The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*KANO TO JIDDAH* by Zahra Muhammad Mahmud
#1
"zancanki gaskiyane,nasan in ta isa birnin jiddah,duniyar sama zata gyarata dakyau kamin tasata akasuwa,dan haka yanzu kije da ita amata e pasport,dan banaso suyi sati akasa batare da an aunasu can ba,kuma kinga ƙafarta akwai kaushi,ga kanta se tsami yake,ki kaita saloon akauda komai,dan kinsan halin duniyar sama batason akaisu ahaka"
Tafawa sukayi,sannan hajiya zaituna tace.
"naga yar sudan nanan dan haka in mun dawo daga saloon din zankaita can abata kayan mata,dan ta jiƙu dakyau sabida kinsan larabawan nan,basason suji rani,sunfiso kullum cikin damuna"
wata uwar shewa sukayi sannan hajiya zaituna tayiwa suhaima umarni data taso suje,ba musu suhaima tabita sabida bata gane manufar zancensu ba.
Gurin gyaran kafa da gyaran gashi takaita aka gyara suhaima,segata tafito fes da ita.
gurin pasport sukaje nanma akayimata.
Daganan gurin me maganin mata suka dire,nan taita ɗirkawa suhaima magunguna,akan dole suhaima takesha duk da batasan maanar su ba amman tanaji aranta ba abun cutarwa bane.
harda na tsugunawa seda suka mata,basu dawo gidaba se shaɗaya na dare.
Tunda aka kawo suhaima gidan,kullum ake koyar dasu salon tafiya,da karayraye karayraye,da fari da ido,kuma tsab suhaima dama yana daga nature ɗinta dan haka be bata wahala ba ta iya.
Ba kalar fitsarar da baa koya musu ba.
sati guda tsakani,jirgi ya ɗaga da su suhaima from kano to jiddah.
Dukansu a tsorace suke barinma suhaima dahar kuka tadunga yi na tausayin kanta.
Awar su huɗu asama,suka iso jiddah.
Dayake basu da wani kaya,basu sha wahalar komaiba,aka buga musu,stamp na shaidar sun shiga ƙasar saudiyya.
Suna fitowa,suka tarar da wata hamshakiyar hajiya wacce dagani duniya na gara mata,gurinsu ta nufa tana yatsina tace.
"sunana duniyar sama,ina fatan kune hajar danayo order?"
Dayake anfaɗa musu sunanta dan haka baki suka haɗa wajan faɗin.
"Eh mune"
"to ku biyoni"tabasu amsa,tayi gaba suka bita abaya zuwa gurin wata arniyar mota.
Dukansu suka shiga taja suka tafi.
Idon suhaima kamar ze faɗo sabida kalle kalle,a ɗaya ɓangaren kuma murna take zataga kabarin annabi da kuma ɗakin Allah,sabida tayiwa innarta addua.
Su suhaima manya,kowa ya faɗamata,a jiddah ɗakin Allah da kabarin Annabi suke oho.
wani katafaren gida suka shiga.
Wanda yagaji da haɗuwa,suhaima har faɗuwa tayi gurin kalle kalle.
Abinci aka basu,bayan sunci sunyi sallah,sannan, aka kaisu makwancinsu.
Sosai abun yaba suhaima mamaki ganin ɗaki ɗaya amman sunfi su talatin acikinsa,kowa da jakar kayanta.
Hira suka shigayi,anan suhaima taji ashe daga gari dabam dabam aka kawosu.
A hakade har bacci ya ɗaukesu dukansu,kowacce cike da kewar gida,bama kamar suhaima,da ita kaɗaice yar garinsu.
muje zuwa.
 
 
 
*11-12*
 
 
Gudu sukeyi,basu tsayaba seda sukaje jikin wani dogon gini,sannan suka tsaya kalle kalle.
 
Can suka hango wata mata wacce da gani sunsan yar nigeria ce.
 
Da gudu suka nufeta,sunaso ta taimakesu tamaidasu gida.
 
