The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*KAINUWA* A Historical Fiction* by Ayusher Muhd
#1
? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

   *H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ??‍♀*

  *40*

   
      Magajiya ce kicinged'e a kilisarta da alama tunani takeyi duba da yanayin da take ciki.
 Jin muryar Hisham ne yasa ta katse tunaninta tare da bashi izinin shigowa.
 Hisham ya shigo sannan ya zauna kusa da ita, ya gaidata.
 Magajiya tad'an ja numfashi bayan sun gama gaisawa tace " Hisham dole ne sai mun kawar da Abu Turab daga gabanmu, domin na kula in bamuyi wasa ba Mai Martaba zai biyo mana ta bayan gida, da farko ya had'a Turab da 'yar sarkin kano sannan mun fahimci yana gani, sannan gashi zamansa a asibiti manyan masu mukamai sunje dubashi sun kuma dawo da yaban d'abi'arsa."

 Hisham ya kalleta yace " Magajiya nikaina abin nan ya damen, me zai hana mu raba shi da du......"
 Wani mugun kallo ta bugamai tace " so kake ka lalata mana shiri irin sanda yana jariri? Duk badadan kaje kayi shirman kona musu gida ba me zaisa Basira tabar gidan nan? Da cikin ruwan sanyi zamu turashi barzahu ba tare da an fahimci komai ba, dan haka karka kuskura ka kara gigin daukan hukunci ba tare da ni na sani ba."

 Ba shakka yaji haushin kalamanta a ransa, sai dai a fili cewa yai " shikenan."
 Tace " nayi tunani sosai na fahimci Basira itace lagwan yaran nan, in har muka sata a tsaka mai yuwa to fa Turab zai zamar mana tamkar akala."
 Hisham yace " Na d'auka Turab muke hari ba wata Basira ba."

 Tsaki tai tace " kai matsalata dakai kenan, kwakwalwarka gaba d'aya bata ja, kai kana tunanin yaran nan ba wani abu bane?"
 Hisham yace " to nawa yaran yake?"
 " nawa yake amma har ya nemi ja min masifa nida Abdulmajid? To bari kaji in fada ma, wlh wannan yaran in ba munyi da gaske ba reshe ne xai juyi da mujiya."

 Tacigaba " so nake kasa a samomin guba amma mara karfi."
 Cikin mamaki yace " guba kuma? Wace iri?badai Basira zaki kashe fa ita ba?
 A fusace tace " wai meyasa in na fadi abu ne yaya sai kace sai na fadama dalili? Kasa a samo abinda na fadama, sannan ka tabbatar kasa anba wannan yarinyar da muka saka a bangaren basira data saka a cikin abincin da za' a kawo min?"
 Idanunsa ne suka firfito yace " bangane abincin da za'a kawo miki ba? Kina nufin kece zakici gubar?"
 Tace " wannan ba damuwarka bace in har kanaso mu d'aura Abdulmajid akan mulki to kawai ka dinga bin abinda na umarceka ba tare da tambaya ba."

  Daurewa yaiyace "to."
 Tace " gobe zasuzo gaisuwa, dan haka ayau zaka samo gubar ka kuma aika da ita a daren nan."
 Yace to, mikewa yai ya fito yana mamakin me take shirin yi.

 Yana fita ta mike, sannan tai murmushin mugunta.


**********

  Shikam Abu Turab bayan ya iso yana gun Mahaifinsa sun dade suna tattaunawa game da bikinsa da kuma wasu al'amura na sarauta da mahaifinsa ya nemi shawarar d'an nasa akai.

 Sun yanke shawarar komawarsa garin kano a wannan sati, in ya dawo kuma sai a tura kayan gaisuwa da na lefe a saka rana.


  Bayan ya fito ne ya nufi gun mahaifiyarsa, duk inda ya wuce mutane sai tayashi murnar warkewa sukeyi har ya isa.

 Basira tasa an mai girke kala kala kana ganinta zakaga tsantsan farinciki a fuskarta.
 Bayan sun gaisa ne tasa aka jera mai abimci kala kala, Abu Turab yai murmushi yace "Umma kenan sai kace wanda na bar garin?"
 Lantaba Tace "ai Uban gidana inaji da kai mace ne in kai aure binka zatai."
 Dariya suka saka, nan ya fara zuba abinci.
 Basira tace " Magajiya ta shirya walima na kusa da zamuje gobe na murnar warkewarka."

 Kallanta yai sannan ya baida kansa kan abincin yace " she is trying hard."
 Basira tace " magana kai?"
 A'a, amma su waye zasu gun?
 Tace "hmm daga dai mu matan Takawa da shi Mai Martaban sai kai da Abdulmajid, amma bansan ko da wasu ba."
    
  Yace "hmm."
 Basira tace " tace insa ayi abinci daga nan, nafi san kowa in mai abincin danasan yafi so, saboda taro ne akayishi saboda d'ana."

  Zuciyarsa d'aya dan bai kawo komai a ransa ba yace " to, amma karki wahalar da kanki Umma."
 Tace " wace wahala bayan ba ni zanyi girkin ba?"
 Murmushi yai ya cigaba da cin abincinsa.

 Sai daya gama ya mike ya fito, bangaren kakarsa ya nufa wacce ta tsufa sosai gashi batada lafiya, yana tafe su Garzali na bayansa.

 Sam bai kula da ita ba wacce ta shigo gidan na sarauta dan kawo ma Abdulmajid sakon da mahaifiyarta ta aikota ta kawo.

 Sai da suka kusan junan su sannan suka ankara da juna.
 Kallanta yai sannan ya d'auke idanunsa ya cigaba da tafiya.
 Wani sanyin dadi ne ya kamata ta karaso da sauri tace " Yaya."
 Tsayawa yai sannan ya juyo ya kalleta fuskarnan a d'aure.
 Murmushi ta saki tace " Yaya baka taba ganina ba ko? Nice Khadija, ahhh nasan kasan muryata, hmm Alhamdulila yau Allah ya amshi addu'a ta."

  Kallanta yakeyi kawai sai dai zuciyarsa ta karaya sosai, Khadija ta share kwallarta data taho tace " Yaya Allah ne kadai yasan farincikin danakeyi ganin idanunka sun bud'u da izinin Allah bud'ar idanunka zai kawoma alheri masu yawa a rayuwarka."
 Ta karasa maganar cikin rawar murya dan kuka na neman kufce mata.
 Sama ya d'an kallan kadan yana neman dake zuciyarsa dan tabbas kalamanta sun ratsashi.
 Kallanta yai yace " nagode, sai dai inaso ko a hanya muka hadu ki daina nuna kin sanni, banasan inzama mai jawo miki bakin ciki shiyasa nake fatan ki cireni daga ranki ki kuma daina damuwa dani."

  Kai ta jinjina ta na kokarin share hawayenta da hannu tace " naji yaya, zanyi abinda kace."
 Kallan mamaki ya mata dan bai yi tunanin abinda zatace kenan ba.

 Khadija ta kara share hawayenta tace " kasan meyasa zan rabu dakai yaya?"
 Kallan ta yai baice komai ba.
 Ta cigaba " saboda ka daina murmushi in kana tare dani, ka daina fara'a, ko farin ciki kakeyi daga kaji muryata sai inga farincikin nan ya tafi daga fuskarka."

  Hawayenta ta kara sharewa tace " kaine mutum na farko dana taba so, banaji zan kara san wani haka, ba kuma naji zan daina ma fatan alkairi da yima addu'a a rayuwarka sai dai bazan taba yarda inzama nice sillar bakin cikinka ba, bansan dalilinka na canzamin hala ba, sai dai ba yanda z........"

 Hawaye ne suka taho sosai wanda ta kasa karasawa, jiyai gaba daya daga tsakiyar kansa har zuwa 'yan yatsun kafafunsa sun amsa, shikansa sai dayaji idanunsa suna neman canzawa na yanayin kawo ruwa.

 Kallansa tai sannan ta kakaro murmushi tamai sannan ta juya ta fara tafiya.

  Kasa motsawa tai daga inda yake, su Garzali na gefe duk da basusan me tacemai ba amma sun fahimci yana bukatar keb'ewa.

 Abu Turab kallanta yakeyi har sai da ya dena hangota sam ya kasa motsawa, yafi minti 20 a haka kafin ya taka kamar wanda aka tsuma a ruwa ya karasa bangaren kakar.

 Jikinta kam ba sauki duba da yanayin tsufan datai, bai dade ba ya taso.

 
  D'akinsa ya nufa ya shige ya kwanta rigingine, rayuwarsu da Khadija ya shiga tunowa, wasu kananan hawayene suka zubo ta gangaren idanunsa, mirginawa yai ya kwanta ganin tunaninta na neman addabarsa ya mike zaune da sauri ya bud'e cikin drawer dinsa ya dauko d'ankwalinta har yayi kamar zai yadda sai kuma ya fasa ya d'aga can kasan kayansa ya saka shi.

 Ya koma kan gado ya kwanta........

 Khadija kam tana fita ta wuce gida dan kuka kawai takeyi, sam bata kula da Hisham ba dayake tsaye gefen kofar shiga gidan shi da su Galadima.

 Hisham ya kula da kukan da takeyi sai dai ba damar magana saboda bayasan a ganta tana kuka.


  *TEAM ABU TURAB ??*
? *KAINUWA*?
     ......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)


*41*

    Yau tun safe ake hidimar yin walimar da Magajiya ta shirya, barin ma bangaren Basira wanda aketa hada hadar girke girke, katon d'akin da suke taro na lokaci zuwa lokaci tasa aka gyara, an mai kwalliya sosai, kowa an waremai gurin zamansa.

  Abu Turab kam yana can gun hutawar mai martaba wanda ya saba zama, yarasa meyasa yakejin hankalinsa bai kwanta da wannan walimar ba sai dai ya rasa ta ina matsalar take, kalaman Magajiya ne suke ta mai yawo a zuciyarsa, ya tabbata akwai abinda ta shirya a wannan taron.

  Ganin bashida amsa da hujjar dazai kama yasa ya mike, ya nufi bangaren Mahaifiyarsa.

  Tana tsaye a kitchen tana kula da abincin da ake tayi, Mairo ma aiki take tukuru, murmushi yai na jin dadin yanda take taimakon mahaifiyarsa.

 Basira ce ta juyo ta kalleshi sannan ta kalli Mairo tace " Mairo bari na shiga ciki."
 Tace " To Umma" kallan Abu Turab tai tace " Yaya Ina Wuni? "
 Yace " Mairo sannu da aiki."

