The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined variable $postsdone - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Trying to access array offset on value of type null - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 16925 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 16926 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 16927 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 16928 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 16929 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 16930 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 16931 - Line: 867 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 867 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key 16925 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 16926 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 16927 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 16928 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 16929 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 16930 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key 16931 - Line: 1576 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1576 errorHandler->error
/showthread.php 1578 buildtree
/showthread.php 879 buildtree
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 880 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 880 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 880 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 880 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $multipage - Line: 33 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 33 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $multipage - Line: 65 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 65 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*KASUWANCI NA* by ASMABAFFA
#8
KASUWANCI NA


76-80


Official

By
AsmaBaffa

Ina mika dubun godiya ta gereku
MAMAN 2 KIDS
AUNTY SUMEE
MEENAL SIDI
MRS HAMZA
ADABIYA ISAH
SAMEERA AHMAD
JAMILA SULE
MAMAN MEENAT

    Sai manya manyana ina jinjina muku
MAMAN MEENAT
MUM SUHAIL
MAMAN HAIDAR
QUEENMERMU
MAMAN WALEEDA
JIDDER ZARIA
MARCYCOOL
PHERTIMARH
AUTA
FLOWER ina kike kwana biyu Allah yasa lfy?
BIBA
HEENDU
HUMAIRAH

Page naki ne AYSHATABDULLAHI Me hadarin Sharhi na gode.??

Kwance nake a jikinsa na lafe luf muna huce gajiyar harkoki da muka kwasa,kin taba soyayya Ne Mufeeda? Naji muryarsa yana tambayata,wow yanda ya furta Mufeeda kamar wasu Aljanu ne suka fada Sabo da dadin sunan ba a cewa komai, kamar gaske nace ae na taba yi,gabansa ya fadi sosai ya shiga damuwa har kishi ya cika shi ya daure yace da wa? KUDI nace ina na san wani so ni ban san komai ba ai ni imani na kudi,ni kudi ne masoyina,Dariya yayi a ransa yasan ban san ma kudin ba ban san dadinsu ba Amma ina kirarin nasan kudi,a fili kuwa yace yanzu idan na baki million daya a hannunki me zakiyi da ita? Yanzu duk kuna ci kuna sha da Sutura ga schl baku da matsala da ita,ta ya zaki kashe million daya fada min naji? Kwanciya ta na gyara a jikinsa tare da fadawa tunanin ta yanda zan kashe kudin da ya fada,na gama tunani na nace na dinga cin kayan dadi,na fantama na Sa kaya irin na matan shugaban kasa,na dinga zuwa wajen da ake gasa kaji ina ci,na siyi fili kato,da mota,dariya yayi yace to kuna da motar hawa duk wacce kuke so akwai,me kike so kici wanda babu a gidan nan?Sannan kuna cin na wajen ma ai ko? Ae to ni dai ina so ace nima ina da nawa na kaina ba na wani ba,sabo dame?kayan mijinki ai naki ne, a'a ba nawa bane kafin a baka ma sai kayi yar murya,ko kuma a dinga bata rai ko kasa mutum ke ebowa ya baka watarana sai ya gaji,sannan Maza dan suna ma abu sai suyi ta juya ka ana ma kallon wata shatara, matan Hausawa kenan kike nufi duk abinda yasa suke karatu da aikin Gomnati don kawai su samu kudi ba sai sun saurari na mijinsu ba,kuma most of them badan Allah suke so su samu kudin ba kawai biyayya ce basa so suyiwa mijinsu shi yasa suke neman kudin, ya fita kin fita,bai Isa ya saki kiyi ba,wani ma in kudinta yafi na namiji zai sha wulakanci dole shi zai kwantar da kai yana mata biyayya.

