The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*RANA D'AYA* BY MIEMIEBEE*
#1
RANA D'AYA
BY MIEMIEBEE

PAGE 05


   "Assalamu Alaikum" ya fad'a a yayinda yake sa kai cikin parlon Abba.

  "Wa'alaikumus salam" Abba dake zaune akan kujera ya amsa tare da ajiye newspaper'n da yake karantawa yana mey maido da kallonsa ga k'ofar.

  "Shigo Prince bismillah" shigowan yayi inda ya nemi waje ya zauna a k'asa. "Ya zaka zauna a k'asa sekace wani bak'o?" Abba ya tambayesa da wuri "Take a seat please."

   A'a Abba I'll be fine here."

  "Non sense, take a seat please" be sake yin gardama ba ya koma kan kujeran ya zauna sannan ya gaishe sa cike da ladabi. Batare da 6ata lokaci ba Abba ya wuce straight to the point "Umminka tace ka makara yau baka samu daman fita office ba ko?"

  "Eh wallahi Abba" ya fad'a yana sosa temple nasa.

  "Toh dama batun maganan jiya ne nakeson in baka hak'uri" ido cike da mamaki da neman k'arin bayani Afzal ya d'ago yana kallon Abba da ya cigaba da magana. "Da kace yarinyan bata da kamun kai bai kamata in sake tilasta maka cewa lallai-lallai seka aureta ba saboda ko addinin musulunci ya hane yin hakan, so kayi hak'uri na maka ba dai-dai ba yanzu haka daga nan zan wuce gidan Alhj Abdallah zan basa hak'uri akan cewa auren nan ba ze yuwu ba ka na iya tafiya nagode."

  "Abba ni bakayi offending d'ina ba saboda koda ka tinkareni da maganan jiya ba lallai-lallai cewa kayi sena auri Nazeefah ba, hasali ma baki na ka tambaya ni kuma na baka amsa bisa rashin tunani. Abba farin cikin ka yafiye min komai a duniyan nan, bazeyi ka bani komai a duniyan nan ba nikuma don for once ka tambayeni abu in hana maka shi ba saboda son rai ko makamancin hakan, Abba na amince da auran Nazeefah idan har yin hakan ze farinta maka rai." A hankali kalamun Afzal suke shiga kunnen Abba suna kwanciya a birnin zuciyansa, don farin ciki ya ma kasa believing abinda kunnansa suka jiye mar, ji yayi son d'an nan nasa na k'ara dad'uwa a birnin zuciyansa, wani sa'in har tambayan kansa yake me yayi wa Allah daya azurta shi da d'a kaman Afzal, yaron da baisan meye kalman son kai ba, yaron da seya kawo tunanin wani kafin ya kawo na kansa, tabbas yasan yayi sacrificing alot to come to this decision, yasan wannan babban hukunci ne Afzal ya yanke ma kansa irrespective of whatever the outcome might be, ya sani idan da har za'a tone zuciyan Afzal ba son auren nan yake ba ya amince ne kawai don ya farinta masa rai kamar yadda shima ya fad'a kuma hakan da yayi ba k'aramin dad'i ya sanyashi ba.

  "Afzal?" Abba ya kirasa da asalin sunansa wanda ya juma beyi hakan ba.

  "Na'am Abba?" ya amsa kansa a sunkuye.

  "Afzal ka d'ago kanka ka kalleni" ya buk'acesa. Hakan yayi "Ka sake nanata abinda ka fad'a" Abba ya buk'ata. Sak abinda ya fad'an ya kuma nanatawa Abba can't help but to feel shocked, surprised and happy duka. Emotions ba wanda Afzal baisa shi feeling ba.

  "Afzal bana son a sanadin hakan rayuwanka ya shiga wani hali idan har kasan you don't mean this and you can't find it in your heart to love that girl somday karkayi forcing kanka nasan yadda zan 6ullowa Alhj Abdallah da wannan magana I want you to consider youself  first."

  "Abba I mean it your happiness means the world to me" ya sake tabbatar mishi.

  "Alhamdulillah Alhamdulillah Afzal ban san da wani bakin zan soma maka godiya ba, tabbas bansan ya rayuwata zata kasance ba idan ba kai, mahaifiyar ka batayi k'arya ba da tace mun babban kyautan da zan iya samu a duniyan nan shine kyautan ka da tayi min, yanzu nake sake jaddada hakan. Afzal Allah yayi ma albarka, Allah cigaba da sa albarka acikin rayuwan ka kamar yadda ka farinta min yau Allah ya farinta maka haka kaima, Allah ya baka yaran da zasu maka fiye da haka kaima wataran, k'arshe kuma Allah cigaba da kai rahama kanarin marigayiya."

  "Ameen Abba."

  "Nagode, nagode sosai Allah yima albarka."

  "Abba godiyan ya isa haka please idan har akan d'an wannan kake gode min haka ni kuma da kamin komai a duniyan nan ya kakeson inji? That am an ingrate?"

  "Sam ba haka bane Prince, komin da nake maka ka cancanta ne. Prince am so proud of the man you've become. Nasan ba k'aramin sacrifice kayi ba just to make me happy and I so much appreciate it" Miqewa yayi ya matso inda Afzal yake "Come here" ya buk'ace sa tare da bud'e mar hannunsa wide open and ready for a hug. A nitse Afzal ya mik'e yayi snuggling kansa cikin arms na Abba, dad'i yaji ba don komai ba se don ya sanya Abbansa farin ciki. Ya sani wannan decision da yayi making might change his life forever amman kaman yadda ya fad'a farin cikin Abbanshi ya fiye mar komai, he is ready to deal with Nazeefah for his Abba.

    *         *          *          *         *          *

     GIDAN ALHAJI ABDALLAH

    Fankacecen upstairs ne me kyawun k'arshe wanda ke cike dam da motoci masu tsada, fakasu akayi accoridng to modality. Kallo d'aya za'ayi ma gidan asan na masu shi ne barin flawoyin da an kayi trimming nasu mutum na iya cewa a garden yake.

     Kyakkyawar budurwa ce wacce baza ta fi shekaru sha bakwai zuwa sha takwas ba (17-18) kwance akan wani makeken Italian bed dake d'aya daga cikin manyan d'akunan da suke saman benin, komin cikinsa ya kasance pink ne banda abubuwa kaman gado da TV stand.
     Ruf da ciki tayi bisa kan gadon a yayinda kunnenta ke manne da headphones wanda ta k'ure music aciki  connecting it to her MacBook. Waya k'irar iphone X ne rik'e a hannunta se faman yin video take tana bin wak'a tana uploading a snapchat. Wannan budurwa itace definition na '6-4 hutu dan kuwa ba damuwa ko d'aya tattare da ita.

   K'ofan d'akin ne aka bud'e revealing wani d'an yaro ko saurayi zance me tsananin kama da wannan budurwa saide shi fari ne tas, ita kuwa skin nata yafi chocolate ne da kad'an. Kallo d'aya mutum ze musu yasan 'yan uwa ne saidai ta girmeshi don ga dukkan alamu shi wannan ba zefi shekara sha hud'u zuwa sha biyar ba (14-15.) Harara mey rai da lafiya ya watsa mata ganin bata ma san an bud'e k'ofan d'akin nata ba har yanzu balle tasan mutum na tsaye gun kasancewar loud music data cika a headphones nata, se kad'a kai take ta tana ta faman recording kanta.

   "Ke Nazeefah!" Yaron ya danna mata kira cike da rashin kunya sekace ba yayarsa ba amman don loud music da takejin bata ma san yanayi ba. Tsuka yaja sannan a zuciye ya k'arisa cikin d'akin tare da damk'o k'afafunta guda biyu yaja seda ta kusan fad'i daga kan gadon. Ihu ta k'urma a firgice tare da juyowa don ganin wani d'an iskan ne zey mata wannan d'anyen aikin, ganin k'anin ta ne yasa ta ma daina mamakin hakan dama tasan ba mey mata hakan se shi, fusata tayi a lokaci guda. Ji take kaman ta wanke sa da mari amman sanin idan tayi hakan shima hannu zai d'aga ya rama saboda yadda ya rainata yasa ta fasa. Headphones d'in ta zare "Kai Khaleefah baka da hankali ne? Dan gidanku ni sa'ar kace da zaka firgita ni ka jani da k'afana? Sa'ar kace ni?" Ta tambayesa cike da tsiwa tana watsa mai harara da dala-dalan idanunta da suka sha artificial lashes.

   "Had it been baki k'ure music a headphones naki ba ai da kinsan mutum yayi joining d'akin ya kuma kiraki, aikin banza kawai."

  "Aww rashin kunya zakayi min?" Ta kuma tambayansa a yayinda ranta ke tafasa.

  "Anyin! Kinfi k'arfin ayi miki ne? Mschww!" yaja tsuka. Miqewa tayi akan gadon a fusace da niyan dukansa nan fa karnukan suka hau haushi. Dambe suka shiga yi sekace age mates ba babba ba yaro, yak'ushinsa take da dogayen faracun data tara a yayinda yake ja mata gashin kai wane ze 6allesu.

   Mummy (mahaifiyar su) da ta san za'ayi haka yasa ta biyo sahun Khaleefah only to catch them in the act: fighting.

  "Ya Rabb!" Tayi exclaiming a kid'ime "Ya haka? Nazeefah me nake gani? Khaleefah ka saketa ko baka san yarka bace?" tayi maganan tana approaching nasu da wuri a yayinda ta shiga rabasu wanda da k'yar ta samu ta cimma hakan. "Sai kun kashe kanku tukuna zaku huta?" Ta tambayi yaran nata da suke matuk'ar kama da ita tamkar an raba kara difference nasu kawai shine adadin shekarun da ta fisu da kuma hasken fata. Fara ce sal wane sadak'ar yallan da ake samu a Kano d'innan. Hak'i duka sukeyi a yayinda suke watsa wa juna harara suna adjusting rigunansu.

  "What has gotten into you two iyyeh?" Ta tambayesu both.

