The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*RANA D'AYA*BY MIEMIEBEE*
#1
RANA D'AYA

BY MIEMIEBEE

  PAGE 02


    Seda ya d'auki tsawon lokacin da ya wuce tsammanin mutum sannan yace, "Ga magunan naki, ina kyautata zaton kin iya karatu za kuma ki iya gane dosage d-" bata basa dama ya k'arisa fad'in abinda yake da niyya ba ta katse shi "Mallam ba seka zageni ba am not an illiterate."

   "Serve you well" ya fad'a ba tare da nuna damuwa ba "Then kina iya tashi in kaiki gida."

  "Nagode kar ka damu I can bring myself home" taga alaman d'an rainin wayo ne shi to ya kwantar da bokatin hankalinsa, kar yace don ya ganta a haka zey raina mata wayo dan kuwa ita ba jahila bace saboda tayi karatun ta na secondary ba kuma a kowani gajan government school ba. No private school ne me kyau wanda ake kira da Ruby springfield college wanda ya kasance one of the best schools in Maiduguri.

  "What gibberish are you saying?" Ya tambayeta a takaice. "See kar ki 6ata min lokaci, kar kiga don tun d'azun ina danne zuciya na ina binki a hankali ki d'au hakan ba a bakin komi ba. Ina da muhimman abubuwa a gaba na wanda sukafi tsayuwa anan ina rok'anki to take you home, now get up" ya buk'aceta cike da tsiwa sede ko motsawa Amal batayi ba. "Are you deaf?"

   "I said to leave me alone!" Ta buga mai tsawan itama "Ka kama ka jawo min asara ina zaman zama na zaka wani kama kace min in tashi ka kaini gida? Me kakeson in cewa Mami bayan duk cafanin dana yo mata ka ta6ar6arar min dasu kabarni da babu? Don Allah ka barni kayi tafiyanka."

   "In ke baki san abunda ya kamata ba toh ni na sani a cewarki bazan biya ki asaran dana janyo miki bane? I'm aware of all that and zan mayar miki da komi kawai ni ki tashi in kaiki gida na bawa iyayenki hak'uri na fita hak'k'inki, I have other important things to attend to" ya sanar da ita. Kaman wacce bazata motsa ba se kuma ta shiga miqewa a hankali wanda a garin hakan ta kusa fad'i kasancewar k'afar nata da ta kasa takashi. Da sauri Afzal ya tarota, ganin bey saketa ba har yanzun kuma baida niyyan yin hakan ta shiga jan hannunta sai dai ta kasa.

   "Don't fight it" yace da ita "Muje" bata sake yunk'urin k'watan kanta ba har suka kai haraban asibitin inda yayi parking motarsa. Sanyata yayi a kujeran gaba sannan ya zagaya ya shiga shima tare da tada motar. A circular road inda ya kad'etan suka koma inda ya buk'ace ta da ta rubuta masa list na abubuwan datayi rashin nasu. Ba gardama ta amshi paper da biron ta lisafo komi harda kud'ad'e da amount nasu. Abu d'ad'd'aiku ne be samu ba wanda yamata alk'awarin bata kud'in idan ya kaita gida. A farko yaso su jesu kasuwan domin ta siyo amman tuna besan kan kasuwan ba sabida bai ta6a shiga ba seya fasa. A karo na biyu kuwa yayi tunanin ko zasu shiga su biyu tayi leading nasu but referring to her wounded leg yaga wuya kawai hakan zai bata so se yayi sticking to first decision d'in kawai: na miyar mata da kud'in. Kwatancen gidansu ya buk'ace ta da tayi mar wanda tayi ba tare da gardama ba. Chan cikin Jiddari suka shige. Tunda Afzal yake be ta6a shiga kwamacalan unguwa ba kaman wannan se yau, yasan war haka motansa ya fita daga kamanninsa ya dawo wani abun na daban saboda potholes da kwatamin daya rink'a shiga. Sun kai wani junction ta buk'ace sa daya tsaya.

   "Ina ne gidan naku?" Abinda ya fara tambayarta kenan.

   "Mota baya iya shiga layin zan k'arisa daga nan nagode."

 "Acewarki kawo ki kawai nayi saboda inada ra'ayin hakan? Am here to apologize to your parents and tsaya ba sekin karya min handle na mota ba" ya buk'ace ta ganin tun d'azun take k'ok'arin bud'ewa amman ta kasa. Fitowa yayi ya zagaya sannan ya bud'e mata k'ofar tare da miqa mata hannunsa.  A cewarta gabad'aya nufi yake da ta sanya nata aciki saboda ya taimaka ya fito da ita daga motan sede wani hanzari ba gudu ba tana gwada yunk'urin sa hannunta cikin nasa kawai taga yaja hannun nasa baya da sauri yana me kad'a mata kai "Tray d'in zaki miqa min" ya sanar da ita. Wani irin kunya kaman ta tone k'asa tasa kanta aciki ta jiyo amman wallahi seta rama ba shakka da gangan ya mata hakan don ya kunyatar da ita. "Kar ka damu ina da hannu I can manage" ta fad'a rai a murtik'e tare da murgud'a mai baki. Murmusawa yayi yaja gefe tare da crossing arms nasa a faffad'ar k'irjinsa yana me kallonta. Yasani sarai bazata iya fitowa ba harta sai ya taimaka mata toh why don't he enjoy the moment?

   Amal tafi minti biyu tana k'ok'arin fitowa amman ta gagara, ko kad'an k'afan nata baison nauyi ai kawai ta rushe da kuka har anan Afzal be motsa ba seda yabari ta sha wahala ta shiga neman taimako da kanta. Ganin ba mahalicci se Allah ta kewayo da kallonta a garesa, dagangan shiko ya shiga duban lokaci a agogon dake d'aure a hannunsa pretending as if beda masaniya game da abinda takeyi tun d'azu.

   "Bawan Allah don Allah ka taimaka min bazan iya fita ba." Dariya ne ya k'eto mar sosai amman ya dage ya danne tare da matsowa kusa da ita. "So kin iya magana da ladabi haka dama?" Ya tambayeta yana me k'are mata kallo.

  "Ni ba abinda na buk'ata ba kenan" ta amsa tana me kawar da kanta haka kawai bata jin dad'in had'a ido dashi, "Ni ka taimaka min in samu in fita daga wannan motar nakan please!"

  "Ohh! Rashin kunya kuma zakiyi min? Kinsan kad'an ne daga cin aiki na in barki har sekinyi tsami cikin motan nan ko? Don't you dare me young lady."

   "A'a kayi hak'uri don Allah." Cike da rashin mutunci ya taimaka mata ta samu ta fito daga motan suka shiga takawa zuwa gidan nasu wanda baida nisa daga inda Afzal yayi parking. Sede duk wani angle da suka wuce se sun zama topic and side of attraction. Surutu babu wanda basu ji ba amman duk haka suka manna musu har suka k'arisa gidansu Amal d'in.

   Gida ne dai-dai da d'an talaka bawan Allah wanda za'a iya cewa be rasa ci da sha ba da kuma tufafi. D'akuna biyu ne gabad'aya a gidan a jere seda toilet d'aya daga other end d'in sekuma kitchen a opposite nashi, suna da famfo a tsakar gidan wanda ba sai anje ibo ruwa daga waje ba. Dai-dai Mami ta fito daga kitchen kenan su Amal suke k'arisowa tsakar gidan da Afzal riqe da ita, ai ba shiri tayi baya ta b'oye kanta cikin kitchen d'in tana me leqensu ta window. Salati kawai ta shiga yi ganin yadda mutumin dake sanye da suits ya riqo mata 'ya a cewarta gabad'aya wani masifa Amal taje ta kwaso musu sanin sharpness na bakin 'yar nata kaman razor. Tun farko dama bata goyi bayan zuwa aiken nan ba don de ba yadda ta iya ne Amal tafi k'arfinta gashi Papi (kakan Amal) da take d'an jin maganansa ma bai gida balle ya mata. Yau ina zata sa kanta Amal ta ibo musu abinda yafi k'arfinsu. Tunani kala-kala ba wanda ba tayi ba. Tunda suka shigo Afzal ke bin gidan da kallo, tabbas talakawa ne amman hakan be maida su k'azamai ba. Ko leather d'aya  be gani a k'asa ba ko ina an share tsaf ga kuma k'amshin turaren wutan dake tashi. Suna k'arisowa dai-dai tsakar gidan suka tsaya, se anan ya saketa tare da jan baya kad'an hakan ya bawa Amal daman sauk'e nauyayyiyar ajiyar zuciya.

   "Ina Mamin naki?" Ya tambayeta ai take zuciyan Mami yawani har6a shikenan nata ya k'are yau ga Papi bayi nan yayi tafiya.

   "Dake fa nake" Afzal ya kuma fad'i jin bata bashi amsa ba. Tsaida kewaye-kewayen da takeyi don neman Mami tayi tana me dawo da kallonta a garesa "Gani nayi tare muka shigo gidan taya kake tsammanin zan san inda take?" Ta tambayesa cike da rashin kunya. Cike da d'ambun mamaki Afzal ya tsaya yana kallonta shin wannan wacce irin fitsararriyar yarinya ce? Ace ko kunyan idonsa batayi ta rage wani abun? Sai dai ya daina mamakin hakan tuna 'yan qauye da masifaffen rashin kunya ga kuma shaidan dayayi mata na 'yar gudun hijira, tama daina basa mamakin. On the other side kuwa cikin Mami ya gama d'iban ruwa ji take kaman ta cafko Amal ta nad'a mata na jaki upon all the trouble data janyo masu still tana da bakin yima wannan security (as yadda ta ma Afzal shaida ganin sa sanye da suits) rashin kunya? Lallai kuwa tayi hak'uri ta rufa musu asiri.

   "Mami!" Amal ta k'walla wa mahaifiyar nata kira, shiru kukeji ba amsa. "Mami don Allah ki fito daga b'uyan nan ni bance miki bala'i na kawo ba wannan mutumin gefe nan ne yazo baki hak'uri ya kad'e miki 'ya" ta sanar a fili. Se anan Mami tad'an ji sukuni but even still ta kasa fitowa gani take kamar k'arya Amal keyi saboda sau dayawa takan yi mata hakan, ta d'ibo bala'i daga waje  sannan ta fake tazo tace alkhairi ta kawo.

