayi, rarrashinta ya farayi.....
Gimbiya zinatu ji take kaman ta tureshi Dan tsabagen kishi, Allah ya sani da badan gimbiya Amina tana kokarin hanata wani Abun ba da Wlh babu abunda zai hana tayi ma Yarima mugun tujara, amma Gimbiya Amina tace tayi hakuri ta Bari Ayi auran zata nema Mata mafita, yarda da gimbiya Amina da tayi shine yasa har take dan jurewa, amma ji take kaman zata mutu dan kishin Yarima take Sosai, bata son ganin ko wace mace kusa dashi......
Toh biki ya rage saura kwana biyu, inda a yau za'a gudanar da dinner, bariki da habib sunyi hayan kawaye Wanda sune kawayen amarya, cikin kawayen harda haulat da khairat, zuwan haulat gidan iyayen bariki yasa ta gane yanda bariki ta shirya auranta, ta gano tayi amfani da iyayen bariki, haulat ta kalli bariki tace gskya kinyi dabara, nima Ina tunanin haka zamma farhan, in samo iyayen bariki
Bariki ganin Haulat ta gano komai, yasa tace inko za kiji shawarata karki Fara yin aure da iyayen bariki, gwara ki koma Gida wajan danginki
Haulat tace Hmmm kedai kawai Ayi sha'ani,
Anyi ma amarya makeup na Kece raini, tayi mugun bala'in yin kyau, gaba d'aya makeup din da aka mata yasa ta canza, ta kara mugun kyau dama yaya balle an kara da wanka, an shiryata cikin wani tsaddan material Mai Kama da less anyi mishi dinkin doguwar riga, k'asan kuma anyishi da fad'i kaman weeding gown, an saka mata head maroon kayanta kuma golden, ba karamin kyau tayi ba, kawayenta kuma sunsa kaya red head golden, ba karamin kyau bariki tayi ba, da kawayenta, 7 dai dai aka turo motoci dan d'aukan amarya da kawayenta zuwa wajan dinner da za'ayi a cikin garin kaduna, duk y'an uwan ango suna kaduna, an d'auki amarya an nufi hall da ita, inda motarsu na zuwa na ango yazo, dan haka Yarima ya fito ya nufi motar da Zainab ke ciki, Yarima daya ganta ido ya kara bud'ewa ganin irin kyau data K'ara kaman ba ita ba, dama yasan tana da kyau gashi anyi mata makeup, lokaci d'aya kuma sai yaji yana kishin ta shiga Ayi ta kallonta, ya dad'e a motar yana nazari akan baiso ta shiga.....
Itama ta gefen amarya fargaba take, karta shiga taga Wanda ta sani, asiri ya tonu.....
Jin Yarima shuru yasa usman yazo yana buga glass din motar
Bud'ewa Yarima yayi tare da fad'in Usman gskya aje abama mutane hakuri, an fasa wannan dinner din, suci abinci kawai su wuce
Usman yace Yarima. Kasan Mai kake fad'a kuwa?? Plz Yarima ku fito mu shiga
Yarima yace kasan inna fad'a magana bana canzawa koh??
Usman shuru yayi yana nazari can yace dan Allah Yarima kayi hakuri ka duba girman Allah karka bamu kunya......
Yarima ya dakatar dashi da fad'in am telling you kayi abunda nace, wannan umarni ne.... Karan wayanshi yasa ya d'auka ganin lil sis
Yana d'auka tace Bros ku shigo mana kowa na jira, dan Allah kuyi sauri
Yace sis am sorry bazan zo ba, kuba mutane hakuri .....
Tace what? Tare da tashi ta fito waje dan taji dakyau, hango usman tayi da Yarima a tsaye da sauri ta nufesu, tana fad'in bros miye haka plz kuzo ku shiga....
Zaiyi magana tace plz koso kake ace akwai matsala ne??
Yace let people say what ever, nidai bazan shiga wannan wajan ba.
Hafsat tace bros akan wani dalili?
Yace ban son ayita Kalle min Mata, inada kishin iyali na
Hafsat hannu ta d'aura a Kai, alaman takaici, danta d'auka wani abune akayi mishi da yasa yace bazai shiga ba, motar da bariki take Hafsat ta nufa, sai gata ta fito
Ganin amarya a waje yasa Yarima ya fara yima Hafsat fad'an Mai yasa zata fito mishi da mata....
Hafsat tace bros nifa bani na fito da itaba
Kallon bariki yayi yace Oya muje in kaiki gida
Tace Yarima plz muje mu shiga, zaiyi magana tace dan Allah, karka sa mutane suyi zargin wani abu tana maganan tare da kokarin San zubar da kwalla.....
Ganin haka yasa yayi dan tsaki tare da fad'in karki Fara cewa zakiyi min kuka a nan, dan naga kina da Arhan hawaye, babu yanda Yarima ya iya dole ya shiga shida abokanan shi da amarya da kawayenta, cikin hall din yayi mugun tsaruwa, wajan zaman amarya da ango daban su biyu, y'an jarida da masu hoto sai d'auka suke, kowa yana fad'in amarya da ango sun dace dinner din ya had'a manyan mutane ciki harda Mai martaba, Yarima bai San zaizo ba saida Ya ganshi shida abokanan shi, harda Mai girma governor da wasu masu mukami a gwamnati sun halarta, anyi watsi da naira kaman baza'a mutu ba, an yanka cake daka nan akace amarya da ango suzo suyi rawa, nan suka fara rawa duk da bariki ba a sake take ba, dan tana jin tsoran ko akwai wanda ya Santa a wajan, nan aka fito ana watsa musu naira mum din Yarima tayi musu liki Sosai, a cikin masu likin idon bariki ya sauka akan Alh madu, dam gabanta ya fad'i, musamman irin murmushin da taga yana sakar mata, gaba d'aya jikinta taji ya saki babu kwari, Yarima kaman ya Lura da ita gashi kuma mutane sunyi yawa ko ince maza dan haka Yarima yaja hannun Zainab suka koma suka zauna, Anci ansha kowa ya watse, Yarima yakai bariki gida da jikinta yake a muce ganin Alh madu a wajan dinner, yanda ta gode Allah ta canza layi ma balle ya mata barazana, toh inya fad'a ma Yarima fah?? Nan taji gabanta ya fara fad'i
Bariki harta Washe gari tana cikin zullumi Kar asirinta ya tonu, haulat Dai da khairat sunyi Mata kara domin a gidan suka kwana, dasu kuma ake komai, bariki na kwance haulat tace wai lafiya kuwa naga kinyi shuru??