  "She started it-"
  "He started it-" duka suka fad'a a tare. "Kawai ina cikin zamana ya shigo min d'aki without my permission sannan ya ja min k'afa sa'ar sa ce ni?" Cewar Nazeefah tana me cigaba da galla mar harara a yayinda ta shiga kama gashinta da Khaleefah ya hargitsa gu d'aya.

  "Liar!" Ya fad'a mata "Wallahi k'arya ne Mummy na kirata sau uku amman bata amsa ba dake ta k'ure wak'a kaman shed'aniya tana ji."

  "Ni kake cewa liar da shed'aniya?" Nazeefah ta tambaya tare da yunk'urin sake kama shi da wani fad'an wanda Mummy tayi saurin shiga tsakaninsu stopping her. "Enough Nazeefah ke bakisan kece babba ba?"

  "Toh Mummy kina ji yana cemin shed'aniya se in barsa?"

  "Khaleefah bazaka daina rashin kunya ba kai kuma ko? Ce ma akayi sa'ar kace?"

  "Ni wallahi toh karki sake turoni kiran ta tunda kullum mukayi fad'a siding da ita kikeyi" daga fad'in haka ya wucesu both ya fita ignoring kiran da Mummy ke ta yi masa, d'akinsa dake adjacent da na Nazeefah ya fad'a tare da miqewa akan gado, ran auta ya 6aci.

   "Nazeefah ki kiyayeni shikenan ke bakida aikin dayafi dambe da k'aninki gabad'aya kin bi kinsa ya raina ki ko shakkan ki baya yi" Mummy ta shiga yi mata fad'a.

  "Toh mutumin da fitsara yake gudu a jikinsa kaman jini daman how will I expect him to respect me? Kuma wallahi ya sake yi min haka sena tattake shi."

  "Wuce Daddy na buk'atan ganinki" shiru tayi kaman bata jita ba "Ko baki jini bane?"

  "Naji zan kashe waqan dake playing ne" ta amsa ta. Kai kawai Mummy ta kad'a ta fice tabi bayan Khaleefah dake miqe akan fankacecen gadonsa a had'add'en d'akinsa da komi aciki yake blue tsan-tsan son kalan da yakeyi. Yana ganinta ya kawar da kansa, dama tasan za'ayi haka k'ofar ta miyar sannan ta k'arasa ciki ta zauna a gefensa.

  "Haba Autan Mummy my Mr handsome yi hak'uri ka juya ka kalleni" sede kaman bada shi take maganan ba.

  "In baka waya na ka shiga Ali express kayi ordering 3D games?" Se anan ya juyo yana kallonta tare da gyad'a kai dama ta sansa da shegen son games. "Toh ka hak'ura?"

    "Kullum sede bamuyi fad'a da Nazeefah ba se kiyita biye mata."

  "Mummy is sorry okay? Bar had'a ran haka."

  "Toh ina wayan naki?"

  "Yana d'akina na sauk'a zan bawa Inna (me aikinsu) ta kawo maka."

  "Toh" ya fad'a simply.

  "Yau ba zuwa playing ball ne?"

   "Se anjima tukuna."

  "Toh barin sauk'a Daddy na nema na" miqawa tayi tare da pecking nasa sannan ta fice bayan ta bawa Inna wayar ta kai ma Khaleefah ta wuce parlourn Daddy da yayi girman d'akuna uku. A gefen Daddy dake zaune akan kujera ta zauna a yayinda Nazeefah ke zaune a k'asa. Tunanin ya Nazeefah zata kar6i wannan bak'on al'amari kawai take, tasan akwai drama.

  "Nazeefah jiya ina kika je da daddare?" Daddy ya soma da tambayarta.

  "Daddy gidansu Eesha naje ba wani gun ba yayanta ne yamana tutorials na physics."

  "Nazeefah kin de san k'arya haramun ne kuma kikeyi ko? Nazeefah yaushe ne zaki daina sani acikin bakin jama'a? Ace 'ya ki gagareni ki gagari Mummynku tun bakije ko ina ba? How old are you? You're just 17. Mey kika nema kika rasa a duniyan nan da bazaki kare mutuncin ki da nawa ba Nazeefah? Kullum ace sekin saci ido na dana Mummynku da daddare kifita yawo? Tarbiyyan da muka baki kenan?" Shiru tayi ba amsa "Dake nake magana." Shirun da tayi ta cigaba dayi a yayinda take maganan zuci shikenan ita Daddy baida aikin dayafi yi mata wa'azi kullum ai ko shaid'an ma ana d'aga mishi k'afa.

  "Tunda wannan ne rayuwan da kika d'au wa kanki na rashin ji, kin nuna neither me nor your mother have a right on you, kin nuna mu ba kowa bane a idonki, kin nuna mu bamu isa muyi iko dake ba toh ni zan aurar dake kawai ki huta nima in huta, wata k'il idan akayi hakan you'll change for good." Aure fa Daddy yace? Wani irin wawan bugu zuciyarta tayi, kode wasa yake mata? 'Yar ita ne zai ce zeyi mata aure? Ma da wa tukuna? No this is a joke.

  "Aure fa kace Daddy?" Ita da wasa ma ta d'au maganar "Haba Daddy!" Ta k'yalk'yale da dariya.

  "Kin d'au wasa nake miki ne? Aure zanyi miki and I mean it ko zan huta ki huta kowa ma ya huta yaso kije chan ki k'arata da mijin naki."

   "Mummy kina jin Daddy? Wai aure zey min at this tender age? Daddy dan Allah idan wasa kakeyi stop it bana son irin wasan nan."

  "Wasa? Wasa fa kikace, yaushe na soma wasa dake Nazeefah? Ko kin ta6a jin inda akayi wasa da kalman aure?" Ya fad'a cikin tattausar muryan daya mugun razana Nazeefah, tabbas ba wasa acikin zancen da yakeyi amman mey ya buga kansa yace zai mata aure? A iya saninta iyayen da suke da k'arancin western education (ilimin boko) ne masu yima yaransu aure da wuri meyasa Daddy zai mata haka bayan shi be fad'a cikin jerin kalan iyayen chan ba.

  "No Daddy don Allah kar ka min haka" ta fad'a a rude'e still finding it hard to believe "Daddy don Allah kayi hak'uri I'll change my ways I promise never to go out in the night again, Daddy I'll be a good girl dan Allah ka ja baya da zancen nan."

  "My decision is irrevocable Nazeefah, na baki enough time da ya kamata ace kinyi amfani da hankakinki kin sauya halayanki amman kink'i yin hakan, idan har ban d'au mataki akan ki ba yanzu to tabbas haka ina ji ina gani wataran zaki d'ibo min abin kunya ki kawo min gidan nan, so the earlier the better."

  "No Daddy please" ta rushe da kuka "Mummy please say something, stop him please! Wallahi na tuba na dena bin k'awayen banza, na daina bin maza from now henceforward I'll be a good girl Daddy don Allah karka min haka Daddy am too young."

  "Kinsan da hakan amman yau kene da wannan a gari gobe da wancan? Samarukan garin nan kaf ba wanda bey sanki ba, you've had your time and it's now over ko kin k'i ko kinso aurar dake zanyi idan kuma har kika ga auran nan be auku ba toh wallahi mutuwa kikayi ko kuwa guduwa wanda idan kikayi zan fidda ki daga sahun 'ya'yan dana haifa I mean it" ya fad'a cikin tattausar murya.

  "Daddy please I'm sorry" kuka take sosai but neither Daddy nor Mummy suka tausaya mata saboda tsan-tsan rashin jin magananta kaman yadda Afzal ya mata shaida.

   "Daddy karatu na fah? Yaushe na fara karatun da kake tunanin min aure? Daddy please don't do this wallahi bazan iya had'a aure da karatu ba."

   "Kije ki shirya Nazeefah" ya ce da ita tamkar beji duk abinda ta fad'a ba "An jima kad'an yaron dana samu ya taimaka ya amince ze aureki zaizo domin in mar godiya so idan yazo zan had'aku even though am sure kin waye shi saboda ba kowa bane banda Afzal yaron amini na Alhj Ahmad Amin."

   "What???" Tayi exclaiming unbelievably "Afzal fa kace Daddy? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" ji tayi kaman zata haukace. Afzal? Noo it's not possible tasani Afzal baze ta6a yarda ya amince ze aureta ba saboda irin tsanan daya mata kaman yadda itama bazata yarda ta aure sa ba cause kamar yadda ya tsaneta haka itama ta tsanesa. Mutumin da kullum idan ya ganta akan hanya yake watsa mata harara ne za'a ce ya amince ze aureta? Wanda idan ya ganta a gidansu yake ji tamkar ya bita da muciya? This is just some kind of game it can't be happening idan har ko ya amincen ma then there's not doubt akwai wata mumunar abinda ya shirya mata in store.

   "Daddy don Allah karka kasheni kafin lokaci na, Daddy I beg you please wallahi bazan sake rashin ji ba, Daddy bana son Afzal bazan iya auran shi ba."

  "Shima ba sonki yake ba Nazeefah taimakawa zeyi ya aureki don ya rufa min asiri, ko a tunanin ki cikin 'yan iskan samarukan naki akwai wanda ze amince ya aureki ne? Abbanshi yace ya amince ne da auren ba don komi ba se don ya farinta masa rai. Rok'an Abbanshi nayi tayi daya taimaka yayi convincing d'an nasa ya aureki Nazeefah saboda bansan wazeyi hakan ba nan gaba. Da kalan gur6arcacciyar rayuwan nan da kika d'au wa kanki inada tabbacin cewa ba d'an na mijin da zaiji sha'awan auranki. So it's better tun ina raye in nemi wanda zai rik'e min ke amana ya kuma kula dake ya d'aura ki akan hanya madaidaiciya and I can't think of anyone else sama da Afzal. Afzal ya amsa sunan d'a a duk inda ake neman hakan, yaro mai hankali da ladabi dakuma sanin ya kamata I just wish you'll follow his steps and change for the good Nazeefah" ya fad'a cike ca takaici kamin ha mik'e "Kina iya tafiya" yana kaiwa nan ya wuce d'akinsa.