    "Mami wallahi zan k'ariso in janyo ki daga kitchen d'innan" tafad'a tana kallon setin windon da Mami ke leqe daga gun ai tuni ta miyar da fuskarta ciki, ashe de Amal ta ganta. Numfasa tayi sannan ta fito alokacin kuwa Afzal ji yake idan be saki wannan dariyan daya k'eto mar ba ze iya mutuwa. Wannan wacce erin matsoraciyar uwa ce? Ai kam dole Amal tayi rashin kunya haka daga ganin mahaifiyar natan batayi kalan me tsiwa ba bale har ace zatayi discipline Amal.

   Da k'yar d'in k'yar ya samu ya maida dariyan ciki ahaka ma seda yayi kad'an a waje wanda a sanadin haka Amal ta juya ta galla mai harara sede be ganta ba dake hankalinsa gabad'aya ya duk'ufa akan Mami yana mey mamakin yadda akayi basu kama sekace ba mahaifiyarta ba. Ashe bashi kad'ai ne bayi kama da Umminsa ba (mahaifiyar shi.)

  "Sannu da zuwa bawan Allah" Mami ta fad'a tana nufo su cike da tsoro da fargaba.

   "Yauwa Mami" Afzal ya amsa. "Ina yini?" Ya gaisheta cike da ladabi had'e da durk'usawa kad'an. Ai gaisuwan da Mami bata amsa ba kenan ta shiga basa hak'uri.

  "Don Allah idan wani abun Baby tayi ma kayi hak'uri bawan Allah wallahi banida abun da zan iya baka banda hak'uri" tace ba alaman kwanciyan hankali a tattare da ita. Ido Amal ta juya cike da takaicin abinda Mami keyi gaban wannan maras mutuncin bawan Allah'n, taya zata tsaya tana basa hak'uri while shi ya kamata yayi hakan?

   Afzal ya bud'e baki zeyi magana kenan Amal ta riga sa "Wai ni Mami yaushe nace miki nayi mar laifi? Dubi fa, dubi k'afa nafa" tayi maganan tana miqar da k'afanta a hankula so Mami could see "Karya min k'afa yayi."

    "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Baby!" Mami tayi exclaiming tare da yin kan 'yar nata tana me zaunar da ita a hankali bisa wani benchin dake kusa tana mata sannu in the process.

   "Look Mami ni ban karya wa 'yarki k'afa ba don't listen to her" Cewar Afzal.

   "Wallahi ya karya" Amal tayi saurin fad'i tana katse Mami "Idan ba karya min k'afa yayi ba toh seya fad'i dalilin daya sa ban iya taka k'afan."

   "Yi shiru Baby na sannu ai ko baki fad'a ba gashi kumburin k'afarki ta nuna kin karye saidai kariya nawa ne?"

   "Kaman biyu ne inji likitan" ta fad'a bayan tasan sarai k'arya take. Se wani zum6uro baki take cike da shagwa6a a yayinda Mami ke ta mata sannu tana shafa k'afan a hankali.
   Shi de Afzal ya rasa nayi, ya rasa menene yayi yau Allah ya had'a sa da dramatic people kallan wad'annan, ace ba babba ba yaro? Hmm shide gado ba gwaninta ba. Da kalan uwa me d'aura wa k'arya gindi haka ai ko hannu Amal ta d'aga ta zagi mutum a kan layi baza'a ga laifin ta ba tunda gashi ba tare da bincike ba mahaifiyar nata ta hau ta zauna akan k'aryan da 'yar nata ta shirya na cewa an karya mata k'afa.

   "Sannu ko Baby bari Papinki ya dawo a yanka miki d'aya daga cikin kajin kiwon nan. A kariya biyun har kika iya kike taka k'afan? Sannu." Har anan bata yi ta kan Afzal dake tsaye duk mamaki yabi ya mamayesa ba.

   "Mami?" Ya kirata ganin wannan draman nasu bana k'arewa bane gashi kuma yana da k'arancin lokaci.

   "Tsaya tukuna bawan Allah in gama da 'yar tawa ita kad'ai Allah ya bani-"

  "Mami!" ya katse ta cike da rashin hak'uri, shi kansa besan lokacinda ya fusata har ya kira ta da tsiwa haka ba. Da mamaki both Mami da Amal suka juyo suna kallonsa, a yayinda zuciyan Amal ke raya mata itama ta miyar masa da masifan.

   "Kinga na farko ni ban karya wa 'yarki k'afa ba I admit I wasn't watching the road attentively na gauce akan hannuna na yo kanta na kuma bugeta and am dearly sorry" ya fayyace mata. "Amman ban karya mata k'afa ba" ya k'arisa.

  "Baka karya mata k'afa bafa kace? Ban gane ba, yo ko nufi kake kawai don ado likitan ya d'aure mata k'afar da bandeji?" Ta tambaya cike da mamaki tana kallon kumburarren k'afan Amal tare da kewayo da kallonta a gareshi, ba shakka akwai rainin hankali anan.

   "Ni ba abinda nake nufi ba kenan amman de kam ban karya wa 'yarki k'afa ba, targad'e ne ta samu tun achan kuma Dr'n ya sanar da ita hakan bansan dalilin da yasa tace miki kariya ne ba."

  "Hakane Baby?" Ta tambaya tana maido da kallonta akan Amal dake faman raba ido.

   "Mami har sekin tambayeta ne? Da girma na ne zan tsaya ina miki wasa da hankali? Kuma idan da har banida niyyan admitting laifin da nayi do you think zan bar duk abinda nakeyi in nemi har gidanku domin in baku hak'uri akan hak'urin dana ba ita Amal d'in? Har kuma in kaita asibiti, think please" Daga yadda yake magana za a san ransa ya soma 6aci kuma bako k'arya acikin duk abinda ya fad'a.

  "Hak'uri? Ni de baka ban hak'uri ba" cewar Amal tana murgud'a baki. "Allah ya karya min k'afa kar ki jisa Mami."

  "Baby kallen shin bawan Allahn nan karya miki k'afa yayi ko kuwa targad'en ce kamar yadda ya fad'i?"

   Ganin fa an ganota ta soma kame-kame "Toh ni ina zan sani ko had'a baki sukayi da likitan don ya rufa mai asiri-" bugi Mami ta kai mata a cinya interrupting her, wanda a sanadin hakan ta sa ihu.

   "Yanzu haka kawai kima bawan Allah sharri ya karya miki k'afa Baby? Shin yaushe zakiyi hankali?" Baki ta zumb'uro tana kukan munafirci a yayinda Mami ta juyo kan Afzal da yayi jugum yana kallon ikon Allah.

   "Bawan Allah don Allah kayi hak'uri wallahi haka take gagara da rashin ji toh wane akanta akayi wahayinsa."

   "Ba sekin fad'a ba naga hakan a tattare da ita" ya fad'a yana meyi wa Amal kallon rainin hankalin dayasa ta murgud'a mai baki. "So am here to say sorry and take full responsibility" ya numfasa "Ga magunanta nan" anan ya miqa wa Mami leathern inda ta amsa "Dr yace karku tada hankalinku she's going to be alright kuma gobe idan Allah ya kaimu zan dawo in maida ta asibitin don a sake dressing ankle natan kaman yadda likitan ya buk'ata. Za a cigaba da yin hakan na sati daga nan in shaa Allah k'afan zai warware." Kafin Mami da akayi ma bayani tayi magana Amal ta hau k'orafi.

   "Ni wallahi ban komawa asibitin" ta fad'a tana buga d'ayan k'afanta a k'asa stubbornly.

  "Rufa min baki do Allah!" Mami ta ce da ita amman still se gunguni takeyi dake sam bata tsoron idon Mami. "Allah sarki bawan Allah lallai ka cika d'an halas mun kuma gode sosai, ina me sake baka hak'uri kuma."

   "Ba komai Mami ya wuce nine da godiya."

   "Allah yima albarka Babana."

   "Ameen" ya amsa da murmushi kad'an.

   "Nace ba kar ka damu ba seka kuma dawowa bama anan tsallake gun wanzami zan kaita a sake duba k'afan nata gobe in shaa Allahu."

   "No Mami, I promised to take full responsibility so karki damu and here" ya fad'a yana ajiye ledojon a k'asa "Sakamakon hatsarin abubuwan da kika aiketa siya suka tarwatse so gasu I'm able to get some wad'anda ban samu ba kuma zan baku kud'in seku siya in kuka samu lokaci, I'm sorry" hannu ya zira a aljihun sa don ciro wallet nasa inda yaji wayam holy sh*t ashe ya baro sa acikin mota. "Excuse me please let me get my wallet."

    "Haba bawan Allah ai da ka bari, hakan ma mun gode wallahi ni na yafe sauran" fad'in Mami.

  "Ni ban yafe ba" cewar Amal wane da ita aka kasa, ko ta kanta Afzal beyi ba yayi saurin katse Mami dake shirin yima Amal fad'a "No Mami please I insist, ai hak'k'in kune."

   "Toh shikenan tunda kace haka mun gode" ta fad'a tare da kewayo da kallonta akan Amal "Ke tashi ki bi bayansa ba seya sake shigowa nan inba yayi sahu biyu tunda duk ke kika jawo komi" cewar Mami.

   "Taya ni na jawo? Ni na kaisa kad'eni?" Ta tambaya cike da rashin kunya.

   "Da bance kibar aiken ba se da yamma kika k'i?" Zata kuma magana Mami tayi yunk'urin gwa6e bakinta nan take tayi shiru. Afzal da yayi shiru yana kallon su ne ya nisanta yace, "Karki damu Mami, let her be."

   "A'a don Allah kar muyi haka da kai. "

  "Mami-"

   "Don Allah fa nace" hakan yasa yayi shiru.

  "Toh shikenan" ya fad'a a hankali.

  "Yauwa bari Baby ta bika seta amso kud'in tashi mana Baby" ta fad'a tana dawo da kallonta akan Baby dake faman zumbure-zumbure ko yunk'urin miqewa batayi ba. "Ko baki ji ni bane?"