  Bata amsa ba sai murmusawa datai.
 Bayan Basira yabi, Suna shiga ciki ta kalleshi tace " Dazu na tura a kiramin Mairo, sai datazo hankalina ya kwanta har nake shigowa ciki."

 Kallanta yai yace " Umma kinaji da Mairo, itama haka."
 Tace " Abu Turab in fadama gaskiya babban burina a duniyarnan a wannan lokacin bai wuce in ganka cikin farinciki ba, sannan banaji akwai mai saka wannan farin cikin daya wuce ta."

 Kasa yai da kansa baice komai ba, ta kalleshi tace " komai da lafiya ko?"
 D'agowa yai ya kalleta cikin wani yanayi yace  " Umma sam hankalina ya kasa kwanciya, inaji a jikina akwai abinda zai faru a gun taron nan sai dai na rasa menene."

 Kallansa tai cikin kulawa tace " Turab nasan me kake tsoro sai dai inaso ka sa aranka ba abinda zai faru in shaAllah, dana menene abin jin? Bai wuce ta zuba mana wani abun a abincin mu ba, to ninake yin abincin kaga ba wani abu da zata iya yi."

 Jitai yace " shine abinda ke damuna Umma, yin girki a nan bangaren."
 Kai ta girgiza tace " Abu Turab kenan, insha Allah ba abinda zai faru."

 Shiru yai baice komai ba, sai dai shikam abin na damunsa menene dalilin barin mahaifiyarsa ta d'au nauyin girke girke?"
 Basira ce ta katseshi tace " ka tashi kaje ka shirya nima shirya wa zanyi tunda ankusa kamala komai, sannan Mairo da Lantana suna gun."

  Mikewa yai ya fito jiki a sanyaye.
 Sai dayazo saitin kitchen sannan ya kalli kitchen din aiki kawai akeyi, Mairo ce ta fito tazo jikin kofa tace " Yaya lafiya?"

 Yace " Mairo dan zo."
 Takowa tai har zuwa inda yake, ya kalleta kamar zaiyi magana sai kuma taji yace " shikenan."

 Kallan mamaki tamai sai dai batace komai ba, juyawa yai zai wuce sai kuma taga ya tsaya ya kalleta yace " Nagode Mairo."

 Nan ma kallan mamaki tamai, sai dai bata iya cewa komai ba.
 Abu Turab ya fita zuwa bangarensa.

 Wanka yai sannan ya shirya cikin wata had'adan yadinsa d'inkin yamai kyau sosai, yasa hula sannan yai sallar la'asar.

 Ya dade yana addu'oi kafin ya mike ya fito.
 Su Garzali dama suna tsaye suna jiransa.

*************

 Magajiya ta sha ado na gani na fada, tayi kyau sosai kamar batakai yawan shekarunta ba, kallan kanta tai a madubi ta saki murmushi a ranta tace " nayi kuskure babba na bawa kishiyoyina maganin hana haihuwa, kaine ka nunamin kuskurena Turab, ba su ya kamata in ba wa magani ba mijina ya kamata inba, sai dai ganin an haifeka ina zaune kamar wawiya yasa na dawo hayyacina, tun kuwa daga lokacin nasa aka amsomin magani akesama Mai Martaba a abinci, ba'a ja dani, ka jirani zan nunamaka wacece Magajiya a ranar yau, zan nuna maka bakasan komai ba a harkar wasa.

  Takalmi ta saka ta zura alkyabbarta kyanta da kwarjininta suka kara fitowa.
 A falonta ta tadda ragowar matan kannan mai martaba da kuma kishiyoyinta.
 Nan suka gaisheta, tana gaba suna bayanta haka har suka isa.

 A zaune suka tadda Basira, a mazauninta, sai matar Galadima da Mamar Khadija.

Tana shigowa ta mike sai data zauna sannan kowa ya samu gu ya zauna, wannan tsarin ita tafito dashi, duk sanda za'ai taro dolene sai ta zauna kafin kowa ya zauna.

 Sun d'anyi gaishe gaishe kafin a sanar da isowar Abdulmajid.
 Nan ya shigo ya gaida Magajiya da matan mahaifinsa sannan yaja ya zauna, a gun zamansa.

 Can aka sanar da Zagi ya sanar da isowar Mai martaba.
 "Lafiya Sarkin yakin Sarkin musulmi
Lafiya maida garin wani kango
Lafiya Barden mahadi
Lafiya Sukukun bakaka
Lafiya Darzaza amalen sarakuna
Lafiya ba hau da wani ba sauke wani
Lafiya hana kangara
Lafiya Sakaka babban bako
Lafiya Bango madafar bayi
Lafiya hadarin kasa maganin mai kabido........."

  Mai Martaba ne ya shigo Abu turab na bayansa.

 Yana shiga kowa yagaidashi.
Sai da ya zauna a gun zamansa.
 Gyaran murya yai sannan yace " Nagode kwarai da zuwanku taron nan na taya murnar samun saukin Abu Turab, Allah ya saka da alkairi."

 Nan sukace Ameen.
 Abu Turab na zaune gefen hagunsa sai tunsu d'aya da Abdulmajid wanda ke zaune a bangaren dama.
 
 Sai daya gaishesu shima kamar yanda Abdulmajid yai sai dai shi sai daya gaida kowa.
 An d'anyi shiru kafin Magajiya tace " D'ana Abu Turab fatan alkairi gareka da kuma rayuwarka, yanda idanunka suka bud'e ina maka fatan kyakyawar rayuwa mai d'orewa."
 Nan kowa yace "amin."
 
 Abu Turab kallanta yai sannan yai kasa dakai yace " ina godiya Umma Babba na kuma gode da addu'arki."
 Murmushi  tamai wanda hakan ya d'ansa shi kara kallanta.
 D'auke idanunta tai daga kansa ta kalli basira sa nan ta kalli sarki tace "  Haikawa Basira ce tace abar mata harkar girke girke."

 Murmushi ya saki sannan ya kalli Basira yace " ai ba laifi, hakan yayi."
 Mamaki abin yad'an ba Basira dan kuwa ba ita ta nema ba, itace ta ba ta, to meye na fadama ma Sarki?"
 
 An d'anyi hira kad'an kafin Lantana ta shigo ta fara jera abinci, wanda masu kula da bangaren Basira ke rike da tire manya manya.

 Da yake abin a tsare yake ,Lantana ta ajiye ma kowa nasa a gabansa.

 Nan Mai Martaba ya bada izinin aci abinci.

 Sai daya fara ci kafin kowa ya bud'e nasa.
 Abu Turab kam ko bud'e nasa bai yiba sai kallan kowa yakeyi yana san yaga inda wani shiri da takesan tadawa.

  Kallansa tai ta saki murmushi dan ta fahimceshi. Nan ta bud'e nata itama hankalinta a kwance.
 Kafin ta faraci sai data kalli Turab tace " D'ana ya naga ko bud'ewa bakai ba?"

  Kallanta yai tare da d'an rage girman idanunsa, sannan yace " yanzu zanci."

 Bud'e nashi yai, kallanta ya sakeyi, gani yai tana tacin abincinta hankalunta a kwance, kowa ya kalla yaga kowa yana ci ciki kuwa harda Basira.

  Yana kokarin kaiwa bakinsa sukaga Magajiya ta fara wani abu, da sauri Abdulmajid ya mike cikin tashin hankali.

 Nan fa kowa ya yo kanta, kumfa ne ke fita ne daga bakinta, idanunta sai farfari suke.
 Abu Turab ya  runtse idanunsa da karfin gaske, sanna ya bud'esu sun kada sunyi ja, hannayensa ya saka duka biyun ya shafi fuskarsa abinda ta shiya kenan?

 Mai Martaba ne cikin tashin hankali ya kalli Abu Turab sannan ya ce " Turab yi sauri kasa a kira mai magani, ya sameta a bangarenta, bari a maidata can."

  Nan akai waje da ita, sai amai kawai takeyi.

 Basira kam gaba d'aya ta gama rikice wa sai yanzu itama ta fahimci dalilin dayasa tace tai girki.
 Abu Turab ya kira mai magani suka isa bangaren Magajiya.

 Nan aka shiga mata magani, amai take har yanzu, mai maganin ta d'ago ta kalli mutanen gun tace " guba ce, guba taci."

 Hankalin kowa a tashe aka kalli Basira.
 Abu Turab yana rasa mai zaice.
 Abdulmajid ne ya shigo da gudu cikin dabara ya tura mata wani abu a bakinta.

 Aman ya tsaya sai dai da alama hankalinta baya jikinta dan a sume take.

 Abu Turab  ya kalleta cikin tsananin mamaki, yau abin harya kai ta nemi halaka kanta? Akan mulki? Akan ta hanashi auren Bilkisu? Ya tabbata yanzu basuda mafita, in zance ya yado zaije har masarautar kano, wani sarkin ne ko wani uban ne zai bashi aure? 

  Fitowa yai waje dakyar yake sa kafarsa.
 Khadija ce ta karaso da sauri, itada Mahaifiyarta.
 Yana kallanta ta shiga ciki kamar bata ganshi ba.
 Kallan waje yai mutane sun cika gun sosai, sai gulmar Basira akeyi, kowa na fadan albarkacin bakinsa, shikansa yana fitowa ya fahimci gulmar hardashi.

 Wato Basira dan taga d'anta ya warke shine take kokarin halaka Magajiya, sannan ta halaka Abdulmajid ta d'aura nata akan mulki.

 Inka ganta kamar bazatai haka ba.
 Gulma dai kala kala...

 Basira kam tana zaune a falo cikin tashin hankali, ta tambayi masu aikinta kowa yace baisan meya faru ba.
 Mairo duk ta rukice itama ta shiga kitchen sai dube dube takeyi cikin tashin hankali.

 Kan kace me? Zance har ya fita daga gidan ya shiga cikin gari.....

