The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*KAINUWA* A Historical Fiction* by Ayusher Muhd
#1
? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
(q _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

  *32*
Magajiya ce xaune a kilisar Mai Martaba, ta umarci kowa ya bargun, sun dade a zaune kafin cikin kasaitarta tace " Ranka ya dade ashe Abu Turab yana kano?"
 "Eh." Abinda yace kenan yai mata shiru.
 Kallansa tai fuskarta dauke da murmushi tace " Daren jiya na aika yazo mu gaisa sannan yaci abincin dare a guna akacemin ai yayi tafiya."
 
  "Ha ka." Nan ma daga fadar haka taji bai ce komai ba, sosai ranta ya b'aci ammabta daure tace " Dama zuwa nai in fadama wata magana."

 "Inajinki."
 Ta nisa sannan tace " tunanin hada auran Abdulmajid da Gimbiya Bilkisu nakeyi."
 Yace " hmm shawarace mai kyau hakan sai ki aika musu da takarda."
 Kallansa tai cikin mamaki tace " ai kai ya kamata ka aika Ranka ya dade."
 Kallanta yai sannan yadan murmusa yace " fadamin kikai ai ba shawara kika zo nema ba, kinga kuwa banida abin cewa."

 Kallansa tai sannan tace " Ranka ya dade ka taba nuna cikakiyar kulawarka ga Abdulmajid? Kana sane lokacin auransa yayi amma sam banga kana nema masa wacce ya kamata ba."
 
 Kallanta yai yace " kin taba bani girmana na uba a kan al'amuransa?"
 "Me kake nufi da kalamanka?"
 "Inkin gama inaso in runtsa kafin na fita fada." 
Ya fada tare da dan lumshe idanunsa.
 Ba shakka ranta yayi tsananin baci ace kamar ita Magajiya ita mai martaba zai wulakanta?
 Kallansa tai rai a bace, mikewa tai ta tako a hankali har inda yake ta tsugunno inda yake ta sakar mai wani sansanyan murmushi tace " Takawa kardai ka manta da Abu Turab idanunsa basa aiki, Abdulmajid shine kadai wanda zai kula dashi, ina ganin ya kamata ka kara karfafa zumuncin dake tsakanin 'yan uwan biyu, ganin Abdulmajid shine babba kuma magajinka."
 Kallanta yai kawai, itakuma ta mike cikin salan tafiyarta, babu wanda ya isa ya juyata ko kuma ya nemi wulakantata, dolene abi abinda takeso inhar ana bukatar zaman lafiya a wannan gidan.

 Mai Martaba kam bayanta yabi da kallo sannan ya girgiza kai har ta fita yana kallanta, a fili yace " nine sarki ba ke ba, sannan da Abdulmajid da Turab karkashin ikona suke da ke kanki, tabbas zan nuna miki kashin namiji da mace ba d'aya bane."

  *********

 Abu Turab kam suna isowa ya wuce b'angaren Mahaifiyarsa, mamaki ne ya kamata da Lantana tace mata ta fito ga Abu Turab nan ya dawo.

 Zama tai a saman kujera, shi kuma yana zaune a kasa ya lankwashe kafafunsa.
 Bayan ya gaisheta ne ya nemi a basu guri, nan su Lantana suka fita.
 Kallanta yai yace " Umma me mai Martaba yake nufi da auran Bilkisu?"
 Kallansa tai sai dai babu mamaki a idanunta tace " Mahaifinka yana san ka gaje shi."
 Yace "in gajeshi? Ban fahimta ba."
 Basira tadan yi yake tace " Ni kaina bansan me yake nufi ba."
 Mikewa yai waje.
 Yana fita Lantana ta shigo da sauri, tace " Tuba nake ranki ya dade, banyi da nufin jin abinda kuke cewa ba sai dai na taho kawoma Uban gidana ruwa naji abinda yake cewa."
 Basira tace " ba komai Lantana."
 Lantana ta ce "Amma Bakya ganin hakan shine ya dace? Ko kin yafe musu abinda suka aika tama Yayanki?"

 Abu Turab wanda ya dawo domin sanar da ita kartama Mai Martaba maganar tukunna yana tsaye jikin kofar yaji wannan kalaman na Lantana.
 Ji sukai yace " Me kike nufi da kalamanki?"
 Basira ta kalleshi a d'an razane,itakam Lantana jikinta rawa ya shiga yi.
 Takowa yai har inda suke, Lantana ta mike da sauri ta koma ciki.

 Zama yai daf da mahaifiyarsa gwiwowinsa na kasa yace " Umma meke faruwa? Dama ni nasan akwai abinda kika dade kina b'oyemin sai dai nayi alkawari bazan taba fara miki magana ba."

 Jiki a sanyaye cikin sanyin murya tace " Tabbas akwai abinda nake b'oyema, a koda yaushe in nai yunkurin sanar dakai sai inji bazan iya ba saboda tsoron kar in sa ma d'aukan fansa a ranka."

 Yace " Umma dan Allah ki sanar dani tun daga farkon rayuwarki."

 Basira ta numfasa sannan tace " Sunana Basira........................................................................"
 Haka Basira ta zayyanemai kaf abinda ya faru da ita tundaga fyaden da aka mata zuwa auranta da Mai Martaba ba da sanin matansa ba, har zamanta a can gidan da kuma zaman da tai anan gidan, da matsalolin data samu bayan ta samu ciki har zuwa haihuwar tashin hankalin da ta fuskanta na zuwan Hisham da jin maganganunsu.

 Tana kuka tace " Kaji dalilin dayasa muka taso a gidan Malam"

 Idanun Abu Turab sun kada sunyi wani mugun jaa, ita kanta bata taba ganinsa cikin wannan yanayin ba, fuskarta ta canza bakinsa kawai yake motsawa ta ciki, sai dai kaga alamu ta waje.

 Handkerchief ya zaro daga aljihunsa ya mika mata baice komai ba ya juya ya fita.

 Tabbas tasan ya shiga cikin tashin hankali, sai dai ita kanta mikin daya fara dishashewa a xuciyarta ne ya tashi.

 Sam ko sandar ma bai d'auko ba, yana kokarin shiga b'angarensa yaji muryar Abdulmajid "Kai Blind man."
 Wani mugun kallo ya juyo ya wurgamai sannan ya bud'e kofa ya shiga ciki.

 Abdulmajid ya juya ya kalli masu kula dashi cikin tsananin mamakin abinda ya gani yace " kunga idanun Abu Turab? Ba kallona yai ba kuwa?"

 Sukam basu gani ba sukace " Tuba muke ranka ya dade amma bamu gani ba."

 Cikin fada yace " karya kuke munafukai, xakuce baku gani ba, anya kuwa idanun makaho ne wannan?"

  Abu Turab kam yana shiga d'aki ya kule ya zauna a kan gado, sai dai ba wanda yasan me yake tunani yake kuma sakawa a ransa, daga shi sai mahallicinsa.


**********

  A kano kuwa Bilkisu da kanta ta sanar ma Mahaifinta tana kaunar Abu Turab hakan yamai dadi dan shi kansa ya mai.

 Shi kuwa Hisham ya isa kano bayan azahar, bangaren Gimbiya Sadiya wato Amarya ga mai martaba, bayan an masa iso.

 Bayan sun gaisa ne kansa na kasa yace " Gimbiya nazone dauke da sakon Gimbiya."
 Murmushi tai tace " Magajiya ikon Allah wani sakon ta aikoka dashi?"
 Yace " Maganar auren Gimbiya Bilkisu da Yarima Abdulmajid"

 Kallan mamaki tamai tace "Me kake nufi? Na da'uka  ai an bar wannan maganar ganin yau d'innan Abu Turab yabar gidan nan, kuma inada labarin Bilkisu ta amince dashi."

  A razane ya d'ago yace " Gimbiya ta yaya Yar sarki guda zata amince da Makaho? Na tabbata asiri suka mata."
 Kallan rashin fahimta tamai tace " waye makahon kenan?"
 "ABU TURAB mana." Ya fada kansa tsaye.
 Tace " ban fahimta ba, a iya dai sanina banji ancemin yaran nan makaho bane."
 Murmushin jin dadi yai yace " kisa a tambayo miki gimbiya."
 Tace " in kuwa hakane na tabbata Mai Martaba bazai aminceba."
 Nan ta aika a kira mata Jakadiya.

 Bayan Jakadiya ta gaisheta ne Gimbiya Sadiya ta kalleta tace " Nikam ya Abu Turab yake ne? Yanada wani nakasu ko abin kushewa a tattare dashi?"

 Jakadiya tace " ban fahimceki ba Gimbiya."

 Gimbiya Sadiya tace " hakkinane a matsayina na matar Sarki intambayi wanda Bilkisu zata aura."
 Jakadiya tace " Tuba nake ranki ya dade, amma Yarima Turab bashida wani nakasu a jikinsa."

