The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*RAGGON MIJI*
#1
➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰



Writing by *MAMAN MAMY*




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION???~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*





5⃣




*Dedicated to SIS ZULAIHAT RANO*



Ya kagara gobe tayi ko yakara ganin kyakkyawar fuskarta. 

Wasa -wasa har dare faseelat taki tafito waje, ummi de ta share ta su abulkhair suna ta tambayarta sede ummi tace bacci take ,

Har abba ya dawo gida  bayan ishai ummi da abba suna daki suna fira while ishak abul da Mubarak na tasu firar, dan auta ya kasa hakura da rashin ganin ta ya leka dakinta tayi rubda ciki amma ba bacci take ba, abin duniya ne kawai ya sha mata kai, ganin idonta rufe yasa yaja mata kofar, 

Dakin abba ya shiga ya samu ummi ya zauna gefenta "ummi kode ya faseelat bata lpy? Naga tundazu da rana bata fito ba yanzu naje dakinta na ganta kwance har yanzu "

Ummi tace "to bana ce maka bacci take ba? Ka tashi kaba mutane wuri "

Yace "to ummi kode a tado ta ni wlh gidan ba dadi da babu ita "

Ummi tace "kai kasani ai "


Abba yace "wai tun dazu bata fito ba? Kuma kika kyaleta haba Hjy kinsan fa ulcer na iya kamata "

"to ya kake so na mata? Ko so Kake naje na rarraso ta tunda na mata laifi "

Abba yace "yaro dan rarrashi ne in kika lallabata se ki shawo kanta amma bata haka ba, kinsan faseelat na da saukin kai ai "

"Alhaji kabarta kawai in yunwa ta kusa kasheta zata fito, nifa duk abinda nakeyi saboda ita ne yarinyar nanfa da kake gani kusan kullum se tayi mafarki, taya kake tunanin hankalina ze kwanta tana zaune gidannan gwara ai mata auren tun kan ai abun kunya "

Abba yayi shiru yana nazari,yace"eh ki de bita a sannu, wa ma ta gado inbake ba da jarabar tsiya in baayi miki 3 rounds ba baki koshi "ya ida yana dariya 

Tace "eh naji din ai kai ma shine da har kake iya yin ukkun "

Suka sa dariya Mubarak fa yadade da barin wurin tunda aka korashi. 

Ummi nata zuba ido faseelat zata fito cin abinci amma bata fito ba, se kuma tafara shiga damuwa. 

Itako faseelat muguwar yunwa takeji ga, zazzabi da ya rufeta kwance kawai take tanata tunanin yadda zatayi rayuwa da khalil. 

Can 12am samarin duk sunyi bacci ummi tafito daga dakin abba har zata wuce se kuma ta shiga dakin faseelat, 

Tana kwance rubda ciki still ummi ta matsa "ke bana hanaki kwanciya haka ba?"

faseelat ta birkita ba tare da ta dago ba 

Ummi tace "wai dani faseelat zaki fushi ?dan kawai ina fadamiki gaskiya? Ya kikeso nayi ne? So kike nabarki na zuba miki ido? Bayan ga hanya Allah ya kawo, haba faseelat wlh kinbani mamaki da har zaki bijirewa magana ta shi dake namiji ya amince da umarnin mahaifiyarsa, amma ke kinkasa ".

faseelat ta fashe da kuka tana sheshsheka ummi tace "aa kidena kuka faseelat bazan takura miki ba tunda bazaki iya aurenshiba shikenan gobennan zankira uwarshi in fadamata bakisonshi tunda burinki ki kunyatar dani, ni wlh daace kinada wanda kikeso da baabinda zesa na matsa miki amma keda bakida kowa ihhhhm? Dama ace ke lafiyayya ce amma kinada larura ki duba fa yanayinki faseelat, shikenan anfasa auren ki tashi kije kici abinci "

Ummi ta juya zata fita faseelat na kuka ta kira sunanta "ummi "!

Ummi ta waiwayo ta cigaba da cewa "Dan Allah ki hakuri baniso ranki ya baci karki fushi dani "

"bazanyi fushi da keba faseelat sede ki sani zaki sani cikin zullumi da tunani dan wlh inde ban aurar dake ba banida kwanciyar hankali "

Faseelat daga kwancen de take magana cikin rashin tunani tace "na yadda ummi zan aure shi inde zakiji dadi "

Ummi tace "dako kinfaranta min rai dan inada tabbacin bazaki kuka ba in Allah yaso"

faseelat tace "na amince ummi kuma kiyi hakuri da bata miki rai da nayi "

ummi tace "bakomi Allah ya miki albarka ki tashi kici abinci karkijawa kanki ciwo"


Faseelat tace "bazan iyaba ummi masassara nake tun dazu "

ummi tace "subhanallahi "tana hawa kan gadon ta fara tattabata gabadaya jikinta rau yake har kafafunta, ummi tace "sannu kinji bari na kawo miki magani "
Ta tashi ta fita wani kuka ne yazowa faseelat ita kanta tasan ta amsa ne kawai amma tasan haka zatai ta rayuwar hakuri harabada, tasa hannu ta share hawayenta yanzu de koba komi ta farantawa mahaifiyarta rai da tun tasowarta tana ganin yadda take fifita ta akan yanuwanta. 

Motsin da taji yasa ta  kara goge fuskarta ummi tashigo dauke da tray ta ajiye ta bude flask ta debo taliyar hausar da ta dafa da daddare ta dora kan bed ta debi ruwa ta ajiye sannan ta zauna bakin gadon tace "tashi ga abincin diyata "

Faseelat na ciza baki ta yunkura ummi taida tadata zaunen jikinta har kyarma yake saboda yunwa, 

Ummi  tafara bata abincin a baki da yake tana jin yunwa taci abincin sosai sannan ta bata magani ta koma ta kwanta se sannu ummi ke mata sede ta daga kai, tashi ummi tayi taja mata kofa tana mata seda safe. 


ko bayan fitar ummi faseelat kuka ta rikayi ga bacci ya kaura cewa idanunta, 
Ba abinda take tunani se fuskarshi da jikinshi tana tunanin yadda zasuyi rayuwa tare wuri daya gida daya daki daya gado daya. 