*TEAM ABU TURAB ??*

  *42*

   Abu Turab ya shiga bangaren mahaifiyarsa, ba kowa a falon sai Lantana dake zaune jugum.
 Tana ganinsa ta mike ta gaisheshi, kallanta yai yace " Umma fa?"
 A hankali tace  "tana d'aki."
 Juyawa yai ya fita, dayake magrib ta duso massalaci ya nufa.
 Ana idar da sallar wasu dan gulma tun a cikin massalacin suke yan gulmace gulmacen maganar, mikewa yai ya fito.
 Bangaren Mahaifinsa ya nufa.
 Jakadiya tana ganinsa ta iso gunsa ta gaidashi.
 Kallanta yai yace " Mai Martaba fa?"
 Tace " Yana ciki, a ma iso?"
 Kai ya d'aga mata alamar eh, har ta fara tafiya sai ta dawo gunsa tace " Hmm nikam Yarima naji abinda ya faru, sai dai kuma hmm tuba nake ranka ya dade amma ni nasan akwai alamar tambaya a al'amarin nan."
 Gefe da gefe ta kalla tace " Sai dai neman Allah ya fitar da ku lafiya."

 Kauda kansa yai daga kanta dan shi sam bayasan harkar gulma tunda kuwa yaga yanda take wani juye juye yaji ransa ya baci.

 Juyawa tai, bata dade ba sai gashi ta dawo tace ya shiga.
 Abu Turab ya shiga.

 A zaune ya tadda mahaifinsa sanye da tabarau, rike da wata takarda da alama karantawa yakeyi.
 Abu Turab ya shiga sannan ya kara gaidashi.
 Sarki ya zare tabarau din ya kalleshi yace " Turab ya akai?"
 Abu Turab ya kalleshi yace " Abba, na tabbata kasan Umma bazata aikata wannan laifin ba."
 Murmushi yai sannan yace " bansan komai ba Turab, bansan ko zata aikata ba ko bazata aikata ba."
 Kallan mamaki Abu Turab yamai yace " Abba."
  Sarki ya kalleshi kallo wanda bazaka tana fahimtar yanayin da mutun yake ciki ba yace " Abu Turab ba dai so kake kacemin in yarda da Basira ba, bayan a gabana Magajiya ta fadi?"

 Abu Turab cikin mamaki ya kalleshi yace " Amma......"
 Katseshi yai yace " In har kanaso in yarda da Mahaifiyarka to inga evidence wannan shine kadai abinda zan fadama."

 Abu Turab yai shiru" nagode." Kawai abinda yace kenan yai waje.
 Mai Martaba ya bi bayansa da kallo cikin tausayawa a fili yace " Abu Turab dolene sai ka yaki weakness dinka, Magajiya ta riga tasan Basira tace lagwanka, tunda nake bantaba ganinka cikin damuwa kamar tayau ba.

 Abu Turab yana fita ya nufi bangarensa, sam ya rasa dalili zuciyarsa ta kasa bashi wata mafita, kwakwaran tunani ma ya kasayi, mahaifiyarsa kawai yake hangowa lokacin da ta kalleshi cikin wani yanayi, kallo d'aya yamata ya fahimci tsantsan tashin hankali karara a idanunta.


  Wannan rana ta zame musu ranar tashin hankali, Abu Turab da Basira.
 Magajiya kuwa ta daina amai sai dai har alokacin bata bude idanunta ba a haka a ka kwana, khadija ce ta zauna a gunta.

 Washe gari da safe yana  zaune a d'aki Garzali ya kwankwasa mai kofa.
 Mikewa yai ya bud'e, kallansa yai yace " Garzali ya akai?"
 Garzali yace " Sabi'u ne ya zo Ranka ya dade."

 Bai koma ciki ba kawai ya jawo kofar d'akin ya fito falo.
 Garzali yabi bayansa.
 A zaune yaga Sabi'u.
 Kusa dashi ya karasa ya mikamai hannu sukai musabaha.
 Sabi'u ya kalleshi cikin kulawa yace " Mutumina are u okay?"
 Murmushin yake ya masa yace " ya akai da safen nan?"
 Sabi'u ya kalleshi yace " maganar Gimbiya Bilkisu ce."
 Kallansa Abu Turab yai yace " ta fasa aurena?" Murmushi yai yace " nasan haka zata faru ai."
 Sabi'u yace "no ba haka bane." Ya fada yana girgiza kai.
 Abu Turab ya kalleshi sai dai baice komai ba.
 Sabi'u yace " nemanka takeyi."

 Cikin mamaki Abu Turab ya kalleshi yace " nema kamar ya?"
 Sabi'u yace " bansani ba ni kaina, bansan me ya faru ba d'azu da safe wambai ya kira gida a landline ya ce abani, ina amsa ya sanar dani, kasan Wamban kano shike auren kanwar Mamana."

 Abu Turab yace " shikenan a satin nan naje."
 Sabi'u da sauri yace " da alama neman na gaggawa ne fa, kasan ana asuba aka kira wayar? Bansan meke faruwa ba amma tabbas yanda aka sanar dani da alama neman gaggawa ne."

 Mikewa yai yace " Kana tunanin zan tafi inbar Umma na da take cikin wannan halin?"
 Sabi'u yace "haka ne sai dai ina ganin ka nemi shawararta, ita kanta nasan cewa zatai kaje."
 Abu Turab yace "zan nemeka duk yanda mukai da ita."

 Daga nan ya wuce ciki.
 Tun dare yake tunanin mafita, sau biyo yana komawa bangaren mahaifiyarsa amma har a lokacin bata fito ba wannan dalilin shi ya kara d'agamai hankali sosai.
    Har ya zauna sai kuma ya mike ya fito bangaren mahaifiyarsa.
 Lantana tana ganinsa ta taso ta gaidashi.
 Kallanta yai cikin damuwa yace " ta fito?"
 Lantana ta girgiza mai kai alamar a'a sannan tai kasa da kanta alamar damuwa.
 Kofar d'akin ya nufa, ya kwankwasa, shiru yaji ya kara kwankwasawa.
 Jin ba alamar motsi yasa ya murd'a kofar d'akin.
 A kan gado ya hangota a kwance lulube da bargo.
 Da sauri ya karasa ciki.

 Bacci takeyi sai dai kana kallanta da yanda take futar da numfashinta zakasan ba tada lafiya.
 A hankali yakai hannunsa kan goshinta.
 Zafin dayaji ne yasa hankalinsa ya tashi.
 Da karfi ya kwallawa Lantana kira.
 Da gudu ta shigo dan yanda ya kirata tasan da matsala, Lantana ta kalleshu cikin tashin hankali ta kalli basira.
 Cikin fada yace " Lanata me kike yi jikin Umma yakai haka?"
 Lantana ta kalli Basira cikin yanayin na ban tausayi tace " Uban gidana jiya da zata shiga tace kar inbar kowa ya shigo mata ciki kuwa harda ni, sannan ko abinci in na kwankwasa mata sai tace min kar na sake shiyasa ban kara dawowa ba."

 Idanu ya runtse cikin tashin hankali yace " kira mai magani."
 Hannu Basira tasa ta rike hannun Turab cikin a hankali tace " a'a Turab inba so kake magana ta kara karfafa ba ka bar zancen mai maganin nan
"
 Kallanta yai cikin tausayawa idanunsa duk sun rine yace " Umma?"
 A hankali tace " Lantana kisa a kira Mairo kice ta tahomin da magani, hakan ya isheni Turab
"

 Rasa abin cewa yai, jiyai tace " Ya jikin Magajiyan?"

 Kallanta yai cikin wani yanayi, yace " wake zancen wannan? Matar da ita tajama kanta ciwo dan ganin bayana? Meyasa in zatai sharrin bazai tsaya iya kaina ba? Menene dalilinta na had'awa dake?"


 Kallansa tai, jiyai zuciyarsa ta kara karaya, mikewa yai da sauri ya fito daga d'akin, bakin ciki ya addabeshi.
 Bangaren Magajiya ya nufa rai a bace.
 Tana kwance, Khadija ce kawai a gunta tana zaune tana matsa mata kafa.
 Kallo d'aya yama khadija ya maida dubansa kan Magajiya, yana kallanta yace " Ta farfado?"

 Khadija ta kalleshi ba shakka tafi kowa sanin yana cikin wani hali sai dai ita kam ta rasa inda matsalar take, ta tabbata Umman Turab bazata taba yin haka ba, to meya faru? Daga ina aka samu matsalar?

 "A hankali ta amsa mai baya farka ba yaya."

 Idanunsa nakan Magajiya yace " d'an bamu guri."

 Mikewa tai jiki a sanyeye tai waje, zuciyarta a karye, ba shakka tasan jiya ya turab ko bacci bai samu ba.
 Juyowa tai ta kurama kofar d'akin ido, ya zatai da ya Turab?ya zatai ta taimaki mahaifiyarsa?"

 Abu Turab bayan ta fita ya kalli Magajiya yace " Kina kokari, na kuma jinjina miki a salo na makirci da iya tugu, kinfi mahaifiyata girma amma saboda kinasan ganin bayana kika ajiye girmanki."

  Gani yai ta bud'e idanunta.
 Kallan mamaki ya mata yace " Idanki biyu?"
 Murmushi ta saki ma tsantsar mugunta tace " Turab naji da ka fahimci na girmi uwarka, kaga alama ce ta ko ita bata isa taja dani ba, duk sanda ka nemi izinin durkusawa da bani hakuri lokacin zan saurareka."

 Tana gama fad'ar haka ta maida idanunta ta rufe, tsananin mamaki ya hanashi magana, kallanta yai cikin takaici yace " zan baki mamaki, wlh wahalar da mahaifiyata da kikai, zagin da kikasa a ka mata......"

 
Kasa karasawa yai jin an turo kofa.
 Abdulmajid ne, yana shigowa ya ce " malam yi waje ko? Tayaya ma Khadija zata barka kai kadai a ciki? In ka karasata fa?"


  Abu Turab ya kalleshi kamar zaiyi magana sai kuma yai waje.
 Khadija tana tsaye taga ya fito, kallansa tai cikin tausayawa, ko kallanta baiyi ba yai gaba.

  Kansa ya dafe cikin tsananin takaici. 
 Sabi'u ne ya nufoshi cikin hanzari.
 Yana karasowa gun Abu Turab ya kalleshi, kafin yai magana Sabi'u yace " Yarima ko zuwa zamuyi kuyi magana da Gimbiya? Na d'auko number data kira da ita muje dan Allah ka kirata, yanzun nan ta sa aka sake kirana tace ko magana ne a hadaku kuyi."

 Abu Turab yace muje to.

 Da yake akwai landline a bangaren Basira nan suka nufa.
 Sabi'u ya danna numbobin, bayan sun gaisa da wace ta d'aga yace " Gimbiya suke nema ga Yarima Turab din."
 Nan tace to.
 Ba'a dade ba Bilkisu ta amshi wayar.
 Nan ya mikama Abu Turab bayan ya gaidata.