 Da sauri Hisham yace " idanunsa fa?"
 Tace " idanunsa kuma? A iya sanina bashida wata matsala na gani da idanunsa."
 Hisham ya kalleta yace " Jakadiya ki tuna da kyau, baki ganshi da sanda ba?"

 Kallan mamaki tamai tace " Na kasa fahimtar wannan tambayar taka, ni dai  a iya sanina bashida wata sanda kuma sunyi magana ta fahimta da Gimbiya, ya kuma shiga gun Takawa."

 Gimbiya Sadiya ta kalleta tace " tashi kije Jakadiya."
  Zufa ne ya shiga ketoma Hisham tsananin tashin hankali, kasa yarda yai da wannan zancen ya mike yace " bari naje gun Mai Martaba mu gaisa."
 A ransa kuwa so yake yaje ya dan tambayeshi a dabara.

  Yana mikewa yaji kafafunsa sun mai nauyi, da kyar ya iya d'agasu.
 Haka ya garzaya fadar sarki.
 Bayan ya shiga ne suka gaisa da Mai Martaba.
 Sarki ya kalleshi yace " Waziri ba dai biyu Abu Turab kai ba?"
 Hisham ya dan yi yake yace " a'a na dai shigo garin ne naga ya dace inzo mu gaisa."
 Sarki yace " hakan yayi,  Abu Turab sun tafi yau."
 Hisham yace " ai na d'auka ma sai zuwa gobe zasu taho, ko dai abin bai yiwu bane?"

  Sarki yai murmusa yace " zamu aiko da amsa cikin wani satin."
 Hisham ya rasa ta inda zaiyi tambayar ganin yanayin Sarki alama ce ta gamsuwa da yai da Abu Turab.
 Sallama yamai sannan ya mike ya fito.
 Sai da ya kara tambayar wasu fadawa kowa ya tabbatar mai ba sanda a hannun Abu Turab  sannan ya juya ya shiga mota.
 Jiyai kansa ya dau wani zafi yana rasa ta inda zai fara tunani.
 Me ke faruwa?
 Kenan kallansu kawai yake?
Tabbas lalai yau yanada mumunan labari, suna mai kallan dan tsako ashe kura ne?????


  Nace Daga Baya kenan Hisham....?

*TEAM ABU TURAB ??*
? *KAINUWA*?
 
 *33*
Hisham ya iso Zariya cikin tashin hankali, ana magrib yana shiga bangaren Magajiya.
 Zaune take gefenta kuma Khadija ce tana duba mata wasu kayayyaki, Abdulmajid kuma na gefenta na hago.
 Hira sukeyi da Abdulmajid sama sama, itakam Khadija bata sa musu baki a zaune kawai take tana aikin da aka sata.
  Can cikin hirar tasu ne Abdulmajid ya kalli Khadija yace " ke dama inada magana dake."
 Kallansa tai batace komai ba.
 Fuskarsa a had'e yace " haryanzu baki daina zuwa b'angaren Abu Turab ba ko? Kina mace ko kunya."
  Magajiya  ce ta kalleta tace " Khadija me kenan?"
  Kanta ta maida kan kayan tace " meye amfanin ma in naje tunda ba kulani yake ba?"
 Dariya Abdulmajid yasa yace " kinji kunya wlh, kina mace kina bin namijin da baya sanki."
 Zatai magana Hisham ya banko kofa cikin hanzari.
 Jin yanda a ka bugo kofar yasa duk su ukun suka maida ha kalinsu kan kofar.
 Hisham na shigowa ya kalli Khadija yace " bamu guri."
  Mikewa tai tsam dan dama ba san zaman takeyi ba sai dai jikinta ya bata ba maganar arziki zasuyi ba.
 Tana fita ta tsaya a jikin kofar d'akin.
 Hisham ya kalli Magajiya cikin tashin hankali yace " Magajiya!"
 Ita kanta hankalinta ya tashi ganin ita data aikashi maganar aure kano? Ya dawo mata a haka?"
 Kallansa tai tare da tattara hankalinta kansa.
 Yawo ya had'iya sannan yace " yaran nan yana gani Magajiya."
 "Yaro? Wani yaro kake nufi kenan?"
 Yace " yaron nan mana da baya gani."
 Idanu tad'an juya tace "wai wani yaran kake nufi? Nibansan wani yaro ba."
 Abdulmajid ma yace " wani yaro kake nufi Kawu?"
 Hisham yace " Yarancan Abu Turab."
 Dariya Magajiya tai tace " Waziri? Ko dai gajiya ta fara ratsaka ne? Me kake san fada takamaimai?"
Hisham ya kallesu cikin wani yanayi yace " Wlh da gaske nakeyi, yarancan Abu Turab idanunsa garau suke."
 Abdulmajid ya mike tsaye yace " ni wlh na dauka maganar arziki zaka fada ashe tsokana kazo da ita, ni nayi masallaci."

Hisham ya kalli Magajiya yace " Magajiya na taba miki karya akan harkar dana san bazata amfanemu ba?"
 Wannan lokacin kam ta kalleshi kallan nutsuwa, Abdulmajid ma ya ja ya tsaya. 
 Khadija kam da baya da baya ta juya tai waje cikin tashin hankali, me kenan?

Hisham ya kalli Magajiya sannan ya kalli Abdulmajid yace " dayaje kano a garau yaje musu."
 Magajiya ta kanne idanuwanta tace " ban fahimta ba."
 Nan Hisham ya zayane mata kaf abinda ya faru na zuwansa.
 Tashin hankali karara ne ya bayyana a idanun Magajiya, kallansu tai cikin tashin hankali tace " ku bani guri."
 Nan suka mike suka fita.
 Abdulmajid ma bangarensa ya wuce cikin d'emuwa da rashin sanin abinda zaiyi.
 Shi kuma Hisham yai waje.
 Magajiya ta kasa zaune ta kasa tsaye ba shakka in har hakan ne lalai kaf duniya ba wanda ya taba rainamin hankali irin yaran nan.

  Kwallawa wata mai kula da ita tai, cikin hanzari ta iso.
 Bata ko juyo ta kalleta ba tace " kiramin Abu Turab."
 To tace kawai tai waje itama.

Abu turab yana zaune kan sallaya tilawa yakeyi cikin daddadan muryarsa, yau ko masallaci bai je ba dan bayasan ganin kowa. 

 Garzali ya mai sallama, sai daya kai aya sannan ya amsa mai.
 Garzali ya matso ya tsugunna sannan ya sanar dashi sakon Magajiya
Ya dade kafin yace " ace mata ina zuwa."
 Nan yai waje.
 Sai dayai sallar isha'i sannan ya mike ya fito, Garzali ya mikamai Sandarsa wacce Lantana ta kawo.
 Amsa yai sannan yai gaba Garzali yabi bayansa.
Bayan an mai iso ya zauna a kilisarta sannan ta shigo cikin takamarta.
 Idanu ta kafa mai har ta zauna shikam fuskarsa a had'e take yana zaune kansa a kasa.
  Bayan ta zauna ne ta kalleshi tace " Abu Turab ka iso?"
 "Barkanki da warhaka Umma Babba."
 Murmushi ta sakarmai sannan bata amsa ba tace " kiranka nai in baka wani labari."
 Shima bai amsa mata ba dan lalai ji yake bazai iya kallanta ba saboda tsananin tsana.
Magajiya tacigaba " Wani dan tsakone kurma ya taso karkashin kulawar kura, ita kurar dama tanada nata d'an hakan yasa ta had'asu duka ta rike, a kwana a tashi sai kurar nan ta tsufa, ta fahimci dole tana bukatar barma d'anta mukaminta a daji.
  Kasan abin mamaki?"
 Abu Turab ya d'ago suka had'a ido, bai d'auke idanunsa daga cikin nata ba yace " bazai wuce wannan d'an tsakon kurma yace shi yake san aba wannan mukamin ba."
Ta kuramai ido itama tace "Haka! Ashe ka harbo jirgin, sai dai kasan wani abun tsoro a labarin?"
 Kallan ban fahimceki ba ya mata tace " Tun daga sanda Kurar nan ta fahimci kudurin wannan d'an tsakon har yau ba wanda yasan inda wannan d'an tsakon yake."
Wani lalausan murmushi ne ya bayyana a fuskar Abu Turab yace " sai dai ban fahimci abu d'aya ba a labarin, d'an tsakon dama can kurma ne ko kuwa yayi hakan ne da saninsa ya noke bakinsa?"
Idanun Magajiya ne suka d'an canza sai dai da sauri ta maida fuskarta cikin yanayin hankali a kwance tace " hmm wannan shine abinda ya sa kurar nan dana sani."
Gani tai ya saki wata yar karamar dariya har hakwaransa suka bayyana ya kalleta yace " Tuba nake Umma Magajiya, na saki a duhu danai na nuna miki nidin bana gani."
Wannan karan kam duk yanda taso ta b'oye bacin ranta ta kasa, karara ya nuna a fuskarta.
 Abu Turab ya rangwadar da kai yace " umm ya zamuyi yanzu?"
 Tace da me kenan?
 Yace " dan banaji zan iya yafemiki."
Kallo tamai cikin mamaki tace " bakaji xaka iya yafemin kamar ya kenan?"
Fuskarsa ce ta canza idanunsa sukai jaa, ya kalleta yace " bazan taba yafe miki ba daga ke har yayanki, abinda yama yayan mahaifiyata da matarsa da ke da kika umarceshi a sanadiyar kokarin rabani da duniya da kukai kuka jamusu mutuwa, ni Abu Turab in har Basira da Abdussamad sune suka haifeni sai na sa an muku hukunci daidai da laifinku."
Wata muguwar dariya ta saki, wanda ya sashi tsayawa yana kallanta tace " kai a suwa kenan?"
 Yace " a wanda yake da damar zama Sarki."
Ta ja tsaki tace " Shekaruna d'aya da mahaifinka, hakan na nuna nid'in batayau bace, ba kai ba hatta mahaifinka bai isa yaja dani ba."
Abu Turab ya d'an juya bakinsa sannan ya had'a lab'ansa yace " well, shi daban nid'in daban, mu zuba mu gani."
Tace " shikenan mu zuba mu gani, na baka sati biyu kacal, ina zaune anan zakazo gwiwowinka biyu ka nemi gafarata."
Yace " ina fatan hakan ta kasance."
 Kallan juna sukai, kansa ya saukar kasa ya juya kansa gefe tare da d'aukan sandarsa yace " Umma Babba nagode ni zan wuce, ki huta lafiya."
 Kallan mamaki tamai, gani tai ya sa sanda a gaba kamar makaho.
 Idanu ta kuramai har ya fita, ta murmusa tace " hmm a kashi 100 na baka 40, ba laifi ka iya b'oye fuskarka da abinda ke ranka, ko dayake d'an Abdussamad ne."
Fuskarta ta kuma had'ewa tace " kai har ka isa? Kamar ni? Kamar ni Magajiya ka rainan hankali?"
 Kwafa ta saki.
Abu Turab kam na fita ya juyo ya kalli bangarenta sannan ya juya ransa a b'ace.
 *********
 Itakam Khadija ta shige d'aki ta kwanta akan gado, me ke faruwa? Ya Turab yana gani? Anya kuwa? Ta yaya? Yaushe?
 Itakam ta kasa yarda da abinda taji, ba dai wani sharrin zasu kullama bawan Allah ba?
 Da sauri ta mike zaune tace " dole in fadama Yaya gobe akan abinda sukace."