"Ayya na tausaya muku,amman kuyi hakuri inkaiku kuyi ayki tukuna seku,samu kuɗin jirgin komawa gida".
 
Cike da faraa,suka amince suka bita.
 
Dayake matar ita a makkah take,dan haka mota suka hau,daga jiddah zuwa cikin garin makkah.
 
Koda suka isa gidan matar,sunsha mamaki,domin shima cike yake da yanmata,yara da manya,sannan ga kekunan guragu nan kala kala.
 
Abinci tabasu sukaci,sannan takira wata halima tace mata.
 
"anjima inzaku harami,kutafi da wainnan,kinga zaa kara samun kuɗin sadakar"
 
sude su suhaima basu san manufarta ba.
 
Suna zaune,halima tazo da bandeji,tasa su suka dora hannayensu a kafaɗarsu ta ɗaure guiwar hannun da bandejin,sannan takawo kalar jini ta shafa akasan.
 
bame cewa ba yanke musu hannun akayiba,sude se kallon abun mamaki suke.
Mamakinsu be ƙaruba seda aka kawo musu keken guragu akace,su hau.
 
ba musu suka haye,wasu suka turasu zuwa harami.
 
Suna cikin tafiya,duk wanda yagansu se yabasu sadaka,ayko suna zuwa daidai,wani hotel,me suna land premiar,suka haɗu da yankame.
 
Suhaima se gani tayi,sauran sun kwasa da gudu,dan haka itama,sauka tayi akan keken,ta ruga da gudu,itako sajida kamin ta gudu har sun kamata,ihu take tana tsillewa dan batasan inda zaa kaitaba.
 
Suhaima leƙowa tayi daga inda ta boye,taga ansaka sajida a mota,fitowa tayi da gudu dan itama akamata,amman ina kamin ta ƙaraso sunja motar suntafi.
 
tsugunawa tayi agurin tanata rusa kuka,daga karshe tamike ta cigaba da tafiya tana share hawaye.
 
Dayake lokacin aykin hajji ne garin na makkah cike yake da baki.
 
Suhaima cigaba tayi da tafiya,har ta iso wani guri dataga jamaa da yawa se shiga sukeyi,kyan gurin da tsarinshine yasa suhaima shaawar shiga ciki taga kome ake gani.
 
Tana zuwa zata shiga da takalminta,taji wani megadin ƙofar yana faɗin,"haram haram"nuni yaymata data cire takalmi ba musu tacire,ya miƙo mata wata farar leda,tasaka aciki,sannan ta rike a hannu ta shiga.
 
Dayake gangarane,haka suhaima ta dunga tafiya kanta akasa,kamar ance ta ɗago kanta.
 
ALLAHU AKBAR.
 
Arba tayi da ɗakin Allah yayiwa sama rumfa.mutsike idonta tashigayi nason tabbatarwa ba mafarki takeba.
 
ay tunda taga dagaske shine seta fashe da kuka,t juya tafice zuwa waje tasha wahala kamin tasamu bahaushiyar data nuna mata gurin alwala.
 
alwala tayi tadawo,gurin kaaba.
 
Dayake batasan ya akeyiba,ita gurin kaabar kawai tanufa,dan ko alwala tayine,sabida tanaso ya amshi rokonta da gaggawane.
 
da kyar tasamu ta isa jikin kaabar,tunda taji hannunta yataba ta,se kawai ta rushe da kuka tana faɗin.
 
"Allah na daɗe ina wahala arayuwata,ka kawomin agaji,ya Allah,nagaji,katausayamin haka,nima baiwar kace ya Allah"ta ƙarasa adduar tana kuka.
 
********
 
Suhaima seda ta kwashe tsawon sati guda acikin harami,tana maimaita wannan adduar,alwala da tsarki kawai ke fito da ita,abinci ko ana raba sabil na dabino da madara,su take ci.
 