 Abu Turab ya amsa, Sabi'u kuma ya fita.

 Shiru ne ya d'an ratsa kafin Abu Turab yace " kuna lafiya?"
 A hankali tace " naji abinda ya faru, ya Umman taka?"
 Mamaki ne ya kamashi dan baiyi zatan abinda zaiji daga gareta ba kenan.

 Bata jira amsarsa ba tace " ance bazaka samu damar zuwa ba."
 Yace " Bilkisu kinsan halin da ake ciki sannan Umma batajin dadi."

 Kai ta jinjina tace " na fahimta, Abbana yace zai sake tunani akan auranmu."

 Yasan hakan zai faru sai dai baiyi tunanin ji daga bakinta ba.
 Murmushi yai yace " Nasani dole ne hakan ya faru, duba da yanayin da muka shiga, ko nine mahaifinki dole ne na sake tunani akan auran."
 Jiyai tace " abinda yasa na kiraka shine inaso in tunama abu 2, kada ka bari wannan abun ya kwantar dakai, bansan meke faruwa a masarautarku ba sai dai nasan abu d'aya in har ka bari akaci galabarka a kan wannan abun banaji zaka farfado daga kuncin abin, zan duba ingani zan kuma sanar da Abbana akan mujira mugani in zaka iya warware matsalar nan daka shiga, na san zuciyarka dakakiya ce, zuciyace kuma ta 'ya'yan da suka kasance jarumai dan wannan dalilin ne yasa na aminta dakai, sai dai jin muryarka yanzu ya nunamin Mahaifiyarka itace lagwanka, inhar aka biyo ta bangaren Mahaifiyarka alamace ta angama cutar ka, an kuma rufema tunaninka da jarumtarka."

  Idanunsa ne suka canza daga kalar tausayawar da suke dazu, Murmushi ya saki yace " Nagode Bilkisu jin kalamanki yasa na fahimci dalilin dayasa aka biyo ta bayan mahaifiyata, dan ansan bazan iya yin komai ba, zuciyata zata raunana ta hanani tunani komai, ta sani cikin rudo da tausayawa."
 Zai sake magana yaji ta katse wayar.

 Ajiye wayar yai yabita da murmushi lalai Bilkisu jinin sarautace ta asali, har daga jin muryarsa ta fahimci abinda ya kamata ta fadamai? Mikewa yai ya nufi waje.

 Mairo wacce ta taho da magani ta ganshi.
 Ta d'auka xata ganshi cikin yanayi na tashin hankali.
 Kallanta yai yace " Mairo kin iso?"

  *43*


Mairo ta tsaya kawai tana binsa da kallo, kai yad'an lank'wasar kadan yace " Lafiya?wannan kalan fa?"

 Cikin mamaki ta amsa mai " Yaya Umma ta warke ne?"
 Kai ya girgiza alamar a'a yace " baki taho mata da ganin bane? Ko samu ne ba'ai ba?"
  Tace " to ko an gano gaskiya ne?"
 Kallan rashin fahimta ya mata yace " menene?"
 Tace " naganka ne kamar abin ya daina damunka, sannan idanunka suna d'auke da confidence."

 Murmushi taga ya sakar mata yace " ni kaina bansan ya akai ba bayan nayi wata 'yar karamar waya na samu kaina cikin wannan yanayin."

 Tana kokarin tambayarsa wace irin waya yai jitai yace " shiga ciki, inada abinyi."


 Kafin tai kokarin magaa ma yayi gaba.
 Komawa yai b'angarensa yai wanka ya d'auko kaya had'ad'u ya saka, shadda ce bugagiya light brown, yayi kyau sosai da sosai.
 In har ka ganshi to fa lalai zaka d'auka wani taro na mahimmanci zaije.

  Haka ya fito hankalinsa kwance, Garzali na ganinsa ya mike ya biyoshi yana tambayarsa inda zasu.
 Turab yace " Bangaren Umma Babba zamu."

  Bayan ya shiga ne yaga ragowar matan sarki da kuma matan kannansa a zazzaune suna gulmar abin, da alama dubiya sukazo suka bige da gulma.

  Ganinsa yasa kowa ya ja bakinsa ya tsuke, Abu Turab fuskarsa d'auke da murmushi mai sanyi ya gaishesu, haka kowa ya dinga amsa gaisuwar a kunyace dan sun tabbata yaji me sukace.

 Kowa sai dayai mamakin ganin yanda ya d'au kwalliya duba da yanayi da suke ciki.

 Kwankwasa kofa yai, Khadija ta taso.
 Tana tura kofar tai ido hudu da Abu Turab, tana rike da kofar take binsa da kallo, kallanta yai kallo na bege sai dai bayanda zaiyi, da sauri ta katse kallon da takemai tace " Barkanka da Zuwa."
 Ta karasa maganar tare da matsamai ta bashi guri.

 Magajiya ce a kwance kamar d'azu sai dai Abdulmajid na zaune a kasa yana cin abinci.
 Murmushi ya saki sannan ya kalli Khadija yace " nima zanci abincin."
 Da sauri Abdulmajid ya kalleshi dan da ya dauke kai dayaji muryarsa.
 Khadija ta kalleshi itakanta tayi mamaki sai dai amsa mai tai dato, tai waje.

  Abu Turab ya kara tura kofar ya shiga bakinsa d'auke da sallama.
 Abdulmajid ko amsa mai baiyi ba sai kallan mamaki da yake binsa dashi, wannam kwalliyar fa?

  Abu Turab ya karaso ciki ya zauna gaban Abdulmajid yace " Abdulmajid Barka da war haka."

 Bai amsa mai ba sai kallan mamaki da yake mai.
 Shima bai nemi amsar tasa ba Kallan Magajiya yai yace " Har yanzu Umman tamu bata farfad'o ba? Inata tsoro kar muje ta wuce ta can kasan matsalar guba akwai illa ta gaske."

 Yanda yake maganar kai kace irin Abokinsa ne Abdulmajid d'in.
 Abu Turab ya kalleshi yace " kayi shiru ko baka neman mata sauki ne?"
 Abdulmajid ya saki wata dariya ta takaici yace " duk duniya inda wanda zai fi damuwa da ciwon ta ai banaji ya kaini ko?"
  

 Jinjina kai ya shiga yi yana cewa " gaskiya ne kuma kayi magana anan, sai dai ni kaina ina mata fatan samun waraka, dan ciwonta duk ya hanani sukuni."

  Mamaki da takaici ma sam ya hana Abdulmajid magana. 
Abu Turab ya d'an furzar da wata iska yace " ta ina zanso Ummanmu ta gangara bayan ko bikina da Gimbiya Bilkisu bata gani ba? Sannan Bata ga d'anta akan mulki ba?"

  Ba shakka wannan kalma ta hawa mulki ta konama Abdulmajid rai, cikin zafin rai ya mike a zuciye ya kaima Turab naushi a kunci, wamda hakan yazo da daidai Khadija ta shigo d'auke da abinci.

 Tana ganin Abu Turab ya fadi ta saki abincin tai gunsa da gudu.
 Kallansa tai cikin tsananin kulawa tace " Yaya sannu."
 Sannan ta d'ago ta kalli Abdulmajid cikin takaicin abinda ya aikata tace " Yaya kana hauka ne? Ta yaya zaka nausheshi?"

 Idanu Abdulmajid ya zaro yace" Khadija? Ni kike fadawa haka?"

 Idanunta ya rufe gaba d'aya cikin masifa tace " an fadama, tayaya zaku dinga abu sam ba tunani? Me ya Turab ya maka? Dan yazo duba Umma? Ko dan ana zargin Mahaifiyarsa?"

 Wannan kururuwar tasa mata dake zaune a falo leko d'akin dan dama Khadija bata ko rufe kofar ba.

 Abu Turab ne ya sauye fuska zuwa yanayin tausayi yace " Khadija ki bari menene hakan kike yi?Laifine in yaya ya hukunta kaninsa?"

  Kallansa tai cikin tsananin tausayawa idanunta sun ciciko da kwalla, tace yaya kalli gefen bakinka fa? Ya fashe."

 Magajiya dake kwance tana jin duk abinda ke faruwa jitai zuciyarsa kamar zata fashe ba shakka sai taci mutuncin yaran nan.

 Abdulmajid ganin yanda Khadija take ma AbuTurab hawaye yasa ma ya kasa magana, tsawa ya buga mata yace " ke dam gidanku fita daga  nan."

 Kallansa tai fuskarta a turbune cikin tsananin bacin rai, Abu Turab yace " fita mana."
 Juyawa tai cikin takaici ta nufi kofa, ta na fita tai gida, tana tafe tana hawaye.

 Magajiya data d'auka Khadija ta fita sannan ba kowa a d'akin kenan sai Abu Turab da Abdulmajid ta mike cikin kunar rai zatai magana.


 Idanunta ne ya sauka akan matan dake labe jikin kofar d'aki, suma kallanta suke cikin mamaki.
 " Laaa Magajiya ta farfado."

  Nan suka shigo ciki, Abdulmajid ya runste ido na takaici sannan ya kalli Abu Turab.
 Gani yai Abu Turab ya sakar masa murmushin rainin hankali.
 Mikewa yai yace " Umma kin farfado? Kin ganeni?"

  Wani irin kallan tsana da takaici takaima Abu Turab dan gaba d'aya ya wargaza mata shirinta ita dataso sai an ma Basira hukunci mai tsanani kafin ta nuna musu ta farfado? Sai an d'auka ta kusa mutuwa tukunna?

    Kowa murna ne ya bayyana a fuskarsa, Abu Turab ya sosa keya yace " Lalai na yadda Mai maganin nan ya iya bada magani daga bata yanzu har ta warke?"


 Kallansa sukai cikin mamaki sukace " Yanzu ka kawo mata?"

 Kai ya d'aga alamar eh sannan ya kalli Abdulmajid yace "ko yaya?"
 Abdulmajid bakim ciki yasa kawai ya d'aga  kai , nan suka fito cikin tsananin farin ciki.

 Suna fita Magajiya ta kalli Turab kallan Takaici tace " kai bazaka tafi ba? Uban me kake jira kuma?"
 
 Fuska ya canza yace " Umma ina kikeso inje bayan yanzu kika farfado ke kanki ai bazaki so d'anki ya barnan ba."

