The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*KAINUWA* by Ayusher Mohd
#1
.? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

*Gaisuwa Gareki Maman Abrar wannan shafin naki ne, Allah yabar zumunci Ameen.......*

*84*



   Ajiyar zuciya yai sannan ya kalli Mairo, kanta ta sadda kasa sannan tai hanyar fita.
Abdulmajid ne ya bita da kallo, sai dataje jikin kofar zata fita sannan ta juyo idanunsa na kanta dan Ji yake kamar kartaje ko ina.

 Murmushi tamai sannan taja kofa tai waje Tare da rufo musu.

 Tana fita ya maida kallansa gun Turab yace " Waziri fa? Ya aka kare?" dan tun jiya abin nan ke damunshi.
 Turab yace " yana gida sai dai Sarki yasa an killaceshi kafin a gama shari'a."

  Mairo taje zata gangara ta hango Magajiya na nufo gun.
 Gefe ta matsa tare da juya baya har ta wuce, har taje zata sauka ta tafi sai kuma ta fasa.

 Turab ya kalleshi yace " Magajiya ta bu'lo da wani sabon al'amari."
 Abdulmajid yace " na me kenan?"

Turab zaiyi magana yaji Garzali na sanar da isowarta.
 Tura kofar tai ba tare da sallama ba, dama tunda taga Garzali tasan Turab na nan.
 Tana shiga ta kalleshi sannan ta kall Abdulmajid.
 Murmushi Tai sannan ta karasa ciki.
Kallan Turab tai tace " kana nan ashe?"
 Turab ya kalleta sai dai baiyi magana ba.
 Girarta ta ja sama sannan ta kallu Abdulmajid tace " zuwa nai in maida kai gida, a kula dakai acan."
 Kallanta yai yace " gida?"
 Tace " eh, sannan dama inasan inma wata tambaya agaban kanin  nan naka, nikam Abdulmajid tsakanin Waziri da Abu Turab wanene ya nemi halaka maka rayuwa?"

  Kallan mamaki ya mata yace " ban gane me kike nufi ba?"
 Tace " tsakanin Turab da yayana wanene yasa aka kamaka?"
 Yace " ni ai ba........"
 Katseshi tai da sauri tace "bakaji tambaya ta bace? Tsakanin Turab da Yayana wanene yasa akama ka?"
 Turab ya kalla wanda daidai lokacin shima ya kalleshi.
 Turab a hankali yamai wani murmushi.
 Magajiya tace " kai nake jira."
 Yace " Turab ne."
 Wata dariya ta saki tace" kaji ko? Ina fatan kasan yanzu amsar da za'a bada a zaman da za'ai, sannan banasan wanda ya nemi kashe min d'a yazo kuma yana neman shiga jikinsa, dan haka karna kara ganinka da Abdulmajid."

  Turab ya kalleta idanunsa na kanta ya taku har inda take yana tafa mata, sai dayazo daf da ita yace " Bravo! Kai gaskiya Umma u are indeed a very dangerous woman."
 Da yake lokacinta ba makaranta tai ba, sai dai tsabar basira datake dashi ta tabbatar magana ce ya fada mata, tunda lokacin karatun mata ba'a wani daukeshi da wani abu ba.

  Kai ta jinjina mai tace " in fadama wani sirri?"
 Kallanta yai, tace " abinda kake dashi akaina ba abinda zasumun, kasan dalili? Ta matso daf dashi saitin kunnenaa tace "Saboda kai jinin mahaifinka ne, bazaka taba sanar dashi d'an dayake tunanin nashi ne ba nashi bane."
 Sannan ta kalleshi tace " kasan dalili?saboda kana tsoron halin da zai shiga."

  Turab kam jiyake zuciyarsa kamae zata fashe saboda takaici, daurewa yai ya kalleta yace " haka kike tunani?to in har haka kike tunani kin bada ni, domin in har irin wannan d'an karamin abun zai firgitashi to ba shakka bai dace da mulki ba."

 Ya juya yai waje.

  Dunkule hannunta tai ta matse a jikin zaninta, ji take kamar ta jawo yaran can ta shake shi.
 Shikansa yana fita ya saku wata ajiyar zuciya sannan ya dan cije labbansa, yai gaba.

  Kallan Abdulmajid tai wanda ganin yanda suke magana yasa ya runtse idanunsa saboda takaici, waje tai a zuciye Ta tambayi inda likitansa yake.

  A hankali ya bud'e idanunsa, hawaye ne suka zubo mai dan ba shakka shikam yasan duk abinda ke faruwa duk saboda shi ne.

 Tura kofar tai a hankali ta shigo, taba kallan sanda Turab ya fita, Sannan taga yanda Magajiya ta fito rai a bace.
 
  A hankalu ta tako inda yake, hannunsa ya rike yana karza babban d'an yatsansa a kan bayan hannunsa sam bai kula ba gun yar ya d'an fashe.

 Har ta karaso gun baimasan tazo ba, hannunta tasaka akan hannun da yake karzawa, idanunsa ya d'ago ya kalleta, kura mata ido yai, daurewa tai tace " me kakeyi hakan?"
 Kasa magana yai sai kallanta kawau da yakeyi, tace " ko me ke damunka addu'a zakai bawai karza hannu ba."
 Ta zare hannunta tace " zan wuce."
 Ganin yanda fuskarta take a had'e yasa yai saurin riko hijab d'inta.

 Tsayawa tai ba tare data juyo ba, yace " kiyi hakuri."
 Kallansa ta juyo tai cikin zafi tace " me yasa kake cutar da kanka? Me yasa in abu baima ba bazaka fadi abinda ke ranka ba? Mahaifiyarka tafi wanda ya halliceka ne? Akan me bazaka dinga nuna mata abinda take aikatama ba daidai bane? Ko zuciyarka ba irinta Turab bace at least kai namiji ne ya kamata in har tai abinda bai dace ba ka nuna mata."

 Ko mai ta tuna, sai kuma tai shiru taja hijab dinta tai waje.

  Magajiya na dawowa ta sa aka sashi a keken guragu aka kaishi mota, sykai gida.


  ***********


  Juyi tai ta ganshi akan sallaya, agoggo ta kalla taga karfe d'aya saura minti goma.
   Farkawa ta kara yi , Abu Turab ta gani a zaune a kan kujerar dake d'akin, ya had'e hannayensa alamar dogon tunani, dayake ba haske sosai a d'akin, sai wata yar karamar fitila dake gefen gado ta d'aya bangaren ne a kunne.

 A hankali ta kalli agoggon d'akin karfe biyu da kwata, mikewa tai ta zauna sannan ta kalleshi.

 Kallanta yai dan yaji motsi, ganinta a zaune yasa ya mike ya taso yazo inda take.
Kusa da ita ya zauna sannan yace " farkawa kikai?"

  Kallansa tai tace " eh, kai fa? Kasa bacci kai?"
 Kai ya girgiza, tace " tunanin gobe kake?"
 Juyowa yai saitin da take kallansa yace " Bilkisu."
 "Uhmm mm"
 Shiru yai sai kallanta da yake, tace " inajinka."

  Hannayenta ya kamo duka biyun ya rike yace "bansan ya zata kaya mana ba gobe, shiyasa nake tunanin wani abu."

  Kallansa tai tare da tattara hankalinta zuwa kansa.
 Yace " idan har Magajiya taci galaba akaina, wani abu ya sameni inaso ki koma gida, ba tare da waiwaye ba, kiyi rayuwarki kamar baki san niba, zan aiko da takardarki......."
 Hannunta ta zare daga cikin nasa sannan ta sa kalleshi tace " me kake sam cewa?"
 Yace " nama mahaifinki alkawari bazan......."
 Katseshi tai tace " kana nufin in had'a kayana kenan kafin gobe ko me?"
 Baice komai ba sai kallanta da yake, mikewa tai ta kunna fitilar d'akin sannan ta bud'e wardrobe dinta cikin kunar rai ta shiga zubo da kayanta kasa.

  
  Ganin yanda take zubo da kayan ne yasa ya mike ya karasa inda take, hannu yasa ya riko hannun da take zubo da kayan, yace " Bilkisu!"

  Juyowa tai ta kalleshi idanunta sun ciciko da kwala tace " na d'auka kai kace in shirya kaya na?"

  Yace " Na fada amma."

  Tace " kanaso ka nunamin ni da kau ba d'aya bane? Kanaso ka nunamin matsalarka ba tawa bace?"

  Bata taba nuna bacin ranta ba a iya zamansu tun kan suyi aure sai yau, hannunta ta shiga kokarin kwacewa.

  Rungume ta yai a jikinsa, sai da yaji tayi sanyi da kokarin kwace kanta sannan yace " ba haka nake nufi ba, banaso insanyaki cikin damuwar da ni kaina bansan sanda zata kare ba."

  Idanunta ta lumshe tace " menene tsakanin miji da mata? Na d'auka duk runtsi duk wahala su shanyesu tare, su birne matsalarsu sannan su taimaki junansu? Da wannan buri nai aure, taya zaka cemin inka shiga matsala in tafi gida? Bakasan gwara kace mu rabu saboda baka sona ko saboda akwai wani abu nawa da baka so ba?"

  Kara rungumeta yai yace " ko d'aya, in fact a kullum nai sallah ina gode ma Allah daya bani ke a matsayin matata, wacce ban taba zato ba, sannan maganar bamu zama d'aya ba ko kad'an ba haka bane."

  D'agowa tai ta kalleshi tace " me yasa kake tunanin fad'uwa? Baka tunanin kaine zaka kada ta?"

  Murmushi yai yasa hannunsa d'aya  a kan kafadar ta, tace " mai gaskiya baya faduwa, sannan Allah na tare dakai, muma muna ma addu'an samun nassara, inaji a jikina matsalar ka ta kusa warware wa, sannan da yardar Allah ba wanda zai cutar dakai."

  Murmushi kawai yakeyi yana binta da kallo, tace " me? Baka yarda dani........."

  Batai zato ba taji bakinsa cikin nata, shikansa bai san sanda zuciyarsa ta sashi hakan ba.

  Sun dade suna aikama juna sakwan ni, abinka da wanda bai taba yi ba, jinsa ya dinga yi kamar ana angizashi.
 Sam ya manta da alkawarin da ya d'aukarma kansa.