   "Daddy please karka tafi" ganin Mummy ma ta miqe da niyyan bin bayansa yasa Nazeefah dawo da kallonta a gareta hawaye take sosai bazata iya tuna when last tayi kuka haka ba. "Mummy don girman Allah karki min haka, Mummy I beg of you please ki bawa Daddy hak'uri."
  Koda wasa Nazeefah bata ta6a kawowa a ranta Daddy ze iya mata abu irin haka ba, saboda coolness nasa da kuma shiru-shirunsa. Daman ance a guji 6acin ran miskilin mutum, duk kalan rashin ji da abubuwan da takeyi Daddy bai ta6a kiranta ya mata koda masifa ba iyaka ya tambayeta maisa tayi hakan ashe for all these while tara ta yake yau data kaisa maqora gashi har mak'ota ya shiga yana neman wanda zai taimaka ya aureta sekace wata bazawaran da tayi kwante, yau wannan wani irin abun kunya ne? Kuka ta cigaba dayi sosai a yayinda take rik'e da k'afan Mummy da jikinta yayi sanyi lis. Ita kanta Mummy bata ta6a  kawowa a ranta Daddy zey iya yima Nazeefah abu haka ba don ko ita be sanar da ita abinda yake ciki ba itama kamar yadda Nazeefah kejin news d'in haka yayi mata breaking d'azu. Sau dayawa takan zauna tayi tunanin mey tayi wa Allah ya bata 'yar da batajin magana ba kuma ta tsoron ido da bakin mutum kaman Nazeefah dukda tasan yin hakan kaman yima Allah shisshigi ne but she can't help it. Yarinya bata je ko ina ba amman ta gagari kowa? Shide Daddy yasan dalilin hakan, yasan the reason behind Nazeefah's naughtiness and everything tabbas past nasa ne yake hunting nashi, tabbas alhak'in baiwar Allahn daya ta6a ci in the past ne yake binsa...

  "Mummy am begging you please ki bawa Daddy hak'uri Mummy so kuke in kashe kaina? Auren dole fa Daddy yake shirin min and you're okay with it."

  "Am not okay with it Nazeefah" ta fad'a da k'yar tana danne hawayenta. "Banida wata option ne Sweetheart, Nazeefah ke kika janyo duk wani abinda yake samunki yau, kin nuna tsan-tsan rashin ji wa Daddy'nku tun yana hak'ura har hak'urin nasa ya k'are, Nazeefah your Dad is not proud of you, ze d'auki Khaleefah sau d'ari bey d'aukeki ba ki taimaka ki rufa mana duka asiri and obey him ayi wannan aure wata k'il ki shirya tsakaninku."

   "Mummy no please dan Allah kar kice haka wallahi zan canza give me one last chance wallahi I'll be the perfect daughter for you and Daddy amman karku min auren dole bana son Afzal, na tsane shi kaman yadda shima ya tsaneni Mummy please save me."

  "Ya zamo dole kenan ki yayyafa wa zuciyarki ruwan sanyi ki koyi sonshi saboda bakida wata option da tafi yin hakan, tashi kije d'akinki ki shirya ina zuwa" tana kaiwa nan ta janye k'afarta ta fice itama. Sabon kuka Nazeefah ta soma tsugune a wajen tamkar zata cire ranta. Seda tayi kaman ba gobe sannan a raunane ta mik'e tashiga takawa nan Khaleefah dake la6e yana sauraran komi a bakin staircase tun d'azu ya ruga sama a kuje to his room kafin ta kama sa. Shi kansa be tsamman Daddy ze iya yin abu haka ba, aiko tun wuri gomma ya shiga taitayinsa kamin ace za'a tura sa boarding kaman yadda Mummy ke fad'a masa kullum idan yayi wani rashin jin.

  *         *            *             *             *         *
     BACK TO GIDAN ALHJ AHMAD AMIN.

   "Oh! Esther seda nace miki kar kisa turaren wutan tukuna kibari se Prince ya fita amman kika k'i ji so kike ki kora min d'an nawa idan ya shigo?" Ummi ta tambayi Esther dake ta raba ido a k'asa.

  "A'a Hajiya kiyi hak'uri hakan baze sake faruwa ba."

  "Kiyi sauri ki fita dashi toh."

  "Toh Hajiya" da haka Esther ta fice waje da turaren wutan ta k'ofan kitchen wato k'ofan baya. Window da labule Ummi ta shiga bud'ewa da d'agawa don hayak'in ya ragu kafin Afzal yazo ya mata tsaye bakin k'ofa yak'i shigowa. Bada dad'ewa ba ya fito daga site nasa yana sanye da farin Gezna d'inkin half jumper data mugun amsar komi nashi, ya kafa hulan nan ras wane a gudu dashi don had'ewa, idan me rubutu ta tsaya describing kalan kyan da yayi to da alama ba inda masu karatu zasu je don haka muje zuwa.

  Duk angle daya bi se k'amshin designer turaren daya juye ajikinsa ya kama gun, cike da k'asaita kaman yadda ya saba tafiya yana juya key'n motarsa ya taka har ya k'ariso site na Ummi. Daga k'ofan ya tsaya don jin ko akwai hakay'i.

  "Toh Malam kana iya shigowa don kai na sa aka fita da turaren" se anan ya shigo ya miyar da k'ofan. A gefenta akan two seater ya k'arisa ya zauna "Prince irin wannan shan kyau haka?" ta tsaya tana admiring nasa wato komi nashi yayi ne "Ai seka sa Nazeefah ta rikice."

   "Ummi please nifa gun Abbanta zanje ba gun ta ba" ya wani murtuk'e fuska, to the mention of Nazeefah's name yaji mood nasa ya 6aci ma gabad'aya.

  "Toh du Allah wasa nike kana iya sake fuskan, so Abbanta yayi requesting ganinka wai ko?"

  "Yup haka Abba yace" ya amsa popping the P.

  "Welldone my son ka sanya Abbanka farin ciki, farin ciki na sosai wanda ko ni matarsa ban tsammanin zan iya sashi ciki. Kaji yadda ya shigo yake ta yaba ka kuwa and tell you what?"

  "What?" Yayi saurin tambaya, bakin ta tayi saurin go6ewa "Subhanallahi wallahi sirri yace mun kayi hak'uri."

  "Shine kuma kika ja min rai?" Ya tambaya yana pouting bottom lip nasa.

  "Kar ka damu bari in baka hint, yace yana son yayi surprising naka."

   "Awww" ya tsaya blushing tamkar a gudu dashi.

  "Kalli kyakkyawan fuskanshi anan Allah yaso da me mahaifiyarka nike."

   "Uhm wai me yake niyyan bani?"

   "Prince sirri ne fah kaga tashi ka fita kafin kayi latti" ta canza topic d'in da wayo "Today is your first impression it can't be ruined."

  "Uhmm toh sena dawo" yayi maganan tare da miqewa.

  "Maganan gaskia kayi kyau Prince yaci ace in d'auke ka hoto kafin ka fita."

   "God help me" ya fad'a murya ciki-ciki "Please Ummi sekace yau kika fara gani na?"

   "Naji nide tsaya tukun" ba yadda ya iya hakan ya tsaya ta d'auke shi, don neman magana ko kallon cameran nata ma beyi ba saidai hakan be hanasa yin kyau ba, se hoton yayi kaman irin unlooking picture d'innan. "Toh a sake bani wani pose mana d'an bani swags naka man kad'an" ta fad'a cike ca wasa trying to stimulate him, murmusawa yayi sannan ya gyara tsayuwan nasa me kyau kaman wani model tare da rik'e hannun riganshi dai-dai gun cufflinks nasa. A dai-dai nan Ummi tayi snapping moment d'in. "Wow! Masha Allah, toh good luck seka dawo."

  "Ummi please ba fa jarabawa zani ba."

  "Uhn-uhn fa Prince" tace dashi wanda ya sanya sa murmusawa, "Kidding, kidding thank you sena dawo."

  "Yauwa ka gaishe min da maman nata idan kun had'u."

  "Alright" ya fad'a lastly before stepping out. Gun motarsa data sha wanki k'al yayi ya shiga ciki tare da kunna ignition d'in. Gidansu Nazeefah yayi direct inda yace abokinsa Sultan ya jirasa.

*****
     Nazeefah na miqe akan gado a d'akinta tanata aikin kuka, damuwa da k'uncin rayuwa sun isheta Mummy tayi mata sallama akan cewa Afzal ya zo Daddy na kiranta. Ko ta kan Mummy batayi ba se kukan da take takanyin ta cigaba, nasiha sosai Mummy tayi mata akan idan har ba so take Daddy yayi mata baki ba toh ta rufa ma kanta asiri tabi umarnin sa ta amince ga auren nan. Ba don tana so ba ta sanya hijabi ta fice, fuskanta ya kumbura tim a yayinda idanunta suka kad'a sukayi jazir. La6ewa tayi daga jikin bango tana sauraran yadda Daddy ke tayima Afzal godiya sekace wanda ya basa gidan Aljannah kokuwa wanda za'a d'auki nakasasshiya a bashi, abin da yafi ci mata rai kenan. Itan da samari suke papa akanta suke binta amman wai ace Daddy har se ya had'a Afzal da Allah tukun ya amince ze aureta wani irin abin kunya da raini hakan ke nufi? Seda ta gama sauraron duk abinda suka ce tukuna tayi sallama ta zauna daga chan baya-baya. Sam batayi niyyan gaishe da Afzal ba amman tuna abinda Mummy tace mata yasa tayi unwillingly. Ko kallonta Afzal beyi ba hasali yima yayi at first kaman baze amsa ba sannan daga bisani ya amsan suka gaisa.

   "Afzal ina sakeyi ma godiya daka rufa min asiri a garin nan ka amince da auren Nazeefah wallahi ga ka ga ita na baka dama aduk sanda tayi wani rashin hankalin ka hukunta min ita saboda ta zama taka yanzu, tarbiyyar ta da komai ya koma hannun ka, ina da tabbacin ba wanda ze kulamin da ita ya kuma d'aurata akan hanya madaidaiciya sama da kai."

  "Ba komai Daddy zamu cigaba dayi mata fatan shiryuwa kai kuma kadena min godiya haka na amince da wannan auren ne don Allah."

