The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*KAINUWA* A Historical Fiction* by Ayusher Muhd
#1
? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

  *55*

   Turab na fitowa daga b'angaren sarki ya hau tafiya, Garzali ya biyoshi da sauri yace "Ranka ya dade ina zamu?"
Juyowa yai ya kalli Garzali yace " akwai makullin mota a hannunka?"
Kai ya girgiza alamar a'a.
Turab yace "d'an hanzarta ka d'auko fita nakesan yi." Garzali ya juya da sauri.

Turab ya shafi fuskarsa zuwa kansa sam jiyake gidan ya mai zafi, duk hirman masarautar jiyai kamar a takure yake.
Inama ya iya mota? Da dakansa zai d'auka yai waje, sai dai matsalar idanunsa yasa bai tab'a koya ba gudun kar asiri ya tuno.

  Bai dade ba sosai sai ga Garzali nan ya bud'emai gidan baya ya shiga shikuma ya shiga gaba sukai waje.
Tafiya kawai sukeyi, ganin baice komai ba yasa Garzali yace "ina zamuyi Ranka ya dade?"
Turab yana kallan window yace " ka cigaba da tafiya kawai, ni kaina bansan inda zamu ba."

Jin haka yasa Garzali ya cigaba da jan mota.

  Komar da kansa yai jikin kujera ya rufe idanunsa kamar maiyin bacci.
Sai da sukai tafiyar a kalla awa d'aya sannan yace mu juya.
Nan Garzali ya juya da kan mota, kasancewar safe ne dan lokacin karfe 10 ne na safe, gashi lokacin damuna ne yasa garin yai luf abin sha'awa ba kuma rana.

  Sai da suka shiga garin Zariya sannan ya kalli Garzali yace " kasan gidan Barde?"
Garzali ya murmusa sannan yace "eh."
Turab ya d'anyi karamin tsaki yace "Garzali a idanuna dana mutane ina ganin kamar nid'in mutumin kirkine sai dai a zahirin gaskiya banida kirki ko kad'an."
Garzali yace "Ranka ya dade ta yaya zaka ce haka?"
Turab ya jingina kansa jikin kujera ya hard'e hannayensa tare da maida idanunsa ya rufe yace " Duk yanda yarinyar nan ke kula da Mahaifiyata da nikaina ace ko gidansu ban sani ba, sai dai ita tazo inda muke."
Ya karasa maganar tare da juyar da kansa gefe.
Garzali yai shiru kafin can yace " Ai kai kaga baka fiya fita ba, sannan yaushe ma ka warke Ranka ya dade?"
Turab bai ce komai ba, sai da suka isa gidan Garzali yai parking sannan ya kalli Turab wanda ya bud'e ido jin tsayawar motar yace " mun isa, a kira maka ita?"
Turab ya kalleshi yace " Cema akai zance nazo ko me? Ka sanarma Barde da zuwana."
Garzali yace to, sannan ya fita.
  Yana fita Turab ya kalli waje, unguwar ya shiga kallo.

  Garzali ne ya dawo da sauri yace " Kunye sab'ani ance d'azun nan ya tafi fada."
Turab yace "ayya, Mairo fa?"
Garzali yace "Ban tambaya ba dan nima dama bance kai bane kazo."
Turab yace " kira min ita, tunda nazo harnan mu gaisa."
Nan ya juya, yaron d'azu wanda da alama a gidan yake ya kara turawa yace "ya kida masa Mairo." yaran yace ince inji wa?
Garzali yace kace inji Yarima Turab.
Nan yaran yai ciki da gudu.

  Mairo ta gama cin abinci kenan tana tattare kwanuka yaran dayake d'an babbar yayarsu ce da aka kawoshi hutu ya shigo da gudu ya rike mata riga yace " Ana kiranki a waje."
Tace " Khalid meye hakan? Waye yake kirana?"
Yace " Wai kije inji Yarima Turab."
Hararar sa tai sannan ta kwace rigarta tai kitchen tana cewa "Lalai Abdulmajid ma Ya raina mata hankali, taje inji Turab?"tai tsaki tace ko kunyar karya ma mutum bai iya ba.
Hannunta ta wanke sannan ta fito tai d'aki, kan gadonta ta kwanta, can kuma ta mike zaune tace karfa inje da gaske ya Turab ne.
Hijab dinta ta jawo tai waje.
Lekowa ta fara yi ganin duk suna cikin mota yasa ta kasa ganewa.
Ta kara lekowa, Abu turab ne ya zuge glass d'in window dinsa sai daya tabbatar itace sannan ya bud'e motar ya fito.
Mamaki ne ya kamata ganin shi d'in ne ya fito, kallansa kawai take d'auke da tsananin mamaki har ha iso soron.
  Bayan kofa ta shige fa sauri tare da bin jikinta da kallo, ko kwalliya batai ba, jitai kamar ta ruga ciki.
Turab ya tura kofar yace " ko dai in juya ne?"
Tana bayyan kofar tace " Ya Tutab."
Takowa yai zuwa ciki yana cewa " Ba dai Abdulmajid har ya fara hanaki kula yayan naki ba."
Fito tai tare da had'e fuska tace " waye shi kuma?ni ai banaji a list d'in yayuna inada mai irin sunan."
Yace " To ko a kirashi sai a tambayeshi? Inga ko zaki iya tambayarsa."

  Dariya tai mara sauti tace "Yaya kana tunanin bazan iya ba?"
Hannunsa yasa ya rufe bakinsa yace " Tab ai na manta ashe fa Mairo ce. mairon data yardani sau biyu."

Juyawa tai da sauri cikin shagwab'a tace "Haba yaya"
Murmushi yai yace " Barde nazo nema ashe bayanan."
Juyowa tai tace " ya tafi fada."
Turab ya kalleta yace "Are u okay?"
Yanayin fuskarta ne ya canza tace " akan me?"
Kallanta yai sai dai baice komai ba, murmushi ta masa tace " I am okay yaya."
Kara kallanta yai idanunsa d'auke da alamar kokonto, jitai idanunta na neman cicikowa, kanta ta d'aga sama tana neman maidasu, sannan ta kalleshi tare da girgiza kai tace " Yaya i am not okay, na rasa yanda zanyi, Abba yace bashida yanda zaiyi, kai baka nan, kunya nakeji in koma gun Umma sannan yaya bazan iya auren mutumin dana san ba sona yake ba, wlh yaya da ace Abdulmajid san tsakani da Allah yakemin ko da banasan sa zan jure na aureshi ko dan neman gyara halayensa." hawaue ne ya zubo mata ta girgiza kai tace "Sai dai yaya ni nasan Abdulmajid nasan irin kallan da yakemin, na tsani kallan da yakemin, na rasa ya....."
Kasa karasawa tai ganin tana neman yin kuka, gashi batasan Turab yaganta cikin wannan halin.
Tsananin tausayinta ne ya kamashi, kallanta yai sannan ya zaro handkerchief daga aljihunsa ya mika mata.
Ansa tai ta goge hawayenta sannan ta kakaro murmushi ta kalleshi tace " Ya yayar tamu? Ka barota lafiya?"
Murmushi ya mata yace " Bilkisu ce yayarki?"
Tace "eh mana, a yanzu dai ba yaha ta bace amma inta aureka ai ta zama yayata."
Kallan tsananin tausayawa ya mata dan tabbas yasan yanda take sanshi, yace " Tana garinsu, sannan Mairo ba kya ganin ya......."
Gabanta ne ya fad'i tana tsoron kar yace ya kamata ta daure ta auri Abdulmajid, da sauri ta katatshi tace " Yaya kasan me? Khadija fa ta d'auka ni kake so, tun kwanaki nakesan fadama sai in manta."

Kallan mamaki ya mata yace " mene?"
Daurewa tai tace " nima bansan ya akai tai wannan tunanin ba."
Iska ya d'an furzar yace " share wannan zancen sannan ni in tambayeki kinji na cemiki Khadija nakeso da bakina?"
Tace " Au sai ka furta? Banda abinda idanunka suka nuna?"
Handkerchief dinsa dake hannunta ya fizga sannan ya kwad'a mata akai, hannu tasa agun da ya daketa tace " Yaya da zafi fa."
Murmushi sukayi a tare, sannan ya saki wani hucci na tunowa da matsalar dake gabansa.
Kallanta yai yace " Karki damu, ke dai kicigaba da addu'a In Allah ya yarda komai zaizo da sauki."
Kai ta d'agamai tace "Nagode Yaya."

  Juyawa yai ya fita, kallan bayansa tai har sai da ya shiga mota.
 
 **********

   A gidan Waziri kuwa, Khadija ce tsugunne gaban mahaifinta.
 Hisham ya kalleta fuskar nan tasa ba wasa yace " Khadija mun riga mun yanke hukunci akan aurenki, dan Magajiya harta sa an sanar ma iyayen Saifullahi akan maganar sa rana, dan haka ki shirya, bazan tab'a yadda da wani zancen banza ba...."

  Kallan mahaifinta tau idanunta fal hawaye tace " Abba tunda akai maganar Saifullahi ban tab'a cewa a'a ba ko wani abu, ni dai naji zan aureshi amma yaya Abdulmajid dan Allah ya janye auren nan na dole da yake neman yima baiwar Allah."

  Kallanta yai ransa ya kara tun zura, mahaifiyarsa ya kalla da take zaune shiru, dan ko baki bata sa musu ba.
 Yace " biyoni ke kuma."
 Ya fad'a tare da yin ciki, Khadija na ganin haka tasan shikenan ta jama mahaifiyarta, da sauri tace " Abba...." bata soma fad'in komai ba Mahaifiyarta ta kalleta tare da girgiza mata kai alamar kartace komai.
 Suna shiga d'aki ya kalleta yace " wai wani irin tarbiyya kikama Khadija? A da na d'auka duk gidan nan tafi kowa jin maganata da hankali amma yanzu na fara tunanin zugata kikai inba haka ba yarinyar da nasan komai nacemata tanayi akan me yanzu akan wani can sokon yaro ta nemi bijiremin, kece kike zigata kome?"