   "Toh ai bazan iya tashi ba."

  "Uhn uhn fa Baby kin san ni."

  "Don kinga Papi bai nan ba? Allah ze dawo dashi kuma wallahi sena k'irga mai komi" ba don tana so ba ta shiga miqewa wanda k'arshe saida Mami ta taimaka mata, k'ingishi ta shigayi tana takawa a hankali. Murmushi Afzal yayi sannan ya shiga bin bayanta.

  "Toh gashi bawan Allah zaka tafi ban san sunanka ba." Kewayo wa yayi cike da ladabi sannan yace "Afzal."

  "Afzal" ta nanata "Sunan larabawa ga me k'iran su, masha Allah" ta fad'a acikin wasa. Murmusawa yayi sannan yayi mata sallama ya fice alokacin har Amal ta isa bakin k'ofa tana tsaye tana kallon yaran dake wasa akan layi.
   "Excuse me" yace da ita ganin tayi tsaye bakin k'ofan ba chance da ze wuce. Seda tayi muttering wasu kalamu chan k'asa iya jinta sannan taja gefe ya samu ya wuce. Bayan sa ta shiga bi sannan ta tsaya daga jikin wani bango a yayinda ya k'arisa gun motan nasa. Wallet d'in ya d'auko, dai-dai yazo bud'ewa kenan don sallamarta wayarsa dake inner aljihun suits jacket nasa ya shiga ringing. Ba tare da 6ata lokaci ba ya zaro, ganin Abba ke kira zuciyansa ya mugun har6awa yau ya shiga uku. Cike da fargaba ya d'aga sede kafin ya samu daman magana Abba ya riga sa.

   "Yanzu Afzal in kiraka sau biyu in ce maka ina neman ka as a matter of urgency shine har yanzu ban ganka ba? Ai ko bangon duniya kake yaci ace ka dawo war haka" daga yadda yake magana mutum zaisan ransa ya 6aci matuk'a ba shakka Abban nan nashi mutum ne mai gajan hak'uri.

   "Abba I'm so sorry-" katse sa Abba ya kuma yi  "Wallahi ban san ka da halin nan ba, bansan kuma meyasa kake hakan ba amman karka damu ba seka zo d'inba domin shi wanda yake neman ma maganan ma ya gaji da jiran ka ya tafi" daga fad'in haka ya katse wayan ba tare da ya basa daman magana ba. Hankalin Afzal ya mugun tashi, rabon shi da ya 6atawa Abba rai irin na yau ya juma, probably tunda yake yaro lokacin da bai gama gano darajan iyaye ba. Yau ina zaisa kansa? A kullum shi me ladabi ne game da umarnin Abba, a kullum Abba na alfahari dashi se gashi yau all because of wannan fitsararriya 'yar gudun hijirar ya 6atawa Abbansa rai to the extent da har Abba ya kashe waya a kansa abinda be ta6a yi ba. Yasani kafin Abba ya sauk'o ya soma mishi magana kuma se ranan da Allah ya nufa.

   Ranshi a murtuk'e ya bud'e wallet d'in be ma san iya adadin kud'in daya d'iba ba tsabaragen all he wanted at that moment was yaga kansa a gida ya samu daman bawa Abba hak'uri tun kafin lokaci ya k'ure.

  "Ke!" Ya daka mata tsawa wanda sanadin haka ta firgita. Tun da tasan kanta bayan wani PHE teacher'n su tun a JSS 3 ba wanda ya ta6a mata tsawa yakuma razana ta irin na yau. "Kinyi tsaye achan nine zan k'ariso miki da kud'in?" Ya jefa mata tambayar cike da tsiwa.

    "Malam dakata fa!" ta tsorata iya tsoro amman dogon bakinta baze barta tayi shiru ba "Haka kawai bazaka sauk'e min haushin da kakeji a ka ba, a dalilin meh? Don wani ya kiraka ya 6ata maka rai se ka hau huce zafin ka a kaina kana min masifa? Da ni nace ka kad'eni kokuwa ni nace ka kawo ni gida? Ra'ayin da ya saka yin all of that shi zai sa ka tako har nan ka bani kud'in da kace zaka baiwa Mami in kai mata" ta fad'a kai a tsaye ko tsoron yadda yake kallonta cike da haushi da tsana batayi. Duban time a wrist watch dake d'aure a hannunsa yayi ganin he is running out of time yasa shi fasa aikata abinda yayi niyyan mata in ba haka ba belt nasa yayi niyyan zara ya nad'a mata na jaki a gurin tunda a gidansu ba meyi mata hakan. K'arisawa spot da take tsayen yayi sede yarinyan naku ko motsawa batayi ba dukda chan k'asan zuciyarta kuwa ta gama tsorata. A duk tunaninta mari ze kai mata setaji ya damqo hannunta, damqan da tana iya rantsewa ba a ta6a mata irin sa ba ai bata san lokacin da ta shiga ihu ba. Ji tayi k'asusuwan ta suna k'ara, wannan wani irin k'arfi yake da shi? Toh ita kam ya agaza ya rufa mata asiri kafin ya karya mata d'an hannu, ace ga kariya ga targad'e? Bazata iya ba.

   "Naga alaman Allah ya had'aki da iyaye masu sanyin da ko tsawata miki basu iya yi as ko mey kikayi dai-dai ne a idansu kisani I'll not let you disrespect me and get away with it, bazan bar k'aramar k'waron da bata kai inyi immediate sibling da ita ba ta raina ni, ko ki iya bakinki ko na koya miki yin hakan, maras kunya kawai."

 Sosai idonta ya cika da k'walla don azaba, "Ni ka sake min hannu kuma kar ka sake sa min sunan iyaye cikin zancenka, musamman na Abba na saboda ya rasu" ta fad'a cike da k'arfin hali. Ganin fa baida niyyan sake ta tasa ihu "Mami!" A lokacin har hawayen na neman gangarowa. Se anan ya saketa cike da wulak'anci regardless of her condition, wanda da ace ba bango a kusa da ita data fad'i a k'asa. Hannunta yaja out of nowhere tare da tusa mata kud'in aciki sannan ya juya ya kama tafiya. Kafin ya isa gun mota har Amal ta zaro kud'in ta k'irga, dubu hud'u ta gani "Hey!" Ta danna mai kira amman yayi banza da ita se a karo na biyu, nan ma ba juyawa yayi ba tsayuwa kawai yayi, "Ce ma akayi Papi na ya rasa na ciyar damu ne ko na sha da zaka wani kama ka bada dubu hud'u na abinda be taka kara ya karya ba?" Se anan ya juyo yana kallonta ashe de dubu hud'u ya zara "Zan d'au dubu d'aya, ban sani ba ko canji ze rage amman idan har ya kasance hakan, I'll return your change for you ga sauran kud'in ka" nan ta zare dubu daga ciki tare da yin watsi da sauran a k'asa ta juya da k'ingishinta ta wuce layin gidansu leaving Afzal da baki wangalau a bud'e cike da mamaki, don shock k'wak'walwarsa tama kasa fahimtar dashi abinda wannan 'yar gudun hijirar ta masa. Ji yake as if ya cafko ta ya nad'a mata na jaki shin wannan ya iyayenta suka girmar da ita? Fitsara sekace 6era, besan na gida ba balle bak'o. Lallai ta guji had'uwansu, yanzu baiwa Abba hak'uri ne ke gabansa dako seta gommaci kid'a da karatu.


PAGE 03




_How can I turn you guys down when the love and devotion speaks this much???? Yanzu haka kuka k'i yarda a cigaba da posting RANA D'AYA after Ramadan? kaman maita harda masu cewa koda sau d'aya a sati ne ? nida mutane na se Allah but know that ina alfahari daku sosai sosai wallahi?. Though my schedule is tight, I'll still manage and squeeze time to type once in a week like you guys requested before Ramadan approaches, so here is chapter three. Juma'ah zuwa juma'ah zakuna samun post in shaa Allah, happy reading!❤️_



     Ta kai ga yankan lungun gidansu kenan sega Mami tafito sanye da mayafi "Ina zaki Mami?" Tayi saurin tambaya "Maggi zan siyo nan shagon Usmanu ashe ya k'are ban sani ba gashi har miya ya kusa nuna. Kiyi sauri kije ki kula min dashi dama na rage ichen seki k'ara" Mami ta sanar da ita.

    "Toh Mami ki dawo lafiya" ta amsata, da k'ingishinta ta shiga takawa amman ta tsaya chak sanadin kiran da Mami tayi mata, hakan yasata kewayowa "Na'am?" Ta amsa.

  "Nace nawa Afzal ya baki ne?" Nan fa oganniyan taku ta shiga kame-kame tana ta6e baki. "Ya haka? Tambaya fa nike miki, nawa ya baki?"

  "Dubu d'aya" ta fad'a chan k'asa-k'asa.

  "Har dubu? Mu gani" ta buk'aceta, nan Amal ta d'ago ta nuna mata. "Yo shine kika tsaya kina rarraba ido kaman 6eran da aka kama yana sata?"

  "Uhnmmm ni zan wuce kar miyan ya k'one" ta fad'a tana dodging had'a ido da Mami tasan tabbas idan suka cigaba da had'a ido Mami na iya gano k'arya take, bata kai ga taka k'afanta ba Mami ta kira sunanta "Baby!" Chak ta tsaya zuciyar ta na har6awa.
   "Na'am?"
  "Juyo ki kallen" saidai ta kasa, seda ta d'au tsawon lokaci sannan ta juyon. "Fad'a min me kikayi? Tabbas babu gaskia a tattare da ke fad'i me kikayi."

  "Mami me kuwa zanyi? Ni shikenan kullum kina cikin zargi na" ta zum6uro baki.

   "Munafuka bazaki bar k'arerayin nan naki da kike tasowa dasu ba ko? Nace fad'a min me kikayi wallahi idan kika bari har Afzal yazo gobe na tambayesa naji gaskiya daga bakinsa jikinki zai gaya miki."