  Kallansa tai tace " mene?" Yace " abinda kikaji nace, ni ai yanzu tunanin dawowa kusa dake nake yu saboda na kula bakyasan nai nesa dake."

 A zuciye Abdulmajid ya fizgoshi yace " kai wai kanka ko ya zare ne?"

 Hannu Abu Turab yasa ya tureshi da karfinsa sannan ya nunashi da yatsa yace " Gargadi ne zan maka shi ka tsaya kajini dakyau, yau inaso ya zama rana ta karshe da zaka kara gigin tabani, wlh duk randa ka sake ina sanarma da duk abinda ya biyo baya kai kuka da kanka."

 Sannan ya kalli Magajiya yace " Umma ya kike jinki? Kina farin ciki da dawowa duniya da na taimaka miki kikai da wuri?kinga yanzu kafin na fita d'aga nan zance zai kaiwa mutane na maganin dana baki kika warke da kuma wulakantani da Abdulmajid yai dan nazo baki magani."

 Ya d'an langwab'e kai yace " ya kika gani Umma? Puzzle din ya shiryo ko?"

  Ta cika taf dan kawai wani kallo takemai, Abdulmajid ma ya gama cika, juyawa yai ya fara tafiya har ya kusa isa kofa sai kuma ya juyo yace " ahhhh ina tayaki murna Umma dan Gimbiya Bilkisu bata yadani ba akan wannan al'amarin, na gode da kara bani karfin gwiwa da kikai na auranta."


  Yana kai nan yai waje.

 Magajiya yana fita ta juyo ta kalli Abdulmajid cikin tsawa tace " fita."

 Waje yai yana fita ta ta kama bargon da aka lulubeta dashi ta matse da karfi kai kace juyemai bakin cikin takeyi.

  Bangaren Mai Martaba ya nufa.
 A hanya yaga Jakadiya tana ganinsa ta iso da sauri tace " ikon Allah ashe yarima kaine ka samu mata magani? "

 Bai tanka mata ba saidai yana tsaye.
 Tace " hmm gaskiya ne amma nikam yarima banso ka cece ta ba Kana ganin halin datasaka mahaifiyarka a........."
 
Katseta yai yace " Jakadiya, in zaki fadi abu ki fada amma banasan zancen gulma."

 Ya juya yai gaba.

 Zance ya yad'o a masarauta akan Abu Turab shine ya nemi mata magani, ba shakka in har mahaifiyarsa ce take neman kasheta bazata taba yarda d'anta ya nemo mata magani ba, wannan labari yasa mutane dayawa sun canza zargin su na cewa Basira ce ta bata gubar nan.


  Zaune yake a gaban Mai Martaba, Sarki yace " Ka kawomin shaida ne?"

 Abu Turab yace " a'a sai dai na rage zargin da akema Ummana."

 Yace " kana tunanin wannan ya isa?"
 Kai ya girgiza alamar a'a yace " sai dai zai rage zagi da gulmar da ake mata, gaskiya kuma zan bayyanata ko ba yanzu, na kula in nace zan nemi gaskiya yanzu bazan taba samun komai ba dan na tabbata Magajiya ta riga ta gyara komai."

 Sarki ya jinjina kai yace " na fahimceka."

  Abu Turab yace " sannan maganar Gimbiya  Bilkisu." Ya karasa fadar sunan yana susa keya.

 Sarki yace " inajinka."

 " Dama ina ganin zan shiga gunta karshen satin nan."
 
Murmushi mai Martaba ya saki yace " Naji dadi da fahimtarka da kuma amincewarka Allah ya kaimu karshen satin lafiya."

 Abu Turab yace Ameen.


*TEAM ABU TURAB ??*



  *44/45*


       Mikewa Magajiya tai daga kan gado cikin tsananin takaicin abinda Turab ya mata, abin haushi jitai baiwarta tana sanar da ita isowar baki dan tayata murnar warkewarta.

  Haka ta bada umarni suka shigo, kan gado ta koma ta zauna, kowa yazo tayata murna sai ya jinjinama Turab da kokarinsa wannan abu yafi kular da ita, wasu dan gulma ma so suke suji me ya had'a Abu Turab da Abdulmajid.

  In taji haka sai dai kawai tace " zancen mutane ne kawai amma su ba abinda ya had'a su."

  Sai wajen Magrib ta samu sauki tai wanka ta sa kaya sannan ta aika a kira mata Hisham.

 *******

   Mairo kuwa bayan ta ba Umma magani nan ta dafa mata abinci ta bata taci, suna zaune labarin abinda ya faru ya isomusu, wannan labari yasa Umma dan jin dama dama.
 Mairo kuwa jitai Abu Turab ya kara birgeta, ba shakka jinin sarauta ma yawo a jikinsa, ba shakka kwakwalwarsa da basirarsa tana aiki.

   Sai wajen Magrib ta baro bangaren, Basira nata mata godiya, tana tafe tana murmushi dan ba shakka hankalinta ya kwanta da abinda ya faru.


  Sam bata kula da shi ba tadai san ta wuce wasu daga gefenta sai dai bata san su waye ba.
 Tana tafiya kawai taji an cafko hannunta ta baya.
 A tsorace ta juyo, dan sai da gabanta ya fadi lokacin daya rikota.

  Kallan mamaki da takaici ta sakar masa, sannan ta kalli hannunta tace " Malam sakeni ko"
 Yace " ina san magana dake."
 Tace " To dan kanasan magana dani sai akace ka rike min hannu? Sakeni tun kafin mutane su gamu."

  Ga mamakita gani tai ya kara kankame hannunta yace " kina tsoron aganmu ne?"

 Kokarin kwace hannunta ta shiga yi tana cewa " meye hakan?"

 Abdulmajid ya matso daf da ita kamar zai rungumeta tsoro yasa tai baya, karfi yasa ya rikota, cikin murya mai kama da rad'a yace " zaki biyoni ko sai na rungumeki anan?"

 Idanu ta zaro ta cigaba da kokarin kwace hannunta.
 Murmushi ya sakar mata yace " Gimbiyata muje ko?"
 Ya karasa maganar tare da sakar mata hannu sannan ya nuna mata hanya.

 Harara ta makamai sannan tai hanyar daya nuna mata.
 Bangarensa ta nufa da ita a tsakar gida taja ta tsaya tare da hard'e hannayenta.
 Kallanta yai yace " muje mana."
 Tace " muje ina kenan?"
 Da kai ya mata alama da ciki.
 Harara ta kara makamai tace " d'ad'in abin ni d'in da hankalina bawai a bola ka ganni ina tsince tsince ba."

  Dariya yai sannan yama masu kula dashi alama da su fita.
 Suna fita ya fara matsowa inda take, hannu ta d'agamai tace " dakata daga nan Malam ko kuma wlh insama ihu."

  Yace " Wayyo da naji dadi, ni ai so nake kisamin ma ihun kinga duk abinda za'ayi na riga na mallakeki kenan dan Sarki zai sani auranki saboda rufin asirin mahaifinki."

  Kallansa tai kallan tsana tace " wai dan Allah in tambayeka? Ana so dole ne?" Sai kuma ta girgiza kai tace " bama haka ya kamata ince ba, dan ba so na kake ba."

  Yace " Mairo abinda zakice kenan? Wlh tunda nake a duniya kece mace ta farko da zuciyata take so, inaji a raina in har ban aureki ba to tabbas zan shiga wani hali."
 Baki ta tabe tace " da alama bada gidan sarauta ka dace ba da d'an siyasa ka dace, to ni ko soyayyar ce nace banayi, ko anayi dole?"

  Kallanta yai sai dai yanzu fuskarsa ta nuna alamun jin haushin kalamanta.
 Mairo tacigaba " Akwai wanda nake so, banaji akwai wani karin bayani dakake nema daga bakina."
 Tana fad'ar haka ta juya zata fita.
 Da karfi ya jawo hijab dinta, jikin bango ya sata, idanunta ne suka firfito. ya kalleta ransa a bace yace " badai wanda kike so d'in a gidan nan yake ba?"

Kai ta juyamai bata bashi amsa ba, cikin takaici ya kara cewa " badai wanda kike so sunansa Abu Turab ba?"

 Juyowa tai ta kalleshi tace " koma wanene wanda nake so d'in banaji yazama dole na sanar dakai."

  Hannu yakai kamar zai kifa mata mari dan har ta rintse idanunta, sai kuma taji shiru, a hankali ta bud'e idanunta.
 Kallansa tai, hannunsa ya ajiye sannan yace "Mairo ko duk duniya zasu had'u dan ganin ban aureki ba wlh sai dai kowa yayi ya gaji, amma wlh nine mijinki, inkuma harni Abdulmajid ban aureki ba to wlh duk duniya ba namijin daya isa auranki sai dai in bana dorar kasa."

  Kafin ta nemo amsar da zata bashi gani tai yayi ciki.
 Da kallo ta bishi tama rasa me zatace.
 Haka ta fito jiki a sanyaye.

 Jakadiya wacce tazo wucewa dan ta dawo daga duba magajiya ta hango Mairo ta fito daga bangaren Abdulmajid, kai ta gyad'a tace " abin harya kai haka?" Dan dama an sha kawo mata gulmar an gansu.


  ************

  Hisham zaune a kilisar Magajiya shi kadai, sai dai kana ganinsa kasan tunani yakeyi.
 Magajiya ce ta shigo cikin takunta.
 Ta karaso ta zauna sannan ta kalleshi tace " Yaya na d'auka na sanar dakai umarnin mikewa in har zam shigo guri ko?"

 Kallanta yai yace " tuba nake Magajiya hankalina ne ya tafi."
 Girarta ta d'aga sama tace " a kiyaye."

 A ransa yace " ki jira hawan Abdulmajid mulki, lokacin ne zan kiyaye."

 Kallansa tai tace " Abu Turab ya wargaza mana shirinmu na hukunta uwarsa."

 Hisham yace " ni kaina abinnan ya kona mun rai."
 Murmushi tai tace " Abu Turab! Abu Turab! Lalai na yadda jinin Abdussamad na yawo a jininsa, dole ne in zamuyi shiri na gaba sai mun shirya yanda ya kamata."

  Kallanta yai sannan yace " ni Magajiya ina ganin kawai mu mikashi kabarinsa."

  Wani kallo ta bugamai tace " na d'auka na fadama ba kisa ko?"
 Yace " haka kikeso to muyi ta yin shiri yana wargaza mana?har sai yaushene zamu d'aura Abdulmajid akan mulki? Sai mun tsufa? Ko......"
 Tsawa ta daka mai tace " YAYA!