*TEAM ABU TURAB

*34*
 
 Washegari.

Da safe zaune yake a gaban Mai Martaba a cikin Turakarsa.
 Mahaifinsa ya kalleshi cikin kulawa yace "Turab me yasa ka dawo tun jiya? Sannan tundaka dawo baka zo ba."
Fuskarsa a d'aure take dan sam ba fara'a a cikinta kallansa yai yace " Dama zuwa nai na sanar dakai zan auri Bilkisu yar gidan Sarkin kano."
 " Alhamdulilah nagode kwarai na kuma ji dadi daka fahimceni."

  "Bayan umarnin auranta daka bani a yanzu auranta yana tattare da amintata, a da auranta zanyi saboda umarninka, sai dai yanzu zan aureta ne dan kaina."
 Fuskar mai martaba ta kara fadada da farinciki yace "naji dadi yanda kuka fahimci juna."
  Kallan Mahaifinsa yai yanajin wani radadin takaici a ransa, yace " zan koma."
    "Abu Turab!"
 Komawa yai ya zauna sannan ya kalli Mahaifinsa dan yanda yaji ya kira sunansa yasan yana bukatar nutsuwarsa.
Mai Martaba ka kalleshi cikin kulawa yace " Abu Turab me yasa kake so ka b'oyemin abinda ke ranka? Me yasa bakasan mudinga raba damuwar dake zuciyoyinmu?"
Shiru yai sai dai zuciyarsa tadan raunana.
 Sarki yace " Meke damunka?"
 Shiru ya kuma yi sai dai a wannan karan ya d'ago ya kalli mahaifinsa da idanunsa da suka canza launi.
 Sarki ya cigaba" Shikenan mubar maganar inhar zuciyarka bata san inji."
 Abu Turab yace " zan koma Abba."
 Mai Martaba ya murmusa yace " to Turab."
 Mikewa yai ya fito daga bangaren mahaifinsa, ba shakka yanasan ya sanar dashi damuwarsa da kuma neman shawararsa sai dai ba yanda zaiyi domin kafin ya kasance mahaifinsa sarki ne shi a wannan garin dole kuma yai abinda ya dace a matsayinsa na sarkin garin.

  Bangarensa ya nufa rike da sandarsa yana gana Garzali da wani na gefensa.
 Sunsha kwanar da zata kaisu bangarensa yaji muryar Khadija tace " Ya Turab."
  Haka kawai ta samu kansa da kin tsayawa dan abinda Mahaifinta sukamai bayaji ko ganin Khadija yana kaunar yi a wannan lokacin.
 Ganin bai tsaya ba yasa ta kara sauri, har tazo inda suke, tace "Ya Turab."
 Tsayawa yai sai dai bai juyo ba.
 Gabansa ta dawo ta kalli Garzali tace " dan Allah kudan matsa kadan zanma Ya Turab magana."
  Nan suka gaisheta suka matsa.
 Kallansa tai tace " Yaya."
 Bai kalleta ba sai dai yace " ya akai?"
 Tace " yaya kana ganina?"
 "Me kike nufi da hakan?"
 Ta kara matsows tace " Yaya ninasan baka ganina, sai dai na rasa dalilin Abba na na zuwa ya fadama Magajiya wai kana gani."

 Kallanta yai, ta kalleshi hakan yasa ya kauda idanunsa, tace " Yaya Please ka kula da su wlh sam hankalina ya kasa kwanciya dasu, na tabbata da abinda suke shiryama."

  Jitai yace " yanzu kinaso ki cemin zuwa kikai kiban shawara akan kula da Mahaifinki? Ko kuwa zuwa kikai ki sanar dani Mahaifinki zai cutar dani?"
  Cikin rashin fahimtar kalamansa tace " Ban fahimceka ba..
.."
 " in mahaifinki zai cutar dani tayaya nake da tabbas din ke bazaki cutar dani ba?"

  Kallansa tai a zabure cikin tsananin mamaki tace " Yaya."
 Yace " da mahaifinki da ni wanene mafi kusanci dake? Wanene wanda yake jininki? Tayaya zan yarda zaki juya ma mahaifinki baya akan wani makaho wanda bakuda hadi dashi?"

 Gaba daya ta ma kasa magana dan batada amsar da zata bashi, tana neman amsar da zata bashi taga ya fara tafiya.
  Idanunta ne suka ciciko a hankali wasu zafaffan hawaye suka xubo mata, me yaya yake nufi?
 Gani tai ya tsaya a jikin kofar bangaren Mahaifiyarsa da alama magana yake da wani, gani tai ya saki fuska ba kamar yanda ya cukule mata ba.

  A hankali ta tako har gefen da suke.
 Mairo ta gani a tsaye a gun rike da kula suna magana, juyawa tai zuciyarta sam ba dadi.

 A bangaren sa kuwa, bayan ya taho daga gun Khadija zai wuce yaji tace " Ya Ina Kwana?"
 Juyowa yai ya kalleta yace " Mairo kece?"
 Tace " nice, Umma ce ta sani in kawo mata abu yau da safe."
 Murmushi yai yace " Mairo kinaji da Umman nan."
  Ta kalleshi tace " Da cemaka akai Ummanka ce kai kadai?"
 Kallanta yai yace " Yar gidan Umma ce ke dama ai."
  Zatai magana yace " ki gaisheta."
 Tace " bazaka shiga ba?"
 Kallanta yai fuska a sake yace " Later."
 Daga nan yai gaba.
  Kallansa tai cikin mamaki dan taga ba haka suka saba ba.

 ************


   Abdulmajid ne zaune gun Magajiya yace " Umma ya kukai Jiyan? An bincika yana ganin?"

 Magajiya ta kalleshi tace " Abdulmajid, ka nutsu sosai kaji abinda zan fada ma."
 Kallanta yai sannan yace " inaji."  

 " Ka shiga hankalin sosai da Abu Turab ka daina masa kallan wanda bashida wayau ko bai san komai ba, wlh wnnan yaran hmmmm"
 Tai shiru sannan tacigaba " kadai bi a  hankali karka kuskura ka fada tarkwansa."

  Abdulmajid ya dan tabe baki yace " ni Umma har wannan yaran ya kai in shiga hankalina a kansa?"
 Ta kalleshi cikin isarta sannan ta ce " Abdulmajid kenan."
 Kara tabe baki yai yace " ni Umma dama maganar aurena nazo muyi, nace tunda dai Bilkisu an riga an hadata da Turab mai zai hana mu juya akalar auran kan Mairo."
 Ya karasa maganar yana dan sosai keya.