  Kallansa tai ranta ya tunzuro dan itakam ta tsani yanda suke neman yima Khadija auren wanda bataso tace "Tunda nake dakai na tab'a musa ma? Ko a sanda ka d'auki d'an dana haifa ka kaima yar uwarka magajiya na hanaka? Ko har izuwa wannan ranar na tab'a kaucewa akan sharad'in daka gindaya min?ko kuwa kana tunanin banajin zafin ganin d'an dana haifa na fari agun kanwarka? Yaro bai san matsayin ba, ko suna uwa bai taba kirana dashi ba."
 
 Hawaye take sosai, kallanta yai rai a b'ace yace " Bazakiyi shiru ba?"

  Cikin b'acin rai tace" kana tunanin tsoronka nake daga kai har Magajiya? Sannan yanzu ni kun gama min abinda kukaga dama 'yar tawa ma haka kuke san juya mata rayuwa? Ko kana tunanin duk wani abu na makirci da kuke kai da Ma"

  Da baya da baya ta fara ja tana girgiza kai, sam ta ma rasa me take ji, tahowa tai dan taba mahaifinta hakuri sai dai me?

  Juyawa tai da gudu ko takalmi bata sa ba tai waje, ko mayafi babu a jikinta.
 Tafiya kawai take bata ma san knda takesa kafar ta.

 Sam bata kula da motar da take mata horn ba, jan burki yai da sauri ganin taki kaucewa, duk da haka sai da motar ta d'an bigeta kadan.
 Turab ya kalleshi da sauri yace " lafiya?"
 Garzali yace " bansan wacece ba, inajina bigeta. " ya karasa maganar tare da bude motar.
 
 Kusa da ita yaje yana tambayarta lafiya?
 D'agowa tai ta kalleshi ganin bibiyi take, mikewa tai kawai tana neman cigaba da tafiyarta.

  Da sauri ya kalli Turab wanda ya bud'e motar ya fito yana tsaye rike da kofa, yace " Ranka ya dade Khadija ce."

  Da sauri Turab ya kalli inda yarinyar take, ganin Khadija yasa ya taho da sauri yace "Khadija?"

 Kallansa tai sai tai baya luu kamar zata fad'i da sauri yasa hannu ya tareta, suka tsugunna, kallanta yai cikin tsananin tashin hankali yace "Khadija?"

  Kallansa tai sannan ta shiga girgiza kai tana cewa " Abba meke faruwa? Wani d'ane umma ta ba kanwarka? Abba...."
  Jijigata yai yace " Khadija? Meke faruwa?"

  Kai ta shiga girgizawa, ta shiga kankame jikinta alamar tsoro.

  Turab ya rasa abinda zaiyi d'aukanta yai cak ya sakata a mota, ya rufe ya koma gaba sannan ya kalli Garzali yace " mu tafi mu kaita gida, da alama bata cikin hayyacinta."

  Sun isa gidan ya rikota ya kalli Garzali ba sai ya tambaya ba dan kana kalla tsari da fentin gidan kasan gidan mai mukami babba ne na sarauta.
 Nan ya nufi gidan da ita.
 Hisham wanda ya fito ransa a b'ace da rainin hankalin da matarsa ta masa yai kicibis da su.

  Mamaki da takaici ne ya kamashi yace " Malam wani irin iskanci ne haka zaka rikomin 'ya......."

  Bayan Turab ta b'oye ta rikemai riga tana cewa " wayyo Allah, dan Allah tafi dani daga nan, wad'an nan......"
 Tsawa Hisham ya daka mata yace " Khadija bakida hankali ne?meye hakan?"

  Turab ya juyo ya kalleta yace "Khadija menene?meke faruwa haka?"

 Kallan Turab tai sai yanzu ta gane shine, hannunsa ta kamo da sauri tace " Yaya Abba da Umma Magajiya..."

  Hisham ya fahimci akwai wani sirri da take san fad'a, da sauri yasa hannu ya fizgota.

 Tace " Kanwar Abba? magajiya kenan, kenan Ya Abdulmajid......"

 Toshe bakinta yai ya sa hannu ya finciketa da karfi yai ciki da ita.
 Turab ya kalli inda suka shiga yace " me ke faruwa?"


*ABU TURAB*

*KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

*56*

  Turab na zaune a cikin mota yai shiru yana tunani, me ya samu Khadija?

A can kuwa Hisham na shiga da ita cikin gida ya rike hannayenta duka biyu yace "Khadija, menene? Me kikaji?"
Kallansa tai tsananin tsoronsa taji ya shigeta, kai ta girgiza batace komai ba, kara jijiga ta yai yace " wanene ni?"
A hankali tace " Abba ne."
Yace " me kike kokarin sanar ma Abu Turab?"
Kai ta girgiza da sauri tace "bakomai."
Idanu ya kankance yana san gano abunda take b'oyewa, mahaifiyarta ce tazo gun tace " Khadija? Lafiya inata kiranki shiru?"
Kwace hannunta tai ta tafi gun Uwarta da gudu.
Hisham cikin zargi ya ke kallanta, Ummanta ta riketa tace "lafiya Khadija?"
Tattaro nutsuwarta tai sannan ta samun kanta da cewa " Bakomai Umma faduwa nai a waje."
Umma ta kama hannunta cikin kulawa sukai ciki.
Hisham ya bisu da kallon zargi sai dai bashida tabbas akan abinda yake zargi, sannan yasan Khadija da ace taji maganar da sukai da matarsa dazu da ciki zata shigo taji me suke nufi bawai waje zatai ba.

*****
Sun isa gida, Turab ya fito sannan ya nufi hanyar b'angarensa.
Abdulmajid ya hango yana tahowa shima da alama shima fita zaiyi, tsaya wai cak yana kallansa sannan yana maimaita kalamun Jakadiya, da kuma Khadija, da alama duk maganarsu a karkashinta dai maganace wacce ta shafi Abdulmajid, to amma me suke nufi? Sam hankalinsa bai kawo ba d'an sarki bane dan shi a ganinsa duk mugunta da makircin magajiya bazata taba tunanin yin wani abu mai kama da haka ba.

  Abdulmajid ne ya iso inda yake kallan banza yamai yai gaba abinsa.
Turab ya bishi da kallo sannan yai gaba.

  Har ya je zai shiga b'angarensa sai ya juya ya nufi bangaren Hajiya.
Yaje shiga yai kicibis damai kula da ita, sam bata san ya taho ba haka shima.
Bigetan dayai ne kufin dake hannunta ya fad'i kasa.

Turab ya kalleta yace " sannu....."
Ganin yanda ta shiga saurin dauke kofin da tayar sam tama manta da bigeta akai, tana d'aukewa tai hanhar fita, kasa ya tsuguna ya d'au yar karamar ledar data fad'o daga jikinta yana kokarin mata magana akan ta yarda abu sai gani yai ba kowa agun.
Mamaki ya kamashi ina tai? Kallan maganin yai sannan ya shinshina maganin, a aljihunsa ya saka sannan ya shiga ciki.
  Sam jikinta ba sauki sai ma karuwa da yakeyi, kusa da ita yaje sannan ya riko hannunta yace " Hajiya nine Abu Turab."
A hankali ta bud'e idanunta ta kalleshi cikin karfin hali ta sakarmai murmushi.
Cikin kulawa da tausayawa yace" Hajiya kinganni shiru ko? Tafiya nai sannan abubuwa sunyi yawa dana dawo, ya jikin?"
Idanu ta lumshe sannan ta bud'e, kallan d'aki yai sannan yace " kin gaji da kwanciya ko?."

  Tunani tai yanzu ne lokacin daya kamata ta yunkura ta fadama Turab abinda ta sani.
Bakinta ta shiga motsawa tana kokarin yin magana, kallanta yai yace " akwai abinda kikesan fad'amin?"
Kai ta d'aga da sauri alamar eh.
Matsowa yai da kansa kusa da bakinta yace "menene Hajiya?abu kikeso?"

Daurewa take sosai da kyar ta iya cewa "Maga...."
Yace "magani?"
Kai ta girgiza alamar a'a yace "Magajiya?"
Kai ta d'aga da sauri alamar eh.
Cikin mamaki ya kalleta yace " wani abun ta miki?"

Da kyar ta kara daurewa tace "Abb duu........"
Yace " Abdulmajid?"
Kai ta jijiga alamar a'a yai shiru yana tunani can a ransa yace Abdussamad?
Kallanta yai yace " Abba?"
Kai ta girgiza da sauri yace " me ya faru?"
Kokarin magana take sai dai ina ta kasa, ganin yanda take shan wahala yasa yace " Hajiya daina magana."

Yawo ne yashiga zubowa mai kumfa, cikin tausayawa ya mike da sauri yana neman mai kula da ita.
Yarinyar nan ya gani a waje tana ta dube dube cikin b'acin rai yace "bakiji ina kiranki ba?"
Tahowa tai gunsa, yace " Hajiya jikinta ya motsa nemo mai magani."
Ya fada tare da komawa ciki ya d'agata yana goge mata, sai far fari take da idanunta, mai bada magani tana zuwa ta shiga mata jike jike tana bata, sai dayaga ta samu bacci sannan ya mike cikin tausaya mata.

  Dakinsa ya shiga ya kwanta akan gado kansa na kallan sama ya d'aura hannunsa akan goshinsa, me Hajiya takesan fada mai? Ya tabbatar yanzu kuma abu ne tsakanin Magajiya da Mahaifinsa.

  Hannu yasa a aljihunsa ya d'auko wannan maganin, mikewa yai ya fito waje.
Garzali ya taso da sauri yazo gunsa, Turab ya kalleshi yace " ka kiramib jakadiya kace ta sameni a gun shakatawar Takawa."

Garzali ya amsa da to, juyawa yai ya fita.

  A kan kujera ya zauna, bai dade ba sai ga Jakadiya.
Tana zuwa ta zube a gabansa ta shiga gaidashi, Turab ya amsa sannan ya kalleta yace " tambaya zan miki, banasan gulma ba kuma nasan had'i sannan kada ki kuskura kimin karya abinda na tambayeki shi kadai zaki amsa min bana bukatar wasu kalamai na daban."

  Kanta na kasa tace " To ranka ya dade" a gaskiya tana ganin girma da kimar yaron tunda yake bata taba ji ance ya nemi jin magana daga bakin wani ba a masarautar, sannan ga kwarjini da izza ta sarauta da yake da ita.
Turab ne ya katseta da cewa " Menene tsakanin Magajiya da Abdulmajid da kuma Hisham? Wani sirri ne a tsakaninsu?"