Yau jummaa,rana ta buɗe sosai agarin na makkah,bayan an idar da sallar jummaa ne,suhaima tafito,wajen haramin sabida tanaso ta siyi riga da kuɗin sadakar da aka bata ranar da aka kama sajida.
 
Tana fitowa,taita tafiya,tarasa mezatace inta shiga shagon,dan ita batajin larabci.
 
Wasu gungun mata,ta hango,zaune,jikin ginin bindau,da sauri tanufesu,sallama taimusu,suko suka amsa amman azatonsu balarabiyace,dan haka se suka mata larabci.
 
ido taware atanta tace dama akwai baƙaƙen larabawa,tunda tagade fatarsu baƙace.
 
Dakyar tace musu ita bahaushiyace,don Allah tanason siyan rigane batasan mezatace.
 
Wata acikin matanne,ta juya tayiwa yar uwarta magana da larabci,seta juyo tacewa suhaima.
 
"amman ke bakuwace ko?"
 
kai suhaima ta ɗaga mata.
 
murmushi matar tayi sannan tace.
 
"karki damu ki bini ni kuma namiki alkawari insha Allahu,zan samar miki ayki,aguri me kyau,yadda zasu dunga biyanki duk wata,inkin amince kibini muje,amman ba anan garin nake zauneba,ni ina riyad ne"
 
Suhaima da sauri ta amince,ayko guri tasamu tazauna jiran matar,har tagama abinda zatayi,suka nufi tashar mota,suka hau,mota zuwa riyad.
 
*13-14*
 
 
Tafiyace me tsayi tsakanin makkah da riyad,dan haka sun jima kamin sukai.
 
Kamarde sauran,shima gidane me ɗauke da yawan mutane mazauna nigeria.
 
Tunda suhaima taje garin hankalinta akwance yake,sabida dankalin turawa kawai suke soyawa su fitar dashi,waje su siyar,hajiya murja sunan wacce takawo suhaima riyad,tana da kirki sosai kuma akwaita da tsoron Allah.
 
Sannu ahankali,suhaima har tasoma jin larabci,kamin wani lokaci taƙware dayin yaren,shiyasa take yawonta ko ina batare da ƴan kamen tikari sun kamata ba,sabida harshenta har ya karye,ko hausarta bata fita da kyau,sannan kamanninta babu mecewa ba balarabiya bace.
 
Watan suhaima biyar tare da hajiya murja,rannan da safe suna zaune sega,wata aminiyar,hajiya murja tashigo,me suna hajiya safiya.
 
fuskarta ɗauke da murna ta faɗo gidan,har tana tuntuɓe,amman bata damuba faɗi take.
 
"hajiya murja,fito,yai nasamo kabar me daɗi,fito fito"
 
da sauri hajiya murja ta tari aminiyar tata tana faɗin.
 
"akbirni kawata,meyafaru,kinsa nafara murna tun kamin naji"
 
guri suka samu suka zauna,sannan hajiya safiya tace.
 
"Dama gidan,sarki Abdulaziz Assa'udi ne,aka kama maaikatan gidan da laifin yunƙuri kashe ɗanshi,tahanyar bashi guba,to shine aka kori kowa,to yanzu sababbin maaikata suke ɗauka,kuma kinsan basa ɗaukar baƙar fata,shine nace ko zaki gwada kai suhaimanki ko zaa dace su ɗauketa,tunda aykine me kyau,"
 
"Gaskiya naji daɗin wannan labarin,sede,abu ɗaya,wlh banaso suhaima tayi nisa dani,sabida,tabani labarinta gaba ɗaya,tausayinta nakeji,ina gudun nakaita,makkah bayan nataho kuma sugano ba balarabiya bace,asamu matsala,"
 
Murmushi,safiya tayi sannan tace.
 
"inbanda abinki suhaima ay tasan hanya,insuka korota seta dawo,nan,nide namata shaawar aykin wlh,ki daure kawai mu kaita mu bita da addua"
 
Ayko da kyar hajiya murja ta amince.
 
Sati guda tsakani,suka shirya suhaima zuwa makkah,da kuka suhaima ta amince da aykin,dan itama batason yin nisa da hajiya murjan.
 