Bariki tace kalau nake
Haulat tace dan bani wayarki in bud'e hotspots banda data gashi Ina son tura Abu.
Password din wayar bariki ta cire sannan ta mi'ka ma haulat wayan.....
Toh rana dai bata Karya inji masu iya magana yau juma'a aka d'aura auren Zainab musa da angonta Yarima Aliyu, akan sadaki naira dubu hamsin inda dubban jama'a suka shaida......
Bariki tunda taji an d'aura take ta godema Allah, domin anyi auranta cikin nasara ba tare da Yarima yasan gaskiya ba, a hankali tace yau zan fad'a maka koni wacece Yarima Indai aka kawo ni gidanka,..... Karfe hud'u dai dai aka zo aka d'auki amarya inda aka tafi da ita Zaria a can zata zauna Kafin a dawo da ita kaduna, gefen Yarima Nada aka kaita inda aka gyarashi harta wanda suka kawo amarya bariki hayansu tayi, an karrama amarya da danginta wajan su abinci da duk abunda suke bukata, nan sukace zasu wuce tunda sun kawota, anyi musu shatara na arziki Kafin nan suka wuce......
Wajan karfe 9 Yarima ya shigo d'akin amarya ba tare da Aboki ko d'aya ba, dan yace kallon da suka mata wajan dinner ya isa haka, bariki na zaune akan gado Yarima ya shigo tunda ya shigo gabanta ke faman fad'i, inda take ya nufa tare da cire mata gyalen dake kanta yace Alhmdlh tsarki ya tabbata da Allah daya nuna min wannan ranan, janyota yayi jikinshi yayi mata wani irin runguma, har tana jiyo ajiyan zuciyarshi, lokaci d'aya ya saketa tare da d'agota ya sauketa k'asa yace my princess muje muyi alwala muyi ma Allah godiya..... Gabanta taji yana fad'i yaka mata Yarima yasan gaskiya Kafin wani abu ya shiga tsakaninsu, wayarshi dake ajiyu yayi kara d'auka yayi yaga number kaman Karya d'aga, sai kuma ya d'auka, ban son mai aka fad'a mishi ba naga ya kashe da sauri tare da fara danna wayar duk wannan abunda ake suna tsaye shida bariki suna kallon juna amma shi idonshi nakan wayar.... Lokaci d'aya hawaye ya fara zuba a idonshi tare da fad'in today is our wedding night, the day dat I have waiting for since d day dat I have meet u, but you destroy my life, you have cheated me..... Cikin tashin hankali tace Yarima maiya far.... Yace keep quiet tare da ri'ke kirjinshi alaman yana mishi ciwo yana kokarin yin magana ya fara tari Sosai lokaci d'aya yayi k'asa......
*TOH MASU MIN KORAFI IN K'ARA YAWAN RUBUTU YAU DAI NA K'ARA, AMMA KUDA KUGA WANI POSTING DIN SAI NAN DA KWANA UKU, BUT IN NAGA COMMENTS DINKU YAU YAYI YAWA MAY BE GOBE IN MUKU*
*not edited*
~MARYAM OBAM~



*PAGE 17*
Tari yake Sosai, bariki kuka ta Fara Tana fad'in Yarima Mai yake damunka?? Tare da tabashi tana son d'ago Shi ,hannunshi da yasa a baki yana tari ya cire ya fara kokarin tureta alaman tabar tabashi, amma jikinshi babu kwari ya kasa tureta din...... Wani irin tari yayi tare da yunkurin yin amai saiga jini nan..... Wani irin ihu ta saki mai ban tsoro tare da kiran nashiga uku Yarima maiya sameka??
Ganin jinin a bakinshi yana fita yasa ta fita da gudu, tana fita taga fadawa tace dan Allah kuzo Yarima zai mutu, tana maganan tana kuka da ihu, kuzo mu kaishi asibiti..... Da sauri suka shiga wasu kuma suka je fad'ama iyayenshi, koda fadawa suka shiga ganin Yarima sukayi a kwance yana wani irin nishi ga jini na zubar mai a baki, da sauri suka D'aukeshi suka fita dashi, suna cikin sashi a mota mum dinshi tazo, ganin halin da d'an nata yake ciki yasa ta Fara fad'in Innalillahi'wa inna ilaihirajiun, Yarima maiya sameka, lokaci d'aya kuma tasa kuka, shiga motar tayi da sauri suka nufi asibiti...... Bariki Kafin ta karaso har Sun wuce dan haka ta Fara cewa sauran fadawan muje ku kaini dan Allah inda suka je..... Ganin kanta ko dankwali babu yasa wasu kuyangi dake tsaye wajan suka karaso suna fad'in Allah ya taimaki gimbiya, ki koma ki saka mayafi sai a kaiki,.
Sai a sannan bariki tasan a halinda take da gudu tayi ciki, inda ta d'auko mayafinta tana kokarin fita wayar Yarima dake d'akin ya fara K'ara dole yasa ta koma ta d'auki wayar babu suna number ne ke kiranshi harya tsinke bata d'auka ba..... Fita tazo yi lokaci d'aya kuma ta tsaya cak domin tunawa da abunda ya faru da Yarima, wanda tunda aka kirashi ta rasa gane kanshi,har wannan abun ya sameshi, danna wayan tayi da nufin ta shiga taga Mai aka turo mishi, gani tayi akwai password, shuru tayi tana nazari Mai Yarima ya gani?? Kodai wani ya fad'a mishi koni wacece?? Gabanta taji ya fara fad'i tunawa da kalaman daya Fara Mata Kafin ya fad'i...... Wani irin kuka ta saki mai ban tausayi, tare da fad'in shikenan2 sunyi nasara Sun fad'ama Yarima koni wacece kuka take Sosai, lokaci d'aya kuma ta fita da gudu inda taga mota na jiranta shiga tayi domin aka kaita asibiti da yake fadawa sun San asibitin da suke zuwa nan aka nufa da ita dan suna da tabbacin can aka Kai Yarima, tana mota tana kuka......
Kafin kace Mai har labari ya bazu cikin masarauta, Yarima Aliyu bashi da lafiya rai a hannun Allah, har wasu na cewa jini ke fita a bakinshi hala amaryanshi ba budurwa bace, wasu kuma suce kodai wani abu tayi mishi?? Haka dai ake ta jita jita, koda kuyangin gimbiya zinatu suka fad'a mata cikin tashin hankali itama tayi asibitin.....