  Gabanta ne ya fadi ta kalleshi tace " Ranka ya dade."
Kallanta yai yace " jiranki nake."
Yawo ta hadiya sannan tace " Amsar d'an kaninta da juyawa a matsayin nata."

  Idanu Turab ya zaro cikin tsananin tashin hankali, mikewa yai tsaye gabansa na wani irin fad'uwa gabansa yai, idanunsa ne suka kada sosai kallanta yai cikin kokonto yace " meye naki na sanar dani wannan babban sirrin? Sannan ta yaya ke kika san haka?"
Jakadiya ta kalleshi cikin tsoro tace " Tuba nake ranka ya dade amma wannan magana haka take sannan sanar dakai danai bawai da wata manufa na fadama ba......"
" Badai kina tunanin kin sanar dani hakan bane dan kar asiri ya tuno kiyi tunanin zan taimaka miki? Sannan meye dalilinki na b'oye wannan siriin bayan ked'in jakadiyar sarki ce?"

  Tsoro ne ya kama Jakadiya jikinta ne ya hau rawa ta kalleshi tace " Ranka ya dade........."

  Kallanta yai cikin takaici yace " ba dai dake aka shirya b......"

  Tsugunawa tai cikin tsoro tace "wlh ba dani bane Ranka ya dade, wlh ba dani bane."

Komawa yai ya zauna sannan yace " jeki zan nemiki in nayi tunani."

Fita tai cikin tsananin fargaba.
Jiyai hannunsa na rawa, da sauri ya had'e hannayensa guri daya sannan ya bud'e idanunsa da sukai jawur.

  Mikewa yai cikin takaici yai bangaren Magajiya.

Tana zaune a kilisarta aka sanar mata da zuwansa.
Murmushin jin dadi tai tace ace ya shigo dan ta tabbata yau dolene ya nemi ya fiyarta.

  Turab ne ya shigo, tsayawa yai yana kallanta cikin tsananin mamaki.
D'agowa tai ta kalleshi tace " meye hakan? "
Murmushi yai sannan ya matso ya zauna tare da gaisheta.
Amsawa tai cikin isa sannan tace " kun yanke shawarar?"

  Turab yace " sosai ma Umma shiyasa nazo miki da umarni."
Kallansa tai shekeke tace " Umarni? Kai zaka ban?"
Kai ya d'aga mata tare da yin murmushin gefe yace " inaso a satin nan ki fara shirya lefe na daga nan zuwa sati biyu ki gama hada komau dan zuwa kaiwa Masarautar kano, sannan in zaki saka lokacin biki banasan kijashi da nisa."

  Kallan mamaki ta mai batasan sanda tasa wata dariya ba tace " me da me?"
Yace "kamar yanda kikaji na baki umarni hakan nakeso ki aiwatar min, sannan sirrin ki da nake rike dashi a hannuna zan aunashi a ma'auni, da namu sirrin da kike rike dashi zan duba inga da ni dake wanene nashi sirrin yafi nauyi, inhar naki yafi nauyi dole ne kiyi tabin umarnin d'anki Abu Turab har sai sirrinki ya kai daidai d'aya da namu inyaso sai kowa ya tona nashi sirrin a lokacin ne zamuga wanda zai ci galaba."

  Gabanta ne ya shiga fad'uwa dan yanda idanunsa suke nunawa tasan tabbas akwai wani babban sirrinta daya sani, menene? Wanene daga ciki?"
Daurewa tai tace " kana tunanin zan yarda da wannan shirman naka?"

Kallanta yai cikin tsana yace " to ko in sanar ma Abdulmajid?"
Gabanta ne yai wani wawan faduwa cikin rawar murya tace " Abu Turab."

Murmushi ya sakar mata sannan ya mike ya kalleta yace " kiyi gaggawar sa d'anki ya janye auren Mairo, ahh ba......" sai kuma yasa yatsa a baki alamar yin shiru yace " sry" ya fada tare da nuna alamar zip a bakinsa.
Juyawa yai yai waje.

Yana fita ta shiga kakkarwa, mikewa tai da sauri cikin tsoro me ya jiyo? Me ke faruwa?

  Turab na fita ya kalli bangarenta cikin takaici sannan yace " kin cuci Abba yanda kika ci amanar sa da cutar da mutane sai na nuna miki abinda kika aikata babbam kuskurene, babu babban yaki sai wanda kika yarda dashi yaci amanarki, kijira juya miki baya da zansa Hisham yai, sai kinyi dana sanin abinda kika aikata."
Darajar mahaifinsa kawai taci amma da....Yai kwafa ya tuna yanda aka bashi labari dadin da mahaifinsa yaji a lokacin da aka haifi Abdulmajid.

Kallan bangarenta ya karayi cikin tsananin takaici sannan yai gaba.

*TURAB*

 ? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

  *57*

Turab na fita Magajiya ta d'auki kofin da ke gabanta ta jefi madubin dake manne a kilisar.
Mikewa tai cikin tsananin tsoro da fargaba tai cikin d'akinta.
Me ya sani? Me ya sani? Me ya sani?
Wannan kalmar ita kawai take mata yawo a kwakwalwarta gaba daya ta rasa inda zatasa kansa, fitowa tai ta bada umarnin a kira mata Jakadiya cikin gaggawa.
Jakadiya na zaune tasa kwanan abinci agaba sam ta kasa ci akazo aka sanar da ita kiran Magajiya.
Zufa ce ta shiga karyo mata, mikewa tai ta fito.
Haka ta karasa tana ta tsoron abinda zai faru.
Magajiya na zaune a kan gadonta yayi shiru tare da kurama kasa ido.
Ko sallamar Jakadiya bata amsa ba, har Jakadiyar ta zauna tare da gaisheta.
Magajiya bata amsa ba sai dai ta kalleta cikin wani yanayi na zargi, sai kuma ta murmusa tace " Jakadiya ba tin yau ba nasan tabbas sai gulna da tsautsau bakinki yasa kin sanar ma Turab sirrin Abdulmajid."
Jakadiya ta zaro ido sannan ta tuno kalaman Turab a yayin da ya mike zai fita bayan ya gama mata fada " Kada ki kuskura ki nunama Magajiya munyi maganar nan dake, duk yanda taso ta bugi cikinki ki tabbatar baki bar wata hanya ba dazai sa ta fahimta, nagode da sanar dani da kikai."
Ya juya ya fita, tunowa datai da kalamansa yasa tai saurin zubewa tace " Gimbiya Magajiya ta yaya zakimin wannan shaidar? Bayan shekaru sama da ashirin ina rike da wannan sirrin? Sai yanzu ne zan tona? Inci ribar me?"
Magajiya ta kalleta tace " Amma ai kwanaki kin min birga akan sirrina da kike rike dashi sannan banida tabbas ke d'in yanzu a bangarena kike duba da abinda kikamin."
Magajiya ta daure tace " Gimbiya bani bace, me nene ma zaisa in fadamai?"
Ganin yanda Jakadiya tai yasa ta gamsu akan ba ita bace, ta kalleta tace " bani guri."
Fita Jakadiya tai, tana zuwa waje ta saki wani ajiyar zuciya.
Magajiya kam tana fita ta dafa kanga cikin tashin hankalu tace " ba wannan bane, tunda duk gidan Jakadiya ce kawai tasan wannan sirrin, tunowa tai da Hajiya, ba dai Hajiya ce ta fad'i dayan sirrin ba?"
Mikewa tai da sauri ta fito, ta sanar ma Bayinta akan zuwa bangaren Hajiya.

   Tana shiga wannan baiwar ta taho gunta da gudu ta gaisheta.
Magajiya ta kalleta bata amsa mata ba tai ciki.
Mai kuka da ita wacce tafi kusanci da Magajiya ce ta kalli Baiwar tace " kina zubawa?"
Cikin tsoro tace eh, dan bazata iya cewa ta batar da maganin ba dan ta tabbata inhar ta fada to lalai kwananta ya kare.
Magajiya na shiga ciki ta rufe kofa.
Kallan d'akin tai a wulakance sannan ta toshe haccinta wai wari.
Zama tai daga nesa da Hajiya sannan ta kalleta cikin jin dadin yanda take shan jiki ba damar magana tace " Hajiya? Kin ganeni?"

  Kallanta Hajiya tai, tana ganin Magajiya ta shiga yunkuri tanasan magana ta kuma kasa, Magajiya tace " Lalai Hajiya kiji da jikinki har kike wani yunkurin magana? Da nadauka ko kinsamu sauki ne harkinyi tsautsayin yin magana amma yanzu naga ba haka ba, bakya tunanin ya kamata ki sallama komai na duniya ki jira mutuwa tazo ta daukeki?"

  Hajiya yunkuri take sosai, ganin ba dama yasa tai shiru sai hawaye da yake ziraro mata ta gefen ido, tunowa tai da abinda ta gani.

  {
" Wasika aka ba da akawo mata tashin safiyar yau, amsar wasikar tai ta bud'e, kana kallan rubutun kaga rubutu ne na 'yan koyo, sai dai da yake bata iya karantawa ba yasa ta ajiye wasikar a tunaninta ba mai amfani bace.
Sai dai me? Kwana hudu kenan ana aiko mata da wannan wasikar sannan yaro ne yake kawowa kuma daga ya bada yake sa gudu yai waje, yau abin ya fara damunga dan da alama magana mai mahimmanci ake san sanar da ita.
Sawa tai a kira mata Rabi'a, bayan tazo sun gama gaisawa ta d'auko wasikar ta bata tace " Karantamin."
Rabi'a ta amsa tare da bud'e wa.
Na farko an rubuta "Hajiya d'anki na cikin matsala."
Na biyu " Hajiya ki yafemin sai dai ba yanda zanyi dolene na cigaba da zuba maganin nan inba haka ba Magajiya halakani zatai."
Na uku "Hajiya ki taimaken ki d'au mataki ko na samu zunubina ya tsaya anan." 
Na hudu " Hajiya kiyi wani abu dan Allah."

  Hajiya ta amshi takardar a taorace tace "Rabi'a kin tabbatar da abinda aka rubuta kenan?"
Rabi'a tace "Hajiya wlh abinda akace kenan amma me hakan yake nufi? Magajiya tana ba sarki magani? Akan me?"