  "Wai duka na zakiyi? Ai Papi baze bar ki ba" da sauri ta buge bakinta tuna Papi bayi gida yayi tafiya.

  "Sam bazan dake kiba amman inada wanda ze daka min ke kaman ganga, Malam Bunu na islamiyyan ku zan kai mai k'arar ki nacewa har yanzu baki daina k'aryan banzan nan ba."

  "A'a don Allah Mami kiyi hak'uri wallahi dorinan shi me baki uku ne na tuba."

   "Yauwa fad'an me kikayi toh."

  "Ki rantse baza kimin komi ba."

  "Sa'ar kice ni? Zaki gayan ne kokuwa?"

 "Mami dan Allah kiyi hak'uri."

  "D'aya" Mami ta shiga k'irge "Biyu-"

   "Zan fad'a zan fad'a" Amal ta katseta a rikice. "Dubu hud'u ya bada shine na miyar masa da sauran saboda kudin abubuwan da suka rage basu kai hakan ba."

   "Oh! Amman 'yar nan anyi wawiya wallahi shi daya k'irga kud'in ya baki besan me yakeyi bane kome? Ai da niyyan kyautatawa ya bada."

   "Toh-" ta fara magana.

  "Rufa min baki da Allah!" Mami ta katseta cike da takaici "Yanzu fisabilillahi Allah ya kawo mana arziki har gida ki miyar da hannun kyauta baya Baby? Meye muke dashi da zaki miyar masa da d'umbun kud'i haka iyye?" Don takaici Mami ji take kaman ta mauje ta, tana gwada yunk'urin hakan kuwa Amal tasa ihu gashi ba halin gudu k'afarta baze barta ba, dan tausayi de kawai Mami ta barta. "Shin ya amshi kud'in yanzu?"

  "Eh mana tun yaushe ma."

  "K'arya kike nace k'arya kike. Fa bazan haifeki ki tsaya kina raina min hankali ba nace ya amshi kud'in da kika miyar masa ko ya?"

  "Ya kar6a..." hannu Mami ta d'aga kaman zata doketa "Nace ya kar6a ko be kar6a ba?" Zata kuma wani k'aryan Mami tayi kaman zata sauk'e mata mari, tuni ta shiga bada asalin rahoton "Wallahi be kar6a ba k'arya nakeyi."

   "Nasan za ayi hakan ai, ki kiyaye nifa Baby! Ki kiyayeni ina fad'a miki wallahi ranan da nace zan tarke ki a lungu bazaki ji dadi ba. Yanzu ina kud'in tunda kince be amsa ba?"

   Chan k'asa-k'asa tana me zum6uro baki tace "Na yasar mai a k'asa da yak'i kar6a."

  "Kud'in kika yasar?!" Tas kukejin sauqan mari a bayan Amal daya sata sakan wani irin rikicaccen ihu bawai don marin yayi zafin da zaisa ta yin kalan ihun bane sai don shagwa6a irin nata. "Amman yau na tabbata kina da ciwon hauka maza wuce muje ki ibo kud'in kuma Allah yasa muje har 'yan tsince-tsince sun d'auke kiga abinda zan gwada miki a gidan nan yau, dama gashi Papin ki bayi nan balle ya shiga miki." Kukan munafurci kaman yadda ta saba ta shiga yi tana me maquro d'an k'wallan daya ciko mata a ido. Haka Mami ta sata gaba da k'ingishin nata suka k'arisa dai-dai spot d'inda abin ya faru wanda a dai-dai lokacin wasu almajirai suke k'ok'arin d'iban kud'in wani ihu Mami tasa "Karku ta6a zaku 6ace" ai kafin tace pim ta nemi yaran ta rasa tasan sarai idan ba hakan tace ba kwashe kud'in zasuyi su gudu su barta da innalillahi. Da sauri taje ta tattara dubu ukun cus ta k'irga, wani hamdala ta saki sannan ta amshe na hannun Amal dake faman murza idonta tun d'azun. "Maza wuce gida kuma Allah yasa miyan ya k'one kiga abinda zan miki."

  "Toh ni Allah ne da zan hana miyan k'onewa?" Ta tambaya tana zum6uro baki.

  "Zan buge bakin nan fah" da sauri ta sa hannu ta toshe bakin nata kafin hannun Mami yayi landing a kai "Maras kunya kawai wuce gida saura kuma ki tsaya hira da Azee a hanya kiga abinda zan gwada miki mutum se shegen almubazaranci." Tana kaiwa nan ta yanki kwanan shagon Usama, itama Amal a hankali ta shiga takawa da k'ingishin har ta isa gida.

   Saidai wani hanzari ba gudu ba, takai gab da shiga ciki kenan sega k'awarta Azee wacce Mami ta ja mata kunne akanta, se ince kusan rashin jinsu d'aya saidai kawai ita Azee a gaban Babanta take hakan yasa tafi Amal jin tsoron ido da bakin mutum unlike Amal.

  "K'awas ya na ganki da bandeji waine a k'afa?" Tayi saurin tambaya tana doso ta, idonta na akan k'afan Amal.

   "Hmm kede K'awa bari kawai wani reckless bawan Allah yau Allah ya had'ani dashi, ina zaman zama na yayo kaina da mota ya bigeni."

  "Subhanallah shine baki sanar dani ba? Sannu ya k'afan toh?" Nan suka hau hira Amal ko gabad'aya ta mance da miyan da Mami tace ta kula dashi.



****       *****        ******       *******

   Isan Afzal gida keda wuya as tun da ya hau tuk'in yake tunanin abinda Amal tayi masa, tafasa ransa yake sosai tabbas baze bari ta gudu unpunished for what she did ba, komin ji da dad'ewa seya rama. She wants to play games? Then she got it. Yana isa gaban wata makekiyar gida da bature ke kira da mansion ya yanki corner inda ya tsaya dai-dai gaban fancy iron gate d'in. Securities biyu ne masu uniform tsaye a bakin k'ofan suna gadi, sannu da zuwa suka mar sannan suka bud'e gate d'in. Tafiya kad'an yayi ya kuma cin karo da wani iron gate d'in nan ma securities biyu ke guarding wajen bayan sun mar sannu da zuwa suka bud'e masa giving him a safe passage. Tafiya yake through the driveway a hankali exploring the beauty of the mansion. A sannu a sannu ya k'arisa last parking lot meh glassy display sannan yasa motarsa ciki ya yi parking ya fito. Makekiyar flat da me bada labari bata san daga ina zata soma labarta saba Afzal ya wuce ciki. Sashin fari ya shiga wanda ko ba a sanar da mutum ba zai san na mai gidan ne wato Abbansa. Knocking yayi bisa entrance door d'in sannan ya bud'e tare da sa kai. Makekiyar parlour ne da aka k'ayatasa da abubuwa masu tsada masu d'aukan hankalin d'an Adam. Komi aciki white, golden and red ne banda cinema'n dake manne jikin bango, ga ko ina tsaf ko dust baka gani illa k'amshin turaren wutan dake tashi. 

   "Sannu da zuwa Prince" wani na miji dake sanye da uniform ya fad'a yana doso Afzal da yayi zaune bisa one of the various golden X red royal chairs.

   "Thank you Abba na gida?" Ya tambayesa.

  "Eh yana d'akinsa" ya basa amsa a takaice.

  "Good, help me speak with him please."

  "Yes sir" ya amsa. Da fad'an haka ya juya ya shiga ciki ta wani k'ofa, yakai tsawon minti biyu sannan ya dawo. "I'm sorry amma kaman Master bai da shirin ganinka" mutumin ya sanar dashi. Dama Afzal yasan za'ayi hakan ba kowa yake blaming ba illa Amal ji yake kaman idan ya kamata karya saketa se ta daina numfashi, 'yar gudun hijira kawai ya furta a ransa. "Please tell him I'm sorry yayi hak'uri ya fito" ya fad'a da damuwa karara bayyane a fuskansa.

  "I did amman baida niyyan fitowan ne, yak'i nakega idan Hajiya tamar magana zai sauk'o, I'm sorry excuse me" daga fad'in haka yayi kan dining table inda ya cigaba da goge-gogen da yakeyi. Ganin fa zaman da yakeyi a gun baze haifar masa da komi ba ya miqe ya fita. Side na Ummi ya nufa direct don neman taimakonta. Kaman kullum seda ya ciro hanky daga aljihunsa ya toshe hancinsa sannan ya k'arisa ciki. Ko bai tambaya ba yasan yau ma da akwai hayak'in kullum d'innan, anayin abu dai-dai amman ita Ummi idan batayi over ba bata jin dad'i. Site nata kullum yana cikin hayak'i da k'amshin turaren wuta. Had'add'en parlourn ta daya k'unshi combination na white, dark and light purple ya wuce making it to her room. Knocking yayi bayan ta amsa da 'yes' ya bud'e ya shiga, miqe akan gado da zani d'aure a k'irjinta ya tarar da ita tayi ruf da ciki a yayinda 'yan mata biyu ke mata tausa, hayaqin d'akin is indescribable ba shakka yau d'inma gyaran jiki ake mata. Shi yarasa amfanin wannan abu, shin ta gyara jikin nata takai ina? Abba deh ba saurayi bane yanzu haka zalika itama ba budurwa bace. Murmushi kad'an ya saki tuna reaction nata anytime idan yace mata ita ba yarinya bace yanzu ta tsufa. Shi de ya rasa ta ina ta zama yarinya, mutumin da ya kusan approaching 50 kam ai ya manyanta. "Waye ne?" Ta tambaya kasancewar kanta na facing opposite direction na k'ofar. Kafin Afzal ya amsa 'yan mata biyun suka rigasa "Prince ne."

  "Oyoyo My Prince" ta fad'a tana k'ok'arin zama a yayinda 'yan mata biyun dake kanta suka ja gefe "Sannu da dawowa Prince" kai kawai ya musu nodding.