  Jin kafafunta suna neman kasa d'aukarta ne yasashi sa hannu ya zareta zuwa kan gado, a hankali ya zare bakinsa daga nata, ya kai fuskarsa zuwa wuyanta tare da sa hannu yana kokarin rabata da kayanta.

  Cak ya tsaya, tare da saurin mikewa idanunsa sunyi jaa sosai.

  Kallansa tai ita kanta duk da tana tsoron wannan rana sai dai abinda takeji a yanzu dadi ne muraran.

  Idanunsu ne suka hadu da juna, dawowa yai ya zauna tare da rungumeta tsam yace " what should i do?"

  A hankali tace " akan me?"

 Yace " the promise......"

  Kanta ta sunkuyar tana murmushi, dan ya bata dariya.

  A hankali yace " ya zanyi?"

  Murmushi kawai takeyi, d'agota yai ya kalleta, idanunta a lumshe a hankali ya maida bakinsa cikin nata...........


Nace su Turab dai to?


*************

 Washegari da sassafe bawan da Magajiya ta aika ya iso, rabansa da gidan sarki yau sati d'aya kenan.
 Tanajin shine ta ce ya shigo.
 Yana gaisheta yace " Magajiya na samoshi."
 Tace "yana ina?"
 Yace " yana wajen gidan."

  Tace yauwa na gode........




 *THE LAST BATTLE ?*


*TURAB*

? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

*Gaisuwa, jinjina gareku Aminan Arziki 'yan Sauyi, Dizzy, Rabes, Faty Shafi'u, Yar Gaya, Salamah, Kozali, Sharubutu, J.B, Rambi, da sauran Yan Sauyi......

*85*


   A hankali ya bud'e idanunsa, sannan ya kalleta, bacci takeyi akan hannunsa na hagu, haka kawai ya samu kansa da yin murmushi, sannan ya tuno abinda ya faru jiya.
 
   Ya akai jiya idanunsa suka rufe? Sam ya kasa controlling din kansa? Har sai da ya maidata mace? Lalai jiya yaci sa'a Bilkisu tayi wankan tsarki, da tabbas yanda yaji jiya in har bata sallah baisan yanda zaiyi ba, abu yaji wanda tunda aka haifeshi bai taba ji ba.
 Lalai wannan rana ta zamar mai ranar da bazai mantata ba, murmushi yai sannan ya tuno da, a da ko zaiyi tunanin aure sam zuciyarsa bata raya mai farin ciki.

 Khadija zuciyarsa take kauna kuma ya tabbata in ba dai wani ikon Allah ba bayanda za'ai ya aureta, shikuma bayaji zan iya rayuwa da wata ba ita ba, sai dai a yanzu ya tabbatar abin ba haka bane.

  In har ka samu mace wacce ta sanka, sani ba wai na suna ba, sannan wacce ta ke sanka, take kokarin farantama rai, zuciyarta da kuma suffarta masu kyau ne, mai addini, to lallai shikam yana gani a hankali zuciyar mutum zata koya ma san wannan yarinyar.

  Zuciyarsa haryanzu tana so da kaunar Khadija sai dai baxai taba auranta ba, saboda har abada ya tabbata bazai taba manta abinda jininta suka aikata mai ba, sannan inya hukunta iyayenta me zaice da 'ya'yan da suka haifa nan gaba in har sun tambayeshi kakaninsu na bangarenta? Kuma abu ne na sarauta wanda zai bar tarihi, ko da ya b'oye musu ya tabbatar labari zai isa har kunnensu, mai zai ce dasu a lokacin? Iyayenta sune suka...........
 Motsin da Bilkisu tai da kanta shine ya katsemai wannan tunanin, kiran Sallah ake tayi a massalaci, idanunta ta bud'e cikin bacci ta kalleshi.

  Ganin idanunsa a bud'e shima ita yake kallo yasa tai saurin maida idanunta ta rufe, sunkuyowa yai ya sumbaci goshinta sannan yace " zanyi alwala."
Kai ta daga mai alamar to, yace " zan dan fita daga nan kina ganin ba matsala? Naga........"
 Da sauri tace " zan iya." dan batasan maganar kunya takeji.

 Kanta ta zame daga hannunsa a hankali, murmushi yai bayan ya mike.
 Bandaki ya shiga yai alwala sannan yai waje.

 Idanunta ta bud'e a hankali bayan taji alamar fitarsa, sannan ta mike zaune, yaye bargon tai, sannan ta mike a hankali.

  Dama tasa an sanar da ita duk abinda ya dace tai, yanzu zamani yazi ilimin addini ya kara wadata balle a mata tonon silili. 
 Bedsheet din ta yaye tai toilet, a roba ta sashi ta zuba ruwa sannan tai wankan tsarki bayan ta gasa jikinta da ruwan dumi wanda sai data dafa a heater.

  Kallo d'aya zakama yanayin tafiyarta ka fahimci ba daidai take tafiya ba, bayan tayi sallah ta dade tana ma mijinta addu'a kafin ta mike.


  Turab kuwa a massalaci, bayan ya gama addu'oinsa ya fito shida Garzali bayan gari yayi haske suka fito wajen gari.

  **********

  Magajiya kam jin an taho dashi yasa taji wani nishad'i ya kamata, gari yana haske tasa aka kira kata matan sarki.

 Bayan sun zauna ne ta kallesu tace " yau munada zama na shari'a da za'ai, hakan ne yasa nakiraku dan inji ta bakinku, da Abdulmajid da Abu Turab wa kuke ganin zai gaji Sarki?"
 Kallanta sukai fuskarsu da murmushi sukace "Abdulmajid mana."

 Tace " ba sai na tsaya bata lokaci na ba tunda kunsan abinda ya kamata, ina fatan zaku bi bayana anjima."
 
  Kallan juna sukai kafin su amsa da to, suka taso suka fita, suna fita d'aya tace " matar nan tana neman maidamu yaranta, da izinin Allah d'an datake takama dashi bazai zama sarkin ba." 
 D'ayar tace "Ameen."

************


  Gimbiya tayi kwalliya tana zaune a falo wata yarinya ta nemi izinin shigowa.
 Bayan ta shigo ne ta mika kata wani dan karamin kwali na agoggo tace " daga fadar mai martaba nake, aikoni yai da agoggo wai aba Yarima Turab, sannan yana mai fatan alkairi."

 Kallanta Bilkisu tai sannan ta amshi agoggon, tana shiga d'aki ta d'aurashi akan madubi dan ita kam bata ji hankalinta ya kwanta da agoggon ba

 Sai daya gama shiryawa yazo kan madubi yana sa turare yaga kwalin agoggo, yace " wannan fa?"
 Ta sanar dashi abinda yarinyar tace data kawo sannan tace " ni amma......."

 Kwankwasa kofar da akai ne ya katse maganar, kofar ya nufa tare da zura agoggon yana tambayar waye.
 Mai kula da Gimbiya tace itace sannan tace wai lokaci yayi, yce to.
 Sannan ya kalli Bilkisu yace " Muje?"
Tace " ina?"
 Yace " gun mana."
 Cikin mamaki tace " harda ni?"
 Murmushi yai sannan yazo inda take ya tsaya yace " bakyasan kije?"
 Tace " inaso inje amma......."
 Kasa tai da kanta alamar kunya.
 Murmushi yai har hakwaransa suka fito yace " kunya kike?"
 Ta mike tace " bafa haka bane, tafiya......"
 Sai kuma tai shiru.
 Yace " menene a ciki? Indai bazaki bane, bazan takura miki ba."
 Ya juya, takunsa uku ana hudu tace " zanje."
 Murmushi yai kafin ya juyo sannan yace " muje."
 Komawa tai ta d'auko babban mayafinta.

********
  Karfe 11 na safe an gyara babban d'akin da za'ai shari'a.

  Basira itada Lantana sun iso gidan, dan Sarki yace duk a kira na cikin gida tunda shari'ar ta cikin gida ce, sai a kara shaidu.


  A d'akin taro kuwa, Hisham na gefe a zaune daga gefe, dogarawa biyu na tsaye kansa.

Galadima da Barde da mai Shari'a su suka fara zuwa.

  Sai Matan sarki ne suka fara isowa a mata, sannan Basira.

Magajiya ce ta iso cikin shigarta ta isa da jin kai da sanin akwai kudi da matsayi, gefenta Abdulmajid ne aka turoshi a kekensa.

  Kallo d'aya tama Hisham ta d'auke ido sannan taje gaba ta bangaren Mata ta zauna, bangaren maza kuma akasa Abdulmajid wanda ya zamana yana saitin ta.

  Ranta ya baci ganib ta riga Abu Turab zuwa.

  Sanar da isowansu akai, shigowa sukai shida Gimbiya a tare, tayi iya kokarinta na ganin ta saita kafafunta kar a gane, shikansa Turab saboda ita yake tafiya a hankali.

  Suna shigowa aka zubo musu ido, Abdulmajid sai a wannan lokacin shima ya ganta.
 Ba shakka ta hadu sosai, Magajiya ce ta dago ta kallesu, takaicinta daya yanda ita kanta sai da kayan jikin Bilkisu suka birgeta, Turab ya samu gu ya zauna kusa da Abdulmajid wanda hakan yasa ta zauna kusa da Magajiya dan Basira ce ta nuna mata gun zama.

  Bilkisu sai data gaida Basira ta gaida matan sarki sannan ta kalli Magajiya tace " Umma Barka da warhaka."
 Magajiya ta kalleta, bata amsa ba.
 Basira tai murmushi tace " Bilkisu da alama bakisan tsarin mu na masarautar zazzauba, a ka'ida sai kin fara gaida Magajiya.

  Bilkisu wacce dama tasan da hakan, tai murmushi sannan ta kalli Magajiya tace "Umma nayi laifi kenan?"
 Magajiya tace " karki damu ai bakisan tsarin bane."
 Bilkisu tace " godiya nake." sannan ta d'auke kanta.

  Shigowar Sarki ne yasa aka tsaya da gaishe gaishe, mai martaba ya samu guri ya zauna.