    Nace hakane ko Ilmi macen tafi namiji sai kaga ko kudin albashi ya dauka ita zai kawowa sai yanda tayi dashi,shi yasa Maza suke tsoron auren macen da ta fisu Ilmi ko ta fisu albashi,sabo da matan Hausawa basu iya samu ba,mace daga tana daukan dan Salary sai kuga ta fara wulakanci kowa taka shi takeyi ita me kudi,dan Allah mata mu gyara halayen mu,wasu gidansu kaje da kyar suke kallonka ma bare mutunci ya hadaku Sabo da tana daukan Salary,mazan sam basa jin dadinsu,ga jarabar son kudi da neman kudi aje nan aje nan ba hutu ba lokacin me gida kuma bai Isa yace komai ba tafi karfinsa sai abinda taga dama,idan ma kishiya zaiyi cewa zatayi ya kara me ya dameni suje can su karata da kudina me nake nema a wajensa ko Sakina yayi zan iya rike kaina da Yara na,abin haushin kuma da zasu rabu sai aga ta koma bin Maza kanana tana kashe musu kudin da ta kasa taimakon mijinta dasu.

    Mun dade muna hirarmu dashi yana wasa da dukiyar fulanina wani dadi na shigata na juyo ina facing dinsa tare da kara shigewa jikinsa,yace ya dai? Wani sonsa nakeji yana ratsani ta ko wacce gaba dake jikina,baki nasa ina lashe lips dinsa kamar mayya nan ma haka muka kara birkita kanmu mun dade muna farantawa juna rai,ni kam yanzu son Aayan ya gama ragargaza min zuciya,kwakwaran numfashi banayi sai da tunaninsa,komai nasa birgeni yakeyi,ji nake kamar a hademu na zauna cikin jikinsa har abada abin fa ya wuce gona da iri yanda nake jin son Aayan ya zarta hankali har mamaki nakeyi,bani da burin da ya wuce na ganni tare dashi ina jikinsa,kallon Aayan kadai idan ina yi a Cikin gidan gaba daya sai naji dadi da sanyi marar misaltuwa,nayiwa zuciyata fada abin yaci tura,ko schl naje ba komai nake ganewa ba kawai tunanin Aayan yafiye min komai a duniya.
     Kwanaki sun dan ja,Ameer ko yaushe yana part dinmu kusan kullum sai yazo,a nan yake cin lunch da Dinner haka kullum suke fada da Meenat,Ma'eesha ce kawarsa kullum suna tare suna danna waya da jin wakoki aikinsu kenan, Meenat bata da time yanzu karatun waec da Neco sukeyi,Ma'eesha kuwa za a shiga Ss1 kwana nan,ni kuma ina ss1 going to 2 Sabo da ya tsallakemin jss3 ban karasa ba aka sani a ss1 shi yasa Amma da Ma'eesha ma ta fini class.
   Ma'eesha ta zama yan mata Sabo da kansu daya da Meenat kusan ma tafi Meenat girma ta kamoni Sabo da dama tana da saurin girma tsayin kafa tayi sai ka rantse ma ba Meenat ce yayarta ba,Sabo da zama da suke yawan yi da Ameer Ma'eesha har ta fara son Ameer sosai Amma boyewa takeyi dan kar mu gane sai dai kullum bata da zance sai Na Ameer.
    Kudi masu yawa Aayan ya bamu muje mu sake uniform tare da schl bags da takalma amma sai yace yasan idan nice me araha zan siyo mu tafi tare da su Meenat Driver ya kaimu.

     Muna mota Driver zai kaimu store nace canja hanya Baba ka kaimu Kasuwar kofar Wambai yafi araha,Meenat tace wlh mu store za a kaimu masu tsada yace a siya mana,Baki na make mata tayi shuru,ya kaimu Kofar Wambai muna gaban table din masu takalma ina ta zabga cikiniki yaki daidaita,na daga wani baki nace nawa wannan Malam? Dubu uku yace,a garin ina za a siyi wannan dubu uku Malam Dubu daya da Dari biyar idan ka siyar, Ma'eesha ce ta matsa gefe tare da kiran Aayan a waya Hello Yaya taki kaimu store wlh muna kasuwar Kofar Wambai kuma a kasuwar ma table din masu araha wai dan Dubu daya da Dari biyar kuma suna ta Surutu da masu saida kayan dan Allah da aurenta fa Yaya.
    Mata masu zuwa kasuwa a zauna ayi ta Surutu da masu saida kaya,da aurenki zaka ga wasu har canja murya suke suna lankwasheta abinda basa yiwa mazajensu sai siyiwa yan kasuwa sabo da suna neman a rage musu ayi musu araha su siya a banza.