  "Allah yima albarka Afzal, Allah cigaba da kareka bazan manta da wannan abu ba nagode sosai bari in barku tare ko akwai abinda kake son sanar da ita zan shiga daga ciki."

  "Not really Daddy nima yanzu zan tafi, Nazeefah in bazaki damu ba ki biyoni waje akwai abinda nakeson nuna miki" daga fad'in haka ya mik'e.

  "Bakiji mey yace bane kike zaune har yanzu?" Daddy ya tambayi Nazeefah dake ta faman kukan zuci tun d'azu hawaye nabin k'uncinta.

  "Naji Daddy" ta amsa in a teary voice tare da miqewa tana bin bayan Afzal. Chan wajen gate inda yayi parking motarsa ya nufa, Sultan abokinsa dake gaban motan ne ya bud'e k'ofan ganin Afzal na isowa. A gefen k'ofan ya tsaya yana jiran Nazeefah ta k'ariso bayan tayi hakan yayi shiru ya tsaya yana kallonta. Kallon dayasa duk wani gashin jikinta tashi, kallo yake mata cike da rashin mutunci da k'yama kusan sau uku idansu ke had'uwa amman har yanzu baice da ita komi ba, ita kuma Allah bai bata ikon cewa wani abu ba.

   Daga bisani yace, "Bazan aure ki ba Nazeefah, bazan ta6a auran k'azamar mace kamar ki ba wacce sama da maza goma sun ta6a kowani lungu na sashi a jikinta, bazan auri macen da take yawo akan hanya dressing almost half naked ba, bazan auri matar da batada kunya da kuma k'arancin ilimin addini ba kamar ki. You disgust me Nazeefah, idan har kinsan ciwon kanki kinsan ina ke maki ciwo baza kibari wannan aure ya auku tsakani na dake ba saboda I'll never learn to respect and regard you as a woman than a wife because kin riga kin zubar da darajar ki da k'ima da kuma mutunci a idanu na. Just to tell you how worthless you're, akuya ma tafiki daraja a idanu na" yana kaiwa nan ya tsaya don jin ko zata fad'i wani abu amman ko uffan ta kasa cewa. Hawaye ke bin k'uncinta kawai, tunda tasan kanta ba a ta6a humiliating nata haka ba, don ya fad'a mata wannan munanan kalamun ne dama ya ma Daddy k'arya yace yana son nuna mata wank abu? Ashe don yaci mata mutunci a gaban abokinsa ne? Don yasata ta tsani kanta? Bata san mey ya hanata miyar masa da magana ba a lokacin saboda sanin kowa ne Nazeefah nada baki ba'a ta6a ta tayi shiru se gashi a lokacin data fi buk'atan bakinta ya bud'u yak'i yin hakan. Toh mey zata ce masa bayan wannan munanan kalamun daya kwatanta ta dasu? Yes he might be right, there is amount of truth acikin duk abinda ya fad'a but just because Daddy yace ya basa ita doesn't mean he has the right to hurt her feelings like this. Ai ko macen da take sana'ar karuwanci ma bata so akira ta da mazinaciya.

    Ganin bata da niyyan cewa komi banda hawayen da take tayi Afzal ya cigaba "They say a word is enough for the wise I hope this is message enough for you, you can go back in, greet your mother when you do sai anjima." Yana kaiwa nan ya zagaya to the driver's side ya tada motar tare da kad'a mata k'ura. Tsaye Nazeefah tayi wajen wane gunki se aikin kuka take, sauk'a har k'asa tayi a wajen tana kukan cire rai.

   Wacce irin rayuwa ce wannan?

RANA D'AYA
BY MIEMIEBEE

PAGE 06



    "Nifa ka sani acikin duhu, wai meke faruwa ne?" Sultan ya tambayi Afzal dake tuk'i cike da rashin hak'uri da neman k'arin bayani. Shiru Afzal ya masa yana me sa hankali sosai akan tuk'in da yakeyi.

  "Triple A?" ya kuma kiransa kusan sau goma kenan tun zamar su cikin motar.

  "Bansan yaushe ka kurmance ba wallahi, referring to abubuwan da kaji na fad'a mata ai yaci kasan auranta mahaifinta yakeson inyi."

   "Nazeefan fah?" Sultan ya tambaya cike da d'umbun mamaki.

  "Ask me again" ya fad'a tare da basa d'aya daga cikin mugayen kallonsa sannan ya maida kallonsa kan hanya.

  "How?? Triple A kabani labari please."

  "Idiot ai labarin nakeson baka yasa nace ka taho."

   "Asshole" ya fad'a tare da kai masa punch a hannu "Am all ears" nan Afzal yashiga zazzage masa dukannim abubuwan da suka gabata tun daga yinin jiya, a haka har suka iso layin dake kusa da gidansu Amal.

   "Tsaya maza mey kuma zamuyi anan? Mey ya kawomu unguwan nan? Kode kayi 6atan kai ne?" Sultan ya tambaya nan take.

  "Nop" ya amsa tare da popping P d'in "Ina yarinyan dana fad'a maka na bugeta accidentally jiya?"

  "Yes" ya amsa tare da gyad'a kansa "Dr ya buk'aci a mayar da ita yau a sake treating k'afan so am here to fetch her" ya fayyace mar.

  "Toh shine se kai ne zaka kaita? Ai tunda ka riga ka biya kud'in komai se ka bawa mamanta transport fee tana kaita."

   "No Sultan I cursed this upon them, ganganci na ya kaini kad'eta I have to take full responsibility."

  "Toh Mr good samaritan jeka ina jiranka" ya amsa shi cike da gatsine. K'aramin mirror dake gaban driver seat Afzal yaja yana duban fuskansa tare da sake daidaita hulansa sannan ya fice. Shi de Sultan baice komi ba illa binsa da kallo da yake.

  Sallama yayi a hankali alokacin da yake sa kai cikin gidan. Amal ya tarar zaune akan benchin jiya da wani novel na English rik'e a hannunta ta zurfafa ciki tana karantawa. Sanye take da wata atamfa riga da skirt wanda ta mugun amshe kalan skin nata, kanta kuwa ba d'ankwali hakan ya bawa Afzal daman ganin silky gashinta dake nan kaman na bak'ak'en 'yan India. Kamashi tayi a tsakan kanta tare na nannad'e jelar wanda a sanadin haka Afzal be samu daman gano k'arshen ba. Kallonta ya tsaya yi musamman yadda ta miqar da k'afan nata me targad'e wane wacce ke jiran koda kuda ne ya ta6a ta hau bala'i da k'orafi.

  "Uhm uhm" yayi gyaran murya wanda hakan yasa Amal tsaida duk wani abinda takeyi ta d'ago kanta domin ganin wanene. Wani irin d'an banzan tsinkewa zuciyarta tayi ganin Afzal tsaye akanta da ratan da befi meters biyu zuwa uku tsakaninsu ba. Da sauri ta dukar da kanta a lokacin da idanunsu suka had'e tana me neman mayafi don lullu6e jikinta sede ba halin yin hakan dan k'afarta. Yadda zama ke bata wuya haka zalika miqewa don haka kawai ta shiga kare k'irjinta dukda cewa bawai ya bayyano waje bane. Shiko Afzal ganin ta soma yin wasu abubuwan yayi saurin juya mata baya totally dan kuwa bega abun gani ba achan da take ta wani faman tarewa.

  A hankali ta d'ago kanta taga gabad'aya ma baya ya juya mata aiko take ta murgud'a mai baki "Tafi nono fari" ta fad'i can k'asa-k'asa sannan ya k'wolla ma kira.

   "Mamiiii!" Dan k'ara irin na muryarta seda Afzal ya toshe kunnensa.

   "Ki fito kinyi bak'o and please ki taho min da hijabi na."

  "Toh" Mami ta amsa daga ciki, bada dad'ewa ba se gata nan ta fito, ganin mutum kaman Afzal ne yasata sakan murmushi. "A'ah Afzal ko?"

  Se anan ya kewayo nan ta tabbatar shi d'inne "Sannu da zuwa Baba na ina yini?" Ta gaishesa tana mik'a wa Amal hijabin data fito mata dashin.

   "Yauwa Mami ina yini? Ya gajiya?" Ya amsa cike da girmamawa.

  "Lafiya k'alau ya kayi tsaye haka? Ka k'ariso ciki mana. Ke Baby haka akeyi ne seki bar bak'o tsaye bazaki ce masa ya k'ariso ba?" Mami ta tambayi Amal data had'e gira gu d'aya.

  "Yo ba nace ya shigo ba yayi tsaye wajen" ta fad'a cike da rashin kunya. Baki Afzal ya bud'e cike da mamaki yana kallonta wato acikin had'uwa biyu da sukayi ya karance Amal is such a big liar, gashi comfortably take yin k'arya kuma bata d'auki hakan a bakin komai ba.

  "Toh gaisuwa fa? Kin gaishe shi?"

"Abinda na farayi kenan daya shigo" ta kuma amsawa. Shide Afzal bece komai ba. "Bari in d'auko ma taburma mana ka zauna Afzal ko ruwa ne kasha."

  "A'a Mami karki damu daga gida nake nazo d'aukan Amal ne ayi dressing k'afan nata kaman yadda Dr ya buk'ata" Kafin Mami tace za tayi magana Amal har ta tsoma baki ta soma k'orafi "Ni wallahi ban komawa asibitin chan in kanayi wa Allah ka koma inda ka fito nagode da kulawarka amman ban sake taka k'ofan asibitin chan." Har anan Afzal bece komi ba saboda yasan abinda ya tanadar mata.

  "Yau ina ganin ikon Allah!" Mami ta tsaya kallonta tare da dafe k'irji "Ke da hankalinki? Yanzu ya dace ki fad'awa mutumin da ke nema maki lafiya wannan kalamu? Wallahi karki bari raina ya 6aci in basa hak'uri yayi tafiyansa yaso k'afan naki yayi tsami ya ru6e in kaiki nan gun wanzan a gintile kowa ya huta." Dariya sosai comment na Mami yabawa Afzal don haka ya shiga gyaran murya don had'iye dariyar sede still seda curves na murmishi suka nuna a fuskansa. Wani kallo Amal ta watsa masa tare da fad'in wasu kalamun chan k'asa-k'asan muryarta yadda ita kad'ai tasan abinda tace.