Koda suka isa masarutar,sun tadda mutane jibge ana musu screening,dan haka suhaima tahau layi,amatsayin me share share.
 
Koda akazo kanta ashe bata saniba se kana da takardar zama ɗan kasa,ido ta dunga warewa inda tace tamantoshi a gidansu dake riyad.
 
 
Kyan suhaima da kwarjinintane yasa mutumin yasa sunanta amatsayin me shara agidan batare da katin ba.
 
ganin sunanta yashigane yasa ta dawo gurin su hajiya murja sukayi sallama,sr kuka sukeyi,ahaka suka rabu,bayan hajiya murja taba suhaima ɗayar wayarta,sabida sudunga gaisawa.
 
Bayan angama tantancrwa ne aka shigar dasu suhaima cikin gidan,aka gabatar dasu ga alummar,gidan,daganan akaba kowa,ɓangarenshi,daze dunga kula dashi,cikin ikon Allah ɓangaren,babban ɗansarkin mesuna.
*SHUREIM ABDUL'AZEEZ AS-SA'UDI* ,ya faɗo acikin bangaren da suhaima zata dunga gyarawa,kuma dama duk inda,aykinka yake to anan ɗakinka yake,amatsayinka name kula da gurin.
 
Danhaka,ɓangaren aka kai suhaima,aka bata ɗakinta,mecike da kayan more rayuwa,kamar bame aykiba.
 
 
********
 
Hajiya duniyar sama sanda ta dawo tasamu labarin su suhaima sun gudu ba ƙaramin baƙinciki tayiba,ranta sosai ya ɓaci.
 
Hakanne yasa takira bokanta dake ƙasar indiya,tashaida mishi tanaso ya haukata suhaima da sajida,
 
alkawari yamata inda yashaida mata,yana da ayyuka sosai agabanshi,amman ta jira bayan wata shida ze kammala yashiga nata.
 
 
bata damuba,sabiɗa tasan boka guru maharaja da cika alƙawari
 
 
Anashi ɓangaren kuwa,boka guru maharaja,yaune waadin daya dibarwa,duniyar sama,dan haka tuni yashiga ɗakinshi na yin tsafin domin aywatar da nufinshi.
 
Wanda yay daidai da shigar suhaima masarautar makkah amatsayin hadima agidan.
 
Sajida kuwa bayan ankamata,sijin aka kaita,watanta biyu aciki,aka sakata,ajirgi,zuwa nigeria.
 
a kano aka sauketa,kuma bata da kuɗin mota hakanne yasa ta ɗauki drop din mota zuwa bauchi.
 
Sosai iyayenta sukayi murna da komawarta gida bayan sun cire ran sake ganinta,sukai taaantar hajiyar sama da tawagarta.
*15-16*
 
Yau da wuri suhaima ta tashi,ta ɗauki injin shara da mopping ta nufi ɗakin yarima.
 
Da sallamarta ta,shiga sede bakowa adakin.
 
Ba abunda yafiba suhaima mamaki,kamar ganin ɗakim kamar bame hankali aciki,sabida mugun dattin dayayi,wadrope a buɗe,kayan daya cire gasunan zube aƙasa wasu akan gado.
 
Tattara kayan wankin tafara yi takaisu cikin worshing marchine,tazuba ruwa da omo,sannan ta kunna,ta dawo taci gaba da aykin ɗakin.
 
Ranar suhaima tasha wuya sosai,dan kwalema tayiwa ɗakin,harda canjawa gado gurin zama,sannan tasa sabon bed shit,kayanshi ko data wanke shanyawa tayi suka bushe ta zauna ta gogesu tas,sannan,ta kwaso na cikin wardrope ɗin gaba ɗaya tasake sabon shiryawa.
 
kamin wani lokaci ɗakin yafito fess kamar bashiba.
 