  Sannan akai addu'a aka tunatar da abinda akazo yi.
 Turab yace "Takawa ina neman izinin shigowar wata bakuwa wacce take da dangantaka akan shari'ar nan."
 Sarki yace " to bismillansu."

 Shigowar Matar Hisham ne yasa Magajiya ta kalli Turab, murmushi yai sannan ya d'auke kai daga kanta, kallan juya sukai da sauri shida Abdulmajid ganin wacce ke tafe a bayanta, Khadija? Me ya kawo ta.

  Khadija kuwa wacce d'an aiken ita ya sanar mawa tace ma Mahaifiyarta ai tare aka ce suzo, ta kalli Turab sannan ta kalli Abdulmajid.
 D'auke kai tai har suka zauna.

  Mai shari'a ya kalli Magajiya yace " Magajiya ta kawo nata sharhin a game da shari'ar da akai kwanaki, in akai duba da kalamanta tabbas suma suna da nasu ma'anar, hakan ne yasa aka daga shari'ar zuwa yau."

    Sarki ya kalli Abdulmajid yace " Abdulmajid sanar dani da bakinka a kuma cikin mutanen nan, wanene yasa a kama ka? Mahaifiyarka tace Turab ne, shi kuka Turab yace Hisham ne ya nemi halakashi kai kuma ka sadaukar da kanka, wanene yake fada mana gaskiya?"

  Abdulmajid ya kalli Magajiya wacce itama kallanshi kawai take yi, Khadija ya kalla wacce itama shi take kallo.

  Juyowa yai ya kalli Turab, wanda yake kallan Kasa.

  Sarki yace " Abdulmajid!"
 Abdulmajid yana kallan Magajiya yace " ni kaina bansan wanene ya sa aka kamani ba."

 Magajiya ta kalleshi tace " mene?"
 Turab kam ko gizau baiyi ba.

 Magajiya ta kalli Sarki tace " ta yaya Turab bazai nemi halaka Abdulmajid ba? Bayan yasan in akaji sirrin mahaifiyarsa shida sarauta sai dai a lahira? Amma in ya halaka Abdulmajid ko ma menene shi kadai ne jinin sarki dole ne a yafe mai."

  Galadima ya kalleta yace " sirri? Mai kike nufi kenan?"

 Kallan Sarki tai wanda idanunsa suka fara canzawa, sannan ta kallu Turab wanda ta tabbatar maganin ta yafara aiki dan yanata lumshe ido kamar mai bacci sannan ta kalli Basira tace " Basira? Me zakice?"

  Umma kam jikinta duk ya fara rawa, Magajiya tace " ina neman izinin shigowar mai bada shaida." 

 Sarki ba yanda ya iya dole yace " ya bada"

  Shigowar mutum ne yasa gaba d'aya jikin Basira ya hau rawa, Bilkisi dake kusa da ita tasa hannu ta rike hannunta tana kallanta, kallan Turab tai wanda gaba daya ta rasa meke damunshi dan kamar baya baya cikin hayyacinsa.

  Basira kam duk ta gama rikicewa. Ganin haka yasa hankalin Sarki ya tashi.
 Magajiya tai murshi sannan tace " Basira kin gane wannan? Badai zaki mance da wanda ya amshi budircinki ba?"

 Cikin tashin hankali kowa yaji maganar, nan fa aka fara kananan gulma, Sarki ya runtse ido saboda tsananin takaici.

  Turab wanda ke kokarin maido da hankalinsa ne ya kalli wanda ake magana, cikin layi.

  Kallo d'aya zakamai kaga alamar shaye shaye da talauci a jikinsa, tsugunne yake yana dan cicila ido.

  Kallan Basira yai wacce gaba d'aya jikinta rawa yakeyi.
 Bilkisu ganin ba wanda yai magana yasa ta kalli Turab da sauri, gani tau kamar baya hayyacinsa.

 Khadija itama kallan Turab tai dan kowa ya san zaiyi magana, yanda taga yanayi da kansa ne yasata kuramai ido tana san gano meke faruwa.
 A zuciyar sarki kuwa addu'a kawai yake akan Turab yai magana.

  Bilkisu ce ta kalli Magajiya wacce ta saki wani murmushin mugunta tare da kallan agoggon hannunsa ta gefe, a tsorace Bilkisu ta kara kallan agoggon tabbas bata karasa sanar dashi ba dazu aka kwankwasa kofa.

  Matsowa tai gun Basira da sauri ta rada mata abu a kunne.
 Basira ta kalleta sannan ta kalli Turab wanda idanunsa ke juyewa.

 Mikewa tai ta zo inda Turab yake, tunda wannan mutumin ya hangota ya taso da sauri ya biyota yana neman rikota yana cewa " kece ko? Kamar kece? Kai na tabbatar ma kece."
 Da sauri Dogarawa suka rikeshi, nan aka shiga tambayar wanene wannam din? Kowa fuskarsa dauke take da tambaya.

  Basira ta daure ta karasa inda Turab yake, kowa yana jira yaga mai zatai, da karfinta ta dage ta wanka mai wani wawan mari wanda yasa kowa kallan Turab.

 Bilkisu da sauri ta mike ta isa inda yake, Turab kallanta yai.
 Basira tace " bakada hankali ne? Ta ina zaka bari magani ya rinjayi jikinka? Bayan ni ina cikin tashin hankali? Ta ina......."

  Kuka ne ya nemi kamata, da sauri Bilkisu tasa hannu ta balle agoggon ta zareshi daga hannunsa, sannan ta kalli Turab wanda ya ke kallan Mahaifiyarsa gaba daya idanunsa sun canza.


? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

  *86*



   Kansa yainta girgizawa saboda gaba d'aya hankalinsa na neman gushewa, Bilkisu idanunta ne suka kada ta taso daga inda suke sannan tazo gaban Mai Martaba ta tsugunna, tare da ajiye agoggon akan tebirin gabansa, tace " Tuba nake Ranka ya dade amma zaka iya gane agoggon nan?"

  Magajiya ce tai saurin katseta tace " Bilkisu wani irin banzan tarbiyya ce wannan? Bakiga magana muke akan wannan dake gaban mu ba?" ta fada tare da nuna wannan namijin da aka rike.

 Bilkisu ta kalleta sannan ta sunkuyar dakai bayan ta juyo bangaren Sarki tace " Tuba nake ranka ya dade amma dan Allah ka bani amsar tambayar nan."
 A kasan ranta kuwa addu'a kawai take akan Allah yasa abin ya sakeshi kafin ta gama maganar nan, dan tana tambayar ne dan neman karin lokaci dan ya wartsake.
Magajiya zata sake magana sarki ya katseta tare da kallan agoggon yace " Agoggon menene?"
 Bilkisu tace " dazu aka aiko ma Yarima akan kaine ka bada a kawo mai."
 Sarki yace " ni kuma?"
 Bilkisu tace " haka ne Takawa, yarinyar ta kawo akan kaine ka bada a kawoma Yarima."

  Sarki ya daga agoggon sannan yace " menene dalilin aika agoggon nan da sunana bayan bani na bada ba?"
 Bilkisu ta kalli magajiya kadan sannan ta kalli Turab wanda yake ta kokarin bud'e idanunsa da kyar tace " ni kaina shine abinda ban sani ba."
 Magajiya tace " to yanzu menene? Abinda ya kawomu shine abinda ya kamata muyi ba wai wani zancen agoggo ba wanda bai damemu ba, da a aikamai da agoggo da kar a aika menene namu?"

  Galadima yace " Takawa ni wannan mutumin nake san sanin wanene? Da matsayinsa."
 Magajiya ta kalli Bilkisu tace " Gimbiya dawo ki zauna ko?"

  Bilkisu ta mike tare da kallan Turab.
Sam hankalin Khadija ya kasa kwanciya ganin halin da yake ciki, idanunta duk sun ciciko da kwalla.

  Basira kam gaba d'aya ta rasa ina zata sa kanta, Magajiya ta kalli mutumin tace " kai ka nutsu a gaban Sarki kake, sannan wannan da kake neman yima magana mata ce a gun Sarki ka kiyayi kanka kafin a kamaka."
 Mutumin yasa dariya yace " mata?"
 Galadima yace " kai! Meye tsakaninka da matar Sarki?"

  Kallan Basira yai yace " Basira in sanar dasu?"

 Kallansa Basira tai idanuwanta sun cika da tsoro, Abdulmajid ne ya kalli Turab ganin har yanzu ba a hayyacinsa yake ba kawai ya fara tari kamar irin ya kware din nan sosai.

 Da sauri Magajiya tace a kawo ruwa. 
Nan aka kawomai ruwa, da yake hannunsa ba kwari sai yai kamar irin rikewa ya kasa kawai ya juye ruwan a kan Abu Turab.

  A firgice Turab ya mike tare da rike kansa.
 Magajiya tace " meye hakan kuma?"
 Turab ya kalleta sannan ya kalli mutumin nan, sai a yanzu maganar take kara dawo mai daya bayan d'ayan.

  Lokacin shi kuma mutumin yana kara cewa " Basira in fada?"
 Turab ne ya taho da sauri basu ankara ba ya kai mai naushi.

  Karfinsa ya sake sosai dan har saida gefen leb'ansa ya fashe.
 Dif d'akin yai da wuta saboda mamaki.
 Turab ya kalleshi sannan cikin murya mai sauti yace "Ka fad'i me?"

  A lokaci d'aya mutane biyar sukace Alhamdulila Turab is back (nasan kun sansu....Lol)
Magajiya kam takaici ya kamata, Turab ya kallesu sannan ya kalli mai shari'a yace " a shaida da tambaya, mutane nawa ne ba'a yarda da amsarsu?"

 Kallansa yai yace " da mahaukaci da......"
 Turab ya katseshi yace " wannan hankali gareshi?"
 Kowa ya kalli mutumin. 
Turab ya kalli Sarki yace " Takawa kayan jikinsa kawai nakeso a kalla, wannan mutumin hankali gareshi?"

  Sarki ya kalleshi sannan yace "da alama babu."
 Turab ya kalleshi yace " bawan Allah ya sunan ka?"
 Mutumin ya kalleshi yace " wani rai...."
 Turab yace " bakasan sunan ka ba ko?"
 Yace " na sani mana."
 Turab yace " meye sunanka to?" yace "wannan wani irin tambayar rainin hankali ne?"