  "Maza tashi karki 6ata min lokaci!" Seda ta gama tsiyarta sannan ta amince Mami ta taimaka mata ta miqar da ita.

  "Toh Allah ya kare Afzal kaikuma Allah ya biya."

  "Ameen Mami" daga fad'in haka ya fice Amal na k'ingishi tana mara mai baya har suka isa gun da motarsa ke. Kasancewar motar tinted ce Amal bata samu daman gane cewa da akwai mutum acikin motar ba shi kuwa Afzal shiru yayi mata daya ga tana nufan k'ofan gaba. Tsaye yayi yana jiran na aukuwa ya faru. Tana bud'e k'ofan kawai setaga bak'on fuska na kallonta, kunya tajiyo sosai yanzu Afzal yasan da mutum cikin motan yamata shiru har ta bud'e? Yamar kyau.

  "Ina yini?" Ta gaishe sa cike da kunya tana ja baya a hankali se kace ba ita ba.

  "Lafiya 'yan mata kin 6ata ne?" Sultan ya tambaya danko besan itace yarinyan da Afzal ke nufi ba.

   "Ban san da mutum aciki bane am sorry." K'ofan ta miyar mishi tare da d'ago kai tana kallon Afzal dake ta faman kallonta shima dariya ya ciko mar dam a baki amman ya dage ya danne. Ba tare da yace mata komai ba ya bud'e motan ya shiga wanda itama tayi hakan. Bayan ya kunna motan Sultan da kansa ya d'aure ya juya ya dubi Amal sannan ya kalli Afzal sam be kawo a ransa cewa budurwa ce Afzal ya buge ba cause yadda Afzal ya basa labarin k'iriniyar yarinyar seyayi picturing nata to be 13-14 years.

  "Itace yarinyar?" Ya tambaya not believing it.

  "Wai ba" Afzal ya amsa sa in an I don't care tone tare da yin reverse suka hau kan hanya. "Kana bani labari" cewar Sultan after a while "Amman Triple A bakada mutunci."

  "Da nayi meh?" Ya tambayesa yana me miyar da hankalinsa sosai game da tuk'in da yake a yayinda Amal dake baya ta ware kunnuwanta domin jin abinda wannan mara mutuncin yayi da har abokinsa ke mamaki haka.
 
  "Kaji kalan kalamun daka fad'awa yarinyan chan mana Nazeefah" ta6e baki Amal tayi, dama tasan za'ayi haka a yayinda ta cigaba da kasa kunne.

  "She needs to be told the truth" Afzal ya miyar masa ba tare da ya nuna damuwa ba.

  "Toh kai kasan ka k'yamaceta haka meyasa ka amince da k'udurin auren nata?"
   Aure de? Amal ta nanata a ranta, lallai ta tausayawa 'yar da zata auri wannan mutumi me uban ji da kai haka, ai kuwa gashi tun ba'a je ko ina ba abokin shi yace baida mutunci be kyauta ba, ko mey ya gaya wa yarinyan se Allah. Shiru tayi tana me cigaba da sauraran hiran nasu.

   "To make Abba happy" ya amsa sa simply.

   "Hmm fire on the mountain sunan wani abu, Afzal da Nazeefah a k'ark'ashin rumfa d'aya ai akwai show" jin Afzal be amsa shi ba ya cigaba "Triple A tell me something mana kode dama kanada interest akan yarinyar ne?"

   "Interest?" Afzal ya nanata cike da mamaki yanzu upon all people Sultan ne ze fad'a masa wannan batu? Lallai amman be kyauta ba, ai wannan zagi ne.

  "Dan Allah ka miyar da kallonka kan hanya kafin kaje ka zubda mu" yace da Afzal daya tsaya yana kallonsa da alama ya manta akan hanya yake domin ko niyyan kau da kansa ba beyi ba.

   "This is an insult to my face Sultan, ai ko Nazeefah ce autan mata I'll never learn to love her, she simply disgusts me."

   "Hmmm nide nayi shiru amm-"

   "Shut up Sultan" yace dashi tare da katse sa. Shirun da Sultan beyi ba kenan ya cigaba da neman tsokan Afzal har sanda suka isa asibitin amman ko uffan Afzal be ce dashi ba, hasali manna mishi yayi. Dukansu uku suka kuguma suka fita inda suka nufi cikin asibitun tun daga harabar Amal ta soma kauce-kauce ita bata so Afzal yayi hak'uri ya maidata gida, ita kad'ai tasan azabar dataji jiya sede ko kallonta beyi ba bale yasan tanayi. Bayan sun gaisa da likitan ya kewayo da fatan ganin Amal se de ya ganta chan tsaye bakin k'ofa ta maraice fuska. Murmushin mugunta ya saki sannan ya dawo da kallonsa akan likitan tare da yin gyaran murya, "Dr ya naga kaman jiya baku ja k'afar yarinyan can kaman yadda ya kamata ba?"

   "Ba'a ja ba kuma Alanguburo? Meyasa kace haka?"

  "Toh gashi k'afan nata yayi tsami ya kumbura-"

  "Wallah bai kumbura ba" Amal da ta kasa kunne tana sauraronsu tayi saurin katsesa "Wallahi be yi tsami ba Dr don Allah karka sauraresa" ta fad'a cike da tashin hankali. Shareta Afzal yayi ya cigaba, "Gashi na kawota yau ina son ku jashi sosai please, a ja sosai saboda kar a samu complications nan gaba."

  "Toh Alanguburo in shaa Allah ina yarinyan ne? Ke shigo mana" yace da Amal yana maida kallonsa a gareta. Ja da baya ta farayi da niyyan ta gudu.

   "Don't even think of running ga nurses da securities kota ina sasu zanyi su kama ki" Afzal ya fad'a cikin tattausar muryar data mugun razana Amal da tuni tasa kuka. Wai don meyasa yake mata haka? Kode don rashin kunyan da take mar ne yayi tunanin ramawa ta nan? Tayi tunanin haka a ranta. Ai kuwa ya zama dole ta basa hak'uri yanzu dukda cewa yin hakan bawai yana nufin bazata kuma mar rashin kunyan bane idan yayi mata abinda be gameta ba.

  "Afzal- no" tayi saurin kad'a kanta "Ya Afzal dan Allah kayi hak'uri wallahi bazan sake ba."

  "Yaya?" Ya nanata a yayinda dariya me k'arfi ya ku6uce mar bashi kad'ai ba harta Sultan. "Ni ne Yaya? Guy kanajin yarinyan nan?" ya juya tare da tambayan Sultan nan suka kuma fashewa da wata dariyar barin ma Afzal da yake sark'ewa. Amal ji take kamar ta bisu da mari, ba abinda ta tsana kaman a tsaya ana yi mata dariya amman ya ta iya?

   "Wallahi a kullum kai Yaya na ne ai ko ido ma ma'auni ne" tayi saurin bashi amsa a rud'e.

  "Kinga karki kaini inda Allah be kaini ba" ya fad'a yana composing kansa, "I don't have any sibling so am nobody's Yaya."

  "Wallahi a'a kai Yaya na ne kuma ai bazaka so a cutar maka da k'anwarka ba ko? Dan Allah ka fad'awa likitan nan karya ja min k'afa da zafi."

  "Nak'i" ya fad'a a takaice.

  "Dan Allah Ya Afzal kayi hak'uri bazan sake maka rashin kunya."

  "Wancan kuma ke ya dama ki shigo suyi miki abinda ya kamata na maidaki gida I have things to attend to."

  "Dan Allah I'm sorry" ta fad'a tana kad'a kai.

  "Doctor ka turo nurses su jawota jiki she's wasting my time."

  "A'a don Allah zan shigo da kaina."

  "Then make it quick" ya fad'a tare da galla mata wata mumunar kallo. "Kina fa 6ata min lokaci" ya kuma fad'i ganin bata motsa ba.

  "Zan shigo zan shigo" ta fad'a a kid'ime sede fiye da minti biyu ta kasa takowa ciki.

  "Ina nurses d'inne kam wai?" Afzal ya tambaya yana kewaya.

  "A'a dan Allah zan shigo, wallahi zan shigo." Da hakan ta k'ariso ciki tana k'ingishi. "Please kace musu kar su ja min k'afan Ya Afzal."

  "Nak'i" ya sake nanata mata ko d'igon tausayi babu a tattare dashi.

  "Bazan sake maka rashin kunya ba wallahi na tuba."

  "Guy pardon her please" fad'in Sultan dake tsaye daga gefe guda sede sanin taurin kai da zuciya irin na abokinsa yasan ba lallai bane ya jisa balle ya sassauta wa yarinyan.

  "Make me" ya ce dashi tare da basa one of his nasty looks. "Ba ruwanka you better stay out of this, nurses take her in ku ja min k'afan nata sosai don idan yayi tsami ina tabbatar muku da cewa zanyi suing asibitin nan naku duk ku rasa aikinku kuma" ya razanasu. Haka nurses suka taho suka ja Amal se ihu take tana had'a Afzal da Allah amman yayi tamkar bada shi yake ba, idan ba hakan yayi mata ba bazata daina mai rashin kunyar ba. Bayan long draman da aka sha tsakanin Dr, nurses da Amal aka samu akayi retreating ciwon aka sa mata sabon bandage suka kuma jashi sosai kaman yadda Afzal ya buk'ata. Fuskan nan duk jirwayen majina da hawaye gabad'aya ta fita daga hayyacinta.

  Dariya sosai Sultan ya saki lokacinda shi da Afzal suka shiga d'akin suka tarar da ita zaune bakin gado tana aikin share hawaye. Shima Afzal d'in dariyar ce ta k'eto mar amman kaman yadda ya saba bonewa hakan yayi.

   "Lets go" yace da ita, da mamaki yaga ta mik'e ba gardama ba suratai. Lallai plan nasa yayi working.

   "Triple A yaci ace an saya mata koda ice cream ne ta d'anji sanyi a ranta da wannan muguntar da kasa nurses sukayi mata" cewar Sultan lokacin da suka wuce ta downtown. D'ago ido Afzal yayi yana hangenta ta mirror yadda tayi tsit a motan kaman ba ita aciki.