 Kallanta yai tare da yin shiru, tace " kana tunanin ni Magajiya? Ni Gimbiya Magajiya wacce mulki da takama da isa suka bi jinina, kanaso kace ni wannan Magajiyar har wani yaro wanda na girmi uwarsa, wanda aka haifa kwanan nan zaici galaba akaina?"

  Kasa yai dakai yace " Tuba nake ranki ya dade, ni din wa? Ina na isa ince haka? Kawai dai gani nai mutuwarsa tafi sauki."

  Idanu ta juya tace" to nace banda kisa, sannan ina tunanin ya kamata Saifullahi ya kawo kudin gaisuwa, in har bamu isa raba Turab da Bilkisu ba dolene mu nemi wanda yakeda mukami a gomnati saboda kudi dan neman taimako nan gaba
"

  Hisham yace " to Ranki ya dade angama."


  Mikewa yai ya fito, yana fita yabi d'akin da harara yace " wlh zakisan ni kikema tsawa, duk 'ya'yan da kike takama dasu na waye? Daga khadijan har Abdulmajid d'in?


    Kiyi ki gama wlh sai nima na gasa miki aya a hannu, wa kike dashi? Wa kike dashi da zai taimakeki? Harni zaki dingama tsawa? Harni zaki ce in mike dan zaki shigo?"
 Kwafa yai
   Magana ta lafa a gidan Sarauta,u . juma'a yau kuma Abu Turab ya shirya shida Sabi'u dan zuwa garin na Kano.

  Mai Martaba yasa ank

   Sabi'u kamar jira yakeyi su shiga mota, suna shiga ya kalli Turab yace " Mutumina wai ta yayo maka? Gaskiya ka birgeni da ka nuna mus

  Abu Turab ya dafa kafad'arsa yace " baka kawo komai a ranka ba da akacema nine na kawo mata magani?"
 Cikin rashin damuwa yace " sosai ma, abu d'aya ne yazomin na tabbas kai ba ruwanka."

 Murmushi Abu Turab Yai yace " then it's okay."
  Sabi'u yamai kallan mamaki yace " ban gane ba? Ba kai kakai mata magani ba?"
 Nine mana.
 Sabi'u yace "yauwa sannan dan Allah inada tambaya, wai wannan yarinyar menene tsakaninku?"
 "Yarinya? Wacce kenan?"
 Fara tuki yai yana cewa " yarinyar gidan Waziru wacce da na d'auka ni take kallo, sai daga baya na fahimci kai take kallo tun kafin idanun ka su dawo gari."

 Kallansa Abu Turab yai sai dai ya kasa cewa komai dan tabbas kasan zuciyarsa begen Khadija yakeyi, dan ranar ya tabbata da b'acin rai ta tafi.
  Duk yanda yaso ya tsani yarinyar abin yaci tura.
 Sabi'u ne ya kalleshi, gani yai Abu Turab yai saurin maida kallansa jikin window.
  Sabi'u yace " yauwa Khadija, na tuno sunan dai sai dana tambaya saboda gulma dake cina."

 Abu Turab ya kwantar da kansa jikin kujera ya lumshe idanunsa yace a hankali yace " wacce ya kamata in tsana, sai dai a duk lokacin dana b'ata mata rai nakejin zuciyata na zafi."
  A hankali yai maganar wanda Sabi'u sam baiji ba yadai san magana yake sai dai bai san jeyake cewa ba, hakan ne yasa yace " me kace?"

 Abu Turab  bai bud'e idanunsa ba yace  " bakomai."
  A zuciyarsa yace " Allah ka cire mata sona, bazan taba addu'a ko dana sani akan san da nake mata ba, dan ko da ace za'a maida hannun agoggo baya na tabbata i will fell for her, i will always pray for her happiness."

  Sabi'u ganin kamar bayasan magana yasa yad'an yi shiru, can yace " Mutumina ni daga waya ne kuka dinke da Gimbiya Bilkisu ne?"

  Abu Turab ya bud'e idanunsa yace " kaidai kanasan kaji gulma, koma me mukai menene damuwarka?"

 Sabi'u yai dariya yace " wlh kayi babban tunani, kun bala'in dacewa da Bilkisu, tun randa na ganta na san ....."
 "To malamin had'aka na sanjin gulmar soyayyar da bata shafeka ba, wai ni Sabi'u kai yaushe zakai aurene?"

 Turab ya katse shi daga maganarsa.
 Sabi'u yai d'an ajiyar zuciya yace " lafinka ne da ka rufe kofa, ai da ka bari an ma kanwa da ba haka ba."

  Turab ya girgiza kai kawai baice komai ba, sai murmushi kawai dayai.
 Sun d'anyi niss ba tare da kowa yace komai ba, can kuma Sabi'u ya d'an cigaba da jansa da hira haka jefi jefi.
 Bayan sun isa garin kano, Mai Martaba Sarkin kano yasa an gyara musu b'angaren da suka zauna waccan karan.
 Shamaki yazo ya musu iso, sai daya tabbatar an kawo musu komai na bukata sannan ya tafi.

 **********
 A zariya kuwa Magajiya zaune a d'aki, Abdulmajid na kasanta.
 Cikin muryar takaici take cewa " Abdulmajid wato kai bakada kishi ko? Bakasan darajar kanka ba ko? Kana kallo Abu Turab ya tafi kano gun Gimbiya Bilkisu amma kai ko a jikinka, wai me yasa ne sam kwanan nan baka abinda zai amfaneka?"

 Fuskar Abdulmajid a had'e yace " Umma to ya kikeso nayi? Kina gani dai Mai Martaba ya fifitashi a kaina, in ba haka ba ta yaya banyi aure ba ya nema ma kanina aure?"

 Magajiya ta mai wani kallon takaici tace " wannan matsalarsa ce, duk da inada takardar da take na shaidar amincewa da yardarsa akan kaine zaka gajeshi sai dai a koda yaushe zuciyata da hankalina sun kasa kwanciya, nasan Abdussamad sarai zai iya yin yanda takardar zata zama bata da amfani nan gaba, dan haka dole ne mu nemo ma mata kaima wacce take 'yar mulki."

 Abdulmajid ya d'ago da sauri yace " Umma ki taimaken ki bar zancen wannan auren na 'yar mulki, ni Mairo nake so 'yar gid.
...."
 Kamin shiru ko sai na kifa ma mari? Kana tunanin na sha guba saboda inji wannan shirman naka ne?

  Shiru Abdulmajid yai kansa na kasa.
 Ta cigaba " inasane da duk fa abinda kakeyi a gidan nan, kar in kuskura in kara ji ancemin ma anganka da wannan yarinyar."
 Abdulmajid ya d'ago ya kalleta idanunsa yai ja yace " amma Umma bakya gani auran Mairo zai taimakeni? Kinfa san yanda Mai Martaba yakesan  Barde bakya tunanin zaiji takaicin rabasu?"

 Kallansa tai sannan tai murmushi tace " Lalai Abdulmajid da gaske san Mairo kakeyi, tunda har tsarani kakeyi, to ni nace banaso."

 Fuska ya had'e sannan yai kasa da kansa.
 Wani kallo tamai tace " tashi kaban guri."
 Mikewa yai ca sauri kamar dama can jira yakeyi.

 *************

Gimbiya Bilkisu tana zaune b'angaren Fulani, lale aka sa mata tana jiran yaci.
 Munnira ta shigo da gudu tacemata "UmmaBilkisu ya iso."
 Sam bata kula da Fulani ba bata kuma kula da Bilkisu dake ta mata alama datai shiru ba.
 Tana gama fadar haka ta kalli Fulani da sauri ta tsuke bakinta tace "Inna Barka da warhaka."
 Ta karasa maganar tana zama a gefen Bilkisu.
 Bilkisu ta harareta sannan tace " Munnira Muhsin d'in ya iso?"
 Sunan kanin Munnira ne, Munnira ta kalleta alamar rashin fahimta.
 Bilkisu ta harareta hakan yasa tai saurin cewa " ya iso."

 Fulani ta saki murmushi tace " Bilkisu ayi maza a cire lale aje a kimtsa kafin Muhsin ya iso, yo dama ai nasan domin Muhsin akai lalan nan."
 Ta karasa maganar tare da mikewa tai ciki.

 Bilkisu ta rufe fuska da bayan hannunta dan tasan Mahaifiyar tata ta fahimci me suke nufi.
 Tana shigewa, Bilkisu ta harari Munnira tace " Ba wakafi ba alamar tsayawa, baki kalkalkal ya iya wassafa zance, wai ke in kina magana bakya kula da mutanen dake zaune ne?"

 Baki Munnira ta turo tace " Ni murna ne yasa wlh sam ban kula ba."

 Bilkisu ta kara harararta tace " murna? Dan kina murna sai kisa a gane komai?"

 Munnira ta turo baki tare da kumburo fuska, Bilkisu tace " na daina ma had'awa dake."

  Munnira tai kamar zatai kuka, Bilkisu tace " jeki ki duba to kiga ko akwai wani abu da suke bukata."
 Munnira cikin zakwad'i ta mike tai waje.

 Bilkisu tai murmushi tare da yin kasa da kanta.


   **************

   Abu Turab yai wanka sunyi sallah sannan suka zauna cin abinci, Sabi'u ne yace " Turab jiya ai munsha hira da Babanmu, na tausaya ma Mahaifinka wlh."
 Turab ya mai kallan tambaya, sannan yace "name?"
 Sabi'u yace " ya dade bai samu haihuwa ba, har fa ya fitar da rai da samun haihuwa."
 Abu Turab ya kalleshi sai dai baice komai ba.
 Sabi'u ya cigaba " Magajiya fa har kasashen waje ta fita saboda neman magani amma ba labari, sai daga baya kawai akace ciki gareta, kumafa inaji sai da cikin yakai wata 3 sannan inaji itama ta sani."

  Kallan sa yai cikin rashin kulawa yace " lalai."

 Sabi'u yace " kasan abin dariya?" 
 Abu Turab  ya kalleshi.
 " duk fa farko wai mutane dayawa basu yarda da cikin ba, harshi Mai Martaban."

 Abu Turab ya kalleshi yace " ban gane ba."
 Sabi'u yace " kasan Magajiya kowa yasan yanda takesan ta haihu shi yasa mutane sukai ta zargin ko ta fadane ba wai gaskiya bane."