Se asuba bacci ya dauketa, ummi na Gama azkhar taje ta gaida abba yake tambayarta jikin faseelat da yake wurinshi ta amso maganin tace dasauki ta fita dubota, tana shiga ta tada ta faseelat bude ido kawai tayi ummi tace "ya jikin "tana tabata faseelat tace "dasauki "

Ummi tace "naji haryanzu da fever din kitashi ki salla inje in hado miki tea kisha kisha magani "

Faseelat tace "I'm off"

Ummi tace "kinada pads ne? "

Faseelat tace "eh amma beda yawa "

"OK anjima zanba Mubarak yasiyo miki wata tashi kije ki kimtsa ko kinji dadin jikin "

faseelat tace "to "ta mike ummi taga har tangadi take ummi tace "zakiiya wankan kuwa "

Faseelat tace "eh "tafara bin bango ummi takamata ta kaita toilet sannan tai kitchen, 

Da dai daya yanuwanta suka rika shigowa suna mata ya jiki kafin su bar gidan, shi ko Mubarak harda hawaye danba karamar shakuwa sukai ba daita. 

Bayan tasha tea din da magani ta koma ta kwanta, 

Can wajen 12pm ummi nata aikace aikacenta wani yaro yazo yace ana kiran faseelat .

Ummi ta danyi jimmm sannan tace "gatanan zuwa "

Yaro yaje ya kai sako

itako ummi tashiga dakin faseelat har lokacin tana bacci ummi tafara tapping dinta tana kiran sunanta faseelat ta bude ido, tana kallon ummin. 

Ummi tace "ki daure kitashi ki dan kimtsa ga khalil can yazo "

Faseelat gabanta ya bada dudum, tasan datace bata iyawa ran ummi ze baci dan dole ta mike tsaye ummi tace "zade kiiya ko? "

Faseelat tace "eh ta jawo hijab har kasa ta saka ai gwara tajema ta kara ganinshi maybe jiya batai masa kallon tsaf ba. 

Tana saka hijab din tafita ummi ta girgixa kai tana kallon yadda take tafiya a kasalance. 

Faseelat na fita taganshi  a..... 




Next page loading........
[6/27, 16:33] +234 802 797 9297: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰





By



*MAMAN MAMY*



https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION???~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



6⃣




*Dedicated to SIS ZULAIHAT RANO*




a zaune kan roba-robar shi kallo daya tai mashi ta dauke idanunta, jikin bango ta jingina kanta na kallon sama ta cije baki saboda Marar ta data murda , 

Shi ko yana ganin fitowar ta ya mike tsaye yana gyara riga ganin ta jingina a bango tana ya mutsa fuska yasa shi jin badadi, 

Bakomi yasa faseelat dauke kai ba se dan ganin kara jiya da yau, shadda ce jikinshi fara kall ya kawo farar hula akanta ga takalmi fari, wayaga balbela? 
Shi gashi baki abin se ya dagule, itada tafito ganin canji se taga gara jiya, shaddar se sheki take tsabar fari. 


Shi ko be samu ganin fuskar taba saboda kanta na facing up ganin Sun kusa minti ukku yasashi cewa "barka da fitowa"

Batare da ta sauke kanta ba ta dan juya shi ta zuba mai jajayen idanunta wanda suka kumbura saboda rashin barci da kukan da tasha ,

Yace "subhanallah, faseelat lpya kike? "

Ta juya sannan tace "ban lpya " 

Cikin jimami yace"miyasameki?"

Tace "fever"tana tabe baki. 

Yace "ayyyah "da karfi wadda tasa seda ta mike daga jikin bango saboda yadda gabanta ya fadi, Ya cigaba da cewa "Allah shi sawwake shi baki lpya "

Faseelat kamar ta dora hannu aka tasa ihu haka takeji, ashe ba karamar illa takeso taiwa Kanta ba ko magana be iya ba, shi ga bahaushe wani abinda ta dan lura dashi shine kamar maganarshi daga hanci take fitowa. 

yakatse mata tunani da cewa "ga wannan"

Ta kai kallonta ga ledojin da yake miko mata, daya babba daya karama, dan dole ta mika hannu ta amsa can ciki ciki tace "Nagode"yayi kamar be jiba sema yace "dama zuwa nai mugaisa gashi bakya jin dadi yanzu ni zantafi se munyi waya ga waya nan da sim da komi "

Batare da wata murna ba ta kalli ledar hannunta ta yamutsa fuska. 

Yace "se anjima agaida ummi "

ta juya kawai ta shige gida tana saka da warwara , yadda zata kuma ganinshi in ya dawo dan kullum kara gano muninshi takeyi. 

tana shiga gida ummi tayi shimfida kan barandar gidansu kafafunta a mike tana huce gajiyar hidimar da tasha, ta je ta kwanta kan kafafunta, 

Ummi tace "sannu faseelat kode mutafi asibity? "

Ta girgiza Kai ummi ta kai dubanta ga ledojin da suke zube ta jawosu tana fadin "shi ya baki wannan?"

Faseelat ta daga kai idonta na kawo ruwa batare da ummi ta dubeta ba ta Fara bude ledojin, daya cosmetics ne kawai ciki, danginsu perfume, Nivea lotion, roll on, powder irin big pack dinnan wadda Zaka samu su concealer da foundation, da janbaki duk a ciki, se lip gloss. 

dayar kuma waya ce ciki me suna infinix hot 6, ummi tace "aaa!masha Allah Allah yasa alheri, faseelat kinga kaya ko? "

faseelat da duk abinda zaa daga wani kululu ke tokare mata makoshi tace "ihhhhm "

Ummi tace "to ga waya faseelat tunda wayarki tasamu matsala har yau alhaji babba be aiko da wata ba toga khalil ya hutar dashi "

faseelat ta mike tsaye zata wuce dakinta dantagaji da jin maganganun ummi, kawai wayar tafara ringing, ummi tace "zo zo gashi har ya kira ashe a bude take "

Faseelat takoma ta amsa kamar zatai kuka tashige daki tana shiga ta danna ta a key dif ringing ya tsaya ummi duk a tunaninta faseelat ta dauki wayar ne, kiran na yankewa shiru be sake kira ba faseelat ta tabe baki, 

Ta haye gado tana tunanin rayuwar da zatayi nangaba, 

Hannunta ta dora kan kirjinta taji yadda yake fat..fat ta fara hawaye. 


khalil yana be koma gida ba se 2pm dan daganan school ya wuce, 

Yana shigarda mashin dinsa yayi hanyar dakinsa Hjy saratu da ke alwala zatai salla tabar alwalar tana bin bayanshi da kallo har ya kusa shigewa Hjy tace "kai zonan khalil"

ya juyo yaisa wurinta dan slope din dakinta da take kai anan ya zauna tana kallonshi tace "lpya kake naga ka dawo haka kamar marar lpya? "

ya cire hular kanshi yana fifita yace "Hjy naje gidansu faseelat na sameta bata da lpya sosai "