  Hajiya tace " jeki gida sannan maganar nan ta zama sirri tsakaninmu koda wani abu zai sameni kimin alkawarin bazaki taba fadan wata kalma ba."
Rabi'a tace "Na miki alkawari, nan ta mata sallama ta fita da tsananin mamaki, bazata taba iya ma Hajiya musu ba."

  Tana fita Hajiya ta kona takardar sannan tai shiru tana tunani, ba wanda ta yarda dashi bare suyi maganar dashi, sannan batasan wacece tayo mata wasikar ba, gashi ita ta tsufa ba wani abu da zata iya yi.

  Abu d'aya ne ya dace tai shine taje gun Magajiya dan nuna mata ba tsoronta ake ba sannan ga fadamata inhar bata daina ba zata sanarma Sarki.

  Yau da safe tasa aka kira mata Magajiya, tun safe aka sanar da ita amma sai yamma liss sannan tazo.
Hajiya na zaune  da charbi, zama tai akan kujera sannan tace" Hajiya kim wuni lafiya?"
Hajiya cikin takaici ta kalleta tace " me kike bawa d'ana?"
Magajiya ta kalleta cikin mamaki tace "me nake ba d'anki kamar ya kenan?"
Hajiya tace "Kamar yanda kikaji haka yake, wani tuggun kike dubgawa Abdussamad, nasan dai ba maganin mutuwa kike bashi ba tunda zamansa a mulki shine zamanki kema a mulki, sanar dani me kike masa?"
Dama Magajiya na tsananin jin haushin Hajiya dan tunda aka aureta tasan ba santa takeyi ba, fuska ta canza ta d'aure fuska tace " koma me nake bashi ai mijinane sannan bakida ikon shiga tsakanin mata da miji."
Ta mike zata fita, Hajiga abin ya bata mamaki tace " waye ya haifa miki har kika aura? Sannan ni dama tunda na fara ganinki wlh nasan ke ba alheri bace a gareshi ba kuma matar zama bace ta amana, ko kiyi gaggawar daina abinda kike bashi ko kuma wlh in sanar dashi, zakiyi mamaki inkika ganki a gidan yayanki da takardar saki, ba'a saki a gidan sarauta bari sakin uwargida wacce take sarauniya sai dai ina sanar miki za'a fara akanki."

  Wata banzan dariya Magajiya tai tace " Me? Ni za'a saka?"
 Hajiya ta kalleta sai dai yanda taga Magajiya tayi yasa tsoro ya d'arsu mata dana sani ya kamata me yasa bata fadama d'anta ba ta sanar ma Magajiya?"

  Magajiya tazo kusa da ita ta sakar mata murmushi tace " ina jiran lokacin da za'a bani takarda, ki kuma tabbatar an bani, sannan maganar magani maganin hana d'aukan ciki ne ki tabbatar kin sanar dashi haka."
 Ta juya ta fita, tana kallan Hajiya duk ta rikice jikinta ya d'auki rawa.
 Bayan Magrib tanashan ruwa shikenan ta kasance ba lafiya tun daga wannan rana har yau ba baki ba zama bare tafiya."
}

  Magajiya ta mike tazo saitin kunnen Hajiya tace " Kijira d'ana ya hau mulki in har kinada rai ni zan taimaka a fitar dake daga gidanan akaiki can bayan gari ki zauna kyafi jin dadin zaman duniyar, in kuma kinaso in hada da jikanki da kuma uwarsa Basira ku zauna tare acan."
 Ta mike tai waje.
 Tsayuwa tai a wajen gidan, me turab ya sani? Bataji akwai wanni babban sirri dazai tsoratata da ya wuce wad'an nan biyu, sauran duk sai dai tasa a aikata amma badai ita dakanta ba, inma zancen kashe yayan Basira ne ai ba ita bace tai Hisham ne.
 
  Dolene ta nemi Turab ta kuma bihi cikinsa da jin sirrin da ya sani.

  Turab zauna akan kujera yana d'an kada dan yatsansa d'aya tunani yakeyi wace hanya ce mafi sauki da kuma bakin ciki da zai sa Magajiya ta fita hayyacinta in taji Yayanta Hisham yaci amanar ta? Ya tabbata Hisham da  Magajiya kowa amfani yake da dan uwansa.
 Ita tana amfani dashi dan cikar burinta, shi kuma yana amfani da ita dan samun matsayin da zai wuceta nan gaba, murmushi yai yace " Badai tana tunanin in Abdulmajid ya hau mulki komai na burinta ya cika ba?"

  Mikewa yai ya fito waje.
 Hango Abdulmajid yai a zaune yana shan iska jiyai tausayinsa ya dan darsu mai, ya zaiji in yaji wannan sirrin? Yauce rana ta farko dayaji tausayin Abdulmajid ya kamashi.

  Ya zaiyi ya sa Magajiya da Hisham su tunama junansu asiri da kansu?
 Khadija!
 Shiru yai jin sunan daya zo mai, tabbas itace a tsakanin mutanen biyu, ita da Abdulmajid, sai dai me? Zuciyarsa zata iya jure amfani da ita?

  Juyawa yai ya koma ciki tare da furzar da iska mai zafi...


? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

*58*

Duk yanda Magajiya tai akan samun mafita ta kasa, da sassafe kuwa ta aika akan a kira mata Hisham.
Ko gaisuwarsa bata amsa ba tace " Yaya inaji fa yaran can yasan wani abu namu."
Gabansa ne ya fad'i kallanta yai sannan ya tuna kawo Khadija gida da yai, ba dai wani abu ta fada mai ba?
Daurewa yai yace " bangane ba? Me ya sani?"
Ta girgiza kai tace ban sani ba sai dai daga yanda yazomin da kuma yanayin kalamansa inada tabbacin yasan wani abu wanda yafi fyaden da akama Basira."
Hisham ya sauke ajiyar zuciya jin da alama ba Khadija bace yace " amma kinsan yaran nan shegen yaro ne anya ba dan karkiyima Mahaifiyarsa wani abu bane?"

Magajiya ta girgiza kai cikin yanayin tunani tace " Yaya bakaga idanun yaran nan ba alokacin, sannan cemin fa yai in fara hada kayan lefensa yaban zuwa sati biyu, kamar ni dan karamin yaron da ko uwarsa na girma yazomin da zancen rainin hankali irin wannan?"

  Hisham shi kansa yayi mamakin jin haka yace " da kuma bakinsa ya fad'a miki hakan?"
Tace " anan gun kuwa, sannan harda cemin in sa Abdulmajid ya janye auren Mairo, umarni fa yazo ya bani wanda ko ubansa bai taba ban umarni akan abinda yasan ina duk wani abu na ganin na hana wannan abun."

  Hisham yace " da alama yasan wani abun to amma ta yaya?"
Magajiya ta juya kai tace " wannan shine  abinda ke damuna." 
Shiru sukai kafin can ta kalleshi tace " Yaya"
Kallanta yai yace " ya zakiyi?"
Murmushi ta saki tace " kamar ni? Abinda yafi damuna kenan dan jiya ko baccin kirki ban samu ba, kamar ni Magajiya ace wannan yaran zai kalla ya bani umarni?"
Hisham a ransa yace " an tabo Masifa."
Magajiya ta kalleshi cikin iza tace " zanyi abinda yace bayan na tabbatar da akwai sirri na a hannunsa, zanyi lefe zan kuma sa a sa rana, zan nuna ma jama'a Turab ma d'anane."
Hisham cikin tsananin tsoro ya kalleta dan ya tabbata wank mugun abun zata fada daga karshen abin arzikin datai, dan yasanta haka take in har aka bata mata rai sai ta nuna bakomai Sai kuma tayi abinda baki bazai fadu ba.

  Magajiya ta kara wani murmushin jin dadi tace "Aure? Auren Bilkisu?" sai kuma ta sa dariya tace " lalai nayi gangancin barinka da rai."
Hisham ya kalleta yace " me kike tunanin yi?"
Kallansa tai sannan ta wani juya ido tace " sai muga ranar auransa waye zai je gun, mai makon kaga ai aure da shi a d'aura da Abdulmajid sannan su gama d'aura aure suzo su tadda angon da aka shirya za'ai dashi a kwance ba numfashi."

Hisham ya kalleta yace " ban fahimceki ba....."
Tace "Zaka fahimceni, dan kuwa kaine zakasa a kamashi a hanyarsa ta zuwa d'aurin auran, sannan musa abokinsa dole ya sanar akan bazai samu zuwa ba dan shi ba auran yake so ba, kaga ran Sarki zai b'aci matuka ya aura ma Abdulmajid Bilkisu sannan mai makon mu sakeshi lafiya sai mu juya abin a matsayin 'yan fashi ko kuma hatsarin mota, kaga mun jefi tsuntsu biyo da dutse d'aya."

  Mamaki ya hana Hisham magana kawai kallanta yakeyi.
Kallansa tai tace " ya? Wasan nawa ya had'u?"

Idanunta ya kalla yace " Magajiya kenan, duk duniya Allah bai taba hadani da mai kaifin basira irinki ba, da ace Basirarki a abu mai kyau kike sa ta lalai da ancigaba a gidan nan."
Harara ta makamai tace " mai kake nufi?"
Jinjina ya mata da hannu yace " komai yayi nake nufi."
Tace " Uwata fa?"
Sai daya had'iyi yawo yace " tana gida ba lafiya."
Cikin kulawa tace " da alama sam yaya baka kula da Khadija, inaji zan dawo da ita gabana har tai aure, munyi magana da Mahaifin Saifullahi yace tunda yara sun daidaita zasu kawo kudi."
Hisham yai murmushi yace "Allah ya kaimu."
 Kallansa ta kuma yi tace " Ya ake ciki a fada akan maganar auran Abdulmajid da wannan sakaryar?"
 Hisham yai tsaki yace " kwana biyu dai anyi shiru da maganar dama Galadima ne uban san kawo maganar da Turaki."
 Magajiya tai shiru kafin tace " Gun Abu Turab zani yanzun nan dan in tabbatar da abinda yake dashi."
 Hisham ya kalleta yace " da kanki zaki? Ba gwara ki aika yazo ba?"
 Murmushun jin dadi tai tace " ai tun yanzu za'a kulla abotar d'a da uwa saboda gudun zargi da zai biyu baya."
 Kallanta yai sannan yai kasa dakai.
 Mikewa tai ta fita sannan shima ya fito.