 Turab yao murmushi yace " me kuka gani anan? Zakuce wannan nada hankali? Mutumin da ko sunansa bai sani ba?"


  A zuciye mutumun ya kwace tare da yowa kan Turab.
Nan aka kamashi da sauri, Turab yace " Galadima mai zakuce game da wannan mutumin?"
 Galadima da Barde suka kalleshi, wanda shikuma takaicin abinda Turab yamai yasa abin ya motsa ya shiga yin gurnanin ihu na manyan 'yan shaye shaye akan lalai sai ya kashe Turab.

 Ba shiri akai waje dashi.
Turab ya kalli Magajiya yace " Umma me zakice ke kuma akan kawomana mahaukaci gun shari'a?"
 Magajiya ta kalleshi sannan tace " ban gane ba....."
 Yai dariya yace " baki gane me ba? Kinaso kicemin mahaukacin nan shi ya kawo kansa......"
 Cikin tsawa tace " kai Turab! Kasan da wa kake magana, ko ka manta wacece ni, ko wacce ta haifeka bata isa ta dinga min magana haka ba."

  Sarki ne ya kalleshi yace " Turab a daidaita kalamai, kar ka manta mahaifiyarka ce."

 Turab ya kalleta sannan ya koma ya zauna tare da sunkuyar da kai yace " tuba nake ranka ya dade, zuciyatace take tafasa."

   Magajiya ta bishi da kallon takaici.
 Sarki yace " munajiran mai shaida na gaba dan jin asalin meke faruwa."
 Turab yai gyaran murya sannan ya zubawa Magajiya ido yace " bansan me yasa ake tunanin nine na sa akama Abdulmajid ba, sai dai ni da bakina bazan taba cewa ba ni bane, sai dai kafin a kawo wata shaida da zata nuna nine nai wannan laifin inaso in gabatar da wani laifi wanda yake bukatar bincike, ina fatan za'a bani dama."

   Mai shari'a ya kalli Sarki yace " mai kake gani?"

 Sarki ya kalleshi yace " menene?"
Magajiya ta kalli Turab cikin takaici da san jin me yake shirin yi."

  Turab ya d'ago yace " godiya nake, magana ce game da Hajiya."
 Da sauri Magajiya ta kalleshi.
 Yai murmushi sannan ya cigaba " Bayan mun kai Hajiya asibiti likita yayi bincike gun warkar da ita, a lokacin ne ya gano cewar guba ce aka bata wacce ta nakasar mata da duk gab'obin jiki."

  Inalilahi wa ina ilaihi raji'un, abinda yake fitowa daga bakin jama'ar gun kenan, Abdulmajid da sauri ya kalli Magajiya.

  Turab ya mika ma dogarin dake tsaye akan Sarki takardar yace " ga abinda likitan ya rubuta."
 Duk da sarki yayi mamakin jin wannan zancen wai likita? Bayan har Hajiya ta warke Turab baisan inda take ba, sai dai bai bari mamakin ya bayana ba a fuskarsa.
 Amsar takardar yai ya gani sannan ya mika aka bi kowa aka nuna mai.
 Sarki nuna bacin ransa yai kamar irin baisan komai din nan ba, yace " Guba kenan aka shayar da Hajiya?"

  Turab yace " sosai, sannan inada shaidar da zata sanar damu hakan."
 Nan yace shigo.

  Yarinyar dake waje aka ce waye xai shigo?
 Nan tace nice, tare da shiga. 

  A tsorace ta shiga, tana shiga ta zube a kasa tare da gaisuwa.
 Sarki yace " kece shaida akan abinda ke faruwa?"

  A rikice tace " Tuba nake ranka ya dade na cancanci hukunci mai tsanani."
 Galadima yace " tashin hankali."

  Turab yace " sanar damu abinda ke faruwa."

  Yarinyar ta d'ago tana kallan Turab a tsorace.
 Turab yace " sanar damu abinda kika sani."

  Magajiya ta kalleta duk ta rasa me zatace.
 Hisham kam idanunsa kawai ya runtse dan yasan yau kam sai dai Allah.

  Yarinyar ta kwashe komai ta sanar dasu.
 Mai Shari'a yace " yarinyar data baki maganin tana nan?"
 Kai ta girgiza alamar a'a, dan mai baiwa ce."
 Sarki yace " wannan alama ce ta kenan wanda ya bada umarnin mutum ne mai mukami."
 Turab yace " a wani bangaren take aiki?"

  Magajiya ta kalla sannan ta sunkuyar da kai.

 Magajiya tace " kanaso kace guba aka ba Hajiya? Wani mara imanin ne zai in aikata hakan?"
 Turab yace " ina muka sani, ko mara imanin na cikin d'akin nan?"
 Bai bi takan me zatace ba ya kalli Yarinyar yace " a wani bangare take aiki yarinyar?"

  Yarinyar ta nuna da yatsa, yatsar kowa yabi sukaga ta tsaya akan Magajiya.

 Magajiya tai murmushi tace " ba dai ni kike nunawa ba ko?"

Kallan Magajiya kowa yai.

  Yarinyar ta sunkuya sannan tace "a bangareki take aiki sannan tace inhar ban sa maganin ba......."
 
 A zuciye ta mike tace " ke dan gudanku sharri zakimin?"

  Sarkin yace " Magajiya me kikeyi hakan?"
 Tace " ban gane me nakeyi ba, bayan ina zaune ana neman ace nine nake neman halaka Hajiya, meye dalilin da xai sani halaka mahaifiyarka?"

  Turab yace " shine yanzu zan sanar."
 Tace " mene?"
 Turab ya kalleta sannan ya kalli ragowar matan sarki yace " ko zaku iya tuna shayin da Magajiya ke baku a shekarun baya?"
 Kallan juna sukai dukansu harda Basira, sannan sukace eh.
 Turab ya kalli Magajiya sannan yace " Magajiya tana saka magani a ciki wanda zai hanaku d'aukar ciki a wannan shayin, bansan dalili ba wanda yasa daga baya ta canza tunani ta koma shayar da Sarki wannan shayin."

  Mikewa tai sannan tai wani murmushi tace " mene?"
 Turab ya kalleta sannan ya kalli Hisham yace " Waziri me zakace game da sharhi na?"
 Hisham ya kalli Magajiya sannan ya tuna ziyartarsa da Turab yai jiya, ya sanar dashi abinda ke faruwa da Hajiya da abinda ta sani har Magajiya ta mata hakan, Hisham yace tabbas shine ya amso maganin dan akan matan sarki aka fara.

  Magajiya ta kalli Hisham tace " Yaya me kenan?kana nufin kaine ka sanar dashi wannam kagagen labarin?"

 Hisham ya kalleta yace "Magajiya sai yaushe ne zaki daina san kanki?"

  Kallan sarki tai tace " bansan wannan labarin ba, sai dai in shi Hisham din shine ya aikata hakan."

  Gaba d'aya d'akin kowa kallanta yakeyi.
 Khadija kuwa gaba d'aya jitai kanta na wani juyawa, Abdulmajid kam idanunsa kawai ya rufe, ita kanta mahaifiyar Khadija ta girgixa da jin wannan muguntar.

 Bilkisu kam kallan Magajiya tai cikin tsananin mamakin wannan muguwar zuciyar tata.

 Sarki ya daka mata tsawa yace " ashe bakida imani?"
 Kallansa tai itama tace " dama abinda kake fata kenan ya faru, ko kana tunanin bansan so kake kaga bayana ba?"
 Sarki yace " mene?"
 Tace " da kai da danka kun hada kai kuna neman mun sharri, shine yanzu zakace wai banida imani?"

 Hisham yace " Magajiya!"
 Kallansa tai tace " yimun shiru tsohon munafuki, ni zakaci amana?"
 Khadija tace inada magana.
 Kallo ne ya dawo kanta, Turab ya zuba mata idanu.
 Khadija tace "tuba nake ranka ya dade amma Umma Magajiya da Abba sun aikata laifin dayafi wannan."

 Magajiya ta kalleta sannan tai dariya tace " khadija ke kam wa kike tunanin zai yarda da maganar ki? Bayan kowa yasan yanda kike bala'in san Abu Turab? Banaji akwai abinda zai saki da bazaki aikata ba."
 Da sauri Bilkisu ta kalli Khadija sannan ta kalli Turab wanda hakan yayi daidai da kallanta dayai.

 Murmushi ya sakar mata sannan ya d'auke idanunsa da sauri ya kalli Magajiya yace " Umma bakya tsoron incigaba da magana? Ko zaki fad'i sauran laifin da kanki?"

  Tace " laifi?ni ba laifin dana aikata."

 Turab yai murmushi yace " idan har zan sanar da laifufukan da kika aikata banaji wannan rana xata ishemu."

  Magajiya tace " good kun kyauta, sai kuce yau ba ranar bincike bace akan abinda akama d'ana, ranar yimun sharri ne."

  Turab ya kalli Sarki yanasan tona d'ayan sirrin sai dai inya kalli Abdulmajid ya kuma kalli Sarki sai ya kasa.

  Kansa ya sunkuyar yana tunanin abinyi.

  Muryar Andulmajid ce ya katseshi dayace " Umma ya isa haka nan, sao yaushe ne zakiyi nadamar abinda kika aikata?"
 Tace " mene?"
 Cikin murya mai sauti yace " Umma please ki tsaya haka nan, a da ina tunanin san da kike mun ne yasa kike aikata abinda kike aikatawa sai dai yanzu jin abinda kikema matan sarki da kuma shi kansa yasa nasan san kaine kawai naki, sai yaushene zuciyarki zata gamsu da abinda take so? Sai na zama sarki? Ko sai kin ganki akan gangarar mutuwa?"

  Tace " Abdulmajid."
 Abdulmajid yace " kin rabani da Mahaifana, tunda nake ban taba kiran matar data reni cikina da sunan uwa ba, ban taba kyautata mata ba a matsayin wacce ta d'au cikina na wata tara ba......."

  Da karfi tace " YA ISA HAKA!"

  Turab ya runtse ido tare da cewa thanks Abdulmajid.