   Aayan kuwa kishi ne ya sokeshi da bacin rai wai yacewa yarinyar nan  suje Mall amma ta kaisu kasuwa cikin maza ana ta cakudewa yanzu haka ma wani ya gogar masa jikin matarsa nan take bai San sanda ya shiga mota ba ya bar Office driver ya ja suka tafi,a hanya ya kira Ma'eesha ta fada masa inda suke minti kadan sai ga Aayan ya danna musu Horn tare da sauke glass.
    Ina ganinsa hankalina ya tashi na rude ko ta kan me kaya banbi ba nayi sauri na isa motar mu na fada ciki,Meenat da Ma'eesha suka shiga bayan mota kusa da Aayan da Kansa ya kaisu Shopping ya siya musu wanda suke so masu tsadar gaske komai har ni ma suka siya min nawa,ni kuwa tuni nasa Baba Driver ya maidani gida.
     Da suka dawo da kyar na fito palo,Ranar da dare nasha warning wajen Aayan sai da ya min ba dadi ina bashi hakuri.

    Anyi mana hutun schl Meenat tana zana waec da Neco dinta,yau Sunday muna zaune a palo ina yankewa Aayan Farce,Ma'eesha na karatu a wayarta da Ameer ya siya mata me kyau,Meenat kuwa abinci take ci dawowarta daga schl kenan yamma lisss,wayar Aayan ce ta fara ruri,da hannuna na daga kiran naga ansa Bobo nasan Yarima ne na kara masa a kunne yace Hey frnd  ya kk,Yarima yace gani a gidanku fa bude min kofa, Ma'eesha yayiwa magana yace budewa Yarima kofa Angel dama haka yake cewa Ma'eesha,Meenat kuma yace mata Preety, ni kuma daga ke shike nan sai ta mugun baci zai ce Mufeeda ina takaicin wannan abun da yake min Amma ya na iya tunda ni ba a sona.

     Ma'eesha na bude kofa Yarima yayi arba da ita wow ya furta a ransa da gani ba sai an fada ba yasan ma kanwar matar Aayan ce Sabo da kama da muke kawai haske zan fisu kadan shima idan baka sanni sosai ba baza kace na fisu haske ba,ba wani me yawa bane,Maeesha akwai fara'a ta gaisheshi tana murmushi sai kallonta yake ta gama Tafiya da Imaninsa gaba daya, bashi da burin auren yarinya karama Amma akan wannan kuwa sai dai a mutu, da sallama dauke a bakinsa ya shigo,Gaskiya Yarima ya hadu Chocolate ne me haske karshen kyau yana da shi dan fulanin Asali ne,ga wanka iya wanka dama duk irin abokan su Aayan ai haka suke basa muamula da garori, Ma'eesha kuwa kunya ma taji irin yanda ya mata Kwarjini gashi ya hadu sai kuma irin kallon da yake mata.
    Yana zuwa ya mikawa Aayan hannu suka tafa shegen gari kwana biyu Aayan ko Saudiyya banga kaje Umrah ba last wk ina can ina ta jiranka kace zaka je har na dawo bamu hadu ba,Tabe baki Aayan yayi tare da cewa gwauro shike yawo lokacin da yaga dama,dariya Yarima yayi lallai Aayan ka canja,juyawa nayi muka gaisa dashi a mutunce yana tsokanata da Abokinsa yayi kiba ya kara kyau me nake bashi ne,Meenat kawo masa ruwa,Kallon wacce aka kira da Meenat yayi tana can Dining tana cin abincinta da alama bata San anyi bako ba,Yarima a ransa yace su wannan gaba daya kama sukeyi da juna amma Ma'eesha irin muryata ce da ita sak,Meenat ce muryarta tafi tamu siranta sabo da iyayinta ta maidata siririya,kayan sanyi ta kawo masa iri iri kana ta gaisheshi a ladafce ya amsa tare da cewa Mufeeda wannan duk kannenki ne? Ae mana wannan Ma'eesha wannan Meenat,yace ke kuma Mufeeda triple M kenan yeah Ma'eesha ta amsa muna dariya,Meenat yan mata uwar iyayi tana ji da yan matan ci sai girman kan tsiya watarana kamar wata yar sarki aka take komawa magana ma sai taga dama,watarana kuma ta zage ayi da ita,Muna zaune ana hira sai ga Ameer ya shugo an ci wanka yazo dan ya birgeni ni Mufeeda wacce ban san me yake bama,Maeesha har taji sanyi data ganshi kusa da ita ya zauna ta gaisar dashi,Yarima ya fara kishin Ameer ya zauna kusa da Ma'eesha kuma yaga Ma'eesha sai wani Fara'a take masa sun fara surutunsu da alama sun saba da juna,s hi kuwa Ameer gaba daya Hankalinsa na kaina yanda na hade cikin Lace riga da skert ba karamin kyau nayi ba,abinda ya bashi haushi ganin ina yankewa Aayan farce gashi kuma kafafun Aayan gaba daya saman cinyata ya dorasu yana kwance dan naji dadin yanke masa farcen.