Yarima Aliyu ko Kafin akai asibiti, ya daina koda motsi, ana zuwa akai emergency dashi, likitoci sukai kanshi aka fara dubashi, tare da bashi taimakon gaggawa....
mum ta kasa zama sai kuka takeyi ga fadawa a wajan da yawa, kowa ya shiga cikin damuwa.
basu dad'e ba saiga bariki ta karaso Tana kuka, tare da fad'in mum Ina Yarima?? Ina Yarima?? Mum din ri'keta tayi tare da rungumeta, ta kasa ko magana sai shafa ma bariki baya takeyi alaman tayi shuru......
Suna cikin haka saiga Zinatu tazo cikin Tashin hankali ganin Bariki wajan mum ko ba'a fad'a mata ba tasan itace amaryan da Yarima ya auro, da sauri ta nufi bariki ta fincikota tare da watsa mata Mari Tana fad'in mai kika ma Yarima?? Mai kika mishi?? Kuka ta saki Zinatu tare daci gaba da fad'in Wlh Idan wani abu ya sameshi saina kasheki W.......
Mum sai yanzu ta iya magana, tace Zinatu kina da hankali kuwa?? A gabana kike wannan abun?? Shi Yarima dinne yace miki ita ta mishi wani abu??
Cikin kuka tace mum, daka ita sai shi, Nasan wani abu tayi mishi......
Mum tace ya isa haka, plz ki barni inji da abunda yake damuna ban son rigima....
Bariki kam tunda zinatu ta mareta take ri'ke da wajan Tana kuka, ko bata tambaya ba tasan itace Uwar gidan Yarima Aliyu...... Bariki tasan lallai ko ba'a fad'a ba dole kowa yayi zarginta, abunda Zinatu ta fad'a gaskiya ne..... Kuka tayi k'asa tanayi tare da fargaban Kar wani abu ya sami Yarima dan bazata iya jura ba.....
Kowa na cikin Tashin hankali, ga doctors har yanzu basu fito ba...... Suna nan zaune saiga Mai martaba shida Hafsat Sun zo cikin Tashin hankali.
Mum ganin Mai martaba yasa ta tashi ta nufeshi tana kuka, tare da fad'in ina jin tsoro Kar Yarima ya mutu Aman jini yakeyi Ina tsor.....
Toshe mata baki Mai martaba yayi, tare da fad'in ki daina fad'in haka, Hafsat itama kuka ta Fara cikin Tashin hankali.....
Duka kowa shuru yayi babu Mai rarrashin wani, suna nan tsaye d'aya daka cikin doctors din ya fito, suna ganinshi suka nufeshi tare da fad'in Dr ya ake ciki, ganin Mai martaba yasa yace ranka ya dad'e wacece Zainab a cikin nan??
Da sauri mum tace ga tanan tare da nuna bariki, yace ok tare da kallon Bariki yace taso muje......
Da sauri ta tashi tabi Dr, kowa da abunda yake sakawa, Zinatu ta Fara fad'in mum kin gani ko kin gani wlh itace tayi mishi wani abu.....
Kowa shuru yayi ya kasa cewa koda uffam.... Suna jira suga ikon Allah......
Koda Bariki suka shiga oxygen din da akasa ma Yarima yana k'asa alaman yana son d'aukewa, kuma yana saka zero shikenan mutum ya mutu, da sauri Dr yace plz ki mishi magana sunanki yake ta kira pls say something karku rasa shi.......
Da sauri ta ri'ke Mai hannu tana kuka tare da fad'in Yarima karka bari wani abu ya sameka..... You know that I can't live without you, plz Yarima ka tashi kasan ina Sonka kaine rayuwa na, wlh bazan iya juran inga wani abu ya faru dakai ba......
Lokaci d'aya oxygen din ya fara k'aruwa alaman numfashin shi yana son dai daituwa.... Likitocin ganin haka yasa suka fara kallon juna alaman jin dad'i an fara nasara..... Bariki kuka take Sosai tana fad'in karya mutu ya barta....
Idonshi dake rufe ya fara zubar da hawaye...... Lokaci d'aya numfashin shi ya dai daita......
D'aya daka cikin doctors din yace ma Bariki yauwa komai yayi dai dai mu jira muga kuma yanda Abun zai kasance amma muna bukatar ki zauna har muga farkawanshi, muna nufin Kar kibar asibitin nan har sai munga ya farka ....
Cikin kuka tace babu inda zani Ina nan tare dashi
Dr din fita sukayi, inda suna fita Mai martaba yace ya akayi?? Mai yake faruwa dashi??
D'aya daka cikin Dr din yace ya samu bugawan zuciya ne, ina tunanin yaga abunda ya bashi tsoro ko mamaki, kuma daka duka alamu abunda ya gani ko yaji yana d'aya daka cikin abu masu muhimmanci a rayuwanshi, hakan yana faruwa wasu ma rasa ransu suke, a gskya masu rasa ransu ma sunfi yawa amma shi yayi Sa'a ko ince mun samu mun ceco rayuwanshi tare da taimakon Allah da kuma wannan baiwar Allah dake ciki, magananta da yaji shine yasa zuciyarshi ta Fara harbawa, inda badan ita ba toh gaskiya dasai dai kuji mummunan labari , dan haka dole ta zauna dashi muga yanda Allah zaiyi.....
Mai martaba godiya yayi ma Dr din tare da fad'in zamu iya ganinshi?? Sannan kana ganin zai tashi babu wani matsala??
Dr yace zaku iya ganinshi amma plz Kar kuyi magana, sannan zai tashi insha Allah Indai yarinyar na kusa dashi kuma yana jin magananta a kusa dashi.....
Mai martaba yayi ma Dr godiya, sannan suka shiga d'akin, ganin Bariki sukayi a zaune kusa dashi hannunta na ri'ke da nashi tana kuka.....