  B'angaren Turab suka nufa, mai kula da kofarsa ne ya bud'e tsananin mamaki ya kamashi na ganin Magajiya.
 Su kansu mutane duk wanda yazo wucewa alokacin sai dayai mamakin ganinsu.
 Bud'e mata kofa yai tare da gaisheta.
 Magajiya ta shiga tana kanta tsaye.
 Garzali ne ga taho da sauri tare da gaishesu.
 Magajiya ta kalleshi tace " Turab fa?"
 Yace " yana d'aki."
 Nan ya nuna mata hanyar falo ta shiga.
 Tsayawa tai tana kallan bangaren, abinda ko bangaren Abdulmajid tunda ya tasa bata zuwa.

  Garzali yai ciki dan kiran Turab.
 Abu Turab ya gama sa kaya kenan yaji ana kwankwasawa, yace waye? Garzali yace "nine kayi baki ne."
 Bai tambayi waye ba sai huka da ya saka ya sa turare ya fito.

  A zaune ya ganta tayi zamanta na isa akan kujera.
 Mamaki ne yasa ya ja ya tsaya tare da jingina kansa da bango, yace " Umma Magajiya da kanta?"
 Alama tama bayin da su fita daga falon,saj da suka fita sannan ta kalleshi tace " tsayuwar anan ta menene? Abun mamaki ne in uwa tazo ganin d'anta?"

 Kallanta yai sannan ya tako a hankali yana cewa " inafa abin mamaki, dama ai hakkinta ne na ta kula da d'anta."
 Ya karasa maganar tare da zama.
 Kallansa tai tace " nayi tunani akan maganar ka sai dai banaji kai ka isa ka bani umarni sai dai In zaka canza yanda kamin magana daga umarni zuwa roko."

 Kallanta yakeyi har saida tazo karshe, gani tai ya sakar mata wani bazawarin murmushi yace " ko?"
 Ranta ne ya d'an soso ta kalleshi.
 Yace " kin fara had'a kayan? Ko dayake jiya mukai maganar bazai yiwu ace kin fara ba, amma ina sanar miki sati biyu na baki kacal in har kika wuce ina tausayin halin da zaki shiga dan banaji Sarki zai barki da ranki, in kuwa har ya barki to lalai a kurkuku zaki karasa rayuwa daga ke har yayanki."

  Gabanta ne ya fadi, ta daure tare da kakaro dariya tace " inji wa kenan? Kai kana tunanin duk duniya akwai wanda ya isa ya hukuntani? Sarki? Hahah lalai yaro yaro ne."

 Turab kallanta kawai yake, jin kalamanta yasa ya mike tsaye yace " Ba sarki bane zai hukuntaki Umma mantawa nai, nine nan d'anki wanda zai hukuntaki, ya kuma hukunta duk masu hannu a abinda kuka aikata."

 "Ahhh, bansan me yasa nake tausayin mutanen da kukai amfani dasu gun cimma burinku ba, sai dai ina tunani anya zasu yafe muku? Sannan Hisham da kike takama dashi...."
 Sai kuma yai shiru tare da yin kasa da kai yana dariya yace " ke kina tunanin zai cigaba da bin umarnin ki har sai sanda kika jefashi halaka?"
 Kallansa tai cikin mamaki tace " mene?"
 Kafada ya d'aga mata ya girgiza kai yace " Bansan komai ba."
 Juyawa yai yace " in kin gama ganin gidan d'an naki kya rufomai kofa."
 Ya juya yai ciki ransa a b'ace, wato bata d'auki Sarki da wani matsayi ba? Gani take tafi karfinsa.

  Ba shakka ran Magajiga yakai gurin tunzura, lalai dole taga karshen yaron nan ita ganin sa ma ta tsani yi yanzu.


Haka ta fito rai a b'ace.

 ************

Abdulmajid kam yana tsaye a kofar gidansu Mairo sai data dade sosai dan sai da mahaifiyarsa ta tsawatar mata sannan ta fito.

 Yana ganinta ya sauko yana washe baki.
Tsayawa tai tare da hard'e hannayenta ta juya mai baya a cikin soron.
 Abdulmajid ya karaso ya kalleta ta baya sannan yace " Gimbiya irin wannan tsayuwa haka kamar mai shirin yin hoto?"
 Juyowa tai ta kalleshi tace " Abdulmajid."
 Da sauri yace " Naam."
 Tace " dan Allah dan Annabi ka kyaleni, wlh wlh ni kam na gaji da wannam abun, ka sanni sarai banaso raina ya bace dan wlh xanyi abinda kaima sai kai dana sani."

  Kalamanra ko a jikinsa yace " eh wlh, dan Allah Mairo kiyi abinda zanji jiki ni wlh so nake yi."

 Wani banzan kallo tamai na takaici tace " wai kana d'an sarki me yasa kake abu kamar karamin yaro?"
 Hannunta ya kamo, da sauri ta fizge tace " Wai Abdulmajid meke damunka ne? Na d'auka na sanar dakai banasan ka dinga tabani ko? Kaje can kun karuwan......."

  Batai auni ba taji yasa hannu ya rufe bakinta.
 Matsowa yai da sauri ta matsa jikin bango tana zare ido tace " meye hakan?"
 Kallanta yai yace " Mairo me yasa kike tunani ni din dan iska ne?"
 Harararsa tai batace komai ba.
Yace " nasan bazaki yarda da abinda zance ba amma wlh kinji na rantse ban taba sanin wata 'ya mace ba, ma sani sarai ina shafa bayin gidan mu dan jin dadi na sai dai ban taba bari abin yakai nan ba."

  Kallansa tai tace " kana tunanin zina sai ka sadu da mace kawai take a matsayin zina?"

  Kallanta yai yace " Mairo ni duk wannan ba sune a gabana ba, in kikace in daina taba mata zan daina nidak dan Allah ki auren, ko na aureki in kikaga dama kice sai kin amince zan kusanceki Wlh zam yarda ni dai dan Allah ki yarda ki auren, ina san......."

  Katseshi tai tace " Ni dai dan Allah ka kyaleni na rokeka da Allah."

  Murmushi ya sakar mata sannan yace" ma tafi yau, sai na dawo zuwa jibi."

 Kafin tai magana har ya tafi, juyawa tai ta wuce gida.

*******


? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

*59*

  Magajiya sam ta rasa yanda zatai, ganin ba mafita yasa ta nufi gun Sarki.
Yayi mamakin jin zuwanta bayan ta shigo ta zauna sannan ta gaidashi.
Kallanta yai tare da amsawa yace " Lafiya dai ko?" ya fada tare da d'aukan ruwan dake gabansa a kofi dan sha.
Fuskarta a sake kai kace cikin farin ciki take tace " dama maganar auren Turab ne, ina tunanin ya kamata in fara had'a lefe....."
Furzo da ruwan bakinsa yai tare da kwarewa, kallanta yai cikin tsananin mamaki yace " me? Me kika ce?"
Dariya tai na salo tace " me? Kana tunanin lokaci baiyi ba?"

Ido ya kura kura mata yace "Magajiya!"
Kallansa tai bata amsa ba, yace " kinsan me kike anan kuwa? Kin tabbatar a hankalinki kike ko kuwa wani tugun muguntar kika shiryo?"

  Sansanyan murmushi ta sakar mai tace " ko d'aya na dai fahimci cewa aikinane wannan, sannan waye Turab? D'anka ne fa wanda daga shi baka kara samun wani ba, ta ya za'ai yara kwaya biyu ace mun kasa kula dasu? A wata masarautar sai kaga 'ya'yan sarki sunfi 30 amma mu a namu haryanzu biyu Allah ya bamu, me zaisa mu zauna muna samun sab'ani akan su?"

  Wata banzar dariya yai dan ko magajiya zata dafa Al-qur'ani bayajin zai yadda da wad'annan kalaman nata, ya tabbatar da abinda take shiryawa.
Kallanta yai yace " yanzu me ake bukata?"
Nan ta fara mai bayani, yace zai bada kudi ayi komai cikin girmamawa da matsayi.

  Tana fitowa yabi bayanta da kallo yana tunani, me ke faruwa? Ya tabbata Turab ko mai zai ce mata bazata taba yarda da zancen nan ba balle ma tasan sirrin mahaifiyarsa, me zai sa ta amince? Ya tabbatar akwai wani shirri da take yi.

  *********

  Turab zaune agun hutawar daya saba zama ya saka ledar maganin nan a gaba a hannunsa yana kallo cilla maganin yai sama kad'an sannan ya cafe yace " kai kuma aikin me kakeyi?" 
Mikewa yai dan dole ne ya binciko maganin menene wannan.
  Bangarensa ya nufa, yana shiga Garzali ya taso ya gaidashi sannan ya sanar dashi nemansa da mahaifiyarsa takeyi.
 Mikamai maganin yai yace " so nake ka bincikomin maganin menene wannan yanzu, sannan ya zama sirri kar ka tambaya a gidan nan, kaje wajen gari"
 Garzali yace " to" sannan yai waje.

 Bangaren Mahaifiyarsa ya nufa, ta sa an shiryamai abinci, Turab ya zauna sannan ya gaisheta.
 Kallansa tai cikin kulawa daga dawowarsa daga kano har ya d'an fada, Lantana ta kalla tace " Lantana zubamai abincin."
 Turab ya kalli Lantana sannan yace " barshi zan zuba da kaina."
 Nan ya jawo plate ya d'ebi fankaso guda biyu ya zuba miyar taushe wanda yaji kaza.
 Hannunsa ya wanke sannan ya fara ci, sai da ya gama yasha zubo sannan ta kalleshi tace " ya kukai da Magajiyan?"
 Murmushi yai mata sannan yace " karki damu Umma, sirrin nan sai dai ta tafi dashi har kabarinta badai ta sanarma wani ba."

  Basira tace "me kake nufi? Kasan halin Magajiya fa?"
 Yace " Nasani Umma sanin ne ma ya sani fad'in haka, sirrinki datake tunanin amfani dashi wajen hanani auren Bilkisu da kuma sa Mai Martaba yin murabus wannan sirrin ba wani abu bane akan sirrinta da nake rike dashi, ke dai kawai ki kula da lafiyar wannan shine kadai abinda nake nema daga gareki."