  "Toh kuma kayi tsaye gun ka k'ariso ciki mana" Ummi ta fad'a tana janyo mayafi tare da lullu6e jikinta. Kyakkyawar mace ce me uban kyawun jiki wanda idan ba wai an fad'i shekarunta bane mutum baze ta6a sanin takai hamsin ba kaman yadda Afzal ya fad'a. Irin skin nata ake kira da kalan wankan tarwad'a gashi kuwa daya samu gyara se wani glowing yake like gold, ga k'iban nan tubarkallah nama du sun nannad'u a wuya. Kallo d'ai za ayi mata asan matar alhaji ce.

   Tana da kyau sosai haka Afzal ma amman abun mamaki sam mutum baze ce mahaifiyar sa ceba saboda rashin kaman su, sam kyawunsu be zo d'aya ba. Afzal yafita haske sosai wasu sukan ce mar fari ma, ita kuwa tafi sa dala-dalan idanu da kuma dogon hanci. Hancinsa na nan shiba dogo ba shiba gajere ba gashi nan de k'arami acikin oval shaped face nasa.

     Da hannunsa yayi mata nuni cewa hayak'in d'akin is unconducive ya mar yawa.

  "Kai deh da ace kanada asthma da turaren wutan gabad'aya zaka hanamu yi a gidan nan toh ya akayi?"

  "Ummi please mana! I want to talk to you" ya fad'a tare da had'e giransa, hancinsa kuwa har a yanzun na toshe da handkerchief.

  "Toh ya kakeson inyi? Bawai kaman ina da k'arfin koran hayak'in nan a lokaci guda bane."

  "Toh kizo muje parlour concentration d'in is less a chan."

  "Halan baka ka gyaran jiki ake yimin ba."

  "Fisabilillahi kullum gyaran jiki, gyaran jiki ko amarya albarka" har anan be sauk'e hanky'n daya toshe hancinsa dashi ba.

  "Jimin d'a!" Tayi exclaiming full of wonder. "Da meye ce inba amaryar ba? Naga da gyaran jikin ne na iya na karkato da hankalin Abbanka kaga har yau bemun kishiya ba."

  "Toh whatever ni ki fito muyi magana."

  "Wai me ne da bazaka iya fad'ansa daga bakin k'ofar ba? Aure zakayi? Kuma ka bar min k'ofa a bud'e tun d'azu ko bakasan hayak'in fita yake ba?"

  "Exactly ki fito muje parlour" ganin batada niyyan motsawa yace da 'yan matan suyi excusing nasu ba gardama suka fita suka basu waje, ita de Ummi binsa da kallo kawai take ko mey yake da shirin yi? K'arisowa cikin d'akin yayi da dogayen k'afafunsa tare da tsayuwa dab a gabanta sannan ya shiga janta. "Ummi dan Allah ki tashi kin de san kina da nauyi."

  "God help me" ta fad'a sannan ta miqe suka fito parlourn inda suka zauna akan two seater side-to-side. "What is it?" Ta tambayesa.

  "It's Abba he's mad at me" ya fad'a a takaice.

   "Toh kuma har wani sabon abu ne wannan? Kade san Abbanka da zafin fushi da zuciya sekace kai anan."

  "Ummi please!" Ya fad'a tare da buga k'afansa a k'asa. 

  "Okay, okay toh meh dalilin?" Labarin duk abinda ya faru ya bata be bar komi ba. Numfasa tayi bayan da ta gama sauraronsa tace, "Toh Allah kiyaye aukuwan na gaba amman meyasa ba ka sanar dashi abinda ya farun ba?"

   "Yak'i ma ya saurareni kashe wayan yayi gabad'aya kuma yanzu ma daga site nasa nake, nasa Micheal ya mar magana still yak'i fitowa."

  "Toh ni yanzu me kakeso in maka?"

  "Like what a question" ya fad'a tare da juya idanunsa da suke nan farare k'al. "Kiyi mishi magana of course, he always listens to you."

   "Nifa banason kana jawo ni cikin matsalarku haka kawai kazo kasa nima yak'i cin abincina na sati."

  "Ummi please kinsan Abba be iya yin fushi da mutum ba yanzu ba k'aramin aikin sa neba ya daina min magana for a whole week!"

   "Toh ai nima abinda nake gudu kenan kar yabar cin abincina na sati."

   "Toh yau aka fara hakan ne?" Ma ta 6ata mar rai. Ai da k'yar idan Abba ya ta6a jera watanni biyu yana cin abincin Ummi ba tare da yayi fushi ba. Haka yake da an 6ata mar rai seya d'aga k'afa wa mutum, abun takaicin kuwa shine se ya nemi abinda zai fi damun mutum sannan yayi using nasa against that person. Se kuma shi gado ba gwaninta ba, shima Afzal haka yake da shegen zuciya da fushin nan irin na Abbansa ko fad'a sukayi da Ummi seya d'aga k'afa daga cin abincinta da kuma yi mata magana in banda gaisuwa ba abinda ke had'asu har se ya sauqo, shima gaisuwan don ya zamo masa dole ne. Abinda ke bawa Ummi mamaki shine bayan shi kansa Afzal d'in ya iya ma mutane fushi meye a ciki don Abbansa yayi masa?

   "Aww abinda zaka ce kenan? Ashe dai ba dad'i, ashe idan aka maka haka bazaka ji dad'i ba amman kake ma mutane, ai halin Abban naka da kai seku ta fama kaga barin je in k'arisa gyaran jikin nan yau Abbanka yace zamu fita date kaga ko zama be kama ni ba."

 "Ummi please talk to him ni wallahi abinda yasa hankalina ya tashi ma saboda yace akwai abinda yake son sanar dani ne kuma daga yadda yake maganar nasan magana ce me muhimmanci."

  "Oh! Dam-" se kuma tayi shiru tuna yadda Abba ya jaddada mata cewa no matter what kan kar ta kuskura ta sanar da Afzal halin da ake ciki yafi son ya mar maganan da kansa.

  "Dama meh?" Yayi saurin tambayarta.

  "Babu bance komai ba bari in shiga daga ciki." Kafin ta kai ga miqewa Afzal ya rik'o hannunta restricting her. "Ya haka Prince?"

  "Ummi there is something you're not telling me" ya fad'a yana mata kallon cikin ido don tabbatar da abinda ya fad'a. 

  "Kai de da assumption se a hankali ni nace wani abu ne? Sakeni du Allah."

  "Ummi please tell me mene Abba keson sanar dani?"

  "Wallahi prince seda Abbanka ya ja min kunne kar na fad'a maka don't worry he is planning on telling you himself."

  "Taya ze fad'an bayan yamin fushi?"

  "Toh ka kwantar da hankalinka zan masa magana, zan mishi bayanin komai anjima idan mun fita in shaa Allah ze sauk'o kar ka damu kaji my handsome Baby?" Ta k'are zancen tare da aza hannunta akan ha6ansa tana mai wasa sekace wani jariri. Hannun nata ya cire yana zum6uro baki ashe de shima ya iya shagwa6an shine yake ma Amal kallon bakwai saura kwata don itama tayi wa Maminta bayan gashi babba dashi shima yana yi.

   "Oww had'a min rai zakayi? Shikenan sena fasa basa hak'urin" ta fad'a da gan-gam.

   "A'a please don't ni ba 6ata miki rai nake ba" yasa murmushin dole. Murmushin ta mayar masa tare da pecking nasa a kumatu "An kai maka abincinka a site naka ko zakaci anan?"

  "Nah am full" yayi maganan yana aza hannunsa kan flat muscled abdomen nashi.

  "Toh sallah fa kayi?"

 "Zanyi idan na shiga" ya fad'a tare da miqewa.

  "Alright I love you."

  "I love you too" ya amsa sannan ya kama hanya ya fita tare da nufan site nasa wanda shi kuma kominsa is in black and white. Abinda ya kama daga parlournsa, dining table, d'aki, closet, toilet and bathroom. Kitchen ne kawai pure white. Bathroom ya fad'a yayi alwala sannan yayi sallah ya rage kayan jikinsa tare da barin shorts da singlet zalla. Akan gado ya miqe tare da k'ure AC'n d'akin, ragowan aikin daya rage mar a office yakeson k'arisawa amman ji yayi ya gaji gabad'aya ko d'aga yatsa bazai iya ba don haka ya jawo wayansa daga kan side table tare da shiga Twitter inda ya shiga bin feeds nasa, yana gamawa dashi ya shiga Instagram se Snapchat, k'arshe ya leqa whatsapp wanda daga nan bacci yayi awon gaba dashi.

   \•\•\•\•\ A cikin City star.

    Zaune Abba da Ummi suke a filin da Abba yayi reserving musu. Ummi ansha kyau kaman ba gobe se k'amshi take. Tana sanye ne da royal blue lace me torches d'in yellow wanda ko ba'a fad'a ba mutum na sani kaya ne me bala'in tsada ga wani arnen d'inkin da akayi mishi wanda ya mugun kar6arta. "Kin ganki kuwa Baby? You're looking so takeaway" Abba dake sanye da sky blue half jamper ya sanar da ita yana mey mata murmushin sosa zuciya. 

  "Kai My Dear kai de bazaka dena flattering d'ina ba ko?" Ta fad'a cike da kunya tana blushing.

  "Ai kema kin san gaskia nake fad'i gashi har yanzu koda wasa 'yan matan waje sun kasa kawar min da hankali daga gareki, ba don komi ba kuwa se don wannan kwalliya, gyaran jiki da son k'amshin naki, keep it up."

  "Kai My Dear toh nagode in shaa Allahu kuma zan cigaba, amman kaima bakaga yadda kayi kyau bafa ai nasha fad'a maka half jumper suna ma kyau kak'i ji na."

  "Na gano hakan nima yanzu shiyasa kika ga na sanya yau." Hira jifa-jifa suka cigaba dayi har izuwa lokacin da orders nasu suka iso. Cike da k'asaita suka shiga ci suna hirar jifa-jifan har yanzu. Sun kusa gamawa Ummi tayi gyaran murya "My Dear?"

  "Na'am?" ya amsa tare da d'ago kansa yana kallonta cike da soyayya sai kace yau ya soma sata acikin idanunsa.

  "D'azu Prince yazo ya sameni" ta tsaya deliberately don jin mey zaice. Shi kuwa tunda yaji ta ambaci 'Prince' yaji yayi losing appetite nasa ma gabad'aya. "Ya da tura plate naka gefe kuma My Dear? Kode na fad'a wani abu ne?" Tayi saurin tambaya.