  Abu Turab ya mike yace " Lalai, kace sai da ta haihu suka yarda." Yai maganar cikin salon rashin damuwa da kuma gamsuwa da labarin.
 Sabi'u yasa dariya yace " shiyasa randa aka haifi Abdulmajid ai anyi murna wai kamar ba gobe."
 Baki Turab ya tabe a ransa yace " ni kuwa sanda aka haifen mutane fiye da rabi bakin ciki sukai, wasu ma tunani hallaka jaririn yaron sukai."


  Ciki ya shiga dan zuciyarsa ta karaya da tunowa da wahalar da mahaifiyarsa tasha.

  Kwafa yai daya tuna sharrin da suka ma Mahaifiyarsa, tabbas dole ne ya sa tun a duniya a hukuntashi.

  Mikewa yai ya d'auko turare ya fesa ya sa hularsa ya d'auko takalmi ya saka, yayi kyau sosai da sosai.
 
 Yana fitowa Sabi'u yace " kai Ango, gaskiya yau inaji sai na rufe kofa dan banaji Gimbiya zata barka ka taho, ko dai in aikama da bargonka can ne? Dan banaji ana san rakiya ta."
 Turab ya kalleshi yace " ba sai ka aikp da bargo ba itama ai tana dashi, d'an rainin hankali, ni taso muje karakani."

  Sabi'u ya mike yana dariya........


 ***********
 A can gidan Waziri kuwa Khadija tun ranar ko waje bata sake yi ba, kullum tana d'aki, abin duniya ya daneta, takaicinta d'aya yanda zuciyarta ta matso dasan ganin Abu Turab.

?? *TEAM ABU TURAB


  *46*


     Jakadiya ce tazo dan kaisu inda aka tanada dan ganawarsu, an kayata gurin sosai, gun kamar rumfa yake, salo da kayata gun da akai duk yanda kaso da karka nuna sai gun ya burgeka.
 Gashi sai hayaki na turaren wuta ne ke tashi.
 Sabi'u cikin mamaki yake kallan gun ya kalli Turab wanda shikansa abin ya kayatar dashi yace " Kai gun nan ya burgeni, amma dai ba dan kai aka shirya gun nan ba ko?"
 Abu Turab ya kalleshi yace " kai kuma sarkin zuga zugi, to kardai ka wuce makad'i da rawa."
 
 Sabi'u ya kara shan mamaki ne a sanda yaga yanda aka saka irin carpet da 'yan tumtum a gun sannan aka jera kayan ciye ciye kala kala, ya jinjina kai yace " Turab da alama gaisawa kawai zamuyi da Bilkisu banaji anyi wannan shirin dan mu biyu."
 Cikin gatse Turab yace " Gaisuwar ma sai ka hakura."
 Sabi'u yace " ahh lalai Turab abin ba kara? To bari inje waje in tsaya in yaso in kungama ganawar na shigo daga baya mu gaisa."

  Turab kai kawai ya girgiza, ya juyo da niyyar mai magana yaga bayanan.
 D'an tsaki yaja kad'an yace " Sabi'u kenan."

  Zama yai a gun da aka shirya dominsa, irin zama na manyan 'ya'yan Sarki.

  Sai dayai minti 15 da zama sannan wani dadadan kamshin turare ya bugi hancinsa.
 Cikin isa da takama take takowa, tafiya takeyi irin ta kasaitatun mata masu mulki.

  Bai d'ago ya kalleta ba haka itama ko data shigo kallo d'aya ta masa ta cigaba da takunta.

 Har sai da ta iso gun da zata zauna sannan ya d'ago ya kalleta, itama a lokacin ta kalleshi.

  Tabbas yarinyar tana da kyau, balle yau datai shiga mai kyau sosai sannan tai kwalliya haka, wani sansanyan murmushi ta sakar masa, shima murmushin ya maida mata, a hankali ta zauna sannan ta umarci bayinta dasu fita.

  Shiru ne ya ratsa gun kafin cikin muryarta mai dadi tace "Barka da isowa Yarima Turab."

 Kallanta yai cikin yarda da amincewa yace " Barkanki da isowa Gimbiya Bilkisu."

 Murmushi tai sannan tace " ka dade a zaune ko?"
 " Ya zama dole ai in jiraki tunda haka tsarin yake, sannan ba wani dadewa nai ba."

 Bata ce komai ba sai shiru da suka sakeyi.
 Kanta na kasa, batai zato ba sai jitai yace " Bilkisu." Yanda ya kira sunanta sai dayasa taji wani yarr a jikinta.

 D'agowa tai a hankali ta kalleshi idanunta sun canza zuwa salon soyayya, murmushi yai yace " Naji dadi da yanda kika amince da ni."
 Idanunta ta lumshe sannan ta bud'esu.
 Yacigaba  " ban taba zatan zaki yarda dani ba haka, duba da rashin sani na da kikai, tunda haduwarmu d'aya dake."

 Nan ma idanunta ta kara lumshewa ta bud'e, yace " A wannan lokacin na sa ma raina tabbas zaki zama mace ta gari a gun duk wanda kika aura, sannan na yaba sosai da yanda kike da tunani."

 Murmushi ta saki sannan ta maida kanta kasa, hannayenta ta had'e gu d'aya tana murza zoben hannunta da d'aya hannun.

 Harya d'auka bazatai magana ba sai jiyai tace " I can feel the pain that hide behind ur smile Turab."

  D'agowa yai ya kalleta sai dai jikinsa yai sanyi, kallansa tai tana murmushi tace " me zakace game da ni?"

 Kallanta yai kallo mai alamar tambaya. 
  Kanta ta d'an karkatar tace " ka taba sanin Fulani ba ita ta haifen ba?"

  Idanunsa ne suka fifito alamar mamaki, Tace " bansan ta ba, bansan ya kamanninta suke ba, tana haifata a gun Allah ya mata cikawa."

  Tausayinta ne yaji ya kamashi.
 Idanunta ne suka d'an ciciko tace " karka kallan da fuskar tausayi  Turab, i am okay, tunda dadewa na cire san ganinta a raina, sannan ina ganin in har na nuna damuwata akan mahaifiyar data haifen ya Fulani wato mahaifiyata ta yanzu zataji?"

  Turab ya kura mata ido yana nazarin kalamanta. Can yace " U are indeed a good woman, sai dai jin zancen nan naki yasa na fara tunani ban kai qualification na aurenki ba, kin cancanci saurayin da zai soki kamar ransa wanda zai kula dake har rabuwa ta rai ta zo."
 
  Hannu tasa ta goge hawayen daya d'an gangaro ta kwarmin idanunta tana murmushi tace " kai bakada confidence na sona kamar haka?"

 Jitai yayi shiru sai dai yanayin kallan da yake mata ya canza, kallansa tai tace " Me kake nufi?"

 Yace " Bilkisu inada abubuwa da dama a gabana wanda sai na ga sun kammala ne hankalina zai kwanta, banida lokacin soyayya ko farin ciki sai na ga mutanen nan an musu hukunci."

  Shiru yai dan tuno abinda aka ma Mahaifiyarsa.

  Baiyi tsamani ba bai kuma ji alamun tasowarta ba sai gani yai ta mikomai kofi.

 Kallanta yai idanunsa sunyi ja, sannan ya kalli kofin ruwa ne a ciki alama tamai da kai akan ya amsa.
 Hannu yasa ya amsa yana murmushi, yace " sry......"
 Katseshi tai tace " naji dadi."

 Fuskarta d'auke da murmushi tace " naji dadin yanda ka nunamin, yarda harka ke sanar dani hakan."

 Kofin ya ajiye bayan ya shanye ruwa ciki yace " Bilkisu i....."
 Kara katseshi tai tace " is okay, na fahimceka, na kuma san tabbas akwai wahalhalu da kasha ko fansar wani abu da kake san d'auka, sai dai inaso in taimakeka gurin d'aukar wannan fansar, bazan nemi soyayyarka ba har sai ka kammala abinda zakai, sai dai kaima bazan yarda kaso wata ba har zuwa wannan lokacin, in kuwa har da wacce kakeso yanzu inaso ka ajiye soyayyar a iya kacin zuciyarka harsai ka gama aiwatar da abinda zakai, a wannan lokacin ne nakeso ka tambayeni abu d'aya."

 Idanunsa na kanta tacigaba " inaso ka tambayeni in har banyi dana sanin auranka ba, in har nace ma banyi dana sani ba to inaso ka tirsasa zuciyarka ta soni in har aka kai wannan lokacin baka sona, in kuma har nace nayi dana sani inaso ka tambayeni abinda nakeso a wannan lokacin."

  Tana gama fad'ar haka ta koma ta zauna sannan ta d'ago ta kalleshi tace "  Deal?"

  Bai san sanda wani murmushi ya bayyana a fuskarsa ba yana murmushi yace " Deal! sannan naji dadi da kalamanki, ba saki a tsarin aure na ko da shi kike tunani a karshe sannan yanda kika amince dani ba tare da kinji abinda nakesan aikatawa ba, zanyi kokari wajen ganin bakiyi dana sanin aurena ba."


  A tare sukama juna murmushi nan tamai alama da hannu akan yaci abinda aka kawo masa.
 


     Tabbas tana bala'in san yaran nan, ko da kuwa zatai dana sani akan auransa bataji zata iya rabuwa dashi a wannan lokacin, sai dai ta d'au alwashin taimaka mai da tayashi d'aukan fansa akan duk wani wanda ya cutar dashi ko da kuwa zatai amfani da karfin mulki na mahaifinta ne.

 Kamar yasan me take tunani jitai yace " for using you, dole ne ma nemi yafiyarki, sai dai zan nemane in na gama komai, is that okay?"

 Kai ta jinjina mai alamar eh, ta bishi da kallo na so tsantsa.

  Bayan sun gama hira ne ya mata sallama sannan ya mike, har ya fara tafiya sai kuma ya juyo ya tako a hankali zuwa inda take.

 Awarwaro ya ajiye mata wanda suke cikin gidansu sannan cikin magana mai kama da rad'a yace " da kunyar badawa nakeyi, sai dai bani na siya ba Sabi'u ne ya siyo"
 Mikewa yai ya fara tafiya, kallansa tai tana murmushi tace " nagode."

 Bai kara magana ba yai gama yana murmushi.
 Tabbas Bilkisu ta samu daraja a idanunsa, yanaji zai iya zama da ita a rayuwar aure dan dama ya ma cire burin ganinsa da Khadija daga sanda yaji abinda mahaifinta ya musu ko da santa zai zama ajalinsa bazai taba yarda ya bakanta ran mahaifiyarsa akan 'ya mace ba.



