09-20-2018, 09:52 AM
? MATA UKU GOBARA ?
Na Mermue ?
41-45
Da sallamarsu suka shiga palon hajiya, mahmoud hankalinsa ya tashi jin kalaman da matansa ke furtawa, suka zube suna kwasar gaisuwa wurin hajiya, ta amsa masu fuska a sake, ganin hakanne ma hankalin Mahmoud ya dan fara kwanciya.
Su kuma hajiyoyin suka gaidasu sai washe baki sukeyi adole ga mutanen kwarai, da sauri humaida ta mik’e ta yiwa zuhra signal, itama ta mik’e suka yiwa hajiya sallama cewar zasu bar, hajiya tace “Ku shiga ciki dai ga mijinku ya zo ai sai ya wuce daku.”
Aa hajiya ki barsu su tafi kawai, ni daga nan ba gida nayi ba, humaida da zuhra sauki ajiyar zuciya sukayi lokaci daya tare da ficewa da sauri.
Hajiya ta kimtse fuska tare da gyaran murya ” yanxu Mahmoud dabi’ar daka daukarwar kanka ta kwarai CE?? Ace mutum ya kama aure-aure har afara lissafasa a gari, yanxu me matanka suka rageka dashi gasu nan Kansu a hade gwanin sha’awa.”
Shidai Mahmoud kansa a k’asa sai zungurin Ahmad yakeyi alamar yayi magana, shikuwa yaki sai noke kafada yakeyi, “can mahmoud yafara bada hakuri dayaga babu sarki sai Allah, tare da tambayar me matansa suka gaya mata??”
Hajiya ta gyara zama fuskarta a daure ” cewa sukayi zaka k’ara aure wai hakane???
Kuma alhalin humaida ta tabbatar min ta gyara halayenta, kuma sun hade Kansu abin sha’awa.”
Amma matsalar da suke fuskanta kwanan nan ka bijiru masu da k’arin aure bayan kana jifarsu da miyagun kalamai, kana wulak’antasu kai suci ko kallo basu isheka ba, kana cewa humaida K’AZAMA ita kuwa zuhra duk da cewa bamu San kuna samun matsala da ita ba, wai kana CE mata GUNKI in fact ni narasa ma meye Kalmar take nufi?
Jin haka ne yasa mahmoud yayi hamdala cikin k’albinsa “ya yiwa hajiya bayanin komai ake ciki tareda Ahmad yana k’arin bayanin abinda yasani.”
Yanxu haka ban Masan zasu fito ba, ba wadda ta tambaya sai fa dariya da suka min rakiya da ita, mahmoud ya k’arasa kamar zai saka kuka.
Hajiya ta rik’e baki cike da mamaki lalle Dan Adam sai abarsa, nikam nayi mamakin ganinsu don duk cikinsu ba Wanda ya damu da kirana ballantana ziyara, shiyasa nima na zuba masu nagani tunda dai kai kana zuwa.
“Toh yanxu Allah yasa JALILAR ta zama mai kawu k’arshen wannan husuma.” Amin suka karbe ballantana mahmoud jikinsa har bari yakeyi, akan hajiyarsa ta amince.
“Yanxu idan kuka gama fahimtar juna da yarinyar sai atura atsaida rana.”
Yawwa hajiyanah Allah ya k’ara maki lafiya da nisan kwana, haj tayi dariya kawai.
Dai-dai nan goggo tayi sallama ta shigo gidan haj, an kammala gaisuwa take tambayar mahmoud ” my son ya naga bakinka kamar gonar auduga gidanka ya samu lfy kenan??”
Hmmmm kibari kawai goggo gidana ya zama gobara.
Haba dai ina zuhrar??
Hajiya ta cafe tace ai zuhra ta bamu kunya, ta labatarwa goggo komai, cikin mamaki ta rik’e haba “amma anyi muguwar sukuwa zuhra yanxu tadawo jaka kawai ta biyewa humaida”
Lallai zanje naci mata mutunci kuwa, hajiya ta katseta kibarta zatayi hankali ne.
Ba tabar dan uwanta ta kama bare ba, zata gane Wanda ya aiketa.
Haka su mahmoud suka mike sukayi masu sallama, sai bayan sun fice goggo kiyewa hajiya bayanin matsalar zuhra, ” tace au dama haka abin yake???
Lalle yaran zamani ba kunya, yanxu suka iya tinkarata da wannan maganan??”
Goggo ta mike bari naje wurin uwarta tasa maman abideen ta gyarawa zuhra zama gidan aurenta tun wuri,Maman abideen itace yayar zuhra, Hjy tace ai kam haka ya dace, sukayi sallama.
Misalin k’arfe shida mahmoud ya dawo gidansa, ya shiga gidan ba kowa, yayi tsayi yana mamaki toh ina matansa sukaje har yanxu basu dawo ba?????