 Kallansa tai tace " Mairo? Wacece hakan?"
 Yadanyi kasa dakai yace " Mairo 'yar gidan Barde."
 Barde?bakada hankali ne?"

 Yace " Umma to...."
 Katseshi tai cikin fada tace " nimeyasa baka tunani ne a al'amuranka? Abu Turab zai auri Gimbiya Bilkisu kai kuma dan hauka kacemin wata Mairo? Me yasa ne bazaka dinga abu da tunani ba?"

 Fuska ya hade dan maganar ta batamai rai, Magajiya ta cigaba " kada ka kuskura ka karamin wannan banzan zancen."
 Tana kaiwa nan ta maike tai ciki.
 Kallo ya bita dashi  da alama zai je gun Sarki ya fadamai kuwa dan shi kam Mairo yakesan aura ko ta wani haline kuwa, dan kwanan nan har mafarkinta yake wai sunyi aure.
?
**************
   Kwana biyar da dawowarsu kuwa Mai Martaba Sarki Shu'aib mahaifin Bilkisu ya aiko mutane daga Masarauta akan amincewa da aure da sukai.

  Wannan labari ya tadama Khadija hankali, sai dai duk yanda taso ganin Abu Turab abin ya faskara, itadai ba dama ta shiga bangarensa dan ya bada umarnin hana kowa shiga bayan Mahaifiyarsa, sannan ko a waje tadaina ganinsa.

 Mairo ma wannan labarin ya d'aga mata hankali, sai dai ba yanda zatai dan dama ta riga tasan komai.

 Yau ta gama aikin gida kenan tana 'yan kukuninta na takaicin abinda ake sata yi, wani yaro ne yazo ya sanar da ita ana san ganinta a waje.
 Hijab dinta ta ja ta saka dan bata kawo saurayi bane ko wani na kunya ba.
  Mamaki ya kamata kwarai ganin Abdulmajid a tsaye a jikin soron gidansu.
 Kallansa tai cikin mamaki sannan ta karasa gunsa tace " Malam lafiya?"
 Abdulmajid ya kallesta kalleta yace" Mairo ina kika shiga ne? Sam na daina ganinki dole kika sani na zaro jiki na fito."
 Kallan sa tai tace " ban fahimci inda ka dosa ba."
 Yace " Kin manta me nacemiki ne? Na dauka na sanar dake kedin matata ce."
 Dariya ta saki tace " Matarka? A yaushe kenan akai hakan? A iya tunanina ban amshi sadakin ka ba."

 Idanu yadan rage yace " An kusa ai indai wannan ne, inkuma kinaso in baki yanzu to."
 Ka bani yanzu? Da alama tunanin ka ya fara tafiya ko?

 Matsowa yai a zuciye hakan yasa ta matsa da sauri sannan ta nunashi da hannu tace " Stop Malam! Tsaya anan karka kuskura ka tabani."

 Kallanta yai rai a bace yace " Mairo."
 Tace " kwarai kuwa sunana Maryam wacce ake cewa Mairo yar gidan Barde kanada magana ne?"
 Kwafa yai sannan yai murmushin mugunta yace " ina tausaya miki yarinya randa kika zo hannu."

 Baki ta murguda tace kafa zanzo ba hannu ba.
 Ta juya tai ciki ranta a bace.

Murmushi ya sakeyi sannan ya juya.

*TEAM ABU TURAB*
  
*35*
Wata yarinyace wacce bata wuce shekara goma sha hudu ba ta, kana ganinta kasan yarinyace da take aiki a gidan duba da yanayin kayan jikinta.
 kwankwasa kofar tai mai kula da kofarsa ya bude tare da tambayar ta me ya kawo ta.
 Yarinyar mai sanyi ce kana ganinta kuma kaga shiru shiru, kanta a sunkuye tace " Yarima Turab ne ya umarceni da inzo." 
 Yace " to, shiga."
 Nan ta wuce ta shiga, yanata mamakin abinda ya kawota da magrib din nan.

 Ka idar rayuwar Abu Turab in yai sallar Magrib to sai yayi Isha'i yake tashi, sannan kwanan nan saboda bayasan haduwa da kowa yasa ko masallaci ma ba zuwa yake ba, sai dai yai sallah a gida yai tilawarsa.

 Yarinyar nan tana shiga ta zauna a cikin falon da ba kowa sai shi dake zaune daga can gefe kan sallaya yana karatu.
  Falon ba wani haske gareshi ba, in ba gabansa dake d'auke da fitila kusa da al_qur'anin sa ba, ya kashe fitilun ne saboda kar a fahimci idanunsa yana gani, sannan karatun ma bada karfi yake yi ba.

 Yarinyar tana zaune a bakin kofa har sai dataji kiraye kirayen sallar isha'i sannan ta mike ta fito, sam Abu Turab bai ma san da zuwanta ba, balle fitarta.

 Haka yarinyarnan ta d'au kwana hud'u tana wannan zuwan, kullum kuwa ana magrib take zuwa.

 Mai gadi kofar kam kullum yana mamakin wannan abu, sai dai bashida ta cewa dan da Abu Turab bai yarda da zuwanta ba tabbas da ya haneshi da barinta ta shigo sannan da ita kanta ya koro ta.

 Yau ne kwanan ta na hud'u da fara zuwan, kamar yanda tasaba zama a kofar yau ma haka tai, sai dataga an dade da sallar magrib sai ta tsiri rage kayayyakin jikinta.


  Ta rage daga ita sai wata yar bes sai zanin dake jikinta, kara ta saka tare da fad'uwa kasa.
 Abu Turab dake karatu ya mike da sauri tare da tahowa inda yaji karar, ganin mace yai a kwance tanamurkususu sam bai kula da jikinta ba ganin yanayin da take ciki, da sauri ya karaso ya d'agota yana tambayarta abinda ke damunta, juyi kawai take tana wash wash.
  Masu kula da bangarensa kuwa suna zaune suna hira sukaji wannan karar nan suka taso da sauri.

 Shigowa sukai ganin duhu yasa Garzali ya kuna fitila dan sun dauka wata matsalarce ta faru jin yanda Abu Turab ke cewa lafiya? Ita kuma tana kiran wash.

 Haske ne ya bayyana a d'akin me zasu gani? Abu Turab ne rike da yarinya, gashi cikin duhun nan yarinyar tai amfani da damar ta ballemai botira guda biyu na saman rigarsa.

  Gaba d'aya turus suka tsaya cikin tashin hankali me zasu gani? Meke faruwa?
 Abu Turab ne ya kallesu sannan ya kalli yarinyar dan sai a lokacin ya kare mata kallo.
 Sai kuma a lokacin ya fahimci sharri ne akazo a kula mai.

 Mikewa yai tare da hankad'e yarinyar, ita kuma ta hade kafafuwanta tasa kanta a ciki tasa wani irin kuka.
 Zaiyi magana sukaga an bud'o kofa.

 Abdulmajid ne, gefensa kuma Galadima.
 Kallan sa Galadima ya shiga yi cikin mamaki da tsana yace " ashe dama abinda ake fadamin da gaske ne? Lalai ka zubar da mutuncin masarautarmu."

 Abu Turab ya kalli Abdulmajid wanda yad'an juya yana dan murmushin mugunta.

  Galadima ne yacigaba da cewa " Yanzu Ka kyautama mahaifinka da mahaifiyarka? Kana makaho? Ace har da neman mata? Wa'iyazubillah, dolene gobe a zauna saboda kai, ko kuma yanzu ka wuce muje gun Mai Martaba tun kafin magana ta fita."

  Abu Turab ya jujuya sannan yace " Galadima?"
 Inajinka.
 Abu Turab yace " ina neman alfarma."
 Tame kenan?
 "Inaso ka taimaka muje gun Mai Martaba a wannan lokacin, sannan mu tafi da yarinyarnan, a kuma taimaka a kira mahaifiyata da kuma Umma Magajiya dan su zama shaidar abinda zai faru."

 Galadima yace " dama ai canzamu yanzu, ya kalli Garzali yace " jeka kira Magajiya da Mamansa."
 Nan yai waje.
 Galadima yace " muje."
  Haka suka isa gun Mai Martaba lokacin yana zaune bayan ya dawo daga masallaci.
 Bayan Zagi ya nemarmusu uzuri sun shiga. 
Mai Martaba ya kalli galadima yace " Galadima lafiya?"
 Kallan Abu Turab yai sannan yace " ba lafiya ba sai dai muna jiran isowar shaidu kafin a fara shari'a."
 Sun dan dade a zaune kafin Basira ta fara isowa sannan Magajiya wacce hankalinta kwance ta iso dan dama jiran kiran take in kuma ba'a kirata ba tana jiran labarin korar Abu Turab ko kuma killaceshi da hanashi fita daga bangarensa, a kuma hana kowa ganinsa.