  Inalilahi wa ina ilaihi raji'un.......
Ba shakka wannan kalaman sunfi tadawa kowa hankali, Hisham kam hawaye ne ya zubo masa, Turab Sarki ya kalla wanda gaba d'aya zuciyarsa tayi wani nauyi, kallan Abdulmajid kawai yake yana nanata kalamansa.
 Bilkisu ce  ta daure ta kalli Abdulmajid cikin mamaki tace " kana nufin ba Umma Magajiya bace Mahaifiyarka? Ba kuma Sarki ne ya haifeka ba?"

  Gaba d'aya zubama Abdulmajid ido akai cikin mamaki.
Khadija kam hawaye ne ke zubo mata, itakam Umman Khadija jitai hawayen ma sun kafe kaf sun kasa ma zubowa........  



*TURAB*

? *KAINUWA*?
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*Wattpad :-AyusherMohd*


  Gaisuwa da fatan alkairi gareku masoyan littafin nan gabaki d'aya, ina godiya kwarai da kaunar da kuke ma littafin nan, nagode da hakuri dani na rashin posting akai akai da kuke, ni kaina ba hakan naso ba.
  Always love u.......


*87*

Wani irin ihu Magajiya ta saka da karfi tace " ABDULMAJID....."

  Mikewa tai a zuciye ta isa inda yake, ta d'aga hannu zata zabgamai mari, da sauri Turab ya tsaya a gabanta.

 Kallansa tai idanunta duk sun kada sunyi jaa, kallan juna suka shigayi, tana mai wani irin kallo wanda ba komai a ciki sai tsantsar kiyayya.
 Mai Martaba idanunsa a rufe kawai suke saboda jin abin yake kawai yana mai yawo akai.
 D'akin yayi tsit kowa da abinda yake sakawa a ransa, wani dogari ne ya shigo da gudu ya tsugunna, Barde ya kalleshi yace " lafiya kai kuma?"

  Cikin in in na yace " mai kula da kofar gidan mai martaba ne na cikin gari."
 Galadima yace " to ya akai?"
 Bakinsa ya shiga motsawa ya kasa magana, Basira tace " ya akai Hadi?"

  Da sauri ya ya maida kansa kasa ya sa kuka, Turab ya kalleshi ganin yanda yake kuka yasa Turab ya matsa daga gun magajiya ya taho inda yake yace " Hajiya......"
 Wani kuka dogarin ya saka, da sauri Sarki ya bud'e idanunsa wanda gaba d'aya sun yi jaa, mikewa yai yana kokarin takawa baya yai da sauri dogarawan dake bayansa suka tareshi, kallansu yai sannan ya kwace jikinsa ya koma ya zauna saboda jirin da yakeji, Dogarin yace " Allah yama Hajiya cikawa yanzun nan......"

 Inalilahi wa ina ilaihi raji'un......Abinda kowa dake d'akin ya shiga fada kenan, Banda Magajiya wacce take tsaye, sai Sarki wanda gaba d'aya yaji kansa ya kulle ya kasa tunanin komai.
 Turab ya karasa inda yake da sauri yace " Abba!"
 Idanunsa ya sauke akan Turab cikin tsananin tausayawa, ba shakka lalai bai cancanci mulkin nan ba, lalai laifinsa ne na kyale Magajiya tun farko ta dinga yin abinda taga dama.
 A hankali ya fara karanto inalilahi a ransa, kallan Turab yai sannan yace " jeka zauna."
 Turab ya mike ya koma gun xamansa.
 Gaba d'aya d'akin yayi tsit kowa ya koma gun zamansa, Sarki ya mike tsaye tare da zare rawanin kansa ya ajiye akan teburin dake gabansa, sannan ya tako a hankali har zuwa inda Magajiya take gaba d'aya kana kallanta kasan a tsorace take, kallan ta Sarki yai ya dade idanunsa na kanta sannan ya kalli Hisham, sannan ya maida dubansa kan Abdulmajid, haka yabi kowa da kallo d'aya bayan d'aya.
 Akan Barde ya tsaya yace " Barde jeka taho da gawar Hajiya."
 Nan barde ya mike.
 Sarki ya kalli Magajiya sannan yace " kafin in sallaci gawar Hajiya inkaita makwancinta inaso in sanar da abu d'aya kafin in yankema Matarnan hukunci, daga wannan lokacin na ajiye mukamin mulkin Masarautar Zazzau, sannan na d'aura d'ana Abu Turab a wannan matsayi, wannan matar a d'aureta da kaca itada d'an uwanta Waziri a rufaffen d'aki, sannan bazan yanke mata hukunci ba d'an da take neman ganin baya, wanda ta makantar dashi bayan neman ajalinsa, wanda ta ke neman halaka masa rayuwa a koda yaushe shine zai yanke mata hukunci da kansa, sannan na umarceshi da yanke mata hukunci mai tsaurin gaske."

  Ya juya ya fara takawa kallo d'aya zakamai kasan lalai yana cikin tashin hankali.
 Matan sarki ne suka mike suka bi bayansa.

  Sunje zasu fita daga kofar Magajiya cikin karaji tace " KAI ABDUSSALAMAD!"

  Gaba d'aya d'akin kowa juyowa yai ya kalleta tace " mene? Kaba Abu Turab mulki? Inji uban wa? Inji uban wa? Kana tunanin ni Magajiya zan yarda wannan dan tsinaniyar yahau mulki? Mafarki kukeyi daga kai har yan d'akin nan, indai har ni inada.........."

  Kasa karasawa tai jin muryarta ta sarke, duk yanda tai gun yin magana ta kasa, tsugunnawa tai da sauri tare da rike wuyanta, a hankali kowa na d'akin ya fita wannan abu yafi komau yi mata ciwo, balle tana kallan Abdulmajid Khadija ta turashi a kekensa sunyi gaba, ga magana ta tsaya cak.
  Masu tsaro ne sukazo inda take rike da kaca, Hisham aka fara sawa kaca, kallan Magajiya yai yace " Allah ya isa tsakanina dake, shawararki itace tasa zuciyata ta rikid'e gaba d'aya, sannan maganarki bazata taba d'aowa ba wannan rana itace rana ta karshe da kikai magana da bakinki, domin kuwa inbaki mantaba da gubar da kikasha danyima Basira sharri, a lokacin dana amshi wannan gubar dama ansanar da sharad'inta, bata fita duka a jiki sannan kar babba wanda ya wuce shekara 45 yasha wannan gubar sannan duk sanda ran wanda yasha gubar nan ya baci sosai to xata cigaba da mai illa ta cikin jikinsa, sannan idan tai nisa xata jawo kurmancewa, sannan zata nakasa gab'obin jiki."

  Kakari ta shiga yi idanunta kamar zasu fito, kirjinta ta shiga bugawa da karfin gaske, Hisham yace " kina tunanin duk abinda kikemin a banza?"
 Ya juya yai gaba.

  Durkushewa tai cikin tashin hankali tana rike da wuya, tana wani irin gurnanin gaske.

   Bayan sun fita ne daga d'akin Turab ya kalli Bilkisu yace " bari muje mu d'auko Hajiya."
 Kallansa tai cikin tsananin tausayawa sannan ta daure ta kakaro murmushi tace " to, bari inje gun Umma."

  Gun Abdulmajid taga ya nufa, ya kalli Khadija yace " kawoshi zamu gun jana'iza tunda anan za'ai."
 Khadija ta saki hannun kujerar data rike tana kallan Turab, bai ko kara kallanta ba ya tura Abdulmajid.
 Suna d'an matsawa kadan Abdulmajid dake hawaye yace " Turab ta yaya xan iya zuwa gun jana'izar Hajiya?"
 Turab yace " me kake nufi? Kai ba d'an Abba bane ko me?"

 Abdulmajid ya juyo ya kalli Turab idanunsa na kara zubar da hawaye, Turab ya kalleshi yace " meye hakan kuma?"

  Abdulmajid ya maida kansa kasa.

 Bilkisu ta kara kallan Khadija wacce ke tsaye kusa da Mahaifiyarta.
 Karasowa tai kusa dasu tace " ciki zaku shiga gun zaman makoki?"
 Umma ta kalleta da idanunta da suka kod'e tace " ta yaya zamu iya shiga ciki? Da wani idon zamu kallesu?"
 Khadija tace " mun gode da kulawa amma....."
 Bilkisu ta katseta tace " in kuna ganin hakan ne yadace ba matsala."
 Ta juya ta fara tafiya.

Sai datai nisa sannan ta juyo ta kara kallen inda suke, can ta hangosu sunyi nisa.

 Juyawa tai ta nufi bangaren Umma.

 An d'auko Hajiya an mata wanka an mata sallah sannan an kaita gidanta.
(Allah ya mana kyakyawan karshe Ameen suma Ameen)


  Ana gama jana'iza Abdulmajid ya kallu bawansa yace " mu fita."
 Turashi yai sukai waje.
 Motarsa ya sakashi sukai waje.
Sai a sukai nisa akan titi sannan Ya juyo yace "ina zamu?"
 Idanunsa a rufe yace " ina zani? Ni kaina bansan inda zani ba, banida gun zuwa......"
 Hawayene suka kara zubomai.
 Yace kaini can bayan gari iska nake san sha, nan ya kara jan motar sukai gaba.

  Sunyi tafiya mai nisa kafin su fita can wajen gari.
 Sai daya gangara gefen titi wajen wata bishiyar darbejiya katuwa yace " nan yayi?"
 Abdulmajid ya kalli gun yace yayi.
 Nan ya fito dashi ya d'aurashi kan kekensa.

Abdulmajid ya kalleshi yace " barni anan kai tafiyarka."
 Yace " Yarima....."
 Abdulmajid yace " ina san kasancewa ni kadai, sannan karka kara kirana da Yarima."

 Jiki a sanyaye ya kalli Abdulmajid sannan ya hau mota ya koma.
 Yana komawa gidan sarki gun Abu Turab ya nufa ya sanar dashi abinda ya faru.
 Turab wanda dama nemab Abdulmajid yake yace " kasan gidan Barde?"
 Yace "eh"
 Turab yace " kaje gidan kace Umma na naiman Mairo in ta fito ka kaita gun Abdulmajid a hanya ka ce mata injini nace Abdulmajid na cikin wani yanayi tai kokari ta taimaka ta dawo dashi nan."