    Muna zaune daf da Magrib wata yar aiki ta shigo wai Meenat tazo tayi bako,Meenat tace ita bata da bako baza taje ba,tun kafin ta fara magana Ameer ya fara dariya,haka Aayan ma,nima na gane me suke nufi ko irin su Kwaja ne suka zo,Yarima yace mene haka daga ana kiran yarinya zaku fara mata dariya bai dace ba,Yar aikin tace a wata fyallelliyar mota yazo Hajiya da gani dan wanine,Nace mu ai bamu damu da wani me mota ba ko talakane indai yana da aikin yi,halaye masu kyau to alhmdllh zamu bashi ba wani sai me mota ko kudi etc,Aayan yace Pretty jeki kiji idan Bai miki ba ki dawo,kawai sabo da Aayan ne yace shi yasa ta figi Hijab tana fushi zata fita,nace ba kwalliya haka za a je? Kallona tayi kamar zatayi kuka ta fita abinta haka, taga mota iya mota tana jira taga wani Handsome ya fito sai taga Fela Gala da gani ba motarsa bace arota yayi, fitowa yayi tare da tsayawa yasa Hannu a aljihu harda Harde kafafu ya basar a jikin mota sai yanzu ma ta gane Ashe Motar tana ganin su Haneefa a cikinta,wato sune suka bashi aro azo a raina mata hankali.

   Ko saurarar Fela batayi ba tayi gaba abinta sai gata ta shugo kamar zata fashe tana wa Aayan magana dan Allah Yaya ka ganshi can ya biyo ni har gida wlh dan Allah ka koreshi sune suka kara turoshi, Ma'eesha tace Fela Gala ne wlh tun daga sunan Yarima shima ya fara dariya bai Sha dariya ba sai da ya leka ya ganewa idonsa harda rike ciki sabo da dariya,Ameer kuwa ba a magana,Aayan ne ya fita ba shiri yayiwa Nasuru fata fata da gudu ya fice daga gidan ya bar motar dama ta gidan ce.
   Meenat ta kalli Ameer tare da zuba masa Harara ta wuce Bedroom ta barsu suna bawa Yarima labari duk kwalliya da iyayin Meenat irin su Nasuru Fela ke zuwa wajenta,Yarima ya kalli Ma'eesha tare da cewa to ke yar ficika wanne kala ne naki? Dariya sukayi Sabo da Fela Gala ne yace mata Yar ficika,Maeesha tace ni yarinya ce ba yanzu ba,wani dadi Yarima yaji a ransa,Maeesha kuwa a ranta cewa take insha'allah Ameer ne ma,Shi ko Ameer tunani ma yake yaushene zai mallaki Mufeedansa,Ni kuwa ina nan zuciyata dankare take da son Mijina Aayan wanda naga Sam bai damu dani ba.
    Sallah sukaje masallaci har Isha basu dawo ba,lokacin na tattara su Meenat muna kitchen muna karasa abincin da muke,suna dawowa na fito da ludayi a hannuna ni ga uwar girki na manta ma da Ludayin juya miyar na fito,Ameer yace ina zaki abun miya kuma? Nace na manta sauri nake nasan Babyna yanzu wanka zaiyi,Ameer nan take mood dinsa ya canja amma ni ban gane ba nace bari ka gani na koma kitchen na ajiye ludayin na fito naji muryar Ameer yace mu dai ki koma ki karasa mana abincinmu yaran nan jagwalgwalo zasuyi mana,murmushi nayi nace sun iya sosai ba matsala,ya kara magana pls Aunty kije ki karasa da kanki,nufin Ameer dan kar naje wajen Aayan shine ya hada min wayo wanda ban sani ba ni kuma sai na koma kitchen din,n a tayasu muka karasa komai na barsu su gyara kitchen tare da shirya Dining,dana fito nace Ameer ina Aayan fa? Baki ya tabe yace suna wancen palon shi da Yarima,palon da ya fada min na nufa