Kowa tsayawa yayi yana mamakin irin wannan Abun musamman mum damai martaba, ita dama zinatu bata shigo ba domin maganan Dr yasa taji wani iri tare da takaici..... Mum ce ta k'arasa kusa da inda Yarima din yake tare da kamo d'ayan hannunshi, fuskanshi tayi fayau ga hawaye a idonshi na zuba..... Mum itama hawayen ne yake zuba daka idonta, kowa dake wajan ya tausaya mishi...... Mai martaba ganin mum nason kuka mai sauti yasa ya kamota sukai waje, Hafsat da Bariki suka zauna a d'akin
Zinatu ce ta shigo d'akin ganin zinatu yasa bariki tashi tabar d'akin domin irin kallon da taga zinatu din nayi mata, kuma ko babu komai ya kamata ta dan bata waje ta gana da mijinta duk da bai farka ba.....
Fita Bariki tayi tana fita, Mai martaba yace Zainab ya kika fito?? Ko wani abu kike bukata??
Tace a'a Abba cikin jin kunya, na d'an basu waje ne.....
Mai martaba ya gane ta fito ne saboda Zinatu.......
Mum tace Zainab bai kamata ki fito ba ai, maza ki koma Kinji.....
Tace toh mum jiki a sanyaye Bariki ta shiga, abubuwa sun mata yawa, na farko Tana zullumin Mai aka fad'ama Yarima a waya, sannan maiya gani, duk wannan Abun suke ta faman Mata yawo a Kai..... Koda Bariki ta shiga zintau fita tayi
Bariki zama tayi kusa da Yarima tare da kurama fuskanshi ido, har yanzu yana hawaye, gaba d'aya zuciyarta ta tsinke, shidai har yanzu bai farka ba, toh wannan hawayen fah????..... Kiran Hafsat akayi a waya ta tashi tabar d'akin Tana fita kaman ance Yarima ya bud'e ido , a hankali ya bud'e idonshi ya sauka akan na Zainab wacce itama shi take kallo tana murna tare dason yin magana murna ya hanata......
Murmushi ya sakar mata, tare da kamo hannunta ya ri'ke tare da matse su.....
A hankali tace Yarima Ina Sonka I can't live without you, tana maganan tana kuka, tace I was scare with your condition I......
Hannunshi yasa ya rufe Mata baki yana kokarin yin magana ya tsaya alaman ya tuna da wani abu....... Lokaci d'aya ya sake mata hannu tare da fad'in leave from hare I hate to see your face........
Cikin kuka tace Yarima zainab din'ka ce Yarima nice maina......
Ya daka mata tsawa tare da ri'ke kirjinshi yace I said leave from here ....... Su mum dake waje Suka shigo harda su zinatu, ganin Bariki na kuka Yarima shima hawaye ne ke zuba a idonshi gashi ya ri'ke kirjinshi...... Kallon iyayenshi yayi tare da fad'in mum tell her to leave from here....... Kowa kallonshi yake cikin mamaki da sauri Hafsat ta fita kiran doctor...... Mai martaba yace Aliyu matarka ce kake koranta?? Maita maka??...... Yace Abba plz tell her to leave I don't want to see her face.... Why am I still alive.... Dai dai lokacin doctor yazo yace kowa yabar d'akin........ Bariki da sauri ta fita Tana kuka lallai ta tabbatar an fad'ama Yarima ko ita wacece kuka take Sosai tare da barin asibitin ba tare da sanin kowa ba......
*Hmmmm Ashe masoya novel's din bariki suna da yawa?? Ban taba sani ba sai jiya??? lallai kuna son posting naga ruwan comments harda Wanda ban San suna karantawa ba, jiya Sun zuba comments, tunda hakane nima daka yanzu zan daina posting kullum Indai bakwa zuba comments kunga 50 50 kenan kuyi rowan comments inyi rowan posting??? Ina sonku masoya novel's dina*
~MARYAM OBAM~



*PAGE 18*
Bariki kuka take Sosai tana tafiya a kafa, tafiya take bata san inda take wurga kafarta ba, ba komai bane a ranta sai yanda Yarima yake nuna tsanan ganinta, ta tabbata abunda take boyewa take burin in sunyi aure ta fad'ama Mai, wanda take burin Sanar Mai an samu wani ya fad'a Mai..... Zama tayi a k'asa gefen titi Tana kuka cikin Tashin hankali, bata taba tunanin abubuwa zasu cabe Mata haka ba, tunda take shirya wannan abun bata taba tunanin Idan ta fad'ama Yarima gaskiya dole iyayenshi Suma su san gaskiya tunda tayi amfani da iyayen bariki, gaba d'aya dana sani takeyi Wanda hausawa ke cewa k'eya ce, da yake dare ne Sosai babu mutane sai motoci dake Faman wucewa, suma motocin jifa jifa suke wucewa ba Sosai ba......
Bayan iyayen Yarima sun fito dasu zinatu, kowa da abunda yake sa'kawa cikin ranshi game da wannan al'amarin.....
Zinatu kam dad'i ya cikata Sosai, tare da aiyana ma ranta lallai Yarima ba virgin ya sami matarshi ba, tunda har Ya nuna baya son ganinta, yake nuna mata tsana k'arara, ji take kaman tai ihu dan murna, tare da fad'in da Gimbiya Amina batai bacci ba dana kirata na bata wannan kyakyawan labarin, amma Allah ya kaimu gobe......
Sunyi wajan 20mnt a wajan, sannan mai martaba yace Ina Zainab??
Nan mum ta kalli Hafsat tace ina tayi??
Hafsat tace nima ban sani ba mum,
Nan mum ta tambayi fadawan dake wajan ko sunga inda tayi??
D'aya daka cikin fadawan yace ta fita, daka ganin alama kuma waje tayi dan yanda ta fita da sauri tana kuka......
Nan mum tayi hanyar waje fadawa suka bita, itama hafsat bayan mum tabi....
Fita sukayi suna nemanta amma basu ganta ba, fadawa sukayi gaba suna dubata, wani daka cikin fadawan ya dawo da sauri yana fad'ama mum ga tacan a zaune a k'asa Tana kuka
Da sauri mum suka nufa inda take, tana nan zaune a k'asa Tana kuka mai cin rai..... Mum d'agota tayi tare da fad'in Zainab lafiyanki kuwa zaki fito bakin titi ki zauna kina kuka??
Zainab bata ce mata komai ba, domin har yanzu kukan take.....
Mum tace maza kuzo a kaiku gida, kuje ku huta tare da kamo hannunta sukai asibitin..... Suna k'okarin shiga sai ga Mai martaba shima yana fitowa, ganinshi yasa suka tsaya harya karaso inda suke.....
Mum tace Dr din ya fito ne??
Yace a'a nazo inga ko kun ganta Ashe ga tanan, suzo a kaisu gida dare yayi......