  "Na k'oshi" ya fad'a yana kawar da kansa yana me kallon gefe.

  "Dan Allah kayi hak'uri nayi shiru barin sake cewa komi ba amman ci abincin kasan banason kana kwana da yunwa yi hak'uri" ta hau lalashinsa, cike da dabara ta mayar masa da plate d'in gabansa da k'yar ya yarda ya cigaba da ci seda ta tabbata ya k'oshi sannan tace, "My Dear kamar hak'uri don Allah Prince yaro ne kuma fushinka a gareshi babban tashin hankali ne wallahi, baka ga yadda ya shigo site d'ina ba d'azu cike da tashin hankali bayan yayi ma Micheal magana daya maka sallama kak'i fitowa dan Allah ka sassauta masa."

   "Hmm Hajiya Mariam kenan, shin ya sanar dake abinda yayi min?" Ya tambayeta "Ya fad'a miki sau biyu ina kiransa bai d'agawa? Bayan da na samu ya d'aga kuma yace min meeting suke inyi hak'uri and I agreed saboda Prince be cika min k'arya ba sede inyi ma yaro jiran duniya da Baban yarinyan nan amman yak'i zuwa, wannan abin kunyan dame yayi kama? Haka mutumin nan ya gaji da jira ya tafi."

   "Bance yayi dai-dai ba amman da kayi mar uzuri My Dear accident yayi encountering wanda daba don Allah ya tsagaita ba da sede a kiraka ace maka kazo ka d'au gawan d'anka."

  "Haka yace miki?"

  "Yes My Dear and ba k'arya yake ba sanin kanka ne Prince bai cika k'arya ba se idan ta kama so I believed him."

  "Allah kare aukuwan na gaba" kad'ai yace.

  "Ameen ka hak'uran?"

  "Da hak'uri na da rashinsa ai du d'aya ne."

  "Taya ya zamo d'aya kuma My Dear? Idan har ka hak'ura muna isa gida ka kirasa ka mar maganan nan da kakeson yi mar ko ze d'an samu peace of mind please." Murmusawa yayi cike da k'asaita yadda manyan alhazai keyi.

   "Hajiya Mariam you're a blessing to this family, a da kafin in aureki ban zata zan iya sake walwala ba a duniyan nan, na d'au bayan rasuwan Fateemah bazan sake tsintan kaina a cikin kalan farin ciki da walwalan da nake ciki ba a yau saidai tun da akayi mana aure kika canza dukannin wad'annan abubuwa.  Ke ce sanadin duk wani walwala da farin ciki da nida d'a na muke ciki a yau, you mended my broken heart. Hajiya Mariam bakida burin dayafi kiga our family stays together and happy yau nasan duk inda Fateemah (asalin mahaifiyar Afzal, yar Mariam wacce suke uwa d'aya una d'aya. Ta rasu ne bayan sunan Afzal da kwana biyu sanadin breast cancer) take tana alfahari dake, kin so Prince tamkar d'an da kika haifa."

   "Dear kenan" ta murmusa cike da jin dad'in wannan kalamai daga bakin masoyinta. "Ai d'an 'yar uwata tamkar d'a na yake so kadena min godiya banida kaman ka da Prince a duniyan nan. Kuma a kullum ina godewa Allah daya bani ikon farinta maka da Prince, addu'a na kuwa baifin Allah hore mana dogon rai mai albarka in cigaba da kula daku ita kuma marigayiya Allah ya cigaba da kai Rahama kabarin ta."

   "Ameen Hajiya Mariam ta" ya amsa a yayinda memories da sukayi sharing da marigayiya suka shiga dawo masa.

  "Zaka mar maganan idan mun koma?"

  "Queen d'ina ta sa baki ai dole na."

  "Kai amma naji dad'i a ringa ma Prince sassauci please kasan yaro ne."

  "Ke kuma ki cigaba da shagaltasa  kinji ba?" Dariya kalan na manyan mata ta saki sannan ta zuk'e cocktail drink da take rik'e dashi. Hira kad'an suka ta6a sannan driver ya dawo dasu gida. Waya Abba yama Afzal akan yazo ya samesa a site nasa yanzu, alokacin Afzal na zaune a parlour yana playing game. Take ya kashe ya mik'e tare da zira farar jallabiyansa daya rataya jikin hanger sannan ya fito. Knocking yayi aka amsa sannan ya shiga, Abba da Ummi ya tarar akan two seater suna zaune looking so takeaway da alama yanzu dawowansu. Besan ya rayuwarsa zata kasance ba without these two: they simply complete him and he loves them so much. K'arisawa yayi ya durk'usa a k'asa tare da gaishe da Abba cike da ladabi da kuma yiwa Ummi sannu da dawowa.


PAGE 04



   "Ashe abinda ya faru kenan toh Allah kare aukuwan na gaba" fad'in Abba.

  "Ameen Abba thank you" ya amsa a nitse. Numfashi me nauyi Abba ya fisga sannan yace, "I'm sorry for my outburst on you, yaci ace na baka dama kayi min bayanin abinda ya faru kafin in yanke hukunci."

  "Ba komai Abba ni ya kamata in baka hak'uri I'm sorry in shaa Allah hakan baze k'ara faruwa ba" ya amsa cike da girmamawa da kansa a sunkuye.

   "Masha Allah, Dama Alhj Abdallah ne keson ganinka."
  Alhj Abdallah? Afzal ya nanata a ransa, wani Alhj Abdallah d'aya? And saboda meh?

  "Alhj Abdallah Abban Nazeefah" Abba ya sake fad'a ganin kaman ya jefa d'an nasa cikin duhu.

  "Ohh!" yayi exclaiming se yanzu ya fahimci wa Abba ke nufi. Alhj Abdallah Abban Nazeefah wanda ya kasance aminin Abba kuma second neighbour'n su, gida d'aya ne a tsakanin su. "Abba ina fatan lafiya dai ko?" Ya tambaya a takaice.

  "Eh toh it depends, kafin nan ina son muyi wata magana da kai Prince shin ka nada tsayayyiya kuwa?" Zuciyarsa yaji ya mugun har6a bade aure Abba ke shirin masa ba don kuwa be shirya ba, sam ba mace d'ayan da ta ta6a yimasa acikin jerin 'yan matan da Allah ke had'asa dasu. To cut the story short, shi baida ko budurwa d'aya ma balle ace ya cire tsayayyiya a cikin su. Ko da yake London karatu 'yan mata ke binsa and not the other way round, kuma koda wasa be ta6a saurara masu ba haka zalika da ya dawo Nigeria ma yanzu, kusan a kullum se 'yan mata sunzo gunshi a office bayan wanda ke binsa har gida. A sanadin hakan ya hana secretary'n shi barin kowa cikin office nasa in ba wanda ya sanar da ita da zuwan su ba.

  "Kayi shiru ko kafi son ku tattauna da Umminka ne tukuna?" Fad'in Abba jin shirun yayi yawa.

  "A'a Abba ba abin tattaunawa don a gaskiya banida tsayayyiya" ya basa takaicaccen amsa bayan nazarin daya samu yayi.

  "Toh Alhamdulillah" Abba ya saki hamdala wanda ya d'aure wa Afzal kai. Meh hakan ke nufi? Kafin ya kawo wani tunanin a ransa Abba ya cigaba, "Dama Alhj Abdallah ne ke tunanin had'a ka da 'yarsa Nazeefah" wani irin mumunan buguwa zuciyan Afzal yayi wanda sanadin hakan yaji zazzafan ciwon kai na neman afka masa.

  "Aure fa kenan Abba?" Ya tambaya cike da mamaki.

  "Yes Prince aure kuma kaga jifa yazo dai-dai da zama kenan tunda kace baka da tsayayyiya." Holy crap! Ji yayi kaman ya kashe kansa domin haushi, meyasa bema Abba k'arya yace mar da akwai tsayayyiyar ba a farko? But he can't blame himself saboda baida masaniya akan wannan zance Abba ke shirin sanar dashi. In da kuma k'aryan yayi yace yanada tsayayyiyar and Abba ya buk'acesa da yayi introducing nata ya zeyi? Meyasa Ummi bata sanar dashi wannan ne maganar da Abba ke shirin sanar dashi ba? Nazeefah fah? Wancan fand'ararriyar yarinyan da sama da friends nasa uku sunyi dating nata. 'Yar karamar yarinya amman se shegen rawan kai da falli, idan za'a k'irga samarukan cikin Maiduguri masu ji da kansu toh d'add'aiku ne basu fita da ita ba sam batada kamun kai ga d'an banzan rainin da take ji dashi a takaice de ya tsaneta. Meyasa Abba ze yarda da k'udurin abokin nan nasa? Meyasa ze yarda ya bada only son nasa wa 'yar da batada ko kamun kai? He need answers.

   "Prince kayi shiru" fad'in Abba sede har yanzu Afzal besan da wani bakin zai soma magana ba couple with the fact that baida ra'ayin aure ko kad'an yanzu. For crying out loud he's just 25 years old ina laifin abar shi yakai koda 30 ne. "Afzal?" Fad'in Abba for second time.

  "Nnn... na'am Abba" yayi stuttering.

  "Bakace komai ba" ya sake ce dashi.

  "Abba bansan me zance ba, Abba yarinyan can batada kamun kai dan Allah kar ka amince da wannan k'udiri" ya fad'a cike da tashin hankali.

  "Tabbas ba k'arya acikin zancen ka Prince, Nazeefah tayi zara ta fi k'arfin iyayenta kullum complain da Abbanta ke min kenan. Amman idan ka duba, rashin kamun kan nata ne dalilin da yasa Abban nata ke son aurar da ita so she can change her ways. Sanin kanka ne Alhj Abdallah d'an boko ne aurar da yaro at a very tender age sam baya d'aya daga cikin tsarinsa, dalili ne ya kawo hakan kuma kaf cikin yaran abokansa tare da ni amininsa ba wanda yaga yayi masa ya kuma yaba da hankali da tarbiyyarsa kaman kai Afzal, ka gane amincewa da wannan aure kaman yin jihadi ne. Wata k'il idan akayi mata aure zata canza wannan gur6a66iyar rayuwar data d'au wa kanta" Abba yayi concluding.