    Direct naje shiga palon naki muryar Aayan yana cewa kyaleta ai wahalar da kanta takeyi bari nayi ta gama shiga hannu zata ga wulakanci,sai suka tafa da Yarima,nan take naji jikina ya dauki rawar sanyi,tsoro da fargaba tare da bakin ciki ya dirar min,ban san wa suke nufi ba,ban san akan me suke maganar ba sai na fassara maganar da naji kawai ba bincike ban tsaya naji dalili ba ko da wa yake nufi kawai sai na yanke hukunci cewar ni suke nufi dani suke,wato ni ya gano ina sonsa wahalar da kaina nakeyi,ya bari na shugo hannu ya wulakantani,ni zai wulakanta ma tab lallai dan Adam,duk abinda nakeyi Ashe baya gani a banza sai ma mugunta da yake hada min,nan take na fara tunano tun farkon haduwarmu irin tsanar da ya nuna min,Ammah ta da suka kashe min tunda sune suka jawo duk so yasa na manta,har aurenmu irin abinda ya dinga min a farko na wulakanci ina ta binsa,so yasa na manne masa nake kai kaina har dakinsa na sakar masa jiki,nasa yaji dadi,na godewa Allah da yasa ba ayi sex ba.
    Mata da dama suna irin wannan daga jin magana bata kai ta kawo ba,basu san ma akan me akeyin ta ba,amma da yake kullum a zargin mazajensu suke irin ko sun daina sonsu,ko suna kula wata,musamman ace suna da kishiya ko zai kara aure,ko wani dalili yasa dai taga mijin ya dan canja to zargi zata kasance a ciki iri iri,komai yayi laifi ne a wajenta,magana idan ta ji ko da abokinsa sai ta fassarata ta koma tashin hankali Babba,wata ma har abokin zata daina kulawa,ko ta masa rashin mutunci,miji na neman aure abokin dole shine a gaba wai dan me zaiyi nan fa zata kulla masa wata ma sai ta rabasu sun bata sun daina abotar,wata kuma duk abokansa ta daina kulawa ko ta ci musu mutunci wai sune suke zuga mijinta,duk da cewa ana samun masu hakan amma mata mu daure mu daina zargi tare da saurin yanke hukunci,ko magana akayi sai a dinga fassara ta bai bai sabo da ba a son zaman lfy.