 Yace to, Turab yace " ni ban isa fita ba cikin wannan yanayin." nan ya amsa da to yai waje.

  Gidan Barde ya nufa yai yanda Turab yace mai, a mota tana shiga ya sanar da ita sakon Turab.
Gaba d'aya ta kagu su isa inda yake dan jitai gaba d'aya jikinta yayi sanyi, dan ta tabbata tunda taji Turab ya ce a sanar da ita haka to tabbas babban abu ya faru.

  Suna isa ta fito da sauri ko motar bata rufe ba ta taho inda yake da sauri.

  Daga dan nesa kadan ta tsaya tare da kuramai ido, kallanta shima yakeyi idanunsa na zubar da hawaye.
 Jitai idanunta sun ciciko, a hankali take takawa zuwa inda yake idanunsu nakan juna.

  Kusa dashi ta tsaya sannan a hankali tace " me kakeyi a nan?"
 Idanunsa ya rufe tare da kokarin shanye kukansa, tace " me kakeyi anan?"
 Kallanta yai sannan yace " Maryam ni ba d'an Abba na bane."
 Tace " mene?"
 Hawaye na zubomai yana dariyar takaici yace " iyayen da kike tunanin iyaye nane ba sune suka haifeni ba."

 Yanzu kam ta fahimceshi sai dai ta tabbatar inta nuna karayar ta to lalai batasan wani hali zai shiga ba, ta daure tace " to sai ka canza daga Abdulmajid dan ba sune iyayenka ba?"

 Ya kara cewa " yariman da nake tunanin ni yarima ne mai jiran gado ashe ni ba kowan kowa bane."

 Tace " dan kai ba yarima bane sai aka canza ka daga Abdulmajid?"

  Hawaye suka sake zubomai yace " wacce ta d'auki ciki na ta haifen ko sau d'aya ban taba girmamata ba da sunan uwar data haifeni."

 Yanzu kam sai da hawaye suka gangaro mata tace " Yanzu lokaci bai kure ba ai..."

  Yace " Maryam duk wata rayuwa da kika sani nawa ta karyace."
 Tace " hakan na nufin a karyar harda san da kake min?"

  Hannu yasa ya share hawayen yana girgiza kai, kara takowa tai wanda takun ya zama ta karasa daf dashi ta tsuguna inda yake sannan tace " then it's okay."

 Kallanta yai sam ya kasa magana, murmushi ta mai sannan tace " me yasa bakazo guna ba?"
 Yace " ta yaya zanzo bayan ina tsoron kiji abinda ke faruwa, da wani ido kike tunanin zan kalleki? Ga takurar da namiki a da, wanda nije sanadin hanaki auran wanda kike......"
 Hararsa tai tace " ka taba ganin wanda ya auri mijin wani? Duk aurab da kaga anyi a duniya to dama wannan auran Allah yayi sai anyishi, duk kuwa kiyayar dake tsakanin masoyan biyu, duk kuma inda kaga aure bai yiwu  ba to lalai dama Allah baiyi za'ai wannan auran ba, duk kuwa da irin san da suke ma junansu."

  Yace " amma ai nasan kinasan Turab, inaji kamar nine sanadi..."
 Tace " ina sanshi kam, sai dai yanzu a wannan lokacin na tabbatar san da nakemai yana neman zama past tense."
 Kallanta yai, murmushi tai tace " Turab yace ka koma ai jana'iza dakai."

 Ta mike dan taji kunyar kalamanta ta rike keken zata tura.
 Kansa ya juyo saitinta yace " Maryam me kike nufi????"
 Harararsa tai tace " abinda nake nufi bansan ragon namiji."

 Kara kallanta yai yace " Maryam kina nufin......"
 Tace " tambayarka nai? Inka fahimci me nace sai ka had'iye a ranka."

 Bai san sanda wani lalausan murmushi ya bayyana a fuskarsa ba.....



  Magajiya kam an rufeta ruf a wani d'aki wanda yake dulum duhu gareshi sosai, an d'aureta cikin kaca, abinci sai dai a turo mata ta karasa ta d'auka taci.

 Gashi bata saba cin irin wannan abincin ba, ga ta da gardamar tsiya, gani take tafi karfin haka, kin cin abincin tai har dare.
 Wani irin ciwon ciki ne ya shiga murd'a mata, ga bata isa yin magana ba.........


*TURAB*

*KAINUWA*?
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

*Nayi mistake wancan page din zan saka 87 na kara sa 86*

*88*

  Gidan ya cika taf ana ta fama zuwa gaisuwa, Turab jefi jefi yake kallan Mahaifinsa wanda yake ta amsar gaisuwa daga manya manyan mutane, bayan anyi sallar la'asar ne Sarki Ya shiga d'akinsa tare da bada umarnin a kira masa Turab.

  Ya dade sosai baiyi magana ba kafin yace " wanene mahaifin Abdulmajid?"
Turab ya kalleshi a sanyaye yace " Abba!"
Sarki yai saurin cewa " su waye iyayensa?"
Turab yace " d'an gidan Waziri ne."
Kallansa Sarki yai yace " waziri?"
Turab yai kasa da kansa.
Idanu ya dan runtse kafin yace " Tun yaushe kasan maganar nan?"
Turab ya d'ago yace " sanda na fahimci abinda sukama Hajiya, daga nan ne abubuwa dayawa suka fara bayyana."

  Shiru ne ya ratsa kafin Sarki yace " Allah kana ganin abinda ya sameni, kaine ka bani mulkin nan ba ni na ba kaina ba, saboda mulki an bani d'an da ba nawa ba a Matsayin nawa, sannan an halakamin matan da zasu haifar min, an kuma halakamun nawa jikin dan kar na haifa, sai dai duk da haka bazanyi fishi ba saboda ka bani wannan d'an da ke gabana, Allah ina rokanka daka karemin wannan yaran daga sharrin duk mai sharri ka kuma bashi ikon rike mulki da taimakon talakawa, ka bashi ikon yin hukunci na gaskiya ba san rai ba, ka karemin shi daga had'uwa da wanda zai nufeshi da sharri, Allah ina rokonka wannan yaran............."

  Kasa karasawa yai saboda muryarsa da yaji ta fara rawa. 
Duk dauriyar zuciya irin ta Turab sai da hawaye suka zubo masa,kallan Mahaifinsa yake cikin tsananin tausayawa, lalai yau Allah ne kadai yasan yanda bawan Allahn nan yake ji a ransa.
Sarki ya kalleshi yace " Abu Turab."
Nutsuwa Turab yai tare da tattara hankalinsa kan mahaifinsa dan ya fahimci magana mai mahimmanci yake san yi.
Sarki ya cigaba " zan d'auki ragowar mata na uku zamu koma can wajen gari inda nai katan gidana, inaso daga anyi sadakar uku inyi murabus in baka mulkina sannan in tattara inbar gidan nan."
Turab yace " Abba akan me zakayi murabus?"
Sarki ya girgiza kai yace " kana tunanin bayan faruwar wannan al'amarin zan iya cigaba da zama akan mulkin nan?"
" to me kayi? Duk ai laifin ba naka bane na Umma Magajiya ne."
Sarki ya girgiza kai yace " Me kakeso ince? A matsayin na sarkin garin zazzau wanda ya kasa kula da matarsa? Ko a matsayina na sarkin garin wanda matarsa tafi karfinsa?"

  Turab ya motsa baki yana sanyin magana, sarki yace " na gama yanke hukuncina sannan umarnine daga Sarki bawai mahaifinka ba."
Turab yai kasa dakai.
Sarki yace " sannan Magajiya, Hisham da Matarsa, inaso kowa kamai hukunci dai dai da laifinsa, sannan kada ka kuskura ka sassautama d'aya daga cikinsu, wannan ma umarni ne."
Turab ya kalleshi yace " Matar Waziri?"
Sarki yace " kwarai, a matsayinta na uwa, akan me zata amince da abinda mijinta da kanwarsa suka tsara?banda itama tana san jininta yahau mulki?"
Turab ya had'iyi wani abu tunowa dayai mahaifiyar Khadija ce. 
Sarki ya cigaba " sannan duk wanda suke da hannu akan al'amarin nan, da al'amarin Hajiya inaso ka hukunta kowa, shima umarni ne."
Turab yace " to Ranka ya dade."
Sarki yace " Abdulmajid......."
Sai kuma yai shiru dan baisan me zai ce ba, Turab ya kalleshi yace " Abba, me zai hana mu bar maganar matsayin Abdulmajid a junan mu?"
Kallansa Sarki yai yace " mene?"

  Turab yace " Abba wace rayuwa Abdulmajid zaiyi in har akasan asalin abinda ya faru dashi?" 
Sarki yai shiru.
Turab yace " Abba idan muka duba wannan lamari wanda akafi cuta ba kowa bane sai Abdulmajid, gaba d'aya shine aka ruguzawa rayuwa, sannan shine wanda za'afi tausayama."
Sarki yace " Abdulmajid ni kaina bazanso akan laifin da banasa ba ya shiga garari na rayuwa ba, amma kana tunanin hakan zai yiwu?"
Turab yace " a lokacin da akai maganar nan akwai mutane dayawa, sannan shi sirri duk yanda akaso da b'oyeshi in har akwai mutanen da suka sani to fa ba wani abu da za'a iya yi, ina tunanin mai zai hana tunda yanada ilimi sannan yanada babbayar hanya na matsayinsa na d'an Sarki a nemar masa aiki babba na gomnati yabar garin nan, yanda baya kusa ma balle gulma a dameshi, sannan yanada matsayin da ko asiri ya tuno ba abinda zai sameshi."