Koda tashiga toilet nanma ta tarar dasi boxsize dinshi da singlet,jibge aciki baa wankeba,a kunyace suhaima ta kwashesu takai,worshing marchine suma tawanke ta goge masa,ta feshesu da turare ta shirya masa.
 
Koda ta koma ɗakinta wanka tayi ta gasa jikinta  sannan tayi sallah,ta nufi kitchen dan samawa cikinta abinda zata ci.
 
Sabida gidan komai a adalce sukeyi,kowanne ɗan ayki a ɓangarenshi akwai,kitchen da store daze dunga girka abinda yakeso yaci ba takurawa.
 
Koda suhaima taje kitchen dambun coucous tayi wanda yasha naman kaza da kayan lambu.tuni,ɓangaren nasu ya buɗe da ƙamshi.
 
tana gamawa,ta juye a kula,sannan tazuba wanda zataci ta fice daga kitchen,tanufi ɗakinta,tazauna taci tasha ruwa,tabi lafiyar gado.
 
***********
 
Shi ko Shureim tunda ɗakinshi yayi datti yadena kwana agidan ya tattara abinda yake buƙata,yakoma kwana a hotel,dan baze iya kwanan ɗakinba.
 
Yau yana tasowa daga office har ya shiga lifter zuw Ɗakinshi,sekuma kawai yaji yanason zuwa gidansu,dan haka fasa hawa saman yayi yadanna ta dawo dashi ƙasa.
 
yana sauka yashiga motarsa zuwa gidansu.
 
 
A aladar gidan basa zaman falo,dan haka be tarar dakowaba,ɗakin mahaifiyarshi yanufa.
 
me suna hajiya fatima,a kishingiɗe yasameta,me mata tausa tana matsa mata ƙafarta.
 
Nufarta yayi da sauri yarungumeta ya sumbaceta,ita kuma ta shafa gashin kanshi tana samasa albarka.
 
kan kujera yaje yazauna,suna hira,duk da cewa shureim miskiline na bugaw A jarida,wanda magana ke matuƙar tsada agurinshi,amman baya yiwa mahaifansa.
 
"Shureim ina kashige kwana biyu bana ganinka?"inji mahaifiyarshi cikin harshen larabci.
 
"Ummi wlh ɗakina yayi masifar dattine,ni kaina kunyar ɗakin nakeyi,shine kawai yasa natare a hotel acan nake kwana,tunda ankori yan aykin gidan"shima ya bata amsa da lataɓcin.
 
Murmushi ummin tayi sannan tace.
 
"Kaide akwai shiririta,to ay ankawo wasu maaikatan jiya,kuma kaima antura me kula da ɓangarenka,nasan angyara komai yanzu,kaje kaduba inbeyi maka ba base a canja kayan ɓangaren gaba ɗayaba"
 
Taɓe baki yayi sannan yayiwa ummin tashi sallama yanufi ɓangaren nashi.
 
Tunda yake betaɓa jin ƙamshin dayakeji aɓangaren nashiba yanzu,kamshin turare ganida ƙamshin girki,tuni cikinshi ya juya,alamun yanajin yunwa.
 
Kasa jurewa yayi yanufi kitchen ɗin,ba kowa se cooler buɗewa yayi wani tiririn ƙamshine ya daki hancinshi,da sauri,ya ɗauki plate ya juye abincin aciki,ya ɗauka yanufi ɗakinshi.
 
Abinda yagani ba ƙaramin mamaki yabashiba,inbanda ƙamshi ba abinda ɗakin yake komai naciki yadawo sabo,wardrop ɗinshi yanufa acan yasha makurar mamaki,ganin komai a wanke a goge se ƙanshi sukeyi.
 
toilet ɗinshi yanufa acanma yasha kallo,besan sanda murmushi ya kubce afuskarsa ba,a fili ys bayyana.
 