  Kallansa tai cikin jin dadi da gamsuwa tace " maganar Mairo fa?"

  Yana murmushi yace " Umman Mairo, wai ni Umma daga ni da alama ba wanda kikeso sai Mairo ko?"
 Tace " Turab kenan, kasan yarinyar nan itace ta taimakeni har nakejin zaman gidan nan bai zaman min takura ba?itace ke d'ebe mana kewa daga ni har lantana, jinta nake kamar 'yata."

  Turab ya jinjina kai yace " haka ne, shi yasa akoda yaushe nake godiya gareta, na sani ta kula dake wanda ni da nake d'anki ban baki wannan kulawar ba."
 Basira ta kalleshi sai dai batai magana ba, sai dai yanayin kalamansa da yanda yake fitowa tasan magana ce wacce ke kwance a kasan zuciyarsa.

  Turab ya d'ago sannan yace " karki damu Umma, Insha Allah ba abinda zai faru sai alheri."

  Tace " Allah yasa."
 Zama sukai shi da Lantana da Basira sukai hira sosai sai da yaji la'asar tayi sannan ya fito.
 Yana shiga Garzali ya shigo falon, tare da mikamai maganin nan.
 Turab ya kalleshi yace "Maganin menene?"
 Garzali yai kasa dakai sannan yace " magani ne wanda zai halaka gab'obin jiki, ya hana mutum yin komai, ya kuma shanye mai b'arin jiki, a takaice dai guba ce mai illar gaske wanda samunta yake da matukar wahala."

  Turab idanunsa ya runtse da karfin gaske dan ji yake gaba daya kamar an kwara mai ruwa.
 Idanunsa a runtse yace " Ka yarda da sanin mai maganin daka tambaya?"
 Garzali yace " kaf garin nan an san dashi dan nima kaini gunsa akai, shikansa yayi mamakin ganina da maganin, sannan ya sanar dani maganin a hankali yake lahanta mutum ba wai tashi d'aya ba."

  Turab yace " jeka na gode."
 Garzali ya mike yai waje.
 Yafi minti goma idanunsa na runtse, wace irin matace wannan? Dan ya tabbatar itace tasa a ba Hajiya maganin nan, amma mahaifiyar mijinta? Wannan wace irin masifa ce?"


  Jiyai kansa ya sara, ya mike yai sallah ya dade yana addu'oi kafin ya shiga bandaki ya sakar ma kansa ruwa.

 Ruwa ne ke zuba a jikinsa hayi shiru yana tunani, ya dade sosai kafin ya fito.
Shiryawa yai sosai cikin wata dakakiyar shaddarsa ruwan madara, hula da takalmi ya saka sannan ua saka agoggo.
 D'ankwalin khadija ya kalla ya dade yana kallan d'ankwalin kafin ya rufe kofar da karfi, takardar daya ajiye a gefen gado.

 B'angaren Magajiya ya nufa yana tafe cikin isa.

  Yayi sa'a Abdulmajid na zaune a gunta.
 Tana jin ance yazo sai dataji gabanta ya fad'i, yauce rana ta farko data taba jin shakkar zuwan wani d'an adam gunta ba sai yau.

  Ba shakka wannan abu ya kona mata rai.
 Abdulmajid yace " ya shigo."
 Turab ya shigo tare da sallama.
 Abdulmajid ya bugamai banzan kallo yace "ina zakaje haka?"
 Turab ya kalli Magajiya sannan ya kalli Abdulmajid yace " zance zanje."
 Abdulmajid ya tab'e baki sai kuma ya zabura yace"badai gun Mairo ta ba ko?"
  Turab ya kalleshi sannan ya maida idanunsa kan Magajiya datake kallansa yace" yau ba gunta zanje ba, gun Khadija zani."

  Tashin hankalin daya bayyana a idanuwan Magajiya ba'a magana, Kallansa tai tace " me? Khadija? Ba dai Khadija wacce take 'ya ga yayana ba?"
 Turab ya d'aga mata gira sannan yace " ya? Kin sanar ma Sarki akan maganar lefe na?"

  Abdulmajid ya sheke da dariya yace "Lalai Turab amma kai ba karamin had'amamen mutum bane, kana tunanin soyayya da aure wata a lokaci d'aya?"
 Turab yai murmushi yace " ba'ayi ne? Da farko dai ni d'in mijin mata hud'u ne banda kwarkwarori."

  Abdulmajid yace " wannan damuwarka ce sai dai ka fita hanyar kanwata dan badai yar uwata ba kai ko kunya ma damu zaka had'a zuri'a?"

  Magajiga kam kallansa take cikin idanunta da suka canza kala wanda bakin ciki ne karara ne d'auke a idanun.

  Turab ya kalli Abdulmajid sannan ya kalli Magajiya tare da ciro ledar maganin nan. Ruwan dake gaban Andulmajid ya jawo ya zuba a kofi sannan ya zuba maganin nan.
 Magajiya ta kalleshi tace " meye hakan kuma?"
 Mika mata kofin yai yace " Umma sha."

  Wani banzan kallo tamai tace " a gabana ka zuba magani kace insha? Nasan ko maganin halaka ne?"

  Kai ya d'an langwab'e yace " kuma fa haka ne, kar in baki maganin dazai kwantar dake ya kashe miki gab'obin jiki sannan ya hanaki magana, ya kuma hana kwakwalwarki aiki yanda ya kamata."

  Gabanta ne ya shiga fad'uwa, daurewa tai ta saki murmushi zatai magana Abdulmajid yace" ansha karya, yanzu kai kana tunanin akwau irin wannan maganin a duniya? Sannan in akwai ma mai zai sa ka saku?"
 Turab ya kalli Abdulmajid yace " shine ai abin tambayar, Umma ya akai kika samu wannan maganin?"

  Kallansa tai tare da fito da idanuwanta, daurewa tai tai wani dariya tace " Turab kenan, kanasan zolaya, yanzu ka shigo da magani kace ni na baka?"
 Turab yace " kin manta? Ke kika bani a sanda muka had'u a b'angaren Hajiya?"

  Magajiya tace " ni bansan wannan zancen ba, sannan mai zai sani in baka?"
 Yace " shine abin tambayar? Mai zaisa ki bani? Sannan me na tare miki da zaki bani irin wannan abin? Karfa ki manta nid'in d'a ne a gunki."

 Idanu suka kafama juna dan magana ce suke yinta a juye wanda su biyu ne suka san me suke nufi, ita tasan Turab sanar da ita yake abinda ta sa akeba Hajiya, shi kuma so yake yaji menene dalilinta na neman halaka kakarsa? Wacce take uwa a gareta?

 Abdulmajid ne ya kallesu, kana kallan yanda suke kallan juna kasan kallo ne mai tatare da ma'anoni kala kala, hannu yasa ya daki kafadar Abu Turab yace " Turab bakada hankalu ne? Umma kakema wannan kallan?"

  Magajiya ta juya kai sannan ta kalleshi tace " bansan me kake cewa ba Turab."

  Yace " wasa nake yi nima, ya maganar lefen?"
 Tace " na d'auka mungama wannan maganar hakki nane a matsayina na mahaifiyarka ai inyima lefe."
 Yace " haka ne, yauwa bari na kira Gimbiya na tabbata ta damu da jina shiru tunda na dawo, bari nai amfani da wayar b'angarenki."

  Magajiya ta gama cika fal, Abdulmajid mamaki ma ya hanashi magana, kallan sa yai harya mike yai falonta, sannan ya kalli kofin ya d'auka yana kallan ruwan ciki, yace "Umma me wannan yaran yake cewa?"

  Sam bataji ma me yake cewa ba dan ta tafi dogon tunani.
 Kallanta yai ganin yanda ta tafi tunani ya sa jikinsa yai sanyi, bai taba ganin ta haka ba, me ke faruwa? Me zaisa Ummansa tama Turab lefe bayan tasan yanda ta tsani auren nan?


*TURAB*

 
? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

*60*

  Abdulmajid ya kara kallan Magajiya yace " Umma wai meke faruwa?"
Tsawa yaji ta dakamai tace " Fita ka bani guri."
Tsananin mamaki ne ma ya hanashi d'auke ido daga kanta, me yai? Yauce ranar daya tabaji tamai tsawa haka balle ma akan wani Abu Turab?
Mikewa yai rai a b'ace yai waje.
  Ko bi ta kansa batai ba ta sa kafa tayi ball da wannan kofin, mikewa tai ta nufi falonta.

  Turab kam number Bilkisu ya danna, ta dade kafin a d'aga, gaisheshi akai sannan akace wanene?"
Turab yace " Ina Gimbiya?"
Daga can akace bari a sanar mata, waz'ace?" yace "Abu Turab."
Da sauri mai maganar ta gaisheshi sannan ta ajiye kan wayar a gefe tai cikin d'aki da sauri.
Gimbiya na Kwance rike da wani littafi tana karantawa.
Bayan yarinyar ta nemi izini ta shigo ta tsugunna sannan tace "Gimbiya, yarima ne ya kira waya."

  Mikewa tai zaune da sauri tace " Turab?"
Yarinyar tace " eh Gimbiya."

  Da sauri ta juya zata sauko, sai kuma ta koma ta zauna tace jekinkice ina zuwa.
Yarinyar ta amsa da to sannan ta mike.

  Bilkisu sai da ta d'an dade a zaune sannan ta sauko a hankali ta fito.

  Sallamar duk masu kula da ita wad'anda ke falon tai sannan ta d'auki wayar, cikin kasalaliyar murya tace " Barkanka da Warhaka."
Turab wanda yasan dolene ya jira saboda mulki, yai murmushi sannan yace " na d'au lokaci kafin na kira Gimbiya, ina fatan za'amin afuwa."

  "Hmmm za'a duba uzurunka sai a maka."
Turab ya kalli kofa dan yasan tabbas Magagiya zata leko dan ganin me yake yi.
  Gefen fuskarsa ya d'am shafa sannan yace " Abubuwa ne wad'anda nikaina banyi tsamanni ba suka dinga bulbulowa wad'anda suka rike tunanina."
Tace " Hmm yanzu fa? Ka warware komai?"
Yai shiru, hakan yasa tace " Karka damu nasan zaka iya, koma menene, kardai kacemin baka yarda da kanka ba?"