  Sarki kallansa kawai yake cikin jin dadi, yace " lalai Kai Kainuwa ne, dashe ne wanda Allah yai, ba shakka kasata xataji dadin mulkin ka."
Turab ya sunkuyar da kai cikin jin kunya.
Sarki yace " ni kuma zan kwabi duk wanda ke d'akin sannan ni zan sa a bashi aikin ba sai ka wahala ba."
Turab yace " Godiya nake, amma Abba mai zai hana ka cigaba da zama anan ko dan shawara da nunamin hanya?"
Sarki ya girgiza kai yace " Turab kasan me yasa ake kishi, gaba, tsana, sharri da mugunta akan mulki?"
Turab ya gurgiza kai cikin rashin fahimta, Sarki yace " saboda duk wanda ya d'and'ani mulki sai yayi da gaske zai iya yageshi daga ransa. Mulki abu ne mai dadi wanda a hankali yake halaka zuciya, idan na zauna anan to lalai zuciyoyinmu sasu dinga samun sab'ani, wannan dalilin ne yasa kaga ba'a fiya yin murabus a mulki ba, har sai rai yayi halinsa."

Turab yai shiru baice komai ba, Sarki yace " ka sa a sanar da matan nawa hukunci na."

  Turab yace "  To Abba."

  Sarki ya mike ya shiga band'aki.
Nan Turab ya taso.

********

A can wajen gari kuwa bayan sun shiga mota ita da Abdulmajid, habu na waje a tsaye ta kalleshi tace " Turab yace amaidakai gun zaman makoki."
Yace " Maryam wai ta ina zan iya zama agun?"
Tace " Dama shakuwa ta d'a da mahaifi bata shiga sai jini ya ratsa?"
Kallanta yai baice komai ba, tace " ka taba ji ance d'a da uba ko d'a da uwa sun hadu amma basu san juna ba?"
Yace " eh in rabuwa ta hada iyayensu ko aka tsinci yaran."
Tace " Shi shakuwa da kauna tana shiga zuciyoyi ne basai jini ya ratsa ba, na tabbata Sarki a zuciyarsa kana nan a matsayin d'ansa, sannan kaima na san yanda kake kaunar Sarki a matsyin mahaifi bazai canza ba."
Murmushi ya mata yace " lalai zuciyata tana cikin kunci sai dai wani bangaren yana cikin tsananin farinciki, dan inaji inhar kina tare dani ba bakin cikin da bazan iya shanyewa ba, sannan duk wani tashin hankali inaji indake to lalai komai zaizomin da sauki."

Harararsa tai tace " a hakan? Kana kukan?"
Yace " ai samun nutsuwa danai ne ya sani kukan."
Ta kara harararsa tace " Gaskiya Abdulmajid kai dan yaudara ne."
Yace " ban gane ba."
Ta hade rai tace " inba haka ba ya akai kasan kalaman da zasu sa mace tai sanyi?"
Dariya yai yace " inhar kalamai nane suka saki yin sanyi lalai ban yarda ba, dan kuwa na tabbatar da tuni kin amince dani."
Hade rai tai tace " amma ai kasan nasan tarihinka da ko?"
Yace " Maryam wallahi ai na rantse miki ban taba sanin wata 'ya mace ba, na dai yarda da nayi lalata na taba mace wanda nake dana sani sosai, sai dai Allah bai taba bani damar lalata da wata ba."
Kallansa tai tace " me yasa to in aka ce kanayi baka musawa?"
Yace " Ince me to?"
Tace " yanzu fa kana tunanin bazaka sake ba?"
Da sauri yace " Maryam baki yarda da irin san da nake miki bane?"
Had'e rai ta sake yi tare da gard'e hannayenta tace " inafa nake da tabbas, abu na d'a namiji?"
Yace " Maryam wallahi........"
Sai kuma ya kalleta yace "Wait...Maryam kina nufin kin amince dani a matsayin abokin rayuwarki kenan?"
Baki ta tabe tace " hmmm waya sani?"

  Wani lallausan murmushi ne ya bayyana a fuskarsa yana mata kallan tsantsar so wanda ba algus a ciki.
Mairo ta kalleshi tace " yanzu zan maidakai gida kai zaman makoki."
Kai ya d'aga kawai yana murmushi, tace " tambaya biyu zan maka, Waziri shine mahaifinka?"

Abdulmajid ya d'aga kai tare da kallan window, tai murmushi yake, tace " Mai zakayi idan Babana ya hanani kai?"
Yace " Zanyi iya kokarina wajen ganin ya aminta dani."
Tace " shikenan."

Murmushi sukama juna, sai da aka fara ajiyeshi ta tabbatar Habu ya kaishi gun zaman makoki sannan ta shiga gun Umma.

  Tana shiga Gimbiya na kokarin fita, Mairo ta bita da kallo, kafin ma acemata jikinta ya bata itace, saboda yanayin shigarta.
Tace " Gimbiya Barka da warhaka."

Bilkisu ta juyo ta kalleta tace " Barka da warhaka."

Sannan tace " ban gane ba...."
Mairo tace " Yar gidan Barde ce."
Bilkisu tai murmushi, zatai magana Lantana tace "Mairo kin iso?"
Mairo ta gaisheta sannan tace " Umma fa?"
Lantana tace " tana ciki."
Mairo ta kalli Gimbiya tace " Zan shiga ciki."
Bilkisu tace " inkin fito zaki shigo?"
Mairo ta kalleta tace " zanzo, dama inatasan inga Matar Ya Turab, sai yanzu Allah yai, amma zanzo."

  Bilkisu ta murmusa sannan tai gaba, da alama akwai shakuwa tsakaninta da Umma da kuma Turab.

Mairo ta bi bayanta da kallo, a ranta tace " Allah mai baiwa, gaskita tanada kyau, dan zata iya cewa tunda Allah ya halliceta bata taba ganin mace mai kyau irin na Bilkisu ba, duk da wani bangaren na zuciyarta na dan kishi saboda shi so ba farat d'aya yake fita gaba d'aya ba indai har san na gaskiya ne."

**************

  Bayan ta gaida Umma kuwa ta nufi bangaren Gimbiya, Bilkisu har tayi wanka lokacin ta canza kaya, aka sanar da ita zuwan Mairo.
Fitowa tai taganta a zaune akan kujera, kusa da ita bilkisu ta zauna.
Mairo ta kalleta tace " Da har ina tunanin guduwa, ganin bansan mai zance miki ba in muka hadu."
Bilkisu tace " tunda nazo garin nan banida kowa sai mutanen gidan nan, shiyasa ganinki yasa naga kamar na samu wata."
Mairo tai murmushi tace " ga Ya Turab ba koda yaushe yake nan ba."
Bilkisu tace " sosai."
Murmushi sukama Juna.
Bilkisu tace " tun yaushe kikasan shi?"
"Ya Turab?"
Tace " eh."
Mairo tace " tun muna yara na dawo daga makaranta da gudu..............."
Nan ta bata labarin haduwarsu da abinda ta dingamai na tsokana ganin baya gani.....
Sosai Bilkisu take dariya tace " lalai kinyu kiriniya."
Mairo tace " hmmm ai a aji shi kullum yana zaune shiru dama Khadija ce..........."
Da sauri ta gumtse bakinta sannan ta wayance tace " Abdulmajid ne ma....."
Bilkisu ce ta katseta tace " kinsan Khadija ne?"
Mairo ta kalleta da sauri tace " Naam?"

*TURAB*

*KAINUWA*?
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

* SECOND TO D LAST PAGE*

*89*

Bilkisu tace " Mairo menene tsakanin shi da Khadija?"
Mairo tace " menene kuwa, zumunci ne na ya da kanwa kamar ni."
Bilkisu ta kura mata ido, da sauri Mairo ta mike tace " bari naje gida naga yamma tayi."
Kafin Bilkisu tai magana tayi wuf tayi waje.

""*******""""
Gimbiya ta dade a zaune tana tunani kafin ta mike ta shiga d'aki, tana shiga ya turo kofar tare da sallama.
Juyowa tai ta kalleshi tare da amsamai.
Karasowa yai inda take kawai sai jitai ya rungumeta tsam a jikinsa a hankali yake fitar da wani numfashi, murmushi tai sannan tasa hannu ta shafi bayansa tace " Weldone dear."

  Sun dade makale da juna kafin ya d'ago tare da rike kafad'unta yana kallanta.
Wani sansanyan murmushi tamai tace " ya akai?"
Yace " jikinkinfa?"
Tace " na ware, sai kadan"
Ya kara rungumeta yace " Sannu, yau nasan kinsha wahala."
Tace "kaine kasha wahala, ni me nai? Ya hakurin mu? Ni ko ganin Hajiyar ban taba yi ba,Allah bai nufa ba."
Yace " Hajiya ta girma sosai wanda kowa yake mata tunanin mutuwa, sannan dan rashin imani matar nan ta nemi halaka mata rayuwa ba tare da tayi duba da tsufanta ba."
Bilkisu tai shiru, jiki a sanyaye.
D'agowa yai tare da kama hannunta suka zauna a bakin gado, kwanciya yai tare da d'aura kansa akan cinyarta yana kallanta yace " Kinji abubuwa na tashin hankali da mamaki yau ko?"
Hannunta tasa akan sumarsa tace " a'a, ni duk abinda ya faru abu d'aya yafi tadamin hankali, ganinka danai cikin wani yanayi kana neman fita hayyacinka."
Yace " abinda Magajiya tai fa?"
Tace "Magajiya? Hmm ko kad'an ban tsorata da ita ba saboda na tabbatar in har hankalinka da ta nemi gusarwa ya dawo to tabbas komai zai daidaita, sannan zaka juya kan akalar muguntar da ta shirya."
Murmushi ya mata sannan yace " Thanks alot for believing in me."
Tace " nima Thanka alot."
Yace " ke kuma for me?"
Tace " bakasan abinda yafi komai min dadi ba?"
Yace "a'a"
Tace " yanda nima ka yarda dani kake kuma sanar dani damuwarka."

Murmushi ya mata yace " ni kaina har yanzu ina mamakin yanda ke kadai zuciyata ke iya bod'ewa damuwarta."
Tace " ina rokon zuciyarka da ta kara sanar dani d'amuwa d'aya da na ke san ji."
Kallanta yai yace " name kenan?"
Kallansa tai sannan tai kasa da idanunta a hankali ta furta Khadija!"

  Kallanta yai sannan ya mike daga kan cinyarta ya zauna yace " Khadija?"
Juyowa tai ta kalli kwayar idanunsa.
Mikewa yai hannu tasa ta riko hannunsa da sauri tace " Yarima."
Tsayawa yai sai dai bai juyo ba, tace " inada tsananin kishi hakan ne yasa nakesan na auri wanda yake sona sosai, sai dai duba da yanayin gidan dana fito nasan tabbas Mahaifina bazai bada ni ba sai ga wani mai matsayi na sarauta, sannan nasan Sarki bazai taba zama da mace 'aya ba, in har ka b'oyemin tsakaninku shine zai sani jin ba dadi a raina bawai shirunka ba."