  "Abba ni kuma fah? Ban shirya yin aure yanzu ba, ban ta6a kawo tunanin aure ba a nan kusa, Abba please don't give me out" ya fad'a a maraice.

   "Kayi hak'uri Afzal am not trying to give you out nasan wannan babban abu nake nema daga gareka shiyasa naso muyi maganan as father and son insan meye point of view naka, idan har baka son yarinyar kuma baka tunanin ko a nan gaba zaka ita yin hakan, fine bazan yi maka auran dole ba. Kai kad'ai Allah yabani Afzal and da sani na bazan ta6a yanke hukuncin da zai cutar da kai ba, ina sonka fiye da duk wani mahaluk'i a duniyan nan. Sanin mune nan kaf yarinyan nan Nazeefah bata kai ta cutar da kai ba in kuwa har zatayi hakan toh wallahi bazan ma bari a yi nisa da zancen nan ba. Da tunda mahaifinta ya tunkare ni da maganar zan ja masa layi but we all know bata kai tayi ma wani abun ba. Afzal I've known Alhj Abdallah for a very long time, tun ina masters dina. Da nauyi Afzal in ba haka ba da zan koma in sanar dashi cewa lallai-lallai kai baka amince da wannan k'udiri ba, bazan bari a cutar min da kai ba Afzal. I'll appreciate it if you'll reconsider your decision amman idan har kai kaga you can't find it in your heart to love that girl zanyi iya k'ok'ari na in fahimtar da shi abokin nawa."

    A hankali maganganun Abba suke shiga jikin Afzal suna tasiri. Kaman yadda Abba ya nuna cewa rashin halacci ne ga abokinsa idan har bai cika masa wannan buri ba shima Afzal haka yake gani. Gani yake idan har be bawa Abbansa goyin baya ba toh rashin kyautatawa ne why because tun zaman shi da Abba wannan ne karo na farko Abba ke neman abu a gurinshi da ya kuma nuna muhimmancinsa haka. Tabbas auren Nazeefah baze kashe sa ba toh why can't he sacrifice his happiness for his father's??

  Ya d'au tsawon lokaci yana nazari amman ya kasa deciding akan komai, ji yayi k'wak'walwarsa ta toshe gabad'aya, a sannu a sannu ya d'ago kansa dake dafe tun d'azu ya shiga magana a hankali "Tabbas k'in amincewa da k'udurin Alhj Abdallah rashin halacci ne a gareka Abba kamar yadda nima rashin baka goyin baya yake rashin kyautatawa a matsayina na d'anka. Moreover, koda ni ne na tsinci kaina a cikin wannan halin da kake ciki I would do thesame" ya tsaya. Sosai Abba yaji dad'in kalamun nan da suke fitowa daga bakin Afzal. A kullum godiyanshi kenan ga Allah na basa d'a mai hankali mai kuma tunani kaman Afzal wanda yake gudun b'acin ransa wane aikata sa6o wa ubangijinsa.
   A hankali Afzal ya shiga magana "sai dai-" wanda Abba yayi saurin katse sa a nitse.

   "Karka damu Prince ba wai don ka auri yarinyan nan hakan na nufin nan a gaba idan Allah ya had'a ka da wacce kakeso bazaka iya auranta bane wallahi ni ko bayan wata d'aya da auran naku ne ka kawo min wacce kakeso I'll respect your decision in aura maka ita kuma ba abinda Nazeefah ko iyayenta suka isa suyi da hakan, you're a husband to four wives, all I'm asking is kayi hak'uri ka amince da k'udurin mahaifin 'yar nan."

  "Abba..." ido Ummi ta masa don haka yayi shiru.

  "Ba seka amince right away ba Prince, take as long as you want to make up your mind I shall respect every decision you take fata na kawai zakayi considering wannan situation, kasani k'in amincewar ka ga auran 'yar nan kaman tozartani ne a idon amini na da kuma duk wani mutumin da labarin nan ya iske sa. Kaje na sallameka Allah yima albarka, thank you for your time."

  "Toh Abba ameen, seda safe Ummi goodnight" da haka ya miqe ya fice zuwa site nasa inda ya zube a kan gado a yayinda kansa keyi masa wani irin sara, ji yayi komi ya dena tafiya masa a duniyan. Ina ma Allah ze d'au ransa cikin wannan dare (wa iyya zubillah) don komi ya wuce. Ina ma ba a ta6a k'addaro masa da rana irin ta yau ba. Upon all the women out there Nazeefah ze aura? Yarinyar daya tsana fiye da mutuwarsa, fiye da duk wani mahaluk'i a duniyan nan kuma yake da tabbacin itama ta tsanesa as much ba don komai ba kuwa se don tsan-tsan tsana da k'yaman da yake nuna mata a fili, a bayyane a fuskan sa anytime path nasu yayi crossing. God help him. A da har ya fara gyangyad'i kafin kiran Abba amman yanzu baccin nasa ya nema gabad'aya ya rasa ba don komi ba se don tashin hankali. Ido ya zura wa ceiling yana k'ok'arin tattaro hankalinsa, ana cikin haka yajiyo knock a bakin k'ofan d'akinsa se yanzu abin ya fad'o masa ashe beyi locking main k'ofar site nasa ba.

  "Come in" ya fad'a cikin wata irin kasalacaccen murya. K'ofan na bud'uwa sega Ummi bayyane a bayansa tana sanye da hijabi tazarce. Kallonta yayi ba tare da yace komai ba har izuwa lokacin da ta k'ariso ciki ta zauna akan gadon ta inda yake kwance. "Prince tashi ka zauna muyi magana" ta buk'ace sa.

  "Ummi dan Allah kibari ba yau ba abinda nakeji is already enough for me to handle just leave me alone I'm sorry."

  "Haba Prince ya kake magana haka? Taya kake tsammanin zan iya barin d'ana k'walli d'aya tal acikin irin wannan yanayi? Tashi ka zauna kaji Baba na yi hak'uri" da k'yar ta samu ya zauna d'in.

  "Gaya min what is going on in your mind me kake tunanin yi yanzu?"

  "Ummi I don't know" ya fad'a abin tausayi "Am so confused I don't even know what am feeling" ya k'arasa tamkar zeyi kuka.

  "Shikenan ya isa ka kwantar da hankalinka in shaa Allah komai ze tafi kamar yadda kakeso it's just a matter of time."

  "Ta yaya Ummi when Abba wants me to desperately marry his friend's daughter? Sanin kanki ne Ummi na tsani Nazeefan nan ko gidan nan ta shigo gaisheki ba k'aunan hakan nake ba yarinyar she's so stubborn."

  "Zata gyara in shaa Allah Prince wannan ba komai bane."

  "Yanzu Ummi kema kin goyi bayan zancen auren nan kenan?" Ya tambayeta tamkar zeyi kuka.

  "Prince da amincewa na da rashin sa duk d'aya ne wallahi one thing am sure is aure bazai auku ba har se idan ka amince kuma har idan baka son yarinyan nan ba wanda ya isa ya saka aurarta."

   Kai ya kad'a cike da takaici "Ummi ki dena magana as if ina da choice, kina ganin yanzu idan na ce wa Abba bazan auri yarinyan nan ba komai zai cigaba da gudana a tsakanin mu kaman yadda yake a da? Kina ganin Abba baze yi holding grudge akaina ba nak'in sake min magana har duniya ta nad'e? Kin deji da kunnenki abubuwan da ya irga a parlournsa d'azu that idan har ban amince da wannan aure ba toh kaman neman tona mar asiri nake shirin yi acikin jama'a which I'll never do so to my own father."

  "Then you have a choice to make, ka yarda da k'udirin Abban naka kawai."

  "It's not that easy Ummi bana son Nazeefah kuma bana tunanin zan ta6a iya sonta wallahi na tsaneta tsana na sosai."

  "Ya Salaam!" Tayi exclaiming "Ya kake magana haka sekace ta gaza ta wani fannin ne iyye Prince? Yarinyan nan de kyakkyawa ce masha Allah son kowa k'in wanda ya rasa gata kuma daga babban gida bugu da k'ari ga iyayenta manyan mutane masu k'ima a idon jama'a, kaf garin nan ana darajasu, what else do you need?"

   "What else do I need?" Ya tambayeta cike da mamaki "Kamun kai, tarbiyya da kuma mace mai addini which Nazeefah is clearly lacking. Sam bata d'aya daga cikin jerin 'yan matan da zan iya so, bana buk'atan kyawunta da kud'in mahaifin ta cause I have all that, I'm rich and handsome."

  Numfasa tayi, "Tabbas ba k'arya acikin maganganun ka Prince addini ma cewa yayi idan na miji zeyi aure abinda ze fara dubawa acikin qualities na matar shine addininta, k'arfin imani kenan, shi arziki da kyau duk a baya suke biyowa."

  "Exactly Ummi that's why I need you to please help me, do something wallahi ina cikin tsaka mai wuya."

  "Ya kakeson muyi Prince? Wallahi in har da akwai wani alternative da na bima don ka ku6uta daga auren wannan yarinya amman babu, hak'ura zakayi ka aureta don ka farintawa Abbanka rai."

  "Ummi ni kuma shikenan kin yarda in jefa kaina acikin k'uncin rayuwa kenan?"

   "Come on Prince" ta fad'a tare da kwanto sa a jikinta tana shafa gashin kansa a hankali. "Ba wanda yace don ka auri Nazeefah zaka jefa kanka cikin k'unci, da ikon Allah zaka koyi sonta, Nazeefah is a very loving lady kawai don baka ta6a ware lokaci ka santa bane, batun rashin kamun kai kuma idan kukayi aure zata gyara, karuwai ma akayi musu aure suka shiryu balle ita da kanta ke rawa kad'ai?" D'ago kansa yayi daga jikin nata sannan a raunane yace, "You like her don't you?"

  "Prince..."

  "Bana sonta Ummi kuma kin san ni idan na tsani abu na tsanesa kenan har abada."