Hjyar tace "ummm se akai yaya? "

yace "shine nakeji nima bani lpyan "

Hjy saratu tai kasake tana kallonshi shi kuma dagaske yake maganarshi ,Hjy tace "to Allah ya sawwake ,saboda bata lpya shine kake wannan yaushin? kamar ba namiji ba, tashi da Allah kaban wuri "

Memakon ya tashi se yace "Hjy yaushe zakije ganinta? "

ta banka mai harara "se ran da na shirya "

"to me ze hana kije yau? "

Cikin haushi tace "saboda ban ga dama ba "

Ze kara magana tace "aa da Allah kyaleni fita xanyi yanzu idan na dawo zan biya ingano tan "

yace "tom "ya mike zakadai -zakadai ya shige dakinshi, wata kan jiya daga jiya zuwa yau faseelat ta zama wani bangare na cikin jikinshi, ku jifa ?kunsan irin su dasaurin shiga hannu  ,

wayar shi ya fiddo a aljihu ya kara kiranta bata dauka ba faseelat lokacin ma batasan inda kanta yake ba dan gabadaya masassara  ta rufeta tana cikin bargo tana kyarma lokacinma ummi na wurinta zaune tana jiran abba yazo su tafi asibity. 

Koda kiran ya tsinke ajiye wayar yayi shi a kaidar shi baya missed call biyu, (audu ka'ida kenan)

Hmmm shifa ba ordinary mutum bane shi rayuwar shi daban take da yadda aka saba gani kude biyoni muji tasu salon soyayyar.

Au ?nayi mistake, kaso a soka ai shine so, kaso a ki ka fa?shi kuma me zaakirashi?

[6/27, 16:33] +234 802 797 9297: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LBBVKSXqmrj3oaalNYWqmS


➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰



By 



*MAMAN MAMY*




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION???~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*





7⃣





Dedicated to *SIS ZULAIHAT RANO*




Abba na zuwa ummi ta kama faseelat da temakon kaninta abul saboda ko tafiya bata iyayi ga zazzabi ga ciwon mara ga tension abun da yawa, har cikin mota akasakata, babansu yana da mota amma ta kwana biyu sede batayi tsufa can can ba ,yayan abba wanda sunansa salisu suna kiranshi baba babba ummi kuma na kiranshi alhaji babba mutum ne me kirki da arziki duk da de bawani arziki ne me yawa ba amma ba laifi tunda yana da zuciyar temakon yanuwan sa shi yakai su ummi hajji ya siya wa abba mota shine ya dauki nauyin karatun ya umar, kuma a gidansa yake zaune a Niger Republic din da yake shi alhaji salisun shima dan kasuwa ne yana yawan zuwa can shine yayi aure kuma yabar matar a can kasar. 



Shi kuma abba tuni ya dena zuwa Niger din iyakar shi nan gida Nigeria duk da ummi can duk ilahirin dangin ta suke amma alhaji be bari ya zauna a wani gida ba se a gidanshi wannan kenan. 


Asibiti suka kaita da zuwan su aka sa mata ledar ruwa, bayan allurai da aka mata, 

Se bayan laasar ta farka likita ya shigo yana tambayarta mike damunta yanzu, 

Jiki ba kwari tace "ciwon mara da nan "
Ta fada tana nuna setin zuciyarta likitan ya dan kura mata ido ta glass sannan yayi yan rubuce rubuce, 

Ya juya wurin ummi da ke tsaye tanajin duk abinda ke faruwa yace "Hjy ire iren ciwon marannan inba aure akayiwa yaranba zeyi wuya ya barsu, sannan batun ciwon heart din rashin cin abinci ne da isashshen bacci wannan kesa ulcer ke kama mutum wuf daya, se akiyaye duk abinda na fada banda abu me tsami ko yaji ko mai da yawa arika bata abinci akai akai "ya juya bayan ya gama jawabin yana kara kallon faseelat, 

ummi tace "insha Allah zaa kiyaye, kuma ankusa yin bikin ta ma "

Likitan ya Mike tsaye yana gyara ta kaddun hannunshi, shi da har ya fara tunanin ya samu ta ukku, matanshi biyu, ya killace a gida dukansu farare ne tass dan yanada gurin ajiye fararen mata kuma dukansu a asibity suka hadu daya ma kauye take daga amai da gudawa ya aure ta. 
Fita daga dakin yayi yana fadin ,"Allah ya sawwake, "

ko da abba ya dawo hospital din samu yayi an sallame su dan lokacin kusan 6:40 ya biya Bill suka wuce gida. 


Bakin wani pharmacy suka tsaya abba ya Shiga ya siyo magungunan da aka rubuta musu sannan suka wuce .

suna isa ummi takama faseelat suka fito har zuwa dakin ta ta kwantar daita malt da milk ta hado mata tasha tasha magunguna ta kwanta baadade ba bacci ya dauketa. 

Can ana kiran sallan ishai se ga Hjy saratu kamar daga sama tana sallama ummi da fitowar ta wanka kenan ta amsa tana mata marhaba Hjy saratu ta shiga ummi tai mata iso har daki, 

bayan sun gaisa take tambayar ummi ya me jiki? 

ummi tace "dasauki dazunnan ma aka sallamomu daga asibity dan seda suka saka mata ruwa"

Hjy saratu tace "Abu beyi dadi ba Allah ya sawwake ya bata lpy ai tundazun naso zuwa se kuma na makara wajen fitar diyar kanwata ta haihu shine muka tafi suna tundazu inata so na taho se yanzu Allah yayi ina rokon Allah yabata lpy "

Ummi tace "amin"


Hiya saratu tace "tunda Khalil ya koma naga ne ba lpya ba dan kamar kwai ya fashe masa a ciki haka yayi "

Ummi tai dariya "khalil kenan ai dazun da yazo ya cika faseelat da abun arziki harda su waya a cikin kayan, Allah de ya kara budi na alheri "

Hjy saratu tace "amin amin,bari naje na dubata na wuce gida"

Suka mike suka fita zuwa dakin da faseelat ke kwance, 
Har lokacin tana bacci ummi tace "bata tashiba kila cikin drugs da aka bata akwai na saka bacci ciki "

Hjy tace "to ni zanwuce Allah ya kara bada lpy "

Ummi tace "amin "

Ta na mata tattaki zuwa bakin kofa seda suka kai can ummi ta dawo ta shige daki ta'ida shiryawa, sannan tafito. 