   "A saya miki kinaso?" Ya tambayeta da gan-gan yana wani murmusawa ta gefe. Idanunta takai inda nasa suke sannan ta kad'a kai a hankali "Karku damu nagode" ta fad'a a nitse ba Afzal kad'ai ba har Sultan yasha mamaki. Wani murmushin ya kuma sakewa sannan ya miyar da kallonsa kan hanyan. U turn yayi suka koma baya inda ya tsaya ya sai mata ice cream d'in.

   Bayan ya kaita gida ya mik'a mata, jira yake ta amsa ta bud'e ta kwa6ar a k'asa tunda de wanka ta biya kud'in sabulu gashi ya kawota gida se kuwa yaga tana kad'a kai "Nagode ni zan wuce gida" ta sanar dashi kanta a sunkuye.

    "Haba 'yan mata, yi hak'uri ki kar6a kinji?" Cewan Sultan cike da dabara. Ba ta kuma yin musu ba tasa hannu ta amsa tare da masu godiya sannan ta bud'e k'ofar.

  "Sekuma gobe ko?" Cewar Afzal da gan-gan domin jin me zatace.

  "Eh Allah kaimu" ta amsa calmly. Killer smile nasa ya saki ashede plan d'in yayi working, frankly ko shi be d'au ze iya yin abinda yasa akayi mata ba, but he had to it is the only way da zesa ta dena masa rashin kunya.

   Tun daga ranan Afzal ya cigaba da d'awainiyar Amal kamar yadda yayi alk'awari. Mostly daga office bayan yaci lunch seya biyo ya d'auketa, wani sa'in sukan taho tare da Sultan mostly kuma shi kad'ai yake zuwa. Amal kuwa tun rana me kaman na ranan bata sake yiwa Afzal rashin kunya ba, cike da girmamawa da ladabi take gaishe sa duk sanda yazo, bata kuma fasa kiransa da Ya Afzal d'in ba, har abin ya zame mata jiki. Shima Afzal kullum daga clinic se sun tsaya a downtown sun sai mata ice cream. Ranan daya kaita dressing na k'arshe bayan ya kawota gida Amal tayita insisting cewa ya shigo ciki suyi final sallama da Mami tunda basu samu daman yin hakan ba d'azu kasancewar Mami bata gida daya taho. Sam baida niyyan shiga ciki again sede kuma yaga Amal nada point idan ba wani ikon Allahn ba kam ai ba abinda ze sake kawosa gidansu, yaci ace sunyi ban kwana da Mami.

  "Kaji Ya Afzal kashigo ku gaisa da Mami please" ta kuma cewa ganin be ko motsa acikin motar ba. "Pleaseeee Ya Afzal." Juyowa yayi yana k'are mata kallo seji yake a jikinsa Amal is upto no good, dama chan bawai ya yarda da wannan d'abi'un da take portraying bane ace for the past 6 days ko rashin kunya bata mishi sema ladabi da biyayya.

  "Amal?" Ya kira sunanta yana k'are mata kallo.

  "Na'am" ta amsa tare da sunkuyar da kanta tana wasa da ledan ice cream daya siya mata.

  "Wani abin kike shirin yi ko? Kinsan I don't trust you not even a single bit."

  "Haba Yaya har mey yayi zafi haka? Mey zanyi maka? Allah ba komai kawai inason kuyi bankwana ne da Mami kaga ai idan ba wani ikon Allahn ba bazaku k'ara had'uwa ba."

  Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauk'e "Let's go" nan ya kashe motan suka fice. Bayan sun k'arisa ciki Amal ta shimfid'a mai taburma tare da yima Mami da Papi sallama, bayan sun fito ta nuna musu ice cream da Afzal ya sai mata. Godiya sosai sukayi mishi sannan suka gaisa, da wayo ta saci jiki ta fice ba tare da sunyi realizing ba.

  Pins da k'usosin da ta tanada ta ciro sannan ta k'arisa gun motan nasa, tayan baya ta sace dana gaba sannan ta gwada bud'e motar haushi taji datayi confirming a kulle ne if not da tayi niyyan kwa6ar mar da ice cream d'in acikin motar ne next time se taga idan ze sake sa mugayen likitocin asibiti su ja mata k'afa kai bama ita kad'ai ba koda wata ta daban. Seda ta ga tayoyin sun soma tsotsewa sannan ta kama hanyan gidansu Azee inda suka hau shan ice cream suna hira. Afzal kuwa bayan sun gama gaisawa dasu Mami sun d'an ta6a hira kad'an yace ze tafi, har wajen gida suka rakasa sannan suka koma ciki. Yana wasa da makullin motansa yana tafiya har ya isa inda yayi parking motan nashi, sam hankalinsa be kai ga patched tires guda biyun ba seda ya shiga yasa key ya shiga neman yin reverse yaji mota yak'i baya balle yayi gaba. Tirk'ashi, accelerator yata dannawa amman ina mota yak'i motsawa hakan yasa ya fito don duban inda matsalar take to his ultimate surprise yaga tire biyu duk a pache. Da farko yayi tunanin ko 'ya'yan unguwa ne suka mai d'anyen aikin nan amman tuna yadda Amal ta dage sam seya shiga sun gaisa da Mami yasa ya soma zarginta.

   Tabbas yarinyan nan bata da kunya, upon duk d'awainiyyan dayayi ta mata da abinda zata saqa masa kenan? Lallai kuwa she's messing with fire. Ji yake kaman ya shiga gidansu ya nunawa Mami da Papinta abinda 'yarsu tayi mar amman tuna ba lallai ne su hukunta ta kaman yadda yakeso ba yasa ya fasa, yafison ya hukuntata da kansa, hukuncin da ko akan layi ta gansa seta canza hanya. Murmusawa yayi ya ciro wayansa daga aljihu tare da kiran mechanic nasa. Within 20 minutes ya iso sede ba pachi kad'ai Amal tayi ba, tiren gaban entirely yasamu matsala wanda idan ba ikon Allah ba se an canza shi gabad'aya. Anan de mechanic yamasa concluding cewa mota bazata gyaru a yau ba. Wayan Sultan ya kira don yazo ya d'aukeshi sede switched off yakeji. Be damu ba yashiga neman driver'n Daddy nan ma network yak'i barinsa. Abu fa kaman wasa se trying yake amman network yak'i bari call ya shiga chan kawai service ya d'auke gabad'aya.  Babban magana! Ji Afzal yake kaman ya k'urma ihu bayan nan yaje ya nemo duk inda Amal take a fad'in unguwansun nan ya nad'a mata na jaki.

  Abu kaman wasa network yak'i dawowa gashi se ci yamma keyi, bayan d'an gyaran da mechanic yayi yakuma cire important parts na motan gudun kar 6arayi suyi gaba dasu dake motan ma se an barta ta kwana anan ya buk'aci Afzal daya bisa cikin keke napep daya taho sesu sauk'eshi a gida. Kallo Afzal ya tsaya yana mishi, wai da shi yake? Shi yake tsammanin ze shiga keke napep? Bawai yana nufin yafi k'arfin shiga bane sede bai ta6a shiga motan haya ba se gashi yau akan 'yar gudun hinirar can ze soma yin hakan? Lallai kuwa duk rananda Allah ya sake had'a path nasu seta gwammaci kid'a da karatu.

  "Kayi shiru ranka ya dad'e yamma ne keyi fah" fad'in mechanic d'in.

  "A'a kayi tafiyanka I'll wait a bit longer halan network ze dawo se in samu in kira gida suzo su d'aukeni."

  "Hmmm kana magana sekace ba a Maiduguri kake ba? Kade san idan network ta d'auke to se wani ikon Allah kesa ta dawo a lokacin da de hak'uran kayi muka kaika gida tunda ga keke free ne na yaron gidanmu."

  "Sekuma aka ce maka gudun kud'in nakeyi? Ni kawai kuje Allah kaimu goben."

  "Toh shikenan seda safe." Da haka suka fice a yayinda Afzal ya cigaba da tsayuwa wajen yana jiran dawowan network, can daya gaji ya bud'e motan nasa ya shiga se duban screen na wayansa yake ko network ze dawo amman ko alamun hakan babu. Around biyar da minti sha biyar na yamma 5:15pm Afzal ya soma losing hope, the earlier the better idan de ba so yake ya kwana cikin motan nan ba toh tun wuri ya kama hanya ya nemi a daidaita sahu ya shiga. Shi tunanin yadda ze fita cikin wannan kwamacalan unguwan ma yake, 'yan unguwa ba manya ba yara duk angle da mutum yabi se sun bisa da ido suna gulma k'asa-k'asa. Cike da takaici ya shiga takawa trying his best not to get distracted. Har bus stop yakai sannan ya soma ganin napep nan ma duk masu passengers aciki ne suke wucewa shi kuma ya rantse saidai dare yayi masa da yashiga me passenger. Yayi kusan minti sha biyar sannan ya samu empty ya shiga, kowani pothole (gargada) aka shiga har cikin k'wak'walwansa yake ji. Se yanzun ya ke sake yima Allah godiya da duk wani abinda ya mallaka masa badon wai yafi sonsa bane akan sauran bayinsa kokuwa don ya kai se don haka yaso abinsa. Isansu gida keda wuya Afzal gabaki d'aya ya galabaita d'ari biyar ya mik'a wa me mashin d'in inda yake tambayarsa ko yanada naira d'ari se ya bashi d'ari hud'u.

  "Ka rik'e duka ko kayi sadaqa da abinda ya rage" ya sanar dashi rai a murtuk'e sannan ya k'arisa ciki aka bud'e mishi gate. Lokacin har an sauk'o daga sallan Maghrib, Abba ya tarar a waje shima yana shirin fita da driver a gaba yana sauri don bud'e mishi k'ofa.

   "Ha'a wancan ba Prince bane?" Abba ya tambayi driver'n yana k'arewa figure'n Afzal kallo don tabbatar da zancen nasa.

   "Shine Alhaji" driver'n ya masa confirming.