  "Kul!" Tayi saurin katsesa "Kar ka kuma cewa haka, ita soyayya ba'a yimata haka, saidai idan baka bud'e mata zuciyarka ba tabbas zata shige, kai deh kawai yanzu kayi k'ok'ari ka bawa Nazeefah chance am sure zaka koyi sonta as time passes by."

  "I don't think so" ya kawar da kansa.

  "Tell me something Prince" tayi maganan tare da sashi maido da kallonsa a gareta, "Kana da watan da kake so ko ba haka ba?" Bata basa daman yin magana ba ta cigaba "Meyasa baka sanar da Abbanka ba toh? Kaga if only you did da duk hakan bai faru ba."

  "Ummi wallahi ba wata ni banida kowa wallahi."

  "K'arya kakeyi Prince" ta fad'a tana kallon cikin idanunsa don gaskata abinda ya fad'a.

  "Ummi ana wasa da wallahi ne? Wallahi babu" ya kuma jaddada mata.

  "Hmmmm" taja nishi cike da k'in yarda "Duk had'add'un kwanukan da ake shigo dasu kusan kullum acikin gidan nan da sunan an kawo wa Prince abinci kace duk cikinsu babu wacce tayi maka?"

  "Hmm Ummi kennan" ya fad'a tare da murmusawa kad'an ta gefen lips nasa wanda a sanadin hakan dimple nasa ya lotsa "Har yanzu baki san waye Afzal ba, bakisan kalan macen da zata iya burgesa ba har ta iya sace zuciyansa. Mace mey kunya nakeso, wacce duniya da abinda ke cikinta basu dameta ba, mace wacce take da Haddan Qur'ani koda ace ba duka ba, wacce ta rik'e addini, wacce zataji kunyan kallon cikin idanu na tace min tana so na, wacce zata lullu6e jikinta idan zata fita waje ba wacce take yawo ba d'ankwali balle mayafi akan layi ba, ko kuwa wacce ke zuwa party tana bin maza. Bana k'aunar macen da za'ace kaf cikin lungunan garin nan ta zagaya da mota sekace BOSEPA (kamfanin kwashe bola da dotti) kokuwa wacce take bin maza here and there. Sam macen da ta fad'a acikin jerin wad'annan basa burgeni."

  "Toh Afzal na ji ka kuma na gamsu da duk wani abinda ka fad'a kuma kamar yadda Abbanka ya fad'a maka nima hakan zan kuma nanata ma wallahi kade ji rantsuwa ko? At any moment ka bud'i baki kace min Ummi ga wannan inason ta da aure zan sa hannu inga sena cimma maka wannan buri na ganin wannan 'ya ta zamo matarka, kaide abinda nikeso da kai kawai kayi hak'uri ka amince da auren yarinyan nan ku rabu lafiya da mahaifinka."

  "Ummi idan kuma banida ra'ayin auren sama da mata biyu fa?"

  "Se kayi adapting hakan Prince kokuwa ka bawa Nazeefah chance a zuciyarka and learn to love her those are the only options you have."Dogon numfashi yaja sannan ya sake a hankali, "Thank you" kad'ai yace da ita.

   "Zan saka a addu'a ni kuma idan har wannan aure alkhairi ne toh Allah ya tabbatar mana dashi ya bada sa'a ya kuma bada zaman lafiya idan har kuma otherwise ne toh Allah kawar da zancen."

  "Shikenan Ummi thank you."

  "Bari in baka waje ka kwanta ko? I don't want you to overthink yourself Prince ka kwanta kayi bacci kawai kabar komi a hannun Allah, kad'au wannan aure as k'addaran da Allah ya k'addaro maka don ya auna iya adadin imanin ka kaji?"

  "Toh Ummi" ya fad'a a hankali.

  "Gobe akwai office ko?"

  "Eh" ya amsa blankly.

 "Toh Allah ya kaimu sleep tight okay?"

  "I will, I love you."

  "I love you too" ta fad'a mar tare da pecking nasa a temple sannan ta miqe ta tashi "Ka tashi kayi locking site naka kuma."

  "Manta dashi please" ya fad'a chan k'asa-k'asa sannan a fili yace, "Toh I'll follow behind you." Tana fita ya cire jallabiyansa yaja comforter ya kwanta ko k'ofan d'akin nasa ya kasa tashi ya rufe balle na site d'in gabad'aya. Baccin da Ummi tace yayin yikeson yi amman sam ya kasa, tunanin ya cigaba dayi har...


   Washegari...

  Saboda rashin samun baccin da Afzal be samu yayi ba yasa ko masallacin dake cikin gidansu ya kasa takawa ya fita sabida se daf Asuba nauyayyen bacci ya afka masa, a d'akinsa ya idar da Sallan ya koma kan gado inda ya soma bacci wane gawa totally forgetting ya kamata ya tashi by 6 ya shirya office.
 
  Ba shine ya tashi ba se goma da rabin safe nan ma don rurin da wayansa keyi ne akan bedside drawer. Cike da kasala idonsa a rufe ya miqa hannu ya ja wayan tare da swiping ba tare da ya duba wa ke kira ba, sauk'e wayan yayi akan kunnensa don ko rik'ewa ma baijin zai iya.

   "Triple A?" Cewar wanda ya bugo wayan daga d'ayan 6angaren.

    "Na'am Sultan?" Ya tambaya wai tsabaragen baccin da yakeji yama kasa tantance muryan aminin nasa. Mutumin da suka kasance tare dashi tun forever, tun kindergarten (nursery school) har ila yau.

   "Don't tell me bacci kakeyi har yanzu" Sultan yayi exclaiming cike da mamaki jin gyangyand'in dake tattare da muryan abokin nasa.

   "Shhh! Kayi magana a hankali please bacci nakeji" yayi chanting har anan idonsa a rufe.

  "You better get your shitty ass up ko ka manta kuna da meeting ne a office naku yau kuma kai zaka wakilta? Yanzu secretary naka ta kirani take cemin she's been trying to reach you but all your lines seem switched off nima if not ina da private numbanka off hand da bansan ya zan iya contacting naka ba."

  "F*ck!" yayi growling cike da tashin hankalin a yayinda ya bud'e idanunsa. Gabad'aya ya mance akwai wani abu wai shi office Gosh! Ya zeyi da meeting d'in yanzu? Daman wakiltan Boss nasa zeyi kaman yadda Sultan ya fad'a kasancewar shi manager'n nasu yayi tafiya seya buk'aci Afzal dayake Assistant nasa da ya wakilce shi.

   "K'arfe nawa ne don Allah maza?" ya tambaya a gigice, gani yake kaman idan ya tsaya neman position na agogon d'akinsan ma ze 6ata mar lokaci.

   "Thirty five minutes pass 10" Sultan yayi stating.

   "The f*ck!" Yayi exclaiming a birkice tare da miqewa "I'm late for the meeting already!" Yayi exclaiming "Meyasa baka kirani ba tun d'azu?"

   "See you! Wato baka gode bama dana kira ka yanzun?" Ya tambayesa cike da mamaki.

   "It makes no difference!" ya amsa a d'an fusace.

  "Ba laifinka bane nasan maganinka, ma tsaya meyasa ka makara haka? Tun jiya fa ban sake ji daga gareka ba are you sure all is well with you?"

  "Guy alot has happened I'm telling you, yanzu call back my secretary ka tsarata kace mata ciwon ciki ya kamani jiya da daddare kaima yanzu Abba ke sanar da kai."

  "A nawa kenan?"

  "Come on!"

  "Alright se yaushe zaka fito?"

  "I dunno yet amman duk abinda akwai zan sanar da kai please call her As Soon As Possible nagode."

  "No big deal" ya fad'a tare da katse wayar. Fad'awa kan gadon yayi da bayansa yana mamakin ya akayi ya makara haka yau amman tuna ya kasa bacci daren jiya sai kusan asuba ya kawar da tunanin daga kansa. Se kuma mamakin da yake ace sa6anin kullum be je ya gaishe da Ummi da safe ba kamar yadda ya saba kafin ya fita office amma ko tazo ta duba sa ko lafiya batayi ba? Ba shakka yanzun tana baje kan gado tana bacci. Kai ya kad'a sannan ya miqe ya fad'a bathroom yayi wanka. Yana cikin karyawa a kan dining table ya soma jin hayaniyan Ummi tana magana da wasu, bada dad'ewa ba se gata nan ta shigo tana sanye da nightie nata da babban mayafi akai, da alama yanzu tashinta daga bacci.

  "Prince?!" Tayi exclaiming cike da mamaki a iya saninta de Afzal baya wasa da aikin shin toh yau meh ya faru? Mey yakeyi har war hakan a gida yau bayan ba wani public holiday bane?
   "Prince lafiya?" Ta kuma tambaya jin be amsata ba.

  "Toh Ummi ki shigo mana a bakin k'ofan ne zan gaisheki?" Ya tambaya yana turo light pink lips nasa.

  "Shikenan Esther ku tafi" ta sallami masu aikin tare da jawo k'ofan sannan ta k'arisa ciki ta zauna a kujeran dake gefen damansa. "Good morning" ya gaishe ta yana sipping coffeen shi.

   "Prince me ya hana ka zuwa office yau?" Ita ko ta kan gaisuwan ma batayi ba, kafin ya samu daman amsata ta shiga auna body tempreturensa k'ila baida lafiya ne tayi tunanin hakan a ranta.

  "Ummi please!" Ya fad'a a tak'ure tare da sauk'o da hannunta daga fuskansa. "Am fine I just happened to overslept lokacin dana tashi kuma na makara shiyasa banje office ba" ya bata amsa.

  "Ban san ka da haka ba fa Prince nima yanzu tashi na kenan daga bacci mai wanke mota ke sanar dani cewa baiga fitowank
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *RANA D'AYA* BY MIEMIEBEE* Gimbiya 1 19,906 08-28-2018, 11:52 AM
Last Post: Deecolee
  *RANA D'AYA*BY MIEMIEBEE* Gimbiya 0 4,205 08-14-2018, 12:35 PM
Last Post: Gimbiya



Users browsing this thread: 1 Guest(s)