Ana gama isha'i duk suka hallara ummi takawo masu babbar cooler datake zuba musu abinci se plates da spoons suko sunbaje akan tabarma, kowa ya dibi nashi suka fara ci, Mubarak yace "ummi ni de nakoshi tunda yaya bata lpya"

Ummi tace "haba dan auta na, ka daure kaci ga faseelat can tana cin Nata itama "

Yace "dagasske ummi? "

Tace "eh kai sauri ka gama cika cikin ka se kaje wurinta yace to "yafara buga loma. 


Su ummi basu dade da barin dakin ba tafarka ba laifi massaran ta sauka tun asibity ciwon ma ya lafa, sede ciwon da zuciyarta ke mata, baa jima ba taji wayarta na vibrate taja dogon tsoki kamar ba marar lpya ba afili tace "dan wahala"

Hjy saratu na'isa gida take bawa khalil labari tace "ashe haka faseelat ke jin jiki ?umminsu tace dazun har seda aka kwantar dasu asibity"

Yace "Hjy suna asibitin yanzu? "

Tace "a, a an sallamo su agida na samesu "

Ya tashi tsaye daga shi se jallabiya ga zungureriyar casbahar shi yana ja yace "bari na dawo hjy "

Hjy na kallonshi tace "kai dawo nan ina zaka? "

yace "yanzu zan dawo fa hjy gidansu zanje "

Tace "Kai  baka da hankali da zaka je gidansu yanzu? "

Kawai ya juya "sena dawo "ya fice 
Niko nace hjy barshi kinsan dogo dama be cika hankali ba ??


Ya fidda babur dinshi yaja akan hanya ya tsaya wata supermarket ya siyi chivita da hollandia da malt da short cake da big biscuits gefen shagon ya siyi fruit irinsu orange, banana da pineapple 

 daya wuce gidansu, lokacin kusan karfe 10pm dan har Sun kulle gida ya yi parking machine dinsa ya fara kwankwasa gidan, 

Be dade da fara kwankwasawa ba ishak ya fito bema sanshi ba hakanan yace masa "inayini "

Khalil yace "lpya lau, ya me jiki? "

ishak yace "dasauki "

Khalil yace "Allah shi kara afuwa, ga wannan ka kai mata "

Ya mika masa ledar ishak ya amsa yace "injiwa? Za a ce?"

Yace "khalil "

ishak ya juya yasaka sakata ya shiga cikin gidan abba da yake zaune shi ma yace "waye ne ?"

Ishak yace "yace khalil ne kuma yabada wannan yace abata "

Abba yace "kai ma ummi tana can wurinta 

Ya juya zuwa dakin ummi kadai ya tadda tana gyara wa faseelat gado ita kuma tana toilet yace "ummi gashi inji khalil yace yana gaida me jiki "

Ummi tace "oh cikin darennan ya taso to kawo "

Ta amsa ta ajiye shi kuma ya fita baa jima ba faseelat tashigo dakin, 

Wajen wardrobe dinta tawuce ta kimtsa kanta sannan ta dawo ta zauna kan bed. 

Ummi tace "ga kayan marmari ankawo me zakisha? "

Faseelat tace "nakoshi ummi ruwan zafi kawai nakeso insha "

Ummi tace "to bari in je inhada miki amma ki tashi ga ayaba nan kici ko kadanne kinsan tana rage menstrual cramps "

Tace "to "

Ta amsa ta bare tana ci tana yamutsa fuska.
[6/27, 16:33] +234 802 797 9297: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰






By        *MAMAN MAMY*





https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION???~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*




8⃣




Dedicated to *ZULAIHAT RANO*




Lokacin da ummi ta dawo har faseelat taci biyu, mika mata tea din ummi tayi tana fadin "bansa sugar ba amma nasa miki citta da yawa saboda tana koro jini da wuri "

Faseelat ta amsa "Nagode ummi "

Ummi ta zauna tana kallon faseelat tace "dazun Hjyarsu khalil tazo kina bacci tana gaidaki da jiki "

Faseelat tai shiru bata ce komi ba, 

Ummi tace "baki tambayi wanda ya kawo miki fruit dinnan ba "

Faseelat ta kurbi tea tace "nayi zaton abba yakawo "

Ummi tace "a, a khalil ne ya kawosu yanzu da darannan "

Kuts-kuts ta zubdo tea din bakinta wani kuma ya sarketa tafara tari, 
Ummi tace "kibi a sannu mana inya miki zafi kibarshi ya huce tukun "

Faseelat ta goge gefen bakinta taajiye copyn tea din tai shiru tana mamakin wane irin mutum ne khalil itade ba sakarmishi fuska take ba sannan bawani sabawa sukai ba ballatana ya dinga yi mata wadannan abubuwan, 

Ummi ta katse mata tunani da cewa "kind ace da miji faseelat alamu duk sun nuna haka yaro me kunya da tarbiyya, duk dade bansan halinsa ba amma ina mai kyakykyawan zato, Dan Allah faseelat ki saki jikinki sosai naga tunda yazo kike ciwo bansaniba ko hakanan kika amsamin amma baki son auren shi "

Faseelat tace "ummi gaskiya na amince ne saboda kawai kiji dadi ba dan inason shi ba "

Ummi tace "ai nangaba zakiso shi "

Faseelat tace "hmmmmm "

ummi tai dariya "kiyi magana mana nasan nangaba ko ance auren hadi akai muku  mutane bazasu yarda ba danni nasan nabaki many lessons daga tasowarki zuwa yanzu Wanda ko bankara da komi ba sunisheki zaman gidan miji, kuma kina da komai da zakija hankalin namiji dashi inde har kinmeda hankali mallake namiji baze miki wuya ba ,zaki so shi ki haifa masa yara Kema kizama uwa me koyarwa kamarni"ummi ta'ida maganar da murmushi fuskarta. 

faseelat batace komi ba batasan komi ze faru nan gaba ba amma bata tunanin zataso khalil ko ta so shi bawani so sosai ba, saboda tadan fahimci wasu abubuwa dangane dashi. 