 Bayan kowa ya hallara Galadima ya sanar da duk abinda ya faru ga Mai Martaba.
 Tashin hankali ne karara ya bayyana a fuskar Basira.
 Magajiya ta kalli Galadima tace " Galadima me kake san kafad'a? Kana tunanin Abu Turab keta mata hadi yai ko me? Na san halin Turab bazai yiwu ba abinda ka fada sannan ta ina ma zai fara yin lalata bayan idanunsa ba gani suke ba?"

 Abu Turab ya saki wani murmushi yace " Haka ne Umma Babba ba gani nake ba tayaya zan kama yarinya ta karfi in keta mata hadi?"
 Abdulmajid ya kalleshi yace " bayan kamaka da mukai?"
 Abu Turab yace " ina yarinyar?"
 Nan Galadima ya kirata.
 A jikin bango ta takure kana ganinta a ido kaga salaha.
 Abu Turab yace " ba gani nake ba sai dai ina fatan yarinyar tana nan?"

 Sarki yace " tananan me zaka ce mata? "
 Abu Turab yai kasa dakai yace " Tuba nake ranka ya dade sai dai ina bukatar yi mata tambayoyi."
 Nan Sarki ya bashi dama.
 Abu Turab yace " baiwar Allah ya sunan ki?"
 Tace " Zulaika."
 Yace " Zulaika kin san ni?"
"Eh yarima Turab sunanka."
" Me yake kawoki bangarena?"
 Kuka ta saka tace "kaine ka ce indinga zuwa duk bayan magrib."
 Abu Turab yace " gaskiya ne, amma a ina muka hadu na fada miki haka?"
 Tace " a waje ranar ka fito."
 Allah sarki me nake miki in kinzo?
 Kuka ta saka hakan yasa Sarki yace " karki damu sanar dani duk abinda yake miki.
 Tana kuka tace " tatabani yakeyi ya cire min....
."kuka ne yaci karfinta hakan yasa tai shiru.
 Abu Turab yace "Galadima a ina kaga yarinyar nan da ni?"
 Galadima yace " a falon ka mana."
 Abu Turab yace " waya taba neman mata na lalata a sarari? To ko mata tace ya kamata a ganni da ita a falo?"
 Galadima yai shiru, Sarki ya katseshi da cewa " in idanun ka ya rufe da alfasha fa?"
 Kai ya jinjina yace " haka ne sai dai inada tambaya ga yarinyar, ni ba gani nake ba wanda kowa yasan da haka, ta ina zan iya janyota? Ko ince ta ina zan iya mata karfi?"
 Sarki ya kalli yarinyar yace " bashi amsa."
 
  Tana kuka tace " kirana yake yi."
 Abu Turab ya ce " Umma babba yi mana shari'a aa nan an ganmu a farko farko gaba da kofa kadan sannan tace kiranta nakeyi me zakice?"
 Magajiya wacce tunda ya fara tambayoyinan ranta yake a b'ace tsananin mamakin rainin hankalin dayake musu yasa tama kasa magana, makaho? Wanda kowa yasan da hakan? Kallansa tai jin tambayar daya mata tace " gaskiya ne wannan abin dubawa ne galadima."
 Abu Turab yace " Umma babba dan Allah inada tambaya, in har yarinyar nan ta karfi nake mata me yasa ba'a taba jin kararta ba sai yau?"
 Magajiya ta kalleshi zuciyarta fal bakin ciki amma a fili tai murmushi tace " Gaskiya ne Turab wannan ma abin dubawa ne."
 A ransa yace "Hajiyar Poker Face."

 Abu Turab yace "Galadima in har lalata nake da yarinyar nan ta yaya za'a ganta a nuste ina nufin kayanta da kuma d'an kwalinta, banda rigarta data cire, inasan in tambayeta wani irin lalata ne wannan."

Galadima ya kalli yarinyar yace " ke dan kwal uba........sanar damu gaskiya ko kuma wlh daga nan sai dai ki sameki a gidan horo."

  Idanunta ta zaro a rikice, Abu Turab yace " ke na taba lalata dake? Wannan shine tambayata ta karshe dake in baki fadamin gaskiya ba......"
 Sarki ya karasa " ni kadai nasan hukuncin da zan mata."

 Da sauri ta zube a kasa tace " tuba nake ranka ya dade."

 "Tuba? Name kenan?"
Magajiya ta saki wani lalausan murmushi tace " yaro yaci galaba a dokan farko, bari muga na biyu."
 Dan tasan ko za'a kashe yarinyar nan batasan wanene ya umarceta da wannan aikin ba, kudi da kaya aka kaimata sai umarnin aikin dazatai da wata ta fada mata, wacce ta fada mata kuwa bama a gidan take ba.

  Kuka take sosai yarinyar tana neman gafara.
 Abu Turab ya kalli Magajiya yace " Umma Babba  na gode da aminta dani da kikai."

  Daga nan aka wuce da yarinyar dan mata hukunci da tambayoyi akan laifin data aikata.

 Abu Turab suna fita ya karasa da saurin gun Magajiya wacce take tafe Abdulmajid na bayanta.

 Yana isa ya sha gaban ta yace "Umma ina kara godiya fa."
Kallansa tai tace " karka damu d'ana ina laifi in uwa ta taimaki d'anta?"
 Ya kalli Abdulmajid yace " ba dai anyimin wannan wasan kwaikwayon bane dan labari yakai masarautar kano?"
 Abdulmajid ya makamai harara yace " Wa kake tambaya?"
 Abu Turab yace " ba tambaya nake ba, shawara dai nazo badawa, in har za'a hanani auren Gimbiya Bilkisu ko kuma a sani in nemi gafara da gwiwowina bana tunanin wannan wasan yaran zaici galaba a kaina maganar gaskiya na fahimci ashe Babbar tamu ba iya babban game tai ba."
 Yana kainan yai gaba.
 Magajiya ta kalleshi tai dariya tace " Abu Turab! Nayi laifin farawa da mafi kankanta daga cikin shiri na."
Abdulmajid ya kalleta yace " Umma kefa yake nufi ko?"
 Tace " kwarai zamu gani ai."

*TEAM ABU TURAB ??*
 Shiru yai baice komai ba, zama tai a kujerar dake jikin gadon da alama wani ne ya jawota ya zauna agun, kallansa tai bayan ta zauna ta sa hannunyenta kan gadon tana wasa da hannu a hankali ta ce " Yaya ina cikin wani hali, duk duniya kai kadai ne nakejin zan iya sanar mawa, na rasa yanda zanyi, ina tsoro abubuwa guda uku."

 Shiru tai kafin tai ajiyar xuciya ta cigaba " ina tsoron Abbana da Umma Magajiya dan na tabbata ba tun yanzu ba suke aikata laifi, na biyu ina tsoron kar a cutar dakai."

 Shiru tad'an sakeyi tad'an furzar da iska sannan tace " yaya, bansan ya zanyi ba da alama maganar Saif tananan, ni kuma......"

 Kasa karasawa tai saboda zuciyarta dataji tayi rauni.

  Abu Turab yana jinta har kuma zuciyarsa yakejin kalamanta.

 Hawayen dayad'an ziraro mata ta goge, tai murmushi sannan tace " Yaya sai dai akwai wani abu da yake sani farin ciki, inajin dadi sosai da wannan aikin da za'ama, na rasa meyasa inaji a jikina lokacin ganinka yayi, sannan inhar kana gani ina ganin ba yanda su Abba zasuyi."

  Murmushin yake ta sake yi tace " Kayi hakuri na takurama da nakeyi, na sani yanzu bakasan kula ni."
 Ta mike jiki a sanyaye tace " Yaya inaso kasa abu d'aya a ranka, wlh wlh ni bazan taba cutar dakai ba bama kaiba, bana fata in cutar da kowani mutum a duniya, ko da kuwa a rashin sani ne."

 Juyawa tai xata tafi, dan dama wannan amsar itace wacce ta dade tanasan ta bashi, tayaya yaya zai dubeta yace mata wai itama tana da tabbas din bazata cuce shi ba?"

 Sai datakai kofa ta juyo tace " Allah ya baka lafiya Yaya."

 Nan ta juya tai gaba, juyowa yai da sauri ya kalleta, bayanta ya kalla lokacin data rufe kofar.
 Idanunsa ya runtse sannan yad'an had'a lab'ansa.

 Ba shakka sai ya jure sosai, dan a lokacin datake magana jiyai kamar ya juyo ya lalasheta, Saif? Saifullahi? Wa kenan?"
Tunowa yai da abinda Mahaifinta ya musu, kwafa yai sannan ya juya.

  Itakam tana fita ana kiran sallar magrib.

  A can gida kuwa sai nemanta akeyi dan kuwa Saif kafin ai sallah ya iso,anan sukai sallar Magriba, sai dai shiru ba Khadija.

  Hankalin Waziri da Mahaifiyarta ya tashi sosai.

 Nan yasa aka fito dan nemanta.

 Saifullahi yaro ne ga Senate Kassim, 'yan siyasa ne sannan bayan siyasa sun gaji kudi.