Da sauri bariki tace ni zan zauna dashi....
Mum tace Zainab kiyi hakuri kuje gida gobe da safe sai kuzo Kinji??
Kai ta d'aga amma badan taso ba, sai dai dan bazata iya musu da mum ba, haka suka tafi gida ita da Hafsat da Gimbiya zinatu damai martaba domin mum ce zata kwana dashi..... Duk da sun so suji maike faruwa in Dr Ya fito amma mum tace suje babu wani matsala tunda aiya farka......
Koda kowa ya fita, Yarima Aliyu ido ya lumshe tare da kwanciya yana Mai jin zafin abunda ya gani.... Dr ne ya mishi y'an dube dube sannan yace haba Aliyu, kana son sama kanka damuwa plz ka kwantar da hankalinka an fad'amin you r a doctor so nasan Idan na fad'a maka ka sami bugawan zuciya zaka San abunda ya kamata kayi wajan cire ma ranka abunda ya razana ka...... Yarima baiko Kalli Dr ba balle ya kulashi sarautar ta motsa..... Dr yaci gaba da fad'in Yarima ka gode ma Allah, amma kana son Zainab dinnan da yawa, Allah y.......
Yarima Aliyu ya Katse Dr da fad'in ina son a sallameni......
Dr yace sallama?
Yarima Aliyu yace yes yanzu
Dr yace a'ah ka Bari ka K'ara samun sauki, domin har yanzu baka dawo Normal ba.....
Yarima Aliyu tashi yayi dakyar ya zauna tare da fad'in Dr i am a Dr too I knw how to handle myself, and kace na samu buguwar zuciya?? So zamana a nan baida amfani dole inje gida a nan zan samu nutsuwa...
Dr shuru yayi yana nazari, maganan Yarima Aliyu gaskiya ne, Idan mutum ya sami buguwar zuciya irin haka, iz either an fad'a Mai wani abu ko ya gani, so inya duba yaga abun iz not true a hankali zai Fara samun lfya domin ya samu nutsuwa.......
Yarima Aliyu tashi yayi jiki babu kwari, kaman zai fad'i yayi sauri ya ri'ke hannun Dr din.......
Doctor din yace kayi a hankali, ka zauna let me call your parent su ri'ke ka, taimaka ma Yarima yayi ya zauna yana cije baki alaman yana jin jiki.....
Yarima Aliyu ba komai bane yasa yace a sallameshi sai dan yayi magana da Zainab bariki, akan yaudaran da ta mishi and baya jin zaiyi accepting d'inta a matsayin mata, matar data gama watsewa a duniya ko wani namiji ya santa t.........
Bud'e kofar da akayi yasa ya d'aga ido da yake zubar da hawaye, ganin mum da fadawa yayi, nan Dr yace su taimaka sukai Yarima Mota, kamashi sukayi suka fita, mum kallon d'an nata take cikin tausayawa.. Bayan an fitar da Yarima mum ta kalli Dr tace nidai banso ka yarda ya koma Gida ba, ina jin tsoran Kar wani abu ya sake samunshi.......
Dr yace karki damu, a gidan zaifi samun nutsuwa, Idan mutum yayi irin haka kika ga yace yana son tafiya akwai abunda yake son tabbatar wane, wanda shine yasa ya fad'a irin wannan matsalan, sannan komai ya faru call me.....
Mum godiya tama Dr sannan ta fita.
Bariki bayan sun karasa gida gefenta da aka kaita nan ta shiga, bedroom tayi Kai tsaye, ta zauna a k'asa tana kuka kaman ranta zai fita, wayan Yarima dake hannunta tayi k'ara alaman an turo Mai sa'ko, ajiye wayar tayi a gefe...... Tabbas tasan wannan ba komai bane, tunda tun Farko ta zabi sabama Allah, dole taga bacin rai, dama duk Wanda ya kauce hanyar Allah kuma yasan yabar hanya Mai Kyau dole ya had'u da ukuba tun a duniya, ita Allah na Sonta da rahma tunda harta gane ta kuma yi nadama, sai dai irin hanyar da tasa kanta koda kayi nadama sai an samu masu goranta maka, in bakayi wasa ba harta jikokinka sai anyi musu gori da fad'in ai kakarsu tsohuwar karuwa ce da, ko kuma ayi ma y'ay'anki ace ai uwarsu karuwa ce, in tayi aure tama miji laifi yace ta biyo halin uwa, tasha a nono, kai Wlh rayuwan bariki batayi ba ko kad'an... Kuka ta K'ara saki cikin jin zafin bata rayuwarta da tayi duk da kaddara ne ya sameta..... Wacce bata san yanda akayi Abun ya sameta ba.....
Gimbiya zinatu kam tana shiga gefenta wa'ka ta kunna Tana ta rawa cikin jin dad'i, tare da fad'in first night ya zama ranan ba'kin ciki dariya ta saki cikin jin dad'i...
Koda su Yarima Aliyu suka Iso gida, cewa yayi zai nufi gefen Zainab, duk da mum taso ya bita amma ya'ki, mum bata sa komai a ranta ba, ita a tunaninta da taji yace zashi wajan Zainab, sai tayi tunani ko abunda yayi mata d'azu yake son bata hakuri, sannan a mota ta fad'a mishi abunda Dr sukace inda badan Zainab dinba toh da zai iya mutuwa..... Fadawa na k'okarin rikeshi yace Nop ku barni, zan iya, tafiya yake dakyar harya shiga cikin falon bai ganta ba
Mum ganin ya shiga yasa itama ta wuce
Yarima bedroom dinshi yayi inda tun Kafin ya k'arasa yake jin sautin kukanta, bud'e kofar bedroom din yayi ya ganta a k'asa tana rasgan kuka a hankali cikin murya irin na marasa lafiya wanda yake jin jiki yace wannan ba kuka kike yiba..
Jin muryan Yarima yasa tayi sauri ta tashi, tare da kallonshi tana mamakin ya akayi ya dawo......
Yarima Aliyu idonshi na kanta yana mata wani irin kallo Mai Kama da I hate you, yace Zainab oh sorry Bariki......
Jin ya kirata da Bariki yasa zuciyarta ta tsinke gaba d'aya, abunda take zargi shine ya faru an fad'ama Yarima.......