Ummi ta katse shirun da cewa "ga kayanda ya kawo ki dauki abinda kikeso na kaiwa yanuwanki sauran "

Faseelat tace "ni nakoshi ki tafi dasu kawai "

Ummi tace "to ki sha tea din kar yayi sanyi kuma "ta dauki ledar tai waje 

Faseelat ta yi tagumi ji yadda komi ya jagule mata lokaci daya saboda kawai ummi ta kamata tana wankan janaba inda bataganta ba bazata matsa mata haka akan aure ba, faseelat sede taji hawaye Sun zubomata anata abubuwa kamar gobe ne auren why? 

ita tai kanta haka ne haka Allah ya halicceta mata nawa ne irinta? Maza nawa ne Irinta suma haka iyayensu ke matsa masu akan aure ko se ita dantana ya mace tilo gun mahaifiyarta? Ta share hawayenta tana daga kai cikin zuciyarta tace bazan kara zubda hawaye na akan batunnan ba zanyi kokarin hakan. 

(yo anya zata iya?) 


ummi nafita ta kaiwa abba kayan ya gani tace "me zaabaka? "

ya dauki hollandia yace "wannan yayi "

Ta tashi su ishak nata fira abul na gefe yana duba handout ummi ta zauna tsakiyarsu tace "Mubarak kawo wuka"

Ya tashi domin daukowa, 

Abul ya kalli kayan "wai ummi waye ya kawo kayan nan "

Tace "kubakusan antinku aure zatayi ba? "

Ishak yace "wannan kai "

abul yace "yaakayi ne"

Ishak yace "lokacin da na bude gida naganshi tsaye ya bani tsoro dogo ne sosai nazata ma aljani ne "

Ummi ta rumtse masa baki da hannuwanta tace "ubanka so kake ka kara tunzura yayarku"ta juya tana kallon wajen dakinta 

Abul ya kece da dariya ,"ummi kibarshi ya ida mana"

Ummi ta harareshi "kayi dede Allah yayi maka albarka "

daya daga cikin sirrin ummi ko wane laifi zaaimata sede tace Allah yayi albarka bata taba cewa komi fiye da wannan sede harara. 
Mubarak ya dawo da wuka hannunshi yana mita wai wukar can karkashin kwandon wanke wanke ya ganta ummi tace "to me kauda kayan bata lpya se inta tashi tukun "ta yanka kayan marmarin suka fara sha sunayi suna labari. 


Hjy najin motsin mashin din khalil tafito waje seda yayi parking tace "kai dogore seda kaje dinko? "

alhajinsu ya leko tunkan khalil yayi magana "ai gwara da yaje zasu kara ganin yadda take da mahimmanci a wurinshi "

Hjy ta rike haba "ah to yayi ka ganta ko? "

Yayi shiru ya shige daki.like mother like son wajen shegiyar tambayar yaya akayi aka haifi uwarka. 

The following day.......
[6/27, 16:33] +234 802 797 9297: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰



By 



*MAMAN MAMY*




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION???~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



9⃣



Dedicated to *sis Rano*



Ta kama ran Friday salla day awurinmu musulmai, bayan ya dawo daga masallaci da asuba ya shiga ya gaida Hjy ta amsa ciki -ciki yace "Hjy lpya? Ko nayi miki wani abu ne? "

tai shiru ya kara memetawa 

Tace "da Allah tashi kaban wuri "

"Hjy dan Allah kiyi hakuri innayi miki laifi bada sani naba "

"bakasan laifin da kayi ba kenan? Jiya ban hana ka zuwa gidannan ba da daddare amma seda kaje, tunda kaje kaga yarinyar nan shikenan ba saura ba kingi duk ka zauce, aka gaya maka haka akeyi ? ko dama can kana santa bansaniba?"

Maganganun hjy sun matukar bashi mamaki yace "haba Hjy kefa kikayi wannan hadin ni ina zan santa ma bare na so ta, kuma ni wlh hjy banga wani abinda nikeyi ba dede ba, jiya kuma Banyi tunanin tafiya ta zata bata miki rai ba, kiyi hakuri "

Tace "to naji why kake ta kashe kudi har haka danna ce kai mata kyauta aiba cewa nai kaita kashe kudi ba .

Shiru yayi kanshi duke tambayar kanshi yake mi yasamu Hjyarsu. 

can zuwa yace " bawani kudi bane fa sosai waya kawai na siyo mata se cosmetics that's all "

Ta Harare shi "eh ba kudi bane masu yawa tashi kaban wuri, ai gwara ayi ai auren ko kasamu kanka, ni wlh dama kauye naje nasamo maka yar yarinya"

ya tashi tsaye ya shafi sumar kanshi can zuwa yace "Allah yabaki hakuri "ya fita 

Tace "amin"

Khalil kusan Karo sukayi da alhaji yayi saurin zukunnawa gaida shi alhaji ya amsa ya wuce ciki. 
Khalil ya tashi ya tafi saboda shirin makaranta .

Alhaji yana shiga yafara wa hjy fada "wato de sararu bazaki bar halinki na banza ba ko? saboda nasan halinki fa shiyasa ban kara aure ba danna san duk wacce na aura kashe ta kadai ke bakiyi, yanzu kuma ga matar danki zaki koma, to kibi Ahankali wlh tun kafin yaronnan ya fahimci manufarki "

komi batace ba ta tabe baki a ranta tace "aini ma bansan haka yake ba nazata ze cigaba da halinsa na rashin son auren. 

7:30 khalil ya fito da shirin shi yau kam yayi kyau wani yadi ne ash color yasa mishi bakar hula da bakin takalmi rigarde tazarce ce da alamu duk haka dinkunansa suke hular ma tayi gaban goshi sosai shima da alama haka yake saka hular shi, ya leka kitchen hjy se diminiya take dan kawai karyayi kalacin danwake ne zatayi amma tai nan tai nan batare da ya damu da rashin hada kalacin ba yace "Hjy natafi "

Tace "Allah ya bada saa "fuskarta ba yabo ba fallasa. 