"ko waye yayi wannan aykin ba balarabe bane,sabida su basu saba da wahalaba,,musamman nacikin birni bankiba kona kauyem zasu iya kwatantawa, nasan koma waye to tabbas namiji ne,dan mace bazata iyaba"
 
da wannan bayanan nashi yaje yazauna yafara cin abincin,ji yake kamar kunnenshi ze fita,dan daɗi sam babu tafarnuwa aciki,shidama yatsani tafarnuwarnan,dande kawai yazamar musu tamkar aladarsu ce cinshi.
 
 
Shureim duk yawan abincin seda yakwasheshi tas yasha ruwa,yamiƙe ze fice ji yayi ya gaji dan hska lafiyar gadonshi daya gaji da haɗuwa yabi,yayi kwanciyarshi tuni bacci yayi awon gaba dashi.
 
*********
Tunda daga wannan lokacin,kullum suhaima seta girka abinci me rai da lafiya ta haɗa harda shureim sabida ta fahimci inta rage s kitchen yana zuwa ya cinye,dan kullum taje gyara ɗakinshi seta fito da plate.
 
tsawon wata guda kenan,tana ɗawainiya dashi,tuni yamurje,har wata kiba yayi,ga ɗakinshi kullum cikin gyara,gashi be taɓa ganin me aykin nashiba,kuma bedamu dason ganin me aykinba dan azatonshi namiji ne.
 
Yau tunda suhaima ta tashi kanta ke ciwo,dakyar ta cire kayanta,ta ɗaura towel tashiga wanka,adaddafe tagama wankan ta ɗauro towel ta fito,tana fitowa tayanke jiki ta faɗi aƙasa.
 
Tsawon kwanaki biyu kenan shureim,bega angyara mishi ɗakiba,kuma baa dafs mishi abincinba,wanda yasan da baa fashi.
 
hakanne yasa yashiga damuwa,nason sanin halin dame aykin nashi yake ciki.
 
Suhaima ko tunda ta faɗi bata tashiba seda ta kwans biyu ahaka,cikin dare ta tashi a haukace,tuni tayi fatali da towel ɗin dake ɗaure jikinta,se buga kanta take a bango tana zage zage.
 
Shureim cikin bacci yaji ana buge buge,a firgice ya tashi,silifas yasaka yafito,falo ananne yafahimci aɗakin me kula dashine abun yake faruwa.
 
Da gudu ya nufi ɗakin,yatura yashiga,ganinta tsirarane,yasa yayi saurin dakatawa gamida runtse idon shi yana fadin.
 
"Auzubillahiminashshaidanirrajeem"
 
itako suhaima se buga jikinta take da bango,har ta jiwa kanta ciwo,ganin zata illata kantane,yasa shureim daurewa ya ƙarasa inda take ya riƙeta,nanfa dambe ya kaure,ita ala dole seta kwace,inda shi kuma ya gwada mata ƙarfe,ta hanyar rungumeta gabaɗaya ajikinshi.
 
Se gurnani takeyi kamar tsohon zaki,ɗaukarta yayi gaba ɗayanta,yanufi ɗakinshi,da ita se son kwacewa takeyi,amman ya hanata.
 
koda yakaita ɗakin,ɗaureta yayi da [color=black][size=medium][font=Cambria]ƙ[/
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 2 36,320 09-14-2018, 12:13 PM
Last Post: Gimbiya
  *KANO TO JIDDAH* by Zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 9 111,928 09-05-2018, 06:57 PM
Last Post: Gimbiya
  *Y'ar Bautar K'asa* A Youth Corper*by Zahra Surbajo Gimbiya 1 17,110 08-10-2018, 01:58 PM
Last Post: Gimbiya
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 0 18,162 07-26-2018, 12:53 PM
Last Post: Gimbiya
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 0 33,643 07-16-2018, 03:44 PM
Last Post: Gimbiya
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 0 13,366 06-26-2018, 01:07 PM
Last Post: Gimbiya
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 0 15,622 06-19-2018, 01:08 PM
Last Post: Gimbiya
  *KANO TO JIDDAH* by Zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 1 73,766 12-07-2017, 03:17 PM
Last Post: Gimbiya



Users browsing this thread: 1 Guest(s)