Katse mata tunani yayi da fad'in how dare you....... Shuru yayi cikin kunan rai hawaye na zuba a idonshi...... Yace kin cuce ni, kin yaudareni, and ina asibiti kin kuma bina har ana fad'in da badan keba dana mutu, Mai yasa kika zo?? Mai yasa ban mutu ba, I wish da mutuwa nayi da Nasan zanga irin wannan ranan, you play with my feelings you all lies to me, you cheat me, kin maida iyayena yara kinyi wasa dasu......
Da sauri tace dan Allah Yarima ka saur......
Yace keep quiet, don't try to say anything, let me speak you cheater......
Bariki kuka take Sosai
Yarima Aliyu yaci gaba da fad'in do you think I will trust you again?? You break my trust, dan shuru yayi sannan yaci gaba da fad'in Zainab I love you from d bottom of my hrt, why are hidden your secret with me??.......
Tana kokarin yin magana yace I said don't try to speak keep your mouth shut, I don't want to listen to ol your lies again,
Bariki kuka take na farko ga Tashin hankalin halinda mijinta ke ciki, gashi ya hanata yin magana
Yarima Aliyu yace but you don't cheat me, you cheat your self, Zainab I was shock to see your pictures with different men's, ido ya rufe yana hawaye domin takaicin abunda yake fad'a ji yake kaman zuciyarshi zata buga, I never expect dat from you, Zainab mai yasa kika bata rayuwanki nawa kike samu? mai kike ji,? mai yasa kika yaudareni,? mai yasa kika boyemin gaskiyan ko ke wacece,? Zainab how old are you kwata kwata da zaki bata rayuwanki just for money?? Mai kika samu Mai kika tara ??
Da sauri tace Yarima plz ka saurareni dan Allah tana maganan tana kuka....
Yace I don't want to listen to ol your lies, komai naki karya ne your love your affection is ol a lies......
Shuru yayi hawaye na zuba daka idonshi Abun gwanin tausayi? sanna yaci gaba da fad'in you break d trust dat I have for you, Zainab kwata kwata shekaranki nawa?? Har kin San ki samu iyayen Karya, ki aurar da kanki da kanki, you fool us, mai kika d'auki aure??? Do you think dat marriage is a joke?? Zainab I truly love but I won't accept you d way you are.....
Ihun data saki Tana bashi hakuri akan ya tsaya ya saurareta tayi mishi bayani akan duk wanda ya fad'a yayi ne danya had'asu......
Yace Yimin shuru, Habib zai miki karya ne?
Cikin razana tace habib.....
Yarima yace eh habib call me and tell me everything ol your plan...... Zainab I feel so sad when I hear d truth about you..... Nayi takaici you never love me habib told me you marry me only for money...... Shuru yayi yana hawaye can yaci gaba da fad'in kin aureni dan ki sami kud'i bakya sona Wanda kike so yayi rejecting d'inki sai yasa kika aureni danki nuna mishi kina da Wanda suka fishi..... After dat he send me your pictures matsawa yayi kusa da ita ya d'auki wayarshi ya fara dannawa nuna mata yayi yace Waye wannan hotunan tane da Alh madu, gashi tsirara ya ri'keta, sai kuma wanda tayi da Hon salis...... Yarima yace have you seen it?? Ok shima wannan it ol a lies ko shima wannan so ake a had'amu?? Jefa wayan yayi a K'asa ta fashe...... Idonshi ya rine yayi ja, ga zuciyarshi dake faman tafarfasa kirjinshi na mishi zafi........ Yace you betrayed me, who did I harm to deserve ol this punishment...... Ban kasance mazina ciba, ban taba sanadin lalacewan wata ba, why matar dana aura kowa ya Santa.......
Bariki kuka take Sosai tare da tunanin irin cin amanan da habib yayi mata, lallai don't trust anyone in life,...... Bakinta na rawa ta Fara fad'in Yarima Nasan ni Mai laifi ce a gareka dan Allah kaban dama just once I need to exp......
Yace I won't give you any chance to tell me another lies, karyan da kikayi min baya ya isa...... My heart only beat for you..... Tun a mafarki na Fara sonki, but you never love me, you hurt me alot...... You marry me for money not for love...... Ok even I, I won't accept you as my wife..... You will live here as my servant har karshen rayuwarki zaki zama mai min bauta, and I will make sure to hurt you d same as you did to me, nd I promise to hurt you, keda duk Wanda kukai wannan abun sai Nayi punishing naku, I will make sure to make you regret knowing me in ur lyf........
Da sauri ta matsa kusa dashi tare da kokarin tabashi ya daka mata tsawa tare da fad'in don't you dare try to touch me.... Karki k'ara yunkurin tabani da wannan kazamin jikin naki......
K'asa tayi da giwowinta Tana kuka tare da fad'in Yarima call me wit wat ever name you like, I deserve it, Yarima just once plz ka saurareni plz.....
Yarima yace do you think zan kara sauraran wannan karyan naki?? Harda cemin kin sauke Al'qur'ani, Wat a funny, kin dai yi hadda a bin maza.....
Tace Yarima iz true na sauke al'qur'ani tun I was 11yrs plz Yarima allow me to speak......... Hmmmmmm bari dai muga ko zai bata daman fad'a mishi ko ita wacece ?
*Plz kuyi manage I have a headache na gaji da typing din, comments dinku yasa nace bari in takura kaina inyi muku posting, ina matukar yinku Sosai da Sosai*
~MARYAM OBAM~


*PAGE 19*
D'an shuru yayi kanshi na k'asa yana zubar da hawaye, yana son Zainab yana mata tsantsar so, but da yasan haka take daya ro'ki mutuwa, daya ro'ki Allah ya d'auki rayuwarshi da yasan zaiga irin wannan mummunan ranan........
Jin yayi shuru yasa ta Fara fad'in Yarim......
Yace I said keep quiet, I don't want to listen to you.... Zainab even at once kin taba tunanin irin yanda zanji in nasan gaskiya a kanki???...... Kin taba tunanin ya iyayena zasu d'auki abun in suka San koke wacece??..... Zainab mai kika d'auki rayuwa?? Mai yasa kikai wasa da feelings dina?? You don't love me...... Wani hawaye mai zafi ya zubo Mai sannan yaci gaba da fad'in, tunda bakya sona Mai yasa kika aureni, Zainab inda kin fad'amin bakya sona tun Farko kud'i kike so, I will give you d money dat you want..... Basai kin yaudareni ba kin aure ni b.....