Ko damuwa beba ya bar gidan se sannan hjy tagama danwaken, 

karfe 9 siyama ta shigo gidan tareda yaranta biyu "Fatima da farida "

hjy saratu tace "oyoyo oyoyo yan albarka "

siyama tana fara'a tace "hjy ina kwananku "

"lpy lau ya jikin kwana biyu da kikai ba lpy kamar kin kwana goma wajen sunan ramla se tambayarki suke "

Tace "eh wlh hjy amma jiya na aika mata da sako kuma Bayan kwana biyu zanje gidan na gano takwara, ai wlh naji jiki hjy danbana iya komi, abdulkadir ke komi har girki "

hjy tace "Allah yasa kaffara ne,"

siyama tace "amin su yaya ana makaranta "

hjy tace "uhm antafi ai yayanki ya kusa zama ango "

siyama na murna tace "dan Allah Hjy wacece yarinyar "

Hjy saratu tace "eh ba wata bace se faseelat "

Siyama tana murna tace "faseelat de wadda nasani Hjy? "

"itafa "

siyama tace "gaskiya naji dadi hjy Allah yasa alheri ai faseelat full option ce komi yaji, tana dariya tace "finally yaya zaayi aure "

Hjy tai dariya siyama ta mike tsaye "Hjy mi zaa dafa muku yau ?"

Hjy tace "komi kikayi yau de jumaa komiye de da miya zaki "

"ayi taliya da miya NE? "

Hjy tace "a, a kide yi shinkafa kinsan khalil beson taliya gwarama in anyita da safe shima se anci saa kawai kiyi shinkafar se ki dafa masa wake, dan kinsan shinkafar ma baya sonta ita kadai "

Tace "to "tai hanyar kitchen. 



Khalil ko school ya wuce ,jss classes yake koyarwa duk jiki mace yake komi maganganun hjy nata mashi yawo yanata kara nazarin su,, ga rashin lpyar faseelat data dameshi. 

12:30 aka tashi saboda sallan jumaa direct supervision store yawuce ya siyi su peak milk , bournvita,cornflakes,block sugar, golden moon da tea bag, da different sweet , kusa da wurin akwai oasis bakery ya saye big bottle ice cream da snacks ya nufi gidansu faseelat .


yana isa yayi dede da dawowar Mubarak daga school , Mubarak se kallonshi yake, khalil ya jawo shi "abokina zo mugaisa "

Mubarak de yayi tsaye yana kallonshi khalil hannunshi ya kamo yasaka a nashi yace "ummi na gida?"

Mubarak ya daga kai 

Yace "yayar ku fa ya jikinta "

Mubarak yace "dasauki dan dazun naganta tafito zatai shara ummi ta hanata "

Yace "good kaje kafadawa ummi cewa khalil yazo yana so ze shigo ya gaidata "

Mubarak yace "to"
ya shige gida seda yafara shiga dakinsu ya ajiye jikkarsa sannan yaje ya fadawa ummi, ummi tarike baki "Allah sarki yaron kirki ,jeka ce ya shigo "har ya tafi tace "Mubarak dawo jirani "

tashige dakin faseelat, faseelat taji sauki sosai dan wayar da yabata tasaka wa tsohon sim dinta, tai checking balance babu kudi ciki tanayin Wanda ya kawo taga 1000 ta tabe baki ta siye data tayi download what's up tai installing messages sunata shigowa ummi tashigo ,"ke ki tashi ki kimtsa ga khalil nan shigowa "

faseelat tace "khalil ?"tana zaro ido 

Ummi tace "eh ki tashi gashinan shigowa "ta juya Tabar dakin faseelat tace "mtssww shikenan fa khalil khalil maganar kenan ta kalli riga da wandon dake jikinta fakistan tace "ni shirye nake danban kara irin gayunnan saboda shi "

Ummi nafita tace yashigo tashige daki ta sako hijab. 

Tare da Mubarak suka shigo yana dauke da katuwar bakko, 
Har bakin dakin ummi yayi sallama ummi ta amsa tace "maraba ka shigo "

ya dan sunkuya dukda tsayin kofar ya shiga memakon ya zauna kan kujera ya xube kasa, a sannu ummi ta saci kallonshi tace "kambuu da wannan ne faseelat ke kushewa ina laifinsa yanda mazannan sukayi tsada, 

Ummi tace "a, a katashi kazauna saman kujera "tana sunkuyar da kai na surukai, 

Yace "ina yini, "batare da yakoma ma waccan maganar ba. 

Ummi ta amsa akunyace yace "ya me jiki? "

Ummi tace "dasauki "

yace "Allah shi bata lpy dama zuwa nai nagaisheku"kanshi a kasa shima kunyar yakeji 

Ummi tace " amin angode kwarai "

Dama da shigowar shi ya jingina bakkon jikin cushion hannunshi ya cusa cikin aljihu ya zaro kudi a kalla sunkai 10 ya ajiye sannan yace"ni zanwuce "

Ummi tace "to angode bari na kira maka faseelat din "
Bece komi ba ummi tafita Mubarak de na zaune ummi nashiga tacewa faseelat "ki tashi ki shiga ku gaisa "

faseelat da tunda taji sallamar shi taji zazzabi ya fara rufeta ta tashi tafita kamar me koyon tafiya, 

Ummi tace "yar rainin hankali har ciwon ya dawo ko "

Faseelat ta shiga da sallama bakinta, wani sanyi ya mamaye zuciyar khalil ya dago kananun idanunsa ya zuba mata, kallo daya ta masa ta samu kujera ta zauna. 

Yace "inawuni malama faseelat,"faseelat ta kalli zungure riyar hijab din dake jikinta tai shiru, 
yanata kallonta yace "ya jiki?"

ta lumshe ido ta bude tace "naji sauki ai "

Yace "da sauki zaki ce de, tunda baki warware ba "

Tai shiru 

Yace "to Allah yasa kaffarane "

Tace "amin "kasa-kasa 

Ta dago ta saci kallonshi Sukai 4 eyes seda gabanta ya fadi ta rasa wane irin kallo yake mata, shiko kallon luv ne yakeyi, to da yake de sabon shiga ne se kallon yayi kama da kallon ruruwa??‍♀Inajin harda kallon luv se kun koya mishi ?

Faseelat ta kauda kai sannan ta dago ta kara kallonshi lokacin ya dauke ido yana magana da Mubarak harda kudi ya bashi, wannan ya bata damar kallon dressing nashi a zuciyarta tace not bad, 

Ya mike tsaye yana jifanta da wannan kallon yace "ni zanwuce "

tafara wasa da hannunta,

yace "ba bankwana?"