 ******,*


  Mairo kuwa da yamma itama ta shirya fes dan zuwa gun Abu Turab saboda shi yace mata tazo akwai maganar da zasuyi.

 Ta fito zata fito ta gami dashi a zaune a ciki motarsa a kofar gidansu.

 Yi tai kamar bata ganshi ba xata wuce, Abdulmajid ya fito daga motar xai nufota, da sauri ta koma ciki.

 Komawa yai ya xauna a saman mota dan jiranta, Mairo kam tana shiga ciki ta dafa kirjinta tace " nikam wannan akwai dan masifa, na tabbata kuma tsabar rainin hankali ne ke damunsa wlh ba so ba, wannan wani irin rainin hankali ne.

  Itakam tsoronta d'aya shine karta fita tana mai magana Mahaifinta ko wani ya gansu a sanar mai.

 Dole ta koma ciki fitar da batai ba kenan.

*ABU TURAB TEAM??*

 *38*

A kwanar gidansu ta tsaya, tana tsaye tana kallan gidansu daga d'an nesa, ita a rayuwarta bataji zata iyama wani saurayi kara, Abu Turab take so ba taji zata iya zance da wani.

  Juyawa tai, sai dai ina zata? Idanunta ta d'an runtse kadan sannan ta cije lab'anta, a hankali take takawa harta kusa isa gidan.
 A waje taga mahaifinta shida masu musu hidima na gida, sunyu carko carko.
 
 Tsoro yasa tad'an hanzarta dan ta d'auka ko wani abun ne ya faru.
 Tana zuwa kusa dagun fitilar dake kofar gidan ta hasko ta.
 Wani daga cikinsu yace " Yallabai gatannan."

 Nan kowa ya juyo ya kalleta, Waziri ya kalleta cikin takaici sai dai alama ya mata akan ta wuce ciki.
 Nan ta shiga gida, ko d'aki bata shiga ba ya shigo ransa a b'ace yace " Khadija ke ba....."
 Kallan idanunta yai yaga sunyi jaa sosai da alama har kuka ma tayi.
 Yana san yarinyar jiyai bazai iya mata fada ba, yace " jeki kintsa kizo ku gaisa da Saifullahi, tun dazu yake jiranki."
 "To, amma banyi sallah ba."

 Kiyi sauri kiyi kizo yana jiranki.
 Tace to.
 Juyawa tai ta shiga d'aki.
  Ummanta tana kitchen tana duba kayayyakin abincin da za'a kaimai.

 Sallah tai sannan ta gyara fuskarta, ta jawo hijabinta ta zura.
 Mahaifiyarta ce ta shigo kallanta tai tace " Khadija ina kika je?"
  Shiru tai hakan yasa tace "ki canza kaya kisa sabo."
 Tana kainan tai waje.
Labanta ta ciza na takaigi sannan ta kwabe kaya tasa wani.
 Fitowa tai ta nufi inda Umma ta nuna mata.
  
 Sallama tai sannan ta shiga.

 Saifullahi ya amsa sallamar tare da kurama kofar ido.

 Tunda ta shigo yake zuba mata murmushinsa na yaudara har sai dataji kafafunta suna neman hard'ewa.
 Zama tai daga can nesa dashi, sannan a hankali ta motsa baki tace " Ina wuni?"
 Gani tai ya mike ya dawo gabanta inda take zaune, kanta na kasa sai gani tai ya sunkuyo inda kanta yake cikin salonsa na soyayya yace " Gimbiyata sai yau Allah yai."

 D'agowa tai tare da d'an jan jikinta baya tace " Saif meye hakan?"
 Ajiyar zuciya yai yace " tun randa na ganki a kano sai yau Allah yai na sake ganinki, nikadai nasan dadin danake ji."
 Baki ta tabe ba tace komai ba.
 Gani tai ya sake matsowa ta d'ago da sauri tana kallansa tana zazzare ido.
 Dariya taga yayi yace " Sry mikewa zanyi so nake in kara ganinki sosai."

  Mikewa yai ya koma gefenta kadan ya zauna yace " Khadija dan Allah ki saki jiki dani, sam banasan inga mace tana wannan kunyar."

 Kallansa tai tace " Ai kuwa mace da kunya aka santa tayaya za'ace ta daina?"
 "Oh God c'mon my Khadija."

 Yanda yaga tana kallansa alamar tsananin mamaki yasa ya saki dariya yace " Khadija wannan kalan fa? Gaskiya xanji dadi in mukai aure dan inasan wannan kalan dayawa."

 "In mukai aure kamar ya kenan?"
 Gani tai ya canza fuska yace " bangane ba, kinaso kice bakisan wani watan iyayena zasuzo gaisuwa ba? Daga nan kuma sai me?"

  Tsananin mamaki da fargabar kalamansa ne yasata yin shiru, nan fa ta tuno da abin begenta Turab.
 Jitai idanunta sun ciciko.
 Saif ya kalleta yace " Deejah na menene?"

 Kaina ke ciwo, tun d'azu.
 Ya kalleta kalar tausaya yace " sannu."
 Mikewa tai tace  "Saif i am sry amma dan Allah zan je na kwanta, kaina saramin yakeyi."

 Kai ya jinjina yace " sannu, jeki kwanta nima gidan kawuna zani gobe da safe zan wuce kano."

 Tace " Nagode Allah ya kiyaye hanya."

 Tana kai nan tai waje.
 Shiru yai sannan ya mike tare da murmusawa.

 Tana fita tai hanyar d'akinta jitai Ummanta  tace " Khadija? Ya tafi ne?"
 "Eh."
 Ta wuce ciki.
 Kwanciya tai ta shiga yin juyi akan gado.

**********
 Magajiya zaune ta a lissafi da hannunta wanda nikaina bansan me take lissafawa ba, Abdulmajid ne ya shigo rai a b'ace, yana shiga ya zauna dabas.
 Harararsa tai tace " kai kuma meye hakan? Zaka shigo ba wani tafiyar takama da isa irin na magajin Sarki?"

 Kallanta yai yace " Umma ki taimaken ki auramin Mairo, in ban koyama yarinyar nan hankali ba ta hanyar auranta ba, banaji hankalina zai kwanta."

 Wani mugun kallo ta bugamai tace " in har koya mata hankalin kake san yi da gaske ai basai ka aureta ba, kawai ka sa a hukuntata."

 Kai yad'an sosa yace " Ai Umma.."

 Katseshi tai cikin fada tace " badai auren Mairo bakam, nasan sarai me kake nufi, kai maza ka cireta a ranka, na fadama
"
Mikewa yai cikin takaici yai waje....

Ita kuwa Mairo yau bakin ciki duk ya hanata sukuni gashi ta ma Abu Turab girki da kanta, haushi da takaici duk ya gama isarta tana kallo kishiyar babarta da 'ya'yanta suka cinye abincin.

 ***********

 Washegari an rufe idan Abu Turab, mutane sai zuwa dubashi akeyi kowa na kawo abubuwa na kayan dubiya.

 Bayan azahar yana zaune yad'an samu ya zare abin da aka d'aure idanun nasa dan hutawa, Garzali ya shigo yace "Ranka ya dade Mairo ce."

 Bai maida ba yace "ta shigo."

 Shigowa tai fuskarta d'auke da murmushi.
 Ta karasa kusa dashi inda kujera take ta zauna, sannan ta kalleshi tace " Inna wuni yaya."
 Bai amsa ba yace " Hajiya Maryam na d'auka jiya zan ganki?"
 Baki tad'an turo tace " wani bunsuru ne ya tare mana kofar gida ya hana ni fita."
 Bunsuru?
 Tace eh, amma karka damu ya gaji ya tafi.

 Yace " ce miki nai na damu?"
 Fuska ta d'an tsuke kad'an tad'an juya kai tace "ba kara?"
 
 Cikin rashin zato taji yace " meye tsakaninki da Abdulmajid?"

 Kallansa tai cikin mamaki, zatai magana sukaji an bud'e kofar da karfi.

 Abdulmajid ne, Garzali na bayansa yana kokarin mai magana akan karya bud'e.
 Abu Turab ya kalleshi sannan ya kalli Garzali yamai alama daya koma.

 Abdulmajid me ya karaso ransa a b'ace ya kalli Mairo sannan ya kalli Abu Turab yace " Tsakaninmu kake tambay?"
 Abu Turab yamai wani kallo sannan yace " banaji dai acikin kalamaina na sako ka,sannan bakasan laifi bane shigowa mutum guri ba tare da neman izini ba?"

 Abdulmajid  ya matso saitin Mairo ya tsaya yace " ke harkin isa jiya inzauna jiranki amma kiki fitowa? Shine yau dan kin rainamin hankali in ganki anan?"