  Turab ya kalle gefen kofa inda ya hango inuwar Magajiya, yiyai kamar bai ganta ba, murmushi yai sannan ya gyara zamansa irin mai jin shaukin nan yace " Kuma fa haka ne, ya kamata in zama mutum na farko mai yadda da kansa."
Tace " A koda yaushe ka dinga tunawa ina tare da kai akan komai, duk da ayanzu bazan iya taimaka maka ba, bazan kuma iya kula da kai ba sai dai inaso kasa a ranka akwai wacce take tare da kai a koda yaushe."

  Har zuwarshi sai da yaji wani sanyi ba shakka Bilkisu macece wacce ta san kanta ya tabbata zasu zauna lafiya, sannan yana ji a jikinsa ita alheri ce a gareshi.
  Jiyai tace " kayi shiru? Ba dai kalamai na......"
Katseta yai da sauri yace " wannan layin nawa ne bance ki fada ba."
Tace " layin me?"
Yace " Kalamanki sun ratsani na kuma ji dadi, ba haka zaki ce ba?"

  Bata san sanda tai dariya ba, tace " mene? Haka nace ma?"
Yace " sosai ma."
Gani inuwar Magajiya yai ta juya.
Fuska ta rufe kamar yana ganinta, Turab yace " zan kiraki zuwa ko zuwa anjima ko zuwa gobe."
Tace " Karka damu dani, yanzu ma da mukai magana ya isa, duk sanda ka samu sarari ka kirani."
Yace " Nagode, ki gaida Munnira."
Bai jira ta amsa da to ba ma ya ajiye kan wayar sannan ya mike.

Magajiya kam ta gama kuluwa da alama ma soyayya suke da yarinyar, itakam duk duniya ba wanda ta tsana yanzu irin wannan dan banzan yaran, ko ganinsa batasan yi, wai kamar ita ace ta zauna yaro yana raina mata hankali? Dolene ta nemi abinda zatai amfani dashi ko da yake ai ta shirya da auransa hmmm tai kwafa tace a ranar aure ka zai kasance jana'izar ka.
  Ta na kokarin shiga d'akinta yace " Umma me kike anan?"

  Juyowa tai fuskarta a had'e sai kuma ta saki fuska tace " Na d'auka ka tafi ai, ashe kana ciki?"

Turab yace " na d'auka zakizo ku gaisa da sirikarki, ko zaki koma in kira miki ita?"
Idanunta ne suka canza har fuskarta sai data nuna bacin ranta, daurewa tai ta saki yake tace " Meye abin azarbabi bayan nice shugabar kai lefe?"

  Kai ya jinjina sannan ya dawo gabanta, fuskarsa a hade tare da kallanta.
Kallansa tai tace " ya akai kuma?"

  Wani banzan murmushi yai yace " maganinki da kika sa a dinga sama Hajiya ina tunanin sai kinsa a nemo wani."

  Idanunta ne sukai rawa alamar mara gaskiya tace " me kake fada?"
  Yace " ba abinda nake fada ina dai sanar dakeni duk wanda ya maida Hajiya haka wallahi wannan rantsuwa ce nai bazan taba kyaleshi ba, sai na sa anmai hukunci daidai da abinda ya aikata, ko da kuwa Umma tace Basira ta aikata hakan, duk da nasan bazata taba zalintar d'an adam ba kamar wasu."

  Magajiya ta kalleshi sannan ta saki wanj banzan murmushi na rainin hankali tace " Ko nima zan tayaka d'aukan hukuncin, sai dai ka tabbatar kana da karfi na hukunta mai laifin? Ba wai karfi na jiki nake nufi ba."
Turab ya kalli kwayar idanunta yace "  Ahhh to wa ya sani?" sannan ya murmusa yace " kece kika sa aka fara game d'in, sai dai ni nake da ikon tsayar dashi, sannan inaso ki tabbatar idanunki na nan a bud'e har sanda zan tsayar da wasan, zakiga inda mara karfi yake kaskantar da masu karfi."

  Magajiya tama kasa magana kallansa kawai takeyi.
Turab ya juya ya fara tafiya, har yayi nisa ya juyo yace " Ahh ki gaida Khadija banaji zan iya zuwa yau ba, ko da yake bata sani ba."

  Kallansa tai cikin takaici tace " Kana tunanin ita Khadijan yarda zatai dakai?"

  Wata dariya ya saki yace " Khadijan? Kin tabbatar Khadijan da kika sani kike fad'a? Ahh Umma ya zakiyi? Dan Khadija ba sai na tambayeta ba dan nasan abinda ke ranta."
Ya juya.
Jiyai tace " Lalai na yarda yarinta na damunka kanka kuma na rawa, ya zakayi to? Dan kuwa an kusa sa ranarta da Saifullahi."

  Bai san me yasa ba amma sai dayaji wani abu ya taba zuciyarsa.
Sai da ya daure ya juyo fuskarsa d'auke da murmushin da yake iya lab'ansa yace " ai mace sai anyi aurenta an shafa fatiha ake tabbatar da mijinta."
Ya juya ya fita.

  Agogon dake manne a bangon gun tasa hannu ta fizgo sannan ta bugashi a kasa, kanta ta dafe sannan ta shiga d'akinta, da karfi ta bugo kofar.
Ji take kamar ta saki kara.

  

**********

  Turab na fita ya dafe kansa, ba shakka matarnan bala'ice, wacce mutum zai dinga neman tsari da ita (irinsu sai a karshe zakaji suna cewa sharrin shaid'an ne)

  Khadija ya hango daga nesa, tafe take kamar mara laka a jiki, da alama batajin dadi.
 Me ya sameta?
 Juyawa yai da sauri dan bama yasan zuciyarsa ta nemi yin rawa saboda ita.

   Ganin ya juya zai wuce yasa ta tsaya cak, idanunta ne suka ciciko dan taga da alama goje mata yake sanyi, ita kanta bataso shigowa ba sai dai dolene ta fadama Magajiya akan bazata auri Saif ba, ita dai su barta ta karashi rayuwarta a haka, inta tunan mumunan abunda suka aikata ji take baxata iya kallan wata zuri'ar da sunan mutum na gari ba.

  Ko me ya tuna sai kuma ya juyo, kallan kallo sukayi daga nesa.
 Juyawa yai a hankali ya fara tafiya.

 Bata san tana binsa ta baya ba, ji take ganinsa kamar yanasa taji abinda ke tokare a ranta na raguwa.

  Yasan tana binsa sai dai ya rasa dalilinsa na nuna mata bai sani ba, sannan ya rasa dalilinsa nayin tafiya a hankali cikin saibi.
 Har ya isa bangaren Hajiya.
  Yarinyar nan ya gani tana shara, kallanta yai yace " ajiye tsintsiyar ki kuma biyoni."

  Gabanta ne ya fadi ta kalleshi tace "Yarima laifi nai?"

 Wani mugun kallo ya mata, da sauri tai kasa da kai tace "Tuba nake Yarima."
 Ajiye tsintsiyar tai tabi bayansa.

   B'angaren sa ya nufa da ita, suna shiga cikin falo ya d'aga hannu cikin zafin rai zai kai mata mari, idanunta ta runtse dan ta gama sadaukarwa.

  Saura kiris ya mareta sai kuma ya tsaya cikin tsananin b'acin rai.

  A hankali ta bud'e idanunta ta tsugunna da sauri tace " Tuba nake ranka ya dade."


*TURAB*

  
? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

  *61*

  Jin bataji saukan mari ba yasa ta bud'e ido a hankali, kallansa tai sannan tai saurin zubewa a kasa ta saki wani irin kuka.

  Turab idanunsa ne suka canza, kallo d'aya zakamai ka tabbatar da tsantsar b'acin rai, maganin nan ya cilla mata.
A tsorace ta d'ago jiginta ya hau karkarwa.
Cikin kakkausar murya yace " Waye ya saki?" ba wai dan baisan amsar bane, a'a yanaso yasan ko tana danasanin abinda takeyi.

  Kasa ta karayi tana kuka sosai tace " Ranka ya dade ka yafe min wlh in na fad'a kasheni za'ai, sannan mahaifina karshensa yazo."

  Magajiya? D'agowa tai da sauri jin abinda yace, yanayin kallan da tai yasan dama abinda yake zargi haka ne, kusa da kafaffunsa ta matso tace " Ranka ya dade wlh nima ba'a san raina nakeyi ba, mahaifina na bukatar aiki na gaggawa a asibiti shine akace in ina sa maganin nan za'a biyamai kud'in aiki, sannan komai ua faru in sanar da ita.

  Fuskarsa ya shafa da hannayensa biyu a ransa yace Inalilahi wa ina ilaihi raji'un.
Zama yai a kan kujera sannan yace " me ya faru tsakanin Hajiya da Magajiya?gaskiya nakeso ki fadamin, ni zan taimakeki, zan kuma bayar da kudin aikin."

  Tana kuka ta girgiza kai tace " wlh ban sani ba, nadai san a ranar da Umma Rabi tazo a ranar ta aika a kira Magajiya, sannan daga ranar aka fara sani aikin."

  Turab ya kalleta yace " naji, zan sa Lantana ta koma dake bangaren Hajiya da kula da ita, zan gani ko kinyi dana sanin abinda kika aikata, sannan ki jira hukuncin da zansa a yanke miki, mahaifinki ni zan taimaka mai sai dai ke dole ki fuskanci hukunci."

  Kuka take sosai tace " na sani Ranka ya dade, na gode kwarai da cetoni da kai daga cikin masifa."

  Turab yace ta tashi ta tafi.
Fitowa yai, ya nufi can cikin gida bangaren kannen mahaifinsa dan zuwa gun Umma Rabi.

Ko Garzali baya yarda ya biyoshi duk da kuwa ya yarda da shi.
  *********

  Khadija kuwa ganin Turab ya shiga bangaren Hajiya yasa ta juya.
Har zata wuce bangaren Abdulmajid sai kuma ta karkata ta shiga.