Tai shiru yace "to natafi amma plss ki rika daukar kira na i have called you several times but you don't pick my calls why? "

Faseelat seda murmushi ya  kufce mata saboda jindadi atleast de yana iya kwantar da murya wajen pleading kuma ya iya turanci daya daga cikin abunda take so wajen mijinta. 

akan idonsa tai murmushin wani farinciki ya mamaye shi ganin smile a fuskar ta, 

Yace "I'm pleading I hope you will accept my request "

kawai ta girgiza kai dariya tazo kufcemata ta jawo hijabinta ta rufe fuskarta. 
yayi dariya yafita ummi bata waje danhaka yawuce har kofar gida Mubarak ya rakashi khalil nata masa labarai,. 

Yana wucewa Mubarak ya shigo gidan dede fitowar faseelat daga dakin taci dariyarta se kuma daga karshe ta dinga buga tsoki, 

sukayi kicibus da ummi. 

Mubarak yace "gaskiya ummi yana da kirki sosai jibi kudinda ya bani "ya fiddo yan 200 guda biyar da yabashi sabbi fill 

Ummi batabi kan maganar shi ba hankalin ta na kan faseelat daketa murmushi ummi tace "wai lpya kike ta dariya ke daya "

Faseelat ta daure fuska "bakomi "tashige daki da sauri 

Ummi tace "hmmm Allah ya shirya ki "

Ta Shiga dakinta, tana zare hijabin jikinta ta jawo bakkon ta bude kaya niki -niki, ta fiddo Ice cream da snacks din ta ajiye gefe guda, 

Kudin da ya ajiye ta kirga nera dubu goma ciff ummi tai murmushi ta jawo wayarta tace "bari na kira hjy saratu nai mata godiya "

Batare da tunanin komi ba ta dannawa lambarta kira.....
[6/27, 16:33] +234 802 797 9297: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰




By 


*MAMAN MAMY*




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION???~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*




?




Ringing biyu Hjy saratu ta daga bayan  gaishe gaishe ummi tace "yanzu khalil ya fita yashigo har gida mungaisa, mun gode da abun arziki "

Hjy saratu tana ta faraa kamar duka knan tace "ah bakomi wlh ai anzama miye aciki "

Sukai bankwana ummi Nata godiya sede bata fada mata yakawo wani abu ba Hjy saratu tace "hmmm yanzu haka wani abun ya kai musu, kowa na haramar tafiya masallaci shi yanata surukai," taja dogon numfashi "nasan abinda zanyi komi zezo karshe "

Shi ko khalil masallaci ya wuce daga gidansu faseelat, hankali kwance, gabadaya jiyake kamar bashi ba, soyayya ta fara sauya masa rayuwa. 

Faseelat kau seda ta shiga daki ta kara jan tsaki "komiye na mishi dariya ma?  Nan fa se yayi tunanin tafara sonshi ne "ta kara jan tsoki, 

Ta jawo wayarta messages sungama shigowa abinda ta lura groups dinta Sun ragu dama inka dade baka online groups fita suke, bin groups din tafara yi taga wadanda suka fitar daita, 

Taga kusan group bakwai ta fita, se tafara bin numbers dinta tayi wa friend dinta magana a medata wasu ,akwai wani group sirrin mu mata, shi ta fara shiga saboda tanajin dadin group din, messages din wasu Sun bude wasu basu bude ba, tatura sallama ,suka amsa tace "plss masu group suyi adding dina ko abada number ta asani nadade bani online ne "

Se akafara mata reply da welcome masu turo sticker na turowa, wata me suna maman amira tace akwai wani group amma se kinbiya 500 ake adding naki ana karuwa sosai ciki,

faseelat tace "anayin share and self? "

Maman amira ta turo mata "eh anayi,  Ko kati ko BTU ko transfer "

Faseelat tace "kiban no din admin zantura mishi through share and self saboda banda kudi "

maman amira tace "ayya zan biyamiki asaki ki dan jira "

Faseelat tace "amma de Nagode aunty Allah yaraya amira "

maman amira ta turo mata smile face. 



daganan faseelat tai taganin new groups na matan aure wasu na novels ana sakata, 


Seta bi maman amira PC tana mata godiya maman amira tace karkidamu sister sunanki kawai ya burgeni ,faseelat tace zan'iya adding number dinki? 

maman amira tace"yes zakiiya nima zanyi adding taki "

Faseelat ta tura mata thanks you" (the Fateful relationship just begun) 

Ko minti 10 baaiba akayi adding nata ta tura" slm "

Maman amira taturo "you are highly welcome friend "

Faseelat tace "I'm grateful "

Fitowa tai a group din tafara bin status daya bayan daya sannan ta sauka online,

fitsari ne ya matseta ta tashi tafita waje dasauri, 

Ummi tagani tafito daga kitchen hiyaki ya korota, tai sauri tashige toilet ta biya bukata ta dawo, ta tafi gun ummi "ummi for god sake miyasa kikeson wahalar da kanki nace naji sauki kibari nayi "

ummi tace "ai gwara narinka shiga ciki ko na saba tunda tafiya zaki kibarni ni daya "

Faseelat tace "eh naji amma bari nashiga inbani nan kyayi din "
Ta kutsa kai kitchen din duk da hiyakinsa inda sabo ta saba .

Hjy saratu kau alhaji ta dannawa kira, bayan ya amsa yace "lpy de ko kira gab Shiga salla "

Tace "eh dama so nike ince maka inason zamuyi magana inka dawo "

yace "To saurin mi akeyi da antaso masallaci zanshigo gidan "
Ko to batace ba ta yanke kiran, 

Siyama ta fito daga kitchen tana kai abinci daki har ta gama sannan ta zauna tana "wash Allah na "

Hjy ta kure ta da ido tace "wannan dan aikin? To ko de ciki gareki "
Siyama tai murmushi batare da tace komi ba, 

Hjy tai dariya "to Allah ya raba lpy "

Siyama tai tsit can tace "bari naje nai salla "

Hjy tace "har lokaci yayi ne "

Tace "eh karfe 1:40pm"

Hjy tace "bari mutashi muma "


Ana saukowa masallaci alhaji ya taho gida yana shiga da sallama bakinsa yaran siyama suka gudu suka tarboshi ya tallabo kawunansu sukayi ciki, yanata jindadi, 

Dakinshi ya wuce kai tsaye ya rage kayan jikinshi ya dan kishingida sega siyama takawo masa abincinsa suka gaisa ya mata ya jiki ta fita tareda yaran. 