Turab ya juyo ya kalleta sannan ya sakar mata murmushi yace " Later, zan sanar dake komai amma ba yanzu ba, banasan wani abu ya shiga zuciyarki a wannan lokacin, zan sanar dake in har kika sake tambayata, sai dai ba wannan lokacin ba."

  Murmushi tai tace " nagode sosai."

  Kusa da ita ya matso ya rikota jikinta.
Sai da sukai sallar isha'i sannanya sanar da ita hukunci sarki da kuma abinda suka yanke akan Abdulmajid sosai ta yaba da shawarar da suka yanke.

  A ranar uku kuwa Mai Martaba Sarki ya tattara mutane ya sanar dasu hukuncinsa, sannan dama ya riga ya hana mutanen dake d'akin zancen Abdulmajid.

  A lokacin ne aka nad'a Abu Turab a matsayin Sarkin garin Zazzau.
Kasancewar anyi rasuwa a gidan yasa ba'ai wani taro ba na biki a gidan Sarautar ba.

Turab na hawa kan mulki Sarki yace " kafin na bar gidan nan inaso ka yankema mutanen da ya kamata su amshi hukuncinsu a hannunsu."

Turab yace a fito da masu laifi su gurfana.

  Abdulmajid na zaune jin ance a fito dasu yasa jikinsa yai wani irin sanyi.
Turab yace " a fara shigo da matar nan data mai sharrin fyade, dannan wacce take sama Sarki magani da kuma wacce take sama Hajiya, dan dama a kwanakin nan duk sai da aka kamosu."
Turab ya kalli Matar data mai sharri yace " duba da yanayin laifinki  an yanke miki hukunci yin aiki a gidan nan, aiki na karfi na jiki na shekara biyu ba tare da an biyata komai ba."
Sannan ya kalli Sarki, murmushi mai martaba yai hakan yasa ya gane hukuncin yayi.
Turab ya kalli Matar da take sama Sarki magani.
Yace " kin aikata babban laifi na sa magani ga Mai Martaba, duk da bakisan maganin menene ba kinyi laifi na sakawa, sai dai rubutama Hajiya da kikai yasa za'a miki sassauci ke kuma zakiyu aiki kema na shekara uku ba tare da biya ba."
Sannan ya kalli matar da itace shaida a garesu yace " kema kinyi kuskuren sawa Hajiya magani duk kuwa da anyi amfani da rashin lafiyar kaninki gun umartarki da yin wannan aiki sannan kin kula da Hajiya kin kuma bada shaida akan abinda aka saki kika aikata hakan ne yasa za'a kaiki asibitin Abu inda kaninki yake dan yin aiki acan na karfi na shekara d'aya."
(In akacema Mace aikin karfi ina nufin, girki, wanki, wanke wanke, wanke band'aki, surfe, daka, sisika da sauransu.)

  Shigowa akai da Jakadiya, kallabta yai sannan yace " Jakadiya kinsan laifin ki?"
Jakadiya ta sunkuyar da kai.
Turab yace " laifin sani tare da takewa, sannan laifin amfani da wannan sanin dan cikar burinki, na cireki daga matsayinki na babbar jakadiya a wannan gida, sannan zaki bar gidan nan batare da kin d'auki komai ba, ki koma kauyenku ki zauna."

  Jakadiya kam jitai kamar tasa kuka dan tabbas tana cikin garari.

Hisham aka shigo da shi.
Turab ya kalleta sannan yai shiru, can yace "Waziri da farko dai daga wannan lokacin na cireka daga matsayinka na waziri sannan kai namiji ne wanda yake uba yake kuma da mutane a karkashinsa, sai dai bakai amfani da wannan matsayin da kake dashi ba, ka kashe mutane biyu a daura, wanda shikadai ya isheka karasa rayuwa a gidan yari, ka biyewa Magajiya kunyi ta tafka laififuka wanda bazasu irgu ba, hakan ne yasa za'a maidakai gidan yari ka karasa rayuwarka acan wato d'aurin rai da rai."

  Hisham ya runtse idanunsa hawaye suka shiga zubomai, mai rayuwar nan ta dada mai? Kallan Abdulmajid yai wanda yai saurin d'auke kansa tare da juya kansa gefe dan yanaji wani abu na ratsashi.

  Hisham yai murmushi tare da rusunawa yace " ina godiya da alfarmar dakama abinda na haifa, ina kuma rokon ka daka taimaka ka sassautawa matata ko dan kula da zuri'a ta."

Turab yace " a d'aukeshi."
Nan akai waje dashi yana kallan Abdulmajid.
Anje fita dashi ana kokarin shigo da Magajiya.
Gaba d'aya ta canza tana ganinshi tahau kakari alamar masifa, duk ta rame, ga wani azababban ciwon ciki da take kwana dashi kullum.

Ana shigo da ita aka fara gulmace gulmace.
Kalan kallo suka fara da ita, wani irin kakari take tana neman kwacewa ganin Turab akan kujerar mulki, sai wani kakari takeyi Tana girgiza kai ba kakkautawa.
Turab ya kalleta duk ta canza, nan aka tad'iye kafarta aka gurfanar da ita, Turab ya kalleta yace " Rashin godiya ga abinda Allah ya maka, rashin sanin darajar mutum, d'aukar rayuwar d'an adam kamar kaice kika bashi, halaka duk wani abu da yake neman kawo miki cikas a rayuwa, san zuciya da tsantsar san kan da kike dashi, laifufukan da kika aikata banaji zasu irgu, wayasan tun wani lokacin kike aikata laifufuka? Ba imani ko kadan a ranki. Sannan a wannan lokacin ma banaji zuciyarki tana dana sanin laifufukan data aikata, na tabbatar da za'a baki wuka to tabbas zaki nemi kawar da abinda bakyasan ganin a fadar nan."

  Turab ya kalli Sarki wanda kallanta kawai yakeyi, Turab yace " Ina rokon Takawa da ya hukunta wannan matar, dan kuwa kai ta cutar cutarwa ta ruwan sanyi wacce tafi ciwo."

Sarki ya kalleshi sannan ya kalleta yace " abinda nake jira kenan, abin kuma da ya tsayar dani kenan, jira nake naga yanda matar nan zatai in zata wanda ta tsana a duniya zai yanke mata hukunci, sai dai inaso tasan abu d'aya a cikin mutanen nan, ni Abdussamad na yanke igiyar aurena da Magajiya, na yanke duk igiya ukun dake kanta."

  Wani irin gurnani ta shiga yi.

  Turab ya kalle ta sannan ya kalli Abdulmajid.

  Magajiya ta shiga kokarin mekewa cikin tsananin tashin hankali, Turab ua runtse ido, a hankali muguntar Magajiya da tsantsar rashin imaninta ya dinga dawomai a zuciyarsa, tabbas ko gidan yari bata cancanta ba, a kalla acan za'a bata abinci zakuma a bata gurin kwana.

Gyaran murya yai sannan yace " Magajiya, daga wannan lokacin an saukeki daga matsayinki, sannan zakibar gidan nan ba tare da komau ba sai kayan jikinki, zan sanar a garin nan akan kar wanda ya kuskura ya bata muhallin zama, wannan umarni ne daga gun Sarki, abinda ya dace da ita shine ta shiga gari taga yanda mutane suke, taga yanda marasa muhalli suke rayuwa, yanda mahaukata suke rayuwarsa, su wad'an nan ba wai tsanarsu Allah yai ba ya gusar musu da hankali, a'a wasu kaddara ce ta Allah wasu kuwa irinku ne wad'anda suka haukatasu, kije kiga yanda ake rayuwa, kije kiga yanda abinci yake samuwa da tsananin wuya, wannan shine abinda ya dace dake, kije kiyi rayuwa wacce yan uwanki basu isa sun taimaka miki ba, in kikai irin wannan rayuwar ta shekara biyar daidai lokacin kin manyanta da yawa, sai a dawo dake gidan yari ki karasa rayuwarki acan."

  Kakari take yi har muryarta ta kakari na neman d'aukewa, wani irin karfi take badawa kamar zata kamo Turab agun nan, yanda kasan mahaukaciya sabuwar kamu.

Nan akai waje da ita kakari take kamar zata ciro ranta........

  

*Turab*

*KAINUWA*?
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

*LAST PAGE*

*90*

Yanda aka fito da Magajiya sai kallanta akeyi, kan kace me an cika ana zuwa kallanta labari duk ya baza akan maganin da take ba Sarki na hana haihuwa, sannan maganin da ta sama Hajiya dan kasheta, nan fa kowa ya fara tofa nashi albarkacin bakin.

  Ana fitar da ita waje a ka tsaya da ita dan jiran umarnin daga sarki na asaketa.
Tahowa yai gadan gadan rike da wani makeken katako yayo kansu, kallo daya zakamai kaga bigegen d'am shaye shaye, dogarawan dake tsaye kanta kuwa suna ganin haka suka fyalla da gudu, yanda taga yayo kanta tasan tabbas sai ya maka mata, da sauri tai kasa ta tsugunna, yana karasowa kuwa ya d'aga katakon nan ya maka mata a gadan bayanta.
Ga ba baki bare ta calla kara, wani irin zakwadi na zafi ta s
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *KAINUWA* A Historical Fiction* by Ayusher Muhd Gimbiya 1 15,759 08-21-2019, 01:53 PM
Last Post: Ebony Lacklock
  *JALILAH* by Ayusher Mohd* Gimbiya 0 20,165 09-10-2018, 09:03 PM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,758 06-16-2018, 10:17 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,349 06-16-2018, 10:09 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,717 05-07-2018, 11:04 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 4,309 05-07-2018, 10:54 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,636 04-30-2018, 01:16 PM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* A Historical Fiction* by Ayusher Muhd Gimbiya 0 4,614 03-29-2018, 11:44 AM
Last Post: Gimbiya



Users browsing this thread: 1 Guest(s)