 Abu Turab a ransa yace " Au kaine Bunsurun?"
 Baisan sanda yai dariya ba.
 Hakan ya kular da Abdulmajid matuka.
 A zuciye ya kalleshi yace " kai kuma me kakema dariya?"
 Abu Turab yace " wani bunsuru na tuna, sannan inka gama abinda kake plz kai waje dan na tabbata ba dubani kazo ba."
 Kallan Mairo yai yace " wuce muje."
 Harararsa tai tace " inje ina? "
 Wuce muje nace ko?
 Tace " yau naga ikon Allah a matsayinka na wa?"
"Mene?" 
Tace " ban fahimta bane ina zaune kawai kace in tashi muje."
 Ransa yakai kololuwar baci dn dama Magajiya ce tasashi wannan zuwa dubiyar anma da yasan abinda zaigani kenan ko abinda zata mai kenan a gaban yaran nan da baizo ba...
 Kwafa yai s
 
 *39*

  Yana fita Abu Turab ya kalleta tare da daure fuska yace " Mairo, Abdulmajid d'in ne Bunsuru?"

 Tace "laa yaushe nace haka yaya? Nifa zancen da nake daban."
 Girman idanunsa ya rage yace " fad'amin tsakaninki dashi."
 Tace " ni meye tsakanina dashi kuwa? Nema kawai yake ya takuramin da kuma san ya wulakantani."

 Shiru yai sannan can yace " amma kamar yana sanki."
 Dariya tad'anyi, sannan tace " kai ka yarda yaya? Wannan ne yake so na? Banaji yasan ma menene soyayya abu d'aya ya sani shi...."
 Sai kuma tai shiru, kallanta yai yace " me ya sani?"
 A ranta tace " neman mata mana, amma a fili tace bakomai."
 Ganin batasan fada yasa yace " ki dai bishi a hankali kinsan halinsa sarai."
 Baki ta tabe batace komai ba.
 Ta dade sosai a asibitin dan sai da su Basira sukazo sannan suka tafi tare da ita, Zuciyar Basira fal da farincikin ganin yanda Mairo take kula da Abu Turab.

*************
 Magajiya ce ta shirya tsaf tasa aka mata girke girke kala kala, kwalliya sosai tai tasa aka jera mata kaya a cikin mota, tana kokarin fitowa Khadija ta shigo.
 Bayan sun gaisa Khadija tace " Umma Babba bacci ne ya d'aukeni sai dana tashi Umma tacemin kina kirana."
 Magajiya ta kalleta tace " fita zanyi ki jirani inje asibiti in dawo."
  Tanajin zancen asibiti tai saurin cewa " zanje Umma Babba inyaso mayi maganar a hanya."
 Kallanta tai tace " ba dai san ganin Abu Turab d'in ne yasa kikesan zuwa ba ko?"
  Dasauri tace "a'a Umma."
 Muje.
 Nan suka fito tare.
 Masu kula da bangarenta ta kalla tace ku sanar da mutane tafiyata duba Turab kunsan me nake nufi ai,  sukace mun gane ranki ya dade.

  Tayi hakan ne dan asan abinda takaimai da kuma nunama jama'a tana san yaran.
 Sun shiga mota, Magajiya ta kalli Khadija cikin yanayin bugat ciki tace " Ashe Saifullahi yazo?"
 Khadija tace " eh yazo jiya."
 "Yace zai dawo?"

Khadija tai shiru dan batasan me zatace ba, Magajiya ta tsuke fuska tace " Badai wulakantashi kikai ba ko?"

 Khadija ta kalleta jiki a sanyaye tace " Umma ni na kasa gane dalilin had'in auran nan....."

 Wani mugun kallo ta mata wanda yasa tai shiru bata iya karasa fadar abinda zata fada ba.
 Magajiya tace " Khadija kina tunanin zamu cutar dake ne? Yaran nan d'an gidan manya ne sannan shi kad'ai ne namiji agun iyayensa, ga kudi ga matsayi auranku dashi zai taimaka ma Yayanki Abdulmajid zai kuma taimakeki."

  Mamaki ma ya hanata magana, au wad'an nan sune dalilin dayakesa ayi aure? Matsayi?kudi?"

 Magajiya ta dafata tace " na yarda dake dan haka karki bani kunya, kinfi kowa sanin Abu Turab bazai taba auranki ba ko matan duniya sun kare dan ko shi ya yarda ni da mahaifinki bazamu taba yarda ba, in ma kina tunanin wani shirme a ranki to kiyi maza ki cire wannan ki maida hankalinki kan Abu Turab."

 Khadija tai kasa dakai kawai batace komai ba.

 Sun isa asibiti nan aka kwashi kaya aka fara shiga dasu.
 Abu Turab na kwance lokacin bacci ne ya fara d'aukansa, Garzali ne ya shigo ya sanar dashi isowar su Magajiya.

 Idanunsa na rufe dama saboda dazu Galadima da Barde suka tafi.
  Tashi yai ya zauna, ta shigo cikin isarta da yanayin tafiyarta, tana kallansa ta saki wani murmushi, ba shakka yaran nan dan rainin hankali ne harda wani rufe ido?
 Shiga tai ta zauna, khadija tana tsaye a jikin kofa bata karaso ba.
 Magajiya ta kalleta tace " dan bamu guri Khadija d'a da uwa zasuyi magana, in na gama sai ki dubashi."
 To kawai tace tai waje.

 Magajiya ta kalleshi tace " Turab bazaka kunce daurin ka gaida mahaifiyarka da kyau ba?"

  Abu Turab yace " ai na gaidake ,sannan nida banda lafiya an min aikin ido ta ina zan ganki?"
 Murmusa wa tai tace "ahhh na tuna ashe fa makaho ne wanda akamai gyaran ido."

  Abu Turab yace  " naji dadi da kika tuna."
 
 Shiru sukai kafin can tace "Mahaifinka ya tura mutane yau sunkai kayan godiya da amsawar da masarautar kano ta basu na auranka."
 
  Batajira amsarsa ba tacigaba " Kaifa kana tunanin kaci galaba ko?za kuma ka auri Bilkisu ko?"
 Tad'an juya kai sannan tace " sai dai kuma inaso ka sani sai har in an gama shafa fatiha na d'aura auranku sannan zan yarda kaci galaba akan Bilkisu, abinda nazo in fadama kenan."

 Murmushi ya saki yace " na d'auka kinzo ne akan mutane susan kinzo duba d'anki? Ashe zuwa kikai kimin kashedi."

 Kallansa tai tace " ai dole ne uwa tazo duba danta."
 Yace " hmm gaskiya kam
"

 Mikewa tai tace " zan koma, ina fatan makaho ya dawo gida a matsayin cikaken ido hakan ne zaisa wasan yafi dadi, muga tsohub hannu da sabon hannu."

  Kai ya jinjina yace " kuma fa hakane."
 Juyawa tai tai waje.
 
 Khadija ce ta ke kokarin shigowa yanaji Magajiya na ce mata wuce muje ba sai kin shiga ba.
 Khadija tace " Umma ba dade wa zanyi ba dan Allah."

 Wuce muje ko? Ko kin taba gani an duba mai lafiya? 
 Zata sake magana ta mata wani kalli, juyawa tai idanunta sun ciciko.

 Komawa yai shima ya kwanta, tunda ta tafi jiya duk yanda yaso ya cire zancen Saif a ransa ya kasa, waye shi? Menene matsayinsa a gunta? Sai dayai yaki sosai da tunanin kafin ya samu ya kawar da shi a ransa.

  Khadija kam harta shiga mota bata ce komai ba, Magajiya duk da ganin Khadija a haka yasa taji ba dadi sai dai inaaa, bazata yarda da yanda Khadija ke nuna tsantsar damuwarta akan yaron ba.


  **********


  Yau ya cika sati d'aya kenan da zuwan Turab Asibiti, yau ne kuma ranar da zai koma, tsaf suka shirya komai, Mai Martaba da kansa yazo dan tafiya da dansa, su Hisham da su Barde duk sunyo rakiya.

  Mairo kam kusan kullum sai tazo dan Basira ma wani sa'in ita take aike, Khadija kam ba damar zuwa, tun randa suka tafi, sai dai kome take Abu Turab na ranta, kullum sai ta tashi tamai addu'a da daddare

*40*
Magajiya ce kicinged'e a kilisarta da alama tunani takeyi duba da yanayin da take ciki.
 Hisham ya shigo sannan ya zauna kusa
 Magajiya tad'an ja numfashi bayan sun gamagaisawa tace " Hisham cire Abu Turab daga gabanmu, domin na kula in bamuyi wasa ba Mai Martaba zai biyo mana ta bayan gida, da farko ya had'a Turab da 'yar sarkin kano sannan mun fahimci yana gani, sannan gashi zamansa a asibiti manyan masu mukamai sunje dubashi sun kuma dawo da yaban d'abi'arsa."

 Hisham ya kalleta yace " Magajiya nikaina abin nan ya damen, me zai hana mu raba shi da du......"
 Wani mugun kallo ta bugamai tace " so kake ka lalata mana shiri irin sanda yana jariri? Duk badadan kaje kayi shirman kona musu gida ba me zaisa Basira tabar gidan nan? Da cikin ruwan sanyi zamu turashi barzahu ba tare da an fahimci komai ba, dan haka karka kuskura ka kara gigin daukan hukunci ba tare da ni na sani ba."