     Ni dai ina tsaye naji kamar ma zazzabi zan fara sabo da yanda nake son Aayan ko kaina ban so haka,bani da burin da ya wuce naga ya soni back amma sai gashi abinda naji ma daga bakinsa,Hawaye na share na daure na shiga palon fuskata ba walwala nayi Sallama suka amsa,Nan take Aayan ya kafeni da idonsa yana ganin yanda lokaci kadan na fita daga hayyacina,dazu lfy lfy muke,kamar ma kuka nayi,ganin yana kallona nayi kasa da kaina,tunaninsa ko yan gidansu ne suka yi min rashin mutunci ya tabbatar idan kuwa sune suka sa na dawo haka yau sai anyi yaki a gidan nan,baya son a taba masa ni yanzu ko kadan, kasa jurewa yayi yace ina zuwa Yarima yaja hannuna mukayi waje dashi muna fitowa a jikin kofar yasa yatsansa tare da dago da fuskata yana kallona sannan a hankali yace lfy? Me akayi miki? Nayi shuru,Hajja ce? Su Haneefa nan ma shuru sai Hawaye dake biyo min a kumatuna a raina ina kara cewa yanzu wannan zankadeden rabuwa zaiyi dani,shike nan baya sona? Yace am asking u me suka miki ya fada da tsawa,duk ya shiga damuwa lokaci guda ya rude Allah sarki So,so banza ne kawai sai ya bani tausayi kuma na batawa wanda nake so rai,har bana ganin laifinsa sai nawa sabo da Aayan baya laifi a wajena so hana ganin laifi,tunowa da maganarsu dana jine yasa na kara birkicewa,kawai nace ni ba wanda ya min komai kawai ji nayi bana son auren Kasuwancin nan ko nawa zan samu,ko yanke talauci ne wlh bana sonsa dan Allah ka sakeni na tafi, wani dum yaji maganar a bazata to ko dai itama sun mata wani asirin ne ko kuma sun sa mata wani abu taci ai ko wlh bazai iya sakinta ba har abada sai dai duk inda zata je da aurensa,jikin Bango ya Dafe kawai yayi shuru yana Innalillahi kawai yake maimaitawa duk zarginsa tunaninsa Su Hajja ne ko asiri ko kuma wani abu suka mata wanda baza ta iya zama ba, da kyar ya dago muka hada Ido sai da na rumtse Idona yanda bazan iya kallonsa ba ya Zama wani iri idonsa yayi jajir,Hannu na ya figa kamar zai tashi sama ya jani muka Haura samansa har Bedroom ni dai kawai binsa nakeyi,a ciki ya tsaya tare da rike kugunsa da hannu biyu kansa ya daga sama yana danne lips dinsa na kasa da Hakoransa yama rasa ta ina zai fara, maganarsa naji a hankali yace Mufeeda! na kalleshi tare da sadda kaina kasa,yace ki fada min me ya faru dake me kike ji me yake damunki ko kuma a gidan ne wasu suka ce miki wani abu ni dai nasan ban miki komai ba,ko kema sabo da bamuyi Xxx ba zaki tafi? Da sauri nace a'a wlh ba haka bane,yana kallona yace to ko bana Haihuwa kike nufi? Nan ma kafin ya rufe baki nace wlh ba wannan bane,to mene tell me,karki rufeni ko ki cuci kanki just tell me what's is going on? Ina Hawayena nace ni kawai na gaji da auren ne Bana son kudin yanzu,Wait bafa Business muke ba wannan wasa ne kema kin san aure ne na sunna aka yishi ba wai akan kudi ba,nace ae na sani kawai bana son auren ne nace ma ni bazan zauna ba kawai,ok yace ko gidan nan ne bakya so? Fada min sai na Canja muku gida,kai na girgiza a'a, yace ko Wacce kasa kike so fada min wlh zamu koma can indai kina so,a raina nace jibeshi kamar gaske salon ya kara mallake min zuciya yaji dadin wulakantani da kyau to bazan je ba,nace bazanje ba ni a fili,Abuja fa?nace ko villa ne banso,to kiyi Hakuri idan wani abu aka yi miki addua akeyi akan komai ba fushi ba haba yan mata nan ya dinga lallashina,sai nayi kamar zan Yarda naji tausayinsa sai kuma na fasa nace nifa bazan zauna ba.