  "Prince ya haka? Ina ka shige?" Abba ya tambaya alokacin da Afzal ya k'ariso inda suke. "Network ya d'auke muna ta neman ka amman bai shiga, ina ka shiga ne? Ina motanka kuma?"

   "Hmm Abba long story motana yayi pachi da keke napep ma na k'ariso gida" ya fad'a tamkar zeyi kuka. Dariya ce ta kauce wa Abba har yana neman sark'ewa, ina irin dariyan nan da alhazai keyi ana yi ana jan nishi? Irin shi Abba yay tayi da k'yar tukun ya samu ya tsagaitar.

   Lallai ma kuwa Afzal ya furta a ransa yana me mamakin Abba yanzu dariya zeyi masa akan ya tausaya masa? Ai yasan Ummi bazata mishi haka ba.

   "Ahhh it's good it's good" fad'in Abba yana neman kame dariyar da ke sake son kauce masa "Kaga ko a babu yau kayi sabon experience koba haka ba?" Saidai shiru Afzal yayi bece komi ba ga girar nan ya had'esu kum waje guda. "Toh ka kwantar da hankalinka wuyan daka sha yau d'innan tattare yake da alkhairi."
   Alkhairi de? Ya nanata a zuciyansa. Kallon Abba ya tsaya yi a yayinda ya zira hannu a aljihu tare da ciro wata k'aramar pack.

   "Gashi open this" ba gardama ya amsa ya bud'e key'n mota ya tarar aciki. Toh fah! Ido ya d'ago yana kallon Abba cike da mamaki da neman k'arin bayani.

   "Danna security ne kuma baka iya ba Prince?" Ya tambeysa jokingly. Nan ya danna inda d'aya daga cikin motocin da suke fake a parking lot tayi k'ara, da sauri ya maida kallonsa wajen tare da kuma dannawa don tabbatar da wace mota ce tayi k'aran. Sabuwar 2017 Mercedes Benz ce C43 AMG biturbo k'al acikin leda yaga tayi wuta, fara tas an k'ayata ta da black satin and ribbons.

  "Abba!" Yayi exclaiming cike da mamaki bil adad alokaci guda ya nemi bak'in cikin da Amal ta tusa masa ya rasa. Shi abinda yafi basa mamaki ma  shine yadda Abba yasan wannan ne motan da yake tason ya siya tun watanni uku da suka shud'e wanda yake dai-dai da lokacin da motar ta fito. Kawai tuna lokacin da ya tura wa Sultan pic d'in yake, har yake cemar ga motan da yakeson ya siya toh har yaushe Abba ya shiga zuciyansa yasan sabon mota yake buk'ata when ko shekara biyu ma na wajensa beyi ba?

  "Abba! Mota ka siya min?" Ya sake tambaya full of wonder.

   "Yes Prince ai na fad'a wa Umminka ta sanar da kai cewa na tanada maka tsaraba fatana de Allah sa tsaraban ya kar6u kuma ya burgek-" Afzal be basa daman k'arisa maganan daya soma ba ya rufe sa da runguma tsan-tsan murna da farin ciki. Da murmushi kwance fal a fuskan Abba ya zagaye hannayensa bayan d'an nasa shima, hugging him back.

   "Abba thank you so much! I don't know how to express my gratitude walalhi you made my evening" ya sanar dashi ba tare da ya katse rungumar ba.
  "Am glad you like it son" se anan Afzal ya sake shi sannan ya juya yana kallon motan.

  "Nasan so kake kaje kaga cikin motar kaman yadda nima nake son fita yanzu inada conference da colleagues d'ina so ina fatan this year will be convenient for you ko?"

  "For what Abba?" Ya tambaya a takaice da farin ciki kwance a birnin zuciyansa.

   "Hajj nakeson kaika inason ka zama Alhajin kanka kaima Prince" Dad'i ninkin ba ninkin na d'azu ne ya ziyarci zuciyan Afzal wai kam ya akayi duk abinda yake dashi in mind Abba ke shirin miyar masa dashi reality? Tabbas ranan sunyi hirar nan da Ummi na cewa yanason yayi aikin Hajji wannan shekaran saboda bai ta6ayi ba a kullum yaje Saudi Umarah kawai yakeyi. Ji yake as if duniyan ma tayi kad'an ta d'aukesa don murna.

   "Abba bazan iya tuna when last nayi kuka ba but with what you're doing you're making me want to. Abba this is the perfect time da nakeson yin Hajji har nayi discussing da brand manager namu ma."

   "Toh Alhamdulillah seka shirya idan Allah ya kaimu lokacin seku tafi tare da Umminka."

   "Abba thank you so much, Allah miyar maka da gidan aljannah ya k'ara bud'i kuma."

   "Ameen Prince."

  "Saide bansan me nayi dana cancanci kyautuka haka ba."

  "Prince farin cikin daka sanya ni da ka amince da k'udurin mahaifin y'ar nan kad'an ne daga cikin wanda kakeji yanzu. Nide ba abinda zance se Allah cigaba da yima albarka ya baka 'ya'yan da zasu kula da kai su kuma farinta maka kaman yadda kake min ko fiye da hakan ma."

  "Ameen Abba thank you so much."

  "You're welcome barin wuce kar na makara."

  "Toh Abba ka dawo lafiya" bayan motan Abba ya fice Afzal ya k'arisa gun sabuwar motarsa har ya shige ciki seya tuna be d'auke ta a hoto ba, nan ya fito ya d'ad'd'auka sannan ya koma ciki ya shiga dubanta. Ba don yana so ba se don beyi sallan Maghrib ba yasa ya sauk'o ya nufi site na Ummi, alokacin tana bayi tana wanka. Guest toilet ya fad'a yayi alwala sannan yayi sallah, bayan ya idar yayi azkhar nasa sannan ya wuce d'akin ta tare da knocking. Tana amsawa ya shiga inda ya tarar da ita zaune kan stool na dresser side tana kwalya.

    "Oyoyo my Prince ina ka shige haka? Gabad'aya ka tada min hankali" ta fad'a tare da kewayowa tana kallonsa.

  "Ummi you can't believe this!" Abinda ya soma ce mata kenan ko ta kan abinda tace beyi ba balle ya gaishe ta.

  "An saya wa baby na mota!"

  "Yes!" Yayi exclaiming "So you knew?"

  "Eh mana ai surprise ne so did you like it?"

  "Yes!" Ya kuma exclaiming yana zama daga bakin kan gadon ta inda take zaune akan stool d'in. "Ni nama rasa ya Abba yayi yasan this car in particular nakeso wallahi kinsan tunda ya fito naketa budgeting yadda za'ayi in siya."

  "Thank your friend then."

  "Wa kenan Sultan?"

  "Shi de, shi Abba ya kira ya tambayeshi ko yanada masaniya akan abinda idan aka baka shi zakaji dad'i sosai ya bada amsa da wannan AMG."

  "Allah sarki Sultan, I feel like the happiest soul alive."

  "Ga kuma zamuje Hajj, it's a wrap!"

  "Ummi please thank Abba once more."

  "In shaa Allahu Prince."

  "Toh tashi muje kiga cikin motan kinga panaromic roof d'in kuwa? Da car radio d'in? My goodness! Wani abun ma sekinga gearbox d'in ga wani k'arar da take badawa kafin engine ya tashi" ya fad'a sounding happy. 

  "Tsaya to in gama jan girar nan se muje." Jirarta yayi bayan ta gama suka fice inda Ummi ta rik'a sawa motar albarka.
  Suna cikin cin dinner ne ta tambayesa inda motarsa take kasancewar bata gani a inda ya soma parking ba.

   "Kede kar ki tuno min da batun motan can kinsan kuwa acikin keke napep na dawo gida yau?" Dariyan da Abba yayi masa haka ma Ummi ta zauna tayi shide ya rasa abin dariya anan, "Wayaga Prince acikin a daidaita sahu" se ta kuma k'yalk'yalewa da wata dariyar.

  "Seki tayi ai" ya fad'a a fusace tare da jan k'aramar tsuka. Bayan ta gama neman tsokanan nasa kwatsam sak'on da Abba ya bata ta isar masa ya fad'o mata.
  "Yauwa Prince Abbanka yace in tambayeka."

  "Me fah?"

  "D'azu Abban Nazeefah na nan ai-"

  "Ni kinma 6ata min mood wallahi" ya katse ta yana mey had'e girarsa.

  "Toh Prince ka manta ka riga ka amince da auren ne?" Ta fad'a a hankali gudun kar ransa ya kuma 6aci.

  "Nikam ba yanzu ba" ya amsa a takaice.

  "Toh se yaushe?" Shiru yayi be sake cewa komi ba se faman latsa wayansa yake yana going through memes da Sultan yayi mentioning nasa a twitter. Hannu tasa ta k'wace wayan "Ummi please give it back" ya fad'a da sauri.

  "Ina maka magana kana latsa waya wallahi ko ka bani takamammen rana ko in bawa Abbanka duk wanda yayi min."

  "Toh kiyi mana ni ina ruwana ban damu da yarinyan ba balle aurenta ya zame min matsala ni bani wayana in wuce site d'ina."

  "Toh fah!" Ta fad'a tare da ta6e baki "Prince ka rufa mana asiri don Allah."

  "Da nayi mey?"  

  "Bade shirin wulak'anta yarinyan nan kake ba bayan anyi auren nan, don Allah kar kayi haka."

  "Kekam da assumption Ummi! Allah kyauta. Meyasa zan wulak'anta ta? Just pass me my phone" ba gardama ta miyar mishi "Toh yaushe kakeso ayi bikin? Kaga se su soma shiri suma, idan ranan is not convenient for them kuma se a zauna ayi adjusting koya kace?"

  "Toh why not su suyi fixing date d'in da kansu nifa adena tak'ura min."
 
  "Amman kai kam ba a iya maka ba wallahi sam bakada mutunci, naga ai girmama ka mahaifin nata yayi har yace kaine zaka za6i rana kasa amman kake wannan shagantakar."

  "Toh naji I'm sorry" ya fad'a tare da sauk'e nauyayyar ajiyar zuciya "Bari bayan mun dawo daga Hajj idan Allah ya kaimu rai da lafiya."