Na Mermue ?
41-45
Da sallamarsu suka shiga palon hajiya, mahmoud hankalinsa ya tashi jin kalaman da matansa ke furtawa, suka zube suna kwasar gaisuwa wurin hajiya, ta amsa masu fuska a sake, ganin hakanne ma hankalin Mahmoud ya dan fara kwanciya.
Su kuma hajiyoyin suka gaidasu sai washe baki sukeyi adole ga mutanen kwarai, da sauri humaida ta mik’e ta yiwa zuhra signal, itama ta mik’e suka yiwa hajiya sallama cewar zasu bar, hajiya tace “Ku shiga ciki dai ga mijinku ya zo ai sai ya wuce daku.”
Aa hajiya ki barsu su tafi kawai, ni daga nan ba gida nayi ba, humaida da zuhra sauki ajiyar zuciya sukayi lokaci daya tare da ficewa da sauri.
Hajiya ta kimtse fuska tare da gyaran murya ” yanxu Mahmoud dabi’ar daka daukarwar kanka ta kwarai CE?? Ace mutum ya kama aure-aure har afara lissafasa a gari, yanxu me matanka suka rageka dashi gasu nan Kansu a hade gwanin sha’awa.”
Shidai Mahmoud kansa a k’asa sai zungurin Ahmad yakeyi alamar yayi magana, shikuwa yaki sai noke kafada yakeyi, “can mahmoud yafara bada hakuri dayaga babu sarki sai Allah, tare da tambayar me matansa suka gaya mata??”
Hajiya ta gyara zama fuskarta a daure ” cewa sukayi zaka k’ara aure wai hakane???
Kuma alhalin humaida ta tabbatar min ta gyara halayenta, kuma sun hade Kansu abin sha’awa.”
Amma matsalar da suke fuskanta kwanan nan ka bijiru masu da k’arin aure bayan kana jifarsu da miyagun kalamai, kana wulak’antasu kai suci ko kallo basu isheka ba, kana cewa humaida K’AZAMA ita kuwa zuhra duk da cewa bamu San kuna samun matsala da ita ba, wai kana CE mata GUNKI in fact ni narasa ma meye Kalmar take nufi?
Jin haka ne yasa mahmoud yayi hamdala cikin k’albinsa “ya yiwa hajiya bayanin komai ake ciki tareda Ahmad yana k’arin bayanin abinda yasani.”
Yanxu haka ban Masan zasu fito ba, ba wadda ta tambaya sai fa dariya da suka min rakiya da ita, mahmoud ya k’arasa kamar zai saka kuka.
Hajiya ta rik’e baki cike da mamaki lalle Dan Adam sai abarsa, nikam nayi mamakin ganinsu don duk cikinsu ba Wanda ya damu da kirana ballantana ziyara, shiyasa nima na zuba masu nagani tunda dai kai kana zuwa.
“Toh yanxu Allah yasa JALILAR ta zama mai kawu k’arshen wannan husuma.” Amin suka karbe ballantana mahmoud jikinsa har bari yakeyi, akan hajiyarsa ta amince.
“Yanxu idan kuka gama fahimtar juna da yarinyar sai atura atsaida rana.”
Yawwa hajiyanah Allah ya k’ara maki lafiya da nisan kwana, haj tayi dariya kawai.
Dai-dai nan goggo tayi sallama ta shigo gidan haj, an kammala gaisuwa take tambayar mahmoud ” my son ya naga bakinka kamar gonar auduga gidanka ya samu lfy kenan??”
Hmmmm kibari kawai goggo gidana ya zama gobara.
Haba dai ina zuhrar??
Hajiya ta cafe tace ai zuhra ta bamu kunya, ta labatarwa goggo komai, cikin mamaki ta rik’e haba “amma anyi muguwar sukuwa zuhra yanxu tadawo jaka kawai ta biyewa humaida”
Lallai zanje naci mata mutunci kuwa, hajiya ta katseta kibarta zatayi hankali ne.
Ba tabar dan uwanta ta kama bare ba, zata gane Wanda ya aiketa.
Haka su mahmoud suka mike sukayi masu sallama, sai bayan sun fice goggo kiyewa hajiya bayanin matsalar zuhra, ” tace au dama haka abin yake???
Lalle yaran zamani ba kunya, yanxu suka iya tinkarata da wannan maganan??”
Goggo ta mike bari naje wurin uwarta tasa maman abideen ta gyarawa zuhra zama gidan aurenta tun wuri,Maman abideen itace yayar zuhra, Hjy tace ai kam haka ya dace, sukayi sallama.
Misalin k’arfe shida mahmoud ya dawo gidansa, ya shiga gidan ba kowa, yayi tsayi yana mamaki toh ina matansa sukaje har yanxu basu dawo ba?????