   Yana gajiya ya tamke fuska ba mutunci yanda na sanshi tun farko,nan take naji tsoronsa jikina ya fara rawa, tahowa yayi kamar zai makeni na fara ja da baya yana Huci yace bari kiji bude kannenki wallah kinji na rantse har uku bazan sakeki ba kuma ba inda zakije idan kika fita ma ko gate ne bada izinina ba sai munyi Shari'a dake a gaban Allah ban yafe miki ba,kiji ni da kyau ba wani Business auren za ayi as from today ni kuma duk Hakkin ki daga yau zan fara baki,yana gama fadin haka ya kwanta a saman Bed yana Dafe kansa dake Sarawa, tausayi kuma ya bani sosai yanda ya nuna ya damu a kaina gaba daya sai na tsani kaina me yasa nayi haka,amma dai zuciyata ta hanani na hakura,ido ya rufe sosai still yana Dafe da kansa ya rike sosai da alama ciwo yake masa da yawa,Hankalina ya tashi nima,mikewa yayi tsaye kamar wanda yasha giya yana maye da tangadi,haba ban san sanda tausayinsa ya gama rufeni ba gaba daya naga ya fini shiga damuwa yazo ya ratsa ta gefen zai wuce ya fita tuni na damko hannunsa ya tsaya cak tare da juyo da fuskarsa ya kalleni gabansa na koma tare da fadawa jikinsa na rungumeshi kam kam sosai da sosai kamar za a kwace min shi, baiyi hugging dina back ba,da kaina cikin kunnensa na rada masa Rug me back am so sorry, bai kulani ba babu zato naji bakinsa cikin nawa ya fara tsotsa ya rabani da kasa dan dagani yayi sama yanda tsayinmu zaizo dai dai ba sai yasha wahalar sunkuyoba,haka muke tsotse bakin juna kamar mun samu wani kayan dadi na tsotsa,wannan kiss din yafi na kullum dadi,gardi,tare da nishadi,yanda nakeji  ya zarce na fada muku,muna ta yi ba ji ba gani kamar zamu cinye kanmu ko nayi kamar zan kwace bakina sai ya kara rikeni kam ya hanani sai da muka dauki dogon zango a haka sannan da kyar na zare jikina daga nasa,amma duk da haka kara jawoni yayi jikinsa tare da fara lashe min wuya,tsigar jikina tashi take kawai gaba daya ya gama kara min sonsa a zuciyata, da kyar nake iya tsaiwa da kafaguna shima haka,ya fara kokarin cire min kaya na tuna yayi maganar hakki dazu da sauri na rike masa hannu tare da cewa abinci still dai ban saki raina ba bana wani nishadi kamar dazu,kyaleni shima yayi fuska ba walwala yace let's go,sai da muka saita kanmu sannan muka sauka kasa,Gaba dayansu Har Yarima da Ameer suna Dining suna ta cin abincinsu muka sakko duk kayanmu ya nuna da gani anyi yamutse yamutse,ga T-shirt din Aayan Fara kar ce duk jambakina red da Powder a jiki duk na shafa masa ba tare da mun sani ba sabo da murzar juna,Yarima da Ameer duk sun gane me akayi,Meenat ma ta gane gani ba jambaki a bakina sannan duk ga wani nan a bata gefen bakina,Aayan harda digon jambakin a hancinsa duk sai yanzu ma muka kula da hakan,Yarima sai dariya yake kunshewa yana kallon Aayan, dan Iska wlh zaka bar gidan nan banza munafiki Cewar Aayan,Yarima yace to me nayi kuma? Bayan ka shanyani,Ameer kishi ya hanashi kallon kowa kawai tura abincinsa yakeyi,Aayan har yau yana cikin damuwa ya kasa cin abincin kuma yunwa yake ji,ni kuwa bakin ciki baya hanani cin abinci ko cuta nake sai naci na koshi haka nake bare kuma kafin naji Maganar da su Aayan sukeyi tun a kitchen muna girkin na cika tumbina, ganin ya kasa ci na Mike tare da Zama kujerar dake kusa da tashi zan bashi da kaina,kafin na fara Ameer ya ajiye spoon yace ina zuwa bari nayi waya ya fice da sauri zuwa part dinsu,Yarima yace nima tafiya zanyi Ma'eesha zo ki rakani mota nan yayi mana Sallama suka fita,Aayan yace sai nazo zanyi maganinka ya furta da alama kawai danne bacin ransa yakeyi,Meenat ma tuni tayi Bedroom zata fara karatu,daga ni sai shi ya Dafe kai tare da rafka tagumi da gani yana cikin damuwa me yawa.