 "Toh ko kai fah? Kaga bayan babbar sallah se a d'aura ko?" Ta tambayesa cike da gastine.

   "A'a k'ullewa ba d'aurawa ba" ya mayar mata da amsa.

  "Me dafa maka abinci Prince ni zaka bawa amsa?" kafin tace zata mik'a hannu takai masa bugi har ya mik'e yana mata dariya

  "Shegen dogin k'afa a wajen" gwalo yayi mata sannan yace, "Ni zan wuce site d'ina it's been a hectic day zanyi Sallah in kwanta idan Abba ya dawo ki sake yi mashi godiya, goodnight I love you."

  "Sleep like a baby" da haka ya wuce site nasa. Bayan ya gama duk wani abinda zeyi ya d'ale gado ya kwanta dai-dai nan Sultan ya danna masa kira bayan sun gaisa yake tambayansa how went his day. Tsuka yaja sannan yace "Kaide ka barni da 'yar gudun hijirar can."

  Bayan dariyan da Sultan ya narka ya buk'aci Afzal da ya basa labarin meya faru. Nan ya labarta mai komi inda Sultan yata dariya kaman zararre yana mamakin guts na Amal, sam idan mutum ya ganta baze ce zata iya yin abubuwan da Afzal ke fad'i a kanta ba.


RANA D'AYA

   BY MIEMIEBEE
 PAGE 07

    

     Rana bata k'arya sede uwar d'iya taji kunya. Yau ana sauran sati uku azumi kenan. Afzal ne da Sultan zaune bisa d'aya daga cikin teburan da suke baje acikin office nasu Afzal a ground floor suna hirar match da akayi jiya tsakanin Roma da Barcelona wanda aka sha Barcelona wane ayi musu kuka. Ana cikin haka ne Afzal da hankalinsa ya duk'ufa a waje yana kallon wasu 'yan mata biyun da suke tsaye da wani d'an saurayi a bakin gate d'in se rashin kunya suke zuba mishi barin ma me d'an haske me maroon hijabi wacce ke tsaye dab gabansa wane zata cukume masa collar. Dukda cewa besan meke faruwa ba alamu sun nuna me marron hijabin na tare wa k'awarta wacce ta kasance me talle fad'a ne. Abu kaman wasa fad'a yak'i ci yak'i k'arewa daga bisani kawai me maroon hijabin tasa hannu ta wafce wani abu kaman kud'i daga hannun saurayin wanda kafin tace zata sa gudu har ya cafko ta, ita ko a garin k'watan kanta ta ture wani glassy sign board me yin wuta-wuta dake gefen gate d'in wanda ke d'auke da sunan bankin aciki. Abu ne wanda ko ba a fad'a ba mutum yasan zeyi bala'in tsada saboda yadda yake a tsare da jan ido. Ba shiri securities sukayi wajen duk anan Afzal na kallonsu daga ciki.

  "Dude wai meke faruwa ne kam achan?" Sultan da se yanzu hankalisa ya iske su ya tambaya.

  "Let's go find out" ya amsa shi inda suka miqe suka nufi wajen. Juyowan da 'yan matan zasuyi kawai suka had'a ido hud'u da Amal. Ashe itace wacce ke sanye da maroon hijabin, wacce ke ta rashin kunya iya gadaman ranta, lallai kuwa ta shirya biya musu sign board. Idonsu na had'uwa Amal taji cikinta ya d'au ruwa a yayinda zuciyarta ta har6a, for a second ta nemi numfashinta ma ta rasa tuna abinda tayi masa last had'uwansu. Yau shikenan kashinta ya bushe ita a iya tsammaninta bazata sake had'uwa da shi ba se gashi Allah yayi proving nata wrong today.

   "Good day Sir" securities d'in duk suka gaishe shi. Wani har6awa bugun ziciyar Amal ya kuma yi jin securities sun kirasa da sir bade anan Afzal ke aiki ba yau nata ya k'are.

  "What's going on in here?" Ya buk'ata cikin tattausar murya a yayinda yayi banza da Amal sam be nuna ya ta6a wayanta ba.

  "Sir wannan yarinyar ce ta ture sign board d'innan ta biya kud'in kuma tak'i wai sam ba ita ta ture ba bayan kowa shaida ne anan itace ta ture so muna shirin yin police station ne da ita" d'ayan security'n yayi bayani. Take Amal taji cikinta ya sake to the mention of police station, yau ina zata sa kanta? Police station? Gidan yari fa kenan! Danqaree!

  "Wallahi bani na buge ba" ta kuma fad'a.

  "Bake kika buge ba?" Tambayar securitin itade k'awar nata me tallen gyad'a ko uffan bata kuma cewa ba har yanzun gudun kar suce zasu had'a da ita akai police station d'in. Dama ita tun d'azu tace wa Amal su bar bawan Allan kawai da Allah tunda ya rantse yace shi baze basu kud'insu ba, Allah ze isar musu amman don rigima irin na Amal tak'i.

  "Eh mana ina wannan ne ya jani baya a garin k'watan kaina se abin ya fad'i wallahi ni bani na fasa muku abunku ba don haka ba abinda zan biya" ta fad'a confidently dukda cewa chan ciki ta gama tsurewa.

  "Se mu gani, se muga idan mukaje police station d'in sukace ki biya ko zaki fad'a musu hakan" Ganin fa dagaske police station d'in suke son yi da ita don kuwa gashi har sun kawo mota Amal ta soma jin fitsari nan take. Ubanwa zeyi bailing nata idan suka kaita chan d'in yanzu? Tasan ko had'a sama da k'asa zatayi Mami ko zuwa dubanta bazata yi ba Papi kuwa baida kud'in bailing nata. Yau kashin ta ya bushe, ashe da taji maganan Falmata sun ja mar Allah ya isan kawai.

  
  "Kai meya faru ne?" Afzal da ya nisanta ya tambayi yaron.

  "Kud'in gyad'an su nikeson basu suka k'i amsa wai sam suna bina bashin d'ari biyu nikuma banda masaniya akan hakan sharri kawai suke shirin min musamman wannan yarinyar" ya nuna Amal.

  "Wallahi bawan Allah bazaka gama da duniya lafiya ba, kullum kata cin gyad'an nan a bashi kace bakasan da hakan ba?" Amal data katsesa ta tambaya.

  "Yanzu akan N200 shine kuka rusar da wannan board d'in?" Afzal ya kuma tambayansa.

  "Oga ni bani na rusa ba itace agarin wafce hannunta ta ture."

  "Yanzu ka basu kud'in gyad'an su" yace dashi.

  "Wallahi ni basu bina kud'i ga kud'in gyad'ansu na yau N50."

  "Nace ka basu kud'in su" Afzal ya kuma nanatawa.

  "Gaskiya ni bazan bada komi ba saboda basu bina komi."

  "Shikenan kayi tafiyanka" hannu ya sa a pants pocket nasa ya zaro wallet nasa tare da miqa wa Falmata d'ari biyar.

  "A'a don Allah ka bari ni na barshi da Allah dama tun d'azu nike cewa Baby da ta barshi da Allah amman tak'i."

  "Karki damu amshi."

  "Toh ai banida canji."

  "Don't worry keep it." Hannu bibbiyu ta miqa ta amsa, "Nagode Allah saka da alheri Baby mu tafi."

 "Ku tafi? Ku tafi ina?" Afzal yayi saurin tambayarta tare da kewayo da kallonsa akan yaron "Kana iya tafiya kema me gyad'a kina iya barin nan."

   "Nagode k'awata fah?" Ta tambaya.

  "Bakiji me securities d'in sukace bane? Police station zasuyi da ita in kuma kinason binta ne fine."

  "A'a a'a!" Tayi exclaiming da mamaki tana ja da baya, "Baby ki bisu zanyi sauri inje gida in sanar da Mami halin da ake ciki." 
   Lallai ma Amal ta furta a ranta yanzu tafiya Falmata zatayi ta barta bayan ta sanadinta komi ya faru? Hmm amman ba amana.

  "Falmata don Allah karki tafi ki barni, Ya Afzal don Allah kayi hak'uri wallahi ba da gangan na buge ba" ta juyo tana kallon Afzal da maraicaccen fuska ko kunya bata ji ba.

  "Securities ku tafi da ita make sure she pays for this or simply lock her up, Sultan lets get back in" ya yi declaring ba tare da ya kalli koda direction na Amal ba.

  Da sauri ta shawo gabanshi "Don Allah karka min haka kayi hak'uri na tuba."

  "Get out of my sight!" ya sanar da ita a tsawace cikin tattausar muryan da yasa ta fashewa da kuka. "Ya Afzal don Allah kayi hak'uri na tuba, wallahi na tuba." Shiru yayi na 'yan lokuta sannan ya nisanta, "Na farko, I don't own this building kinyi 6arna dole ki biya there's nothing I can do."

  "Eh nasan ba naka bane amman alamu sun nuna kana da matsayi anan don Allah ka basu hak'uri su barni in tafi kafi kowa sanin cewa Mami da Papi basu da k'arfin bailing d'ina, ba don hali ba amman don Allah ka rufa min asiri Ya Afzal."

  "Sultan mu tafi mana me kake jira ne wai kam?" Yayi banza da ita.

  "Ya Afzal don Allah karka min haka kayi hak'uri I'm so sorry" nan ta kuma fashe da wani kukan a yayinda hawaye ke ambaliya a fuskarta sede ko kallonta Afzal beyi ba balle tausayinta ya kamasa.

  "Guy kayi mata hak'uri please I will settle the bill" fad'in Sultan da Amal ta basa tausayi dukda cewa beji dad'in abinda tayi ma abokinsa
Reply
#2
Them don come again

OP how i wan take translate this now?

[Image: 7644212_7614943761443675469244116e6609e0...9d5805afe1]
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *RANA D'AYA*BY MIEMIEBEE* Gimbiya 0 4,549 08-14-2018, 01:34 PM
Last Post: Gimbiya
  *RANA D'AYA*BY MIEMIEBEE* Gimbiya 0 4,205 08-14-2018, 12:35 PM
Last Post: Gimbiya



Users browsing this thread: 1 Guest(s)