  
  *47*


      Duk yanda taso ta danne zuciyarta ta kwanta ta kasa, mikewa tai ta zura alkyabbarta sannan ta kalli Mai kula da ita tace " yau kwanan waye?"
 Kasa tai dakai tace " naki ne ranki ya dade."
 Magajiya ta d'an d'aga gira sama sannan tace muje inasan ganin me martaba.
 Tayi mamaki sosai dan rabon da Magajiya taje turakar mai martaba da niyar kwana har ta manta.

  Haka suka fito suka nufi b'angaren Mai Martaba.
 Sunje shiga soro bangaren nasa sukaji ana gulmar Abdulmajid da Mairo, d'ayar tace " wlh jakadiya ce ta gansu da idanta yar gidan Barden ta fito daga b'angaren Yariman."
  Magajiya ta cusa kai suna ganinta suka rude a tsorace suka tsugunna sukace " Barkanki da zuwa Magajiya."

  Kallansu tai fuskarta dauke da iza tace " ina san dukanku kuje  bangarena ku jirani, kada kuma ku manta a tsaye nakeso kuntsaya har na iso."

  Kara runkufawa sukai suna neman bada hakuri, wani kallo ta musu da ya sa sukaja bakinsu sukai dif.

 Nan suka karasa ciki.
Jakadiya ce ta fito da sauri kana kallanta zaka gane abinci takeci ta taso.
 Wani banzan kallo Magajiya ta mata, da sauri tai rusuna tana gaisheta.
 Magajiya bata amsa ba sai alamu da ta mata na ta mata iso.
 Mikewa tai ta nufi b'angaren Sarki.

  Rubuce rubuce yake tayi, yana jin sallamar Jakadiya yai saurin had'e takardun nan ya sa a kasan carfet din da yake kai.
 Jakadiya ta shigo ta gaisheshi sannan ta sanar mai da zuwan Magajiya, alama kawai ya mata da kai akan ta shigo.

  Magajiya ta shigo ta zauna a inda ta saba zama, sannan ta kalleshi tace " Barka da dare Haikawa."

  Sarki ya amsa sannan yace " lafiya dai da daddaren nan?"

 Tace " ina tunanin yau kwanana ne? Banaji na cancanci inji wannan kalmar daga bakinka."

 "Kwana? A tun wani karnin kenan?"
 Murmushi tai sannan tace " Turab na garin Kano ko?"
 Kallan ta yai sai dai bai amsa mata ba, a ransa yace abinda ya kawoki kenan?"
 Murmushi ne ya bayyana a fuskarta tace " na yaba da d'ana Turab ba shakka yanada hazaka da tunani, ina kuma kara godemai da maganin da ya bani."

  Sarki ya jinjina kai yace " ai dama hakkin d'a ne ya kula da uwarsa, in har ita uwar tana neman cutar dashi to shi ya kamata ya nuna mata yana santa."

  Kura mai ido tai dan tasab magana yake gwab'a mata.
 Isakar ta d'an firzar kadan tace " haka ne, sai dai inaso uban d'an ya cigaba da nunama d'an nan hanyar dazai kula da mahaifiyar tasa."

  Murmushi Mai Martaba ya saki tare da d'an juya kai kad'an harzaiyi magana sai kuma ya fasa.
 Kallansa tai dan fuskarta cikin fara'a tace " yaushe zaka yima babban d'anka mata? Dan na tabbatar kanada babban buri akansa shiyasa ka kasa yimai cikin gaggawa
"
 Ya fahimci me takesan cewa hakan yasa yace " ni ai danayake na d'aura buri akansa shiyasa nai tunanin barinki ki nemomai mata."

 Fuskarta ta tsuke dan tabbas taji haushin maganarsa. 

 Takarda ta d'auko ta taso a hankali tazo ta ajiye mai agabansa.
 Kallan takardar yai yace " na menene?"
 Tace " tuni nake maka akan rubutu dakai na cewa Abdulmajid ne zai gajeka."
 Fuskar shi ya d'aure yace " sai akai yaya kuma?"

 Kallansa tai tace " ba abinda akai Takawa kawai dai ina tunatar dakai ne, saboda tsaru."

 "Tsaro? Kina tunanin wannan takardar kad'ai zata iya canza abinda ke zuciyata?"

 Idanunta ne suka canza ta kalleshi, yace " eh, kina tunanin ita zata canza min ra'ayi? In na ce bani nayi ba fa?"

 Kallan tsananin mamaki tamai sam tama kasa magana, murmushi ya sakar mata sannan ya kamo hannayenta yana shafa samansu yace " kin tab'a ji nace miki inaso in d'aura Turab akan mulki? Banaso kidinga zargin abinda bakiji daga bakina ba, ko warkewa bakiyi ba kin sa abinda bashida tabbas a ranki."

  Wani kallo tamai dan tabbas tasan bakar magana yake gaya mata a cukurkud'e, kai ta d'an rankwfo sai tin kuncinsa kamar mai shirin sumbatar sa sannan tace " ina fatan Takawa zai tsaya kan maganarsa."

  Juyowa yai inda bakinta yake hakan yasa bakinsu suka kusa sumbatar juna, wani lalausan murmushi ya mata yace " banaji na d'auraki akan mai bani shawara."

  Fuskarta ce ta canza hakan yasa ta mike tsaye, tace " Ranka ya dade zan koma."

 Alama ya mata da ido akan ga fili ga mai doki.

  Duk yanda kaso ka gane ranta a b'ace yake bazaka taba ganewa ba saboda fuskarta d'auke take da annashuwa.


  Jakadiya tana ganinta ta taho da sauri, Magajiya ta kalleta tace " biyoni."
 Haka kawai ta fada tai gaba.

  
  Haka jakadiya ta bita har suka isa b'angarenta ta wuce cikin d'akinta nan ma Jakadiya ta bita.

 Bayan sun shiga ta juyo tace " rufe kofar."
 Gaban Jakadiya ne ya fad'i ta tura kofar a hankali ya rage daga ita sai Magajiya.

  A jikin kofar Jakadiya ta tsaya tana tunanin abin cewa.

  A hankali Magajiya ta tako har inda take, fuskarta tayi bala'in canzawa zuwa tsananin b'acin rai.
 Tana zuwa kusa da ita ta d'aga hannu ta zubawa Jakadiya mari.

  Da yake sam batai zatan hakan ba jin marin yasa hankalinta yayi tsananin tashi.

  Kanta na kasa sai dai hankalinta ya tashi sannan takaici ya cikata, kamar ta?duk girmanta? A kalla ta tabbata taba Magajiya shekara 4 amma ko kunya ta sharara mata mari?

  Magajiya ta kalleta sannan ta ce " d'ago."
 Jakadiya ta d'ago sai dai yanzu ta dake tace " Mai na miki? Banaji nayi wani abu daya cancanci duka."

  Magajiya ta kanne ido tace " ke harkin isa kidinga yad'a gulma akan Abdulmajid? D'an nawa? Da alama kin gaji da aikinki. "

  Ran Jakadiya ya kara tunzura jitai tsoron da ke zuciyarta yakau ta kalleta tace " Magajiya d'anki fa kikace?"

  Gaban Magajiya ne ya fad'i ta juyo da sauri ta kalleta.
 Jakadiya ta daure tace " sharri na masa? Ki tambayeshi da kanki kiji wannan karan ya fara jan hannun Mairo zuwa b'angaren sa? Sannan maganar aiki da kikeyi ni da kaina zan sauka in lokaci na yayi, ina sanar dake hakan ne domin kar akaini bango dan zan iya sanarma Yarima Turab komai."

  Tana kai nan ta rusuna tace " Tuba nake Ranki ya dade in bakisa wani sakon zan koma kar Mai Martaba ya nemi ni."


  Gaba d'aya ma Magajiya ta kasa magana tana tsaye sororo har Jakadiya ta fita.

  Tana fita Magajiya ta saki wani kara na takaici tace " me yasa komai baya tafiya daidai? Dole ne na saita komai su koma yanda suke."





 
 *************

  D'agowa Barde yai hankali a tashe ya kalli Abdulmajid yace " Yarima me kake nufi?
 Abdulmajid yace " Mairo nakeso, kuma zan aura dan gobe nake shirin sanar ma Mai Martaba shiyasa naga ya dace in sanar maka a matsayinka na mahaifinta."

  Barde cikin rawar murya yace " na kasa fahimtarka ne ai, ta yaya kamar kai zakace kanasan Mairo? Ta yaya? Dan Allah Yarima kabar maganarnan anan."

  Abdulmajid  ya mike tsaye yace " zan jira a waje inaso ka turomin Mairo in ganta kafin na koma."

  Barde sam ya kasa yin komai tsaya wa yai sororo har Abdulmajid  ya fita.
 Mairo kuwa da yanzun nan Ummanta ta sanar da ita zuwan Abdulmajid ya sa ta shigo falon da gudu ko sallama babu tana shiga ta tsaya ganin Babanta.
 Jiki a sanyaye tace " Baba!"

  Kallanta yai a sanyaye yace " me nake ji Mairo?"

 Kai ta girgiza dasauri tace " wlh Baba ba haka bane, shi kad'ai yake kid'ansa yake rawarsa, kaima kasani Baba wlh ni......"

 Katseta yai da cewa " Me yasa baki sanar dani ba?"

  Hawaye na fara zubo mata tana girgiza kai tace " wlh na d'auka shirmansa ne, na kuma d'auka zai hakura tunda nace mai banaso."

 Mikewa yai yace " kije yana jiranki a waje, mayi magana daga baya, kije in har kinaso komai ya rabu
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *KAINUWA* A Historical Fiction* by Ayusher Muhd Gimbiya 1 15,759 08-21-2019, 01:53 PM
Last Post: Ebony Lacklock
  *JALILAH* by Ayusher Mohd* Gimbiya 0 20,165 09-10-2018, 09:03 PM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,758 06-16-2018, 10:17 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 6,907 06-16-2018, 10:16 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,349 06-16-2018, 10:09 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,717 05-07-2018, 11:04 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 4,309 05-07-2018, 10:54 AM
Last Post: Gimbiya
  *KAINUWA* by Ayusher Mohd Gimbiya 0 3,636 04-30-2018, 01:16 PM
Last Post: Gimbiya



Users browsing this thread: 1 Guest(s)