  Bayan an sanar da zuwanta, Abdulmajid dake zaune abin duniya ya dameshi yace ta shigo.
Khadija ta shiga, kallan bangarensa tai sannan a ranta tace " yafi na ya Turab kyau sosai, da ban kula da hakan ba amma yanzu na gani, ya zakai in kaji kai ba toshen gidan nan bane?"

  Idanu ta kura mai tana wannan tunanin, ji tai tsananin tausayinsa ya kamata.

  Batasan ma ya miko yazo kusa da ita ba, sai jitai yasa kafa ya d'an harbota.
Kallansa tai tace " Yaya."
  Abdulmajid ya hard'e hannayensa ya shiga zagayeta yana kallanta yace " me ya kawoki? Ba dai zuwa kikai akan rabamu da Mairo ba?"

  Hannu tasa ta riko rigarsa tace " Yaya wannan zagayen fa? Ai sai jiri ya kamani."

  Murmushi yai sannan ya koma ya zauna.
Kallansa ta karayi a ranta tace " ya ya zanyi? in har kaji abinda suka maka wace rayuwa zaka shiga? Alokacin ba ka da wanda zaka gani kaji dadi, komai da kake tunanin naka ne a lokacin xakaga babu abu ko d'aya daya kasance naka, dama ace Mairo na sanshi ne....."

Khadija meye hakan?
Abinda ya fadane ya dawo da ita daga tunaninta.
Fara'a ta saki sannan tazo ta zauna kusa dashi tace " Yaya."

  Ya kalleta yace " menene? Nifa na fara shakkar me kikazo dashi naga sai wani kafeni da ido kikeyi."

  Murmushi tai tace " yanzu ace kai ba dan sarki bane wace rayuwa kake tunanin zakai?"

  Dariya ya saki sosai yace " ban taba wannan tunanin ba, dan tun ina d'an shekara uku Umma ta fara horar dani akan magajin sarki, kinga kuwa banda wannan lokacin."

  Khadija ta jinjina kai tace " Haka ne, amma ka taba tunanin rasa mulki?"

  Wani  kallo ya mata yace "Khadija meke damunki? Kinsan tun ina dan shekara uku Umma take sanar dani ni kadai ne magajin sarki, shi kanshi Abba a lokacin nunamin yake nine magajinsa, a haka na taso har sai bayan zuwan Turab sannan na fahimci canji daga gun Mahaifina wanda hakan na kona min rai, sam ya daina wasa dani gaisuwa ce kawai ke had'amu, bayan da shi dakanshi yake aikawa a kirani."

  Yai wani murmushin takaici yace " Khadija duk wani abu na rayuwata a da ina yinsa ne dan faranta ran mahaifina, burina naga ya dubeni yacemin Abdulmajid kayi daidai, sai dai inaa duk wani abu dazanyi bana birgeshi, ko jarabawa ta na kawomai banaji ma yana bud'ewa...."
Wani abu ya had'iya sannan ya kalleta, hawaye ne yaga ya zubo mata.
Harararta yai yace " tausayi na kike?"
Shiru tai batace komai ba.
Yai murmushi yace " tundaga lokacin na tsani Abu Turab tsana mai yawa sannan akoda yaushe Umma na sanar dani shi din fa makiyinane, kar na kuskura ba barshi."
Yai ajiyar zuciya yace " kinsan me?"
Kai ta girgiza alamar a'a
Ya matso alamar rad'a yace " ko kiran mata da nakeyi bangarena yi nakeyi dan in batama Sarki yai ko naki dadin rashin damuwa dani dayakeyi."

   Idanu ta rufe a hankali wasu zafaffan hawaye suka biyo mata, kallanta yai yace " Karki damu Khadija, na saba da rayuwa, kinsan tunda nake a gidan nan ba wanda ya taba tambayata ya nake? Tambaya ta kulawa, ina nufin Umma na ko Abba na, ita burinta shine in zama abinda takeso, shikuma dama bana cikin shafinsa."

  Hawayenta ta share tace " Yaya me yasa baka taba fad'amin ba?"

  Dariya yai sannan ya mike yace " na fizan na zama bad guy, hakan ne zaisa in rage takaicin abinda ke raina, sai dai Khadija kiyi hakuri amma bazan taba ba Abu Turab Mairo ba, ya kwacemin uba, mutane, na bar masa amma banda wannan."

  Jitai tama kasa magana, me yasa itama a koda yaushe takejin zafinsa? Gani take baya kyautawa sannan shidin mutumin banza ne? Ashe bakincikin dake ransa ne yake amfani dashi dan kuntatawa na kusa dashi? Ya zaiyi in yaji sirrin nan?

  Daurewa tai tace " Yaya kana tunanin Mairo zata soka? Bayan kai din mutum ne wanda yake had'uwa da Magajiya su aikata abinda bai daceba na zalunci?"

  Yace "Ahhh zalunci? Hmmm Khadija kenan bana tunanin kinsan Umma."

  Kallansa tai tace " bansan ta ba sannan bana bukatar Saninta, sannan kaima Yaya zuciyarka na neman riked'ewa gaba d'aya ta koma ta Umma, ka gaggauta kaucewa daga sharrinta."

  Murmushi yai sai dai baice komai ba, a ransa yace "hakan na nufin in bijiremata ita kuma ta yarda ni, ita kadan da nake sa rai tana sona itama ta juyamin baya."
Khadija ta mike tare da kallansa tace " Yaya zanje gurin Umma Magajiya ne, akan maganar aurena da Saif."

  Yace " Ya ya? Maganar auren an kusa ne?"

  Kai ta girgiza tace " a'a."
Juyawa tai ta fita, aranta tana mai fatan kub'uta daga sharrin Magajiya da Mahaifinsu."

  ********

  Falon yai tsit kamar ba kowa a ciki, Umma Rabi tai shiru kamar ruwa ya cinyeta sannan ta d'ago ta kalleshi.

  Abu Turab yace " Umma ki taimaka ki sanar dani, Hajiya na cikin wani hali."

  Tace " Turab sirri ne...."

  Yace "wa ke zancen Sirri rayuwar Hajiya na cikin had'ari?"

  Umma Rabi tai shiru kafin can ta d'ago ta kalleshi.
Nan ta sanar da shi abinda ta sani.

  Shiru yai kafin yace "ita waccan d'in wacece? Wacce ta aiko da wasikar?"
 Umma Rabi tace " ban santa ba sai dai kafin Hajiya ta fara rashin lafiya da yamma na koma gunta, a lokacin ne ta sanar dani wani sirri wanda ahi nake tsoron sanar dakai."
 Yace " na menene?"

  Ta dade batace komai ba, yace Umma dan Allah ki fadamin.
 Tace " ka tabbatar zaka iya ja da Magajiya?"
 Yace " kwarai kuwa."
 Yanda yai maganar ya bata kwarin gwiwa tace " Maganin da ake zubawa sarki na hana d'aukan ciki ne."

  Tashin hankali.

  Bakinsa ne ya shiga rawa yama rasa mai zaice.
 Umma Rabi ta kalleshi sai dai itama batasan me zatace mai ba, a hankalu tace " ni kaina ina zargin ciwon Hajiya da Magajiya, sai dai banida shaida sannan bansan wa zan tara da maganar ba."
 
  Turab mikewa yai kamar wanda bashida laka a jikinsa.

 Tafiya kawai ya keyi yana tunanin wannan al'amari.

  Jiyai kansa ya d'au wani zafi, tsayawa yai a jikin wata bishiya ya dafata, addu'a kawai yakeyi Dan neman sauki a zuciyarsa.


   Ya dade sosai kafin ya nufi bangaren Hajiya.

  Hajiya kam babu, dan jikinta ba dadi to abune da anriga an gama halakata, ba shakka bai taba ganin mutum irin Magajiya ba, kenan duk wanda yasan sirrita ajali shine zai biyoshi?

  Kallo d'aya zakama Hajiya kasan inaa sai dai wani ikon Allah.


***********

  Magajiya na kwance a d'aki dan tun tafiyar Turab takejinta haka, a kwance take taji sallamar Khadija.
 Daurewa tai ta mike zaune, Khadija ta shigo.
 Bayan ta gaisheta, Magajiya tace " Khadijata ina kika shiga? Kwana biyu sam ban ganki ba."

  Khadija fuskarta a had'e tace "Ina gida."
 Magajiya ta kalleta cikin kulawa ganin duk ta rame, tace " Khadija mai kike tunani akan dawowa nan da zama kafin lokacin aurenki?"


  Khadija ta kalleta duk da gabanta na fad'uwa saboda tsananin kwarjini da Allah yaba Magajiya ta daure tace " Dama zuwa nai in fadamiki akan bazan auri Saifullahi ba."

  Magajiya ta zaro ido tace " mene? Wace irin banzar magana ce hakan?"
 
  Khadija tace " dama abinda nazo fadamiki kenan."

  Magajiya ranta ya b'aci tace " Akan Abu Turab?"

 D'agowa Khadija tai ta kalleta, Magajiya tace " ke kina tunanin zan baki Abu Turab?"

 Jitai zuciyarta ta dake tace " ina fa zance Ya Turab zan aura? In ba so nake ku halakashi ba?"

  Magajiya ta kalleta cikin tsananin takaici tace " in kin san da haka to kiyi gaggawar cireshi a ranki."

  Khadija jitai ranta ya b'aci wato duk abinda sukeyi baya damunsu? Tace zasu halakashi amma ko a jikinta.

  Sun biyu suna neman ruguza rayuwar mutane dayawa, na farko sun gama cin amanar sarki, sun jefa Abdulmajid cikin halaka, suna neman jefata sannan sun takurawa wanda yake jinin gidan, suna neman halakashi.

  Ita kanta batasan tace " To ko Ya Abdul
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *KAINUWA* A Historical Fiction* by Ayusher Muhd Gimbiya 1 15,759 08-21-2019, 01:53 PM
Last Post: Ebony Lacklock
  *JALILAH* by Ayusher Mohd* Gimbiya 0 20,165 09-10-2018, 09:03 PM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,758 06-16-2018, 10:17 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 6,907 06-16-2018, 10:16 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,349 06-16-2018, 10:09 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,717 05-07-2018, 11:04 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 4,309 05-07-2018, 10:54 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,636 04-30-2018, 01:16 PM
Last Post: Gimbiya



Users browsing this thread: 1 Guest(s)