Kafin ya k'arasa abunda yake son fad'a ta Fara matsawa kusa dashi, daka mata tsawa yayi tare da fad'in karki zo inda nake..... Tari ya farayi Sosai......
Da sauri ta nufeshi tare da rik'eshi Tana buga mishi baya a hankali, tana kuka ta Fara fad'in Yarima I knw dat I have lies to you, na boye maka koni wacece Nasan wannan gaskiya ne, but Yarima abunda aka fad'a maka Akan son da nake maka karya ne..... Yarima you are my life, Yarima I love you, I can't live without you...... Tsagaitawa yayi da tarin da yakeyi tare da kallon idonta itama idonta nakan nashi...... Taci gaba da fad'in Yarima sonda nake maka shine yasa na boye maka koni wacece, saboda ban son in rasaka....... Yarima in zaka tuna nasha kuka ina son fad'ama wani abu, sometimes wani abu ya shigo koka katseni.... Yarima I try to tell you who I am but whenever I try to tell you wani abu saiya shigo, and habib yana fad'amin Indai na gaya maka gaskiyan who I am you will hate me and leave me..... Yarima sonda nake maka bazan iya juran rashinka ba..... Yarima Wlh Ina Sonka Ina Sonka, how I wish in bud'e maka zuciyata Kaga irin sonda nake maka..... Yarima plz ka amshi kaddara ta karka juya min baya kaman yanda mahaifina yayi min, Wlh Yarima Idan ka juya min baya zan iya mutuwa...... Jin haka Yarima Aliyu yayi sauri ya rungumeta dukansu kuka Yarima hawaye ita kuma kuka mai sauti....... Bariki tana rungume a jikin Yarima Aliyu ta Fara fad'in Yarima........
Ni d'aya mahaifina ya haifa......
Nice y'ar mahaifina ta Farko kuma tun daka kaina bai k'ara samun haiyuwa ba, tun ina y'ar shekara Goma mum dina ta rasu, lokacin na shiga gararin rayuwa, gaba d'aya na tsani komai dake duniya .
Mahaifina babban malami ne a k'asa nan wanda kowa ya sanshi bama kasar nan ba harta kasashen duniya, mahaifina malami ne mai sani Sosai sannan d'an kasuwa ne wanda yayi fice Sunan mahaifina sheik musa monguno...... Dan maiduguri ne, sunyi auren soyayya da mahaifiyata tun a k'asar misra suka had'u lokacin sunje karatu mum dita y'ar Sokoto ce soyayya Mai karfi ya shiga har takai da aure..... Tunda mum dina ta rasu mahaifina bai kara tunanin yin aure ba, shi yaci gaba da kula dani har Nayi hadda na sauke al'qur'ani da sauran littafai lokacin ina shekara shad'aya a duniya..... Ina karatun boko komai nawa dad dina yake min tare da taimakon Mai aikin mum dina wata tsohuwa Wanda na dauketa kaman kakata nake kiranta da Ummaa,
Dangin mahaifina sun dameshi akan ya k'ara aure, domin zamanshi haka bamai yihuwa bane, ya nuna musu babu tsarin k'ara aure a ranshi, domin bai yarda yayi aure ya bada ri'kona wajan matar daya aura ba, domin yana matukar jin tausayi na, ya nuna musu Ummaa na kula dani baya bukatar ya auri wata mata, koda zaiyi aure yace saiya aurar dani shine zai samu nutsuwa......
Haka dai suka barshi Ina shekara shabiyar a duniya Ummaa ta rasu ??, naji mutuwar Ummaa Ina tunanin Nafi jin Nata akan sanda naji mutuwar mum dina, har saida na kwanta a asibiti, a lokacin na k'ara yarda ba mutuwa akema kuka ba, shakuwa ce da Sabo akema kuka, haka na k'ara fad'awa cikin gararin rayuwa tare da kadaici, mahaifina yana matukar jin tausayina Sosai.....
Bayan rasuwan Ummaa family din dad dina suka k'ara taso mishi da maganan aure, wannan karan basu mishi da wasa ba, kusan duka y'an uwanshi suka had'u harda mamanshi wato kakata tunda mahaifinshi ya dad'e da rasuwa, dole yasa ya amince ganin yanda suka nuna fishinsu akan ya k'ara aure........ Wata y'ar uwarshi aka aura Mai Mai suna Falmata wacce mijinta ya rasu ya bar mata yara biyu Mata, ganin abbana yana da kud'i yasa akace zai iya ri'ke yaran dan haka tare aka kawota da yaran, gidan dad dina dake Abuja.
Falmata Tana nuna min so Sosai, bata Bari koda kud'a ya tabani, mahaifina yana jin dad'in hakan, sannan komai zai mana tare yake mana da Kananan yaranta, haka dai rayuwa taci gaba dad dina wata rana ya d'aukeni mukaje bank aka bud'emin account, gaba d'aya kud'in da mum dina ta bari aka samin kud'i masu uban yawa a lokacin kusan 20mil banda kadarori data bari tare da gidan gona Wanda kullum cikin samun kud'i ake, komai na mum dina dad dina yace cikin account dina za'a dinga sawa.... Na nuna ma dad dina daya Bari a wajanshi amma yace a'a in ri'ke hakki nane........ Mahaifina yana nuna min tsantsar so Sosai har baya iya boye son da yakemin gaban kowa kullum magananshi ni tare da fad'in irin tausayi na da yake ji......... Dad dina yana yawan zuwa gari gari wa'azi da kasashe, ganin matarshi Tana kula dani yasa ya yarda yake tafiya yabar mata ni....
Lokacin da nake shekara Goma sha bakwai komai nawa Ya fito, kyau diri Kirjina komai nawa dai tubarkallah, Falmata duk kawayenta kana kallonsu zaka gane y'an duniya ne, sannan basa zuwa gidan sai dad dina baya k'asar........
Wata rana Ina d'aki na fito daka wanka daka ni sai towel, ina zaune ina shafa mai saiga Falmata ta shigo, da sauri na tashi Ina kokarin in d'auko abu in rufe jikina A Kai rashin Sa'a towel din ya fad'i, gaba d'aya idon Falmata na kaina, da sauri na shige towel na rufe Ina kuka domin naji kunya Sosai ranan
Ranan dai a d'aki na wuni banko le'ko ba
Washegari na fito da yake lokacin ina zana waec kuma ranan shine paper na karshe na fito zani skul cikin jin kunya, saiga Falmata tazo ta ri'ke min hannu tare da fad'in haba zainab, mai yasa tun jiya kika k'i fitowa nifa mamanki ce kiyi hakuri dana shigo ba tare dayi miki nocking ba, tunda ta ri'ke min hannu sai wani murmurzawa take kaman filo ta ri'ke, ganin zanyi lati gashi tana ta wani shafa min hannu yasa nace ummi zanyi lati.