     Hannun da yayi tagumi na janye a hankali ba tare da nace komai ba na ebo abincin a spoon na fara bashi da kaina yanda yake ci zaka San baya jin dadinsa ko kadan,kamar kurame haka muke har yace ya koshi nace ko spoon biyar baka ci ba fa? Zan fara masa magiya ya Mike kawai ya haura sama ya barni a nan,ban damu ba na tattara komai na kai kitchen tare da gyara komai na shiga Bedroom dinmu nayi wanka da duk wani abu da zanyi nayi nasa Night gown dina da kawata Sayyah ta bani wai inji mamanta kala Uku hadaddu amma basu fiye tsaraici ba nasa light blue din masha Allah nayi gaskiya karshe na daura ta samanta na fita lokacin Ma'eesha ta dawo daga wajen Yarima tana nuna min chocolate masu Uban yawa da kudi masu yawa wai a bani inji shi,na karba nayi godiya nace bari na nunawa Aayan kafin Ku fara sha nayi waje zuwa Bedroom dinsa,gefen Bed na hangoshi a zaune yayi shuru kawai yana kallon sama da alama tunani yakeyi yaji Sallama ta,amsamin yayi kawai tare da kwanciyarsa saman Bed ya barni a tsaye,banji dadi ba ni kaina muna zamanmu lfy na jawo bacin rai kuma shi dama kafin a lallasheshi aikine.

    Haneefa ce Zaune tare da Mommynsu suna hira,Mommy tace Ameer naga fa kamar kwanan nan ya Mannewa wajen yan iskan can a part dinsu ban san ko Hajja tasan labarin ba,Haneefa tace Mommy ki barshi ai da alama bata sani ba gwara ma da kika tuna min bari naje na fesa mata tayi maganinsa ya daina zuwa na tsani Su Mufeedan nan Shegu wai su masu kyau,Mommy baki ta tabe tare da cewa je ki sanarwa Hajja ni ma yau zan fadawa Abbi abin na Ameer yayi yawa, da sauri Haneefa ta tafi part din Hajja,ta samu Hajja sai Mulki take zubawa tana wani takama da isa tare da bawa yan aiki umarni.

     Haneefa ta zauna gefenta tare da cewa Hajja wani labari na kawo miki marar dadi so sad wlh abin kunya ma,Ina jinki Hajja ta furta tana gadara,Haneefa ta gyara Zama tare da sanarwa Hajja yanda Ameer ya koma bangarensu Mufeeda.
   Hajja da masifa tace to azukwi uwar munafunci me yasa kuke takurawa Ameeru ne,ina ruwanki Algunguma to nasan da zuwansa aikina yake ni na turashi,kinzo da guntun munafuncinki ai zai shigo ne zan fada masa me kika ce ya farfasa miki jiki,Haneefa ta fara bata hakuri daga fadar gaskiya sai a lullubeni da fada to daga yau bazan kara fada ba ko mene zai faru ya faru,Hajja ta dakko yar sandarta ta karfe tayi kan Haneefa da gudu ta fice ta bar Hajja na Masifa ta gaji da Gulmar Ameeru da akeyi a gidan nan.


AsmaBaffa 
    Loves u all ❤?
Reply


Messages In This Thread
*KASUWANCI NA* by ASMABAFFA - by Gimbiya - 01-20-2019, 01:26 PM
RE: *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA - by Gimbiya - 01-20-2019, 01:32 PM
RE: *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA - by Gimbiya - 01-20-2019, 01:33 PM
RE: *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA - by Gimbiya - 01-20-2019, 01:35 PM
RE: *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA - by Gimbiya - 01-20-2019, 01:36 PM
RE: *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA - by Gimbiya - 01-20-2019, 01:56 PM
RE: *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA - by Gimbiya - 01-20-2019, 01:57 PM
RE: *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA - by Gimbiya - 01-20-2019, 01:58 PM

Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA Gimbiya 1 32,229 03-26-2019, 10:46 AM
Last Post: Gimbiya
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA Gimbiya 4 120,151 02-22-2019, 08:04 AM
Last Post: Gimbiya
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA Gimbiya 0 7,552 01-18-2019, 09:17 AM
Last Post: Gimbiya
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA 0 2,511 Less than 1 minute ago
Last Post:
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA 0 3,072 Less than 1 minute ago
Last Post:



Users browsing this thread: 2 Guest(s)