 Ba shakka yaji haushin kalamanta a ransa, sai dai a fili cewa yai " shikenan."
 Tace " nayi tunani sosai na fahimci Basira itace lagwan yaran nan, in har muka sata a tsaka mai yuwa to fa Turab zai zamar mana tamkar akala."
 Hisham yace " Na d'auka Turab muke hari ba wata Basira ba."

 Tsaki tai tace " kai matsalata dakai kenan, kwakwalwarka gaba d'aya bata ja, kai kana tunanin yaran nan ba wani abu bane?"
 Hisham yace " to nawa yaran yake?"
 " nawa yake amma har ya nemi ja min masifa nida Abdulmajid? To bari kaji in fada ma, wlh wannan yaran in ba munyi da gaske ba reshe ne xai juyi da mujiya."

 Tacigaba " so nake kasa a samomin guba amma mara karfi."
 Cikin mamaki yace " guba kuma? Wace iri?badai Basira zaki kashe fa ita ba?
 A fusace tace " wai meyasa in na fadi abu ne yaya sai kace sai na fadama dalili? Kasa a samo abinda na fadama, sannan ka tabbatar kasa anba wannan yarinyar da muka saka a bangaren basira data saka a cikin abincin da za' a kawo min?"
 Idanunsa ne suka firfito yace " bangane abincin da za'a kawo miki ba? Kina nufin kece zakici gubar?"
 Tace " wannan ba damuwarka bace in har kanaso mu d'aura Abdulmajid akan mulki to kawai ka dinga bin abinda na umarceka ba tare da tambaya ba."

  Daurewa yaiyace "to."
 Tace " gobe zasuzo gaisuwa, dan haka ayau zaka samo gubar ka kuma aika da ita a daren nan."
 Yace to, mikewa yai ya fito yana mamakin me take shirin yi.

 Yana fita ta mike, sannan tai murmushin mugunta.

**********
  Shikam Abu Turab bayan ya iso yana gun Mahaifinsa sun dade suna tattaunawa game da bikinsa da kuma wasu al'amura na sarauta da mahaifinsa ya nemi shawarar d'an nasa akai.

 Sun yanke shawarar komawarsa garin kano a wannan sati, in ya dawo kuma sai a tura kayan gaisuwa da na lefe a saka rana.

Bayan ya fito ne ya nufi gun mahaifiyarsa, duk inda ya wuce mutane sai tayashi murnar warkewa sukeyi har ya isa.
Basira tasa an mai girke kala kala kana ganinta zakaga tsantsan farinciki a fuskarta.
 Bayan sun gaisa ne tasa aka jera mai abimci kala kala, Abu Turab yai murmushi yace "Umma kenan sai kace wanda na bar garin?"
 Lantaba Tace "ai Uban gidana inaji da kai mace ne in kai aure binka zatai."
 Dariya suka saka, nan ya fara zuba abinci.
 Basira tace " Magajiya ta shirya walima na kusa da zamuje gobe na murnar warkewarka."

 Kallanta yai sannan ya baida kansa kan abincin yace " she is trying hard."
 Basira tace " magana kai?"
 A'a, amma su waye zasu gun?
 Tace "hmm daga dai mu matan Takawa da shi Mai Martaban sai kai da Abdulmajid, amma bansan ko da wasu ba."
    
  Yace "hmm."
 Basira tace " tace insa ayi abinci daga nan, nafi san kowa in mai abincin danasan yafi so, saboda taro ne akayishi saboda d'ana."

  Zuciyarsa d'aya dan bai kawo komai a ransa ba yace " to, amma karki wahalar da kanki Umma."
 Tace " wace wahala bayan ba ni zanyi girkin ba?"
 Murmushi yai ya cigaba da cin abincinsa.

 Sai daya gama ya mike ya fito, bangaren kakarsa ya nufa wacce ta tsufa sosai gashi batada lafiya, yana tafe su Garzali na bayansa.

 Sam bai kula da ita ba wacce ta shigo gidan na sarauta dan kawo ma Abdulmajid sakon da mahaifiyarta ta aikota ta kawo.

 Sai da suka kusan junan su sannan suka ankara da juna.
 Kallanta yai sannan ya d'auke idanunsa ya cigaba da tafiya.
 Wani sanyin dadi ne ya kamata ta karaso da sauri tace " Yaya."
 Tsayawa yai sannan ya juyo ya kalleta fuskarnan a d'aure.
 Murmushi ta saki tace " Yaya baka taba ganina ba ko? Nice Khadija, ahhh nasan kasan muryata, hmm Alhamdulila yau Allah ya amshi addu'a ta."

  Kallanta yakeyi kawai sai dai zuciyarsa ta karaya sosai, Khadija ta share kwallarta data taho tace " Yaya Allah ne kadai yasan farincikin danakeyi ganin idanunka sun bud'u da izinin Allah bud'ar idanunka zai kawoma alheri masu yawa a rayuwarka."
 Ta karasa maganar cikin rawar murya dan kuka na neman kufce mata.
 Sama ya d'an kallan kadan yana neman dake zuciyarsa dan tabbas kalamanta sun ratsashi.
 Kallanta yai yace " nagode, sai dai inaso ko a hanya muka hadu ki daina nuna kin sanni, banasan inzama mai jawo miki bakin ciki shiyasa nake fatan ki cireni daga ranki ki kuma daina damuwa dani."

  Kai ta jinjina ta na kokarin share hawayenta da hannu tace " naji yaya, zanyi abinda kace."
 Kallan mamaki ya mata dan bai yi tunanin abinda zatace kenan ba.

 Khadija ta kara share hawayenta tace " kasan meyasa zan rabu dakai yaya?"
 Kallan ta yai baice komai ba.
 Ta cigaba " saboda ka daina murmushi in kana tare dani, ka daina fara'a, ko farin ciki kakeyi daga kaji muryata sai inga farincikin nan ya tafi daga fuskarka."

  Hawayenta ta kara sharewa tace " kaine mutum na farko dana taba so, banaji zan kara san wani haka, ba kuma naji zan daina ma fatan alkairi da yima addu'a a rayuwarka sai dai bazan taba yarda inzama nice sillar bakin cikinka ba, bansan dalilinka na canzamin hala ba, sai dai ba yanda z........"

 Hawaye ne suka taho sosai wanda ta kasa karasawa, jiyai gaba daya daga tsakiyar kansa har zuwa 'yan yatsun kafafunsa sun amsa, shikansa sai dayaji idanunsa suna neman canzawa na yanayin kawo ruwa.

 Kallansa tai sannan ta kakaro murmushi tamai sannan ta juya ta fara tafiya.

  Kasa motsawa tai daga inda yake, su Garzali na gefe duk da basusan me tacemai ba amma sun fahimci yana bukatar keb'ewa.

 Abu Turab kallanta yakeyi har sai da ya dena hangota sam ya kasa motsawa, yafi minti 20 a haka kafin ya taka kamar wanda aka tsuma a ruwa ya karasa bangaren kakar.

 Jikinta kam ba sauki duba da yanayin tsufan datai, bai dade ba ya taso.

 
  D'akinsa ya nufa ya shige ya kwanta rigingine, rayuwarsu da Khadija ya shiga tunowa, wasu kananan hawayene suka zubo ta gangaren idanunsa, mirginawa yai ya kwanta ganin tunaninta na neman addabarsa ya mike zaune da sauri ya bud'e cikin drawer dinsa ya dauko d'ankwalinta har yayi kamar zai yadda sai kuma ya fasa ya d'aga can kasan kayansa ya saka shi.

 Ya koma kan gado ya kwanta........

 Khadija kam tana fita ta wuce gida dan kuka kawai takeyi, sam bata kula da Hisham ba dayake tsaye gefen kofar shiga gidan shi da su Galadima.

 Hisham ya kula da kukan da takeyi sai dai ba damar magana saboda bayasan a ganta tana kuka.

  *TEAM ABU TURAB ??*
Reply
#2
Contemplation of the future and all items has been done for the struggle for the future offers. The announcement of the essayontime review is marked for the dangers for the humans. It is amended for the official account for the people. The judgment is fixed for the fulfillment of the goals for the humans. The charge is done for the justified items for the citizens.
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *JALILAH* by Ayusher Mohd* Gimbiya 0 20,165 09-10-2018, 09:03 PM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,758 06-16-2018, 10:17 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 6,907 06-16-2018, 10:16 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,349 06-16-2018, 10:09 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,717 05-07-2018, 11:04 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 4,309 05-07-2018, 10:54 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,636 04-30-2018, 01:16 PM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* A Historical Fiction* by Ayusher Muhd Gimbiya 0 4,614 03-29-2018, 11:44 AM
Last Post: Gimbiya



Users browsing this thread: 1 Guest(s)