Murmushi tayi tare da fad'in muje in rakaki mota, har mota mukaje ta sani tare da fad'ama driver ya kaini a hankali
Tun daka ranan Indai Falmata zata min Abu saita tabani ban taba zarginta da wani abu ba, duk tunani na tanayi ne saboda in saki jiki da ita, domin tunda Abun nan ya faru nake jin kunyanta Sosai, haka zatai taja na da fira ni gashi ban cika son magana ba......
Wata rana dad dina yaje saudiya umra ,ina d'aki ina karanta wani hadith daka ni sai kayan bacci a jiki na, kawai Falmata ta fad'o d'akin dama kwana biyu ban cika bari muna had'uwa ba inma mun had'u nesa nesa nake da ita domin ban son yanda take yawan tabani..... Ganin ta shigo d'akin yasa na tashi tsaye domin taban tsoro irin kallon da take min..... Nufoni tayi tana y'ar murmushi tare da fad'in baki bacci ba har yanzu?
D'an murmushi nayi tare da fad'in eh ummi.
Matsowa tayi gab dani tare da min wani irin kallo da yasa gabana ya fara fad'i....
Tace Zainab nazo ne muyi wata magana wacce nake fatan zaki amince min??
Cikin rawar baki nace eh ummi insha Allah
Shafamin fuska tayi tare da fad'in yauwa my daughter
D'an ja baya nayi kad'an
Murmushi tayi tare da matsowa kusa dani ta janyoni jikinta ta rungume har ina jiyo sautin ajiyan zuciyarta, a hankali tace Zainab plz ina son ni dake mu dinga biya ma juna bukata, Wlh sonki ya kamani dan Allah ki yarda kiban had'in Kai.....
Da sauri na fara kokarin tureta amma na kasa domin tayi min ru'ko Sosai, bakinta take kokarin kaiwa nawa ina kuka ina tureta har Allah yaban Sa'a na cije ta a hannu da sauri ta sakeni, na shige toilet na rufe, kuka nake Sosai tare da tsoro da mamaki, dama ummi tana yin mad'igo Innalillahi'wa inna ilaihirajiun, ranan na tsorata Sosai tare da k'ara jin tsoran duniya..... Tunawa da irin azaban da Allah ya tanadar ma masu yin mad'igo sannan zamanin annabi ludu an kifa duniya saboda luwadi da mad'igo, yau shine ummi take aikatawa...... Tunawa tayi da sanda malaminsu yake musu wa'azi akan masu aikata mad'igo ko luwadi...... Inda yace
Mad'igo ko luwadi babban zunubi ne a musulunci, wanda za'a iya cewa Idan aka cire shirka, da kafirci to yana iya biyo baya.......
Sannan hukuncin wannan mummunan aikin luwadi ko mad'igo yana kusan dai daine da mutumin daya zagi Manzon Allah..... Kuma Kun San hukuncin Wanda ya zagi Manzon Allah.....
Manzon Allah (S A W) yace
Mafi girman abunda yake jin tsioranshi akan Al'ummata shine aikin mutanan Annabi LUD....
mai nene aikin mutanan Annabi LUD??...... shine luwadi da mad'igo Allah ya tsare.....
A wani hadisi so uku ajere Manzon Allah yana tsinema Wanda yake aikata irin aikin mutanan Annabi LUD.....
Manzon Allah (S A W) Yace....
*ALLAH YA TSINEMA WANDA YAKE AIKATA IRIN AIKIN MUTANAN ANNABI LUD, ALLAH YA TSINEWA WANDA YAKE AIKATA IRIN AIKIN MUTANAN ANNABI LUD, ALLAH YA TSINEMA WANDA YAKE AIKATA AIKIN IRIN MUTANAN ANNABI LUD*
Asara da tabewa ta gama tabbata akan mutumin da Manzon Allah ya jera Mai tsumuwa har guda uku akanshi.???
Sannan Manzon Allah yace.... Duk Wanda kuka samesu suna aikata irin aikin mutanan Annabi LUD to kukashe maiyi da wanda akeyi dashi
Sai dai a cikin hadisai ana samun rauni da wanda bai inganta ba.......
Sannan malamin mu ya kara dacewa duk mai aikata luwadi ko mad'igo hukuncin shi Indai aka kamasu wasu sunce........
A jefesu wasu kuma sunce a k'ona su, wasu kuma sunce a sami bene ginin gidan sama wanda yafi tsawo a jefo su aita musu haka har sai Sun mutu????? Wlh muji tsoran Allah, y'an mata da samari kunji wannan babban laifi ne wlh masuyi ku tuba ????
Bariki kuka take Sosai tare da tsoran Falmata lallai Asara da tabewa ya tabbata akanta aikata lesbians, kuka take Sosai tare da burin Dad dinta ya dawo ta fad'a Mai......
*May be anjima inyi muku wani ko gobe da safe*
~MARYAM OBAM~
Reply


Messages In This Thread
RE: BARIKI NA FITO*BY* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA**(Maryam Obam) - by Gimbiya - 09-09-2019, 12:36 PM

Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  BARIKI NA FITO*BY* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA**(Maryam Obam) Gimbiya 3 172,167 09-09-2019, 12:10 PM
Last Post: Gimbiya
  BARIKI NA FITO*BY* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA**(Maryam Obam) Gimbiya 0 11,779 07-24-2019, 10:16 AM
Last Post: Gimbiya
  BARIKI NA FITO*BY* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA**(Maryam Obam) Gimbiya 0 8,334 07-24-2019, 10:08 AM
Last Post: Gimbiya
  Yadda na taba yin soyayya da kanwata Maryam a fim Gimbiya 0 2,741 11-16-2017, 10:24 AM
Last Post: Gimbiya
  BARIKI NA FITO*BY* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA**(Maryam Obam) 0 3,823 Less than 1 minute ago
Last Post:
  BARIKI NA FITO*BY* *MARYAM ALHASSAN DAN'IYA**(Maryam Obam) 0 2,047 Less than 1 minute ago
Last Post:



Users browsing this thread: 1 Guest(s)