Yana tsakiyar cin abinci Hjy tashigo ta zauna sannan tace "sannu da zuwa "

yace "yawwa yana Kai loma bakinsa "

yace "wai maganar mi cece da baajira na dawo "

Tace "dama bawata magana bace seta khalil da faseelat "

Ya ajiye cokalin hannunsa yace "inajinki"

Tace "nace mi zaihana akai kudin neman aurensu tunda de akwai su, bayan ansa rana se su cigaba da fahimtar juna kafin auren, nasan shima khalil din zeso hakan."

yadanyi nazari for some minutes sannan yace "yanzu de kifara yiwa mamanta maganar duk yadda kukai se inji saboda kamar abun yayi wuri "

Tace "haba bawani matsala amma bari na kirata "

ta kwalawa siyama kira tace mata ta miko mata wayarta, takawo mata ta juya. 


hjy tayi dialing number ummi 

Tadanyi ringing sannan ummi ta dauka da sallama, 

Hjy tace "kinga na sake kira ko,dama maganar yarannan ce to munyi magana da alhaji kiyi magana da abbansu in anbada izini zaaturo "

Ummi tace "to ba matsala nasan yanakan hanyar dawowa Inya dawo zamuyi maganar duk yadda mukayi zakiji "

Hjy tace "to Nagode kwarai se na jiki "
Ta yanke kiran 

Alhaji bece komi ba ya cigaba da cin abincinsa.

Khalil siyama nafita ya shigo tafara zaulayar shi, yana dariya yace "siyama bakiji ni kuma ake zolaya? Ni yayan. "

Tace "hmm yaya kenan ,yanzu de kabar number anty ta mufara gaisawa "

yace "zanbaki amma ba yanzu ba, kije ki daukomun abinci na tukun inna gama se muyi maganar "

Ta kawo masa abincin yafara ci dan mutuminnaku be wasa da k'oto. 


Seda ummi tabari abba yagama cika cikinsa da daddadan abincin da faseelat ta dafa sannan tafada mishi yadda akai yace "kunde nace ga hadin nan auren hadi matsala ne dashi in aka samu sabani, "

Ummi tace "insha Allah bawata matsala"

Yace "to yanzu de su bamu lokaci kamar nanda sati daya, dan inaso nayi bincike, bama wannan ba ita faseelat din ta amince ne? "

Ummi tace "eh mana ko akirata ka tambayeta? "

Yace "eh kiramin ita "

Ummi tatashi ta fita kiranta daga can bata dawo dakinba, 

Faseelat ta zauna "gani abba"

ya kalleta sannan yace "kinji iyayen khalil zasu aiko me kikace? "

Faseelat gabanta ba karamin faduwa yayi ba tai shiru ta sadda kai kasa, 

Abba yace "kin amince? Yanzu kina sonshin? "

Kuka ne yazowa faseelat tai saurin rufe fuskarta da hijabin jikinta, 

Abba yayi tunanin ko kunya ce yace "to tashi kije? "

Ta tashi da gudu tashiga dakinta ta fara kuka me cin rai.
[6/27, 16:33] +234 802 797 9297: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰





By 


*MAMAN MAMY*




https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION???~*


*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*



*dedicated to rano sister*



1⃣1⃣



Kukan nata bame sauti bane ,zeyi wuya kaji shi inba dakin kake ba, 

Tadau tsayin minti 15  tanayi, se tafara magana da zuciyar ta, 

"ba kince bazaki kara kuka ba to me kikeyi yanzu"

Dayar zuciyar tace "i have to ko don na rage zafin da ke tsatstsafowa a raina"

Dayar zuciyar ta tace " you're only wasting your tear, ba abinda zaafasa, so you better stop it"

"you are right fa "ta sa hannu ta share hawayen nata. 

Tambayar zuciyarta take "to me yakamata nayi? "

Dayar tace "don't ever take decision in haste, kibari ayi auren mana "

Shiru tayi tana tunani 

Can zuwa ta Saki murmushi ita kadai tasan abinda ta kulla, se ta mike zaune, ta jawo wayarta ta fara chart. 

Bangaren khalil ko seda cikin shi ya cika tabbb sannan yasha ruwa sukafara labari da kanwar shi, har yabata number faseelat din kamar yadda ta bukata, shiru shiru Hjyrsu bata fito ba seya fita zuwa wurin best friend nashi wanda suke tun suna yara amma saboda irin yanayin khalil basa sharing problems nasu ma juna, ana taren ne kawai. 


Ummi na komawa abba yace "ba matsala tunda ta yarda ki kira ita hjyar ki fadamata yadda mukayi "

Ummi tace "to "
Ta kira hjy tafada mata duk da de hjy ba haka tasoba amma se tace "ai bakomi sati ai kamar gobe ne "

Alhaji najin yadda Sukai yace "to Allah yakaimu satin zanyiwa su yakubu magana dan su shirya da sunbamu rana se suje "

hjy saratu tai murmushin jindadi. 


Faseelat na tsaka da charting kiran siyama ya shigo ta dauka tai sallama, daga can bangaren aka amsa, 

Akace "antinmu inawuni "

Faseelat tace Anti kuma? Ai batada kanwa mace sannan bama haka ake kiran taba ta daure tace "wa ke magana? "

Siyama tace "kanwar mijinki ce siyama"




 sora kirisss faseelat tai ta bargaza dan harta hade baki da niyyar yin tsoki tai saurin fasawa, tace "ina yini "

Siyama tace "lpy lau anty dama cema yaya nayi yaban number ki mugaisa "

Faseelat tace "ihhhhn Nagode "

Siyama tace "bakomi se anjima agaida su ummi "

Faseelat tace "ihhhhm "takatse kiran ta turo baki gaba tare da cewa "Se kuyi tayi ai nide nawa ido"

Kiran wata number yashigo wayarta da alamu number Niger ce saboda digit din farkon number din, tadesan baze wuce danginsu ba ko ya umar, yaushe rabon ma suyi waya ankwana biyu 

Ta daga kiran ta kara wayar a kunne "assalamu alaikum"
Ta fada ,murmushi ya doki kunnenta akace "waalaikumussalam"

Tunda taji murmushin ta gane me magana, yanayin yanda ya amsa mata sallama da zolaya ya sata tafara dariya, 

Tana dariya tace "yaya na, kaine kamanta dani kwana biyu ko? "

shima yayi dariyan yace "ina ni ina mantawa dake duk in mukayi waya da ummi ina cewa ta gaidaki bata fadamiki ne? "

"Allah ni bata fadamin"ta zumburo baki kamar yana ganinta.

Yace "to laifin ummi ne ba nawa ba tunda kinsan bakida waya yanzu ma hakanan nace bari nakira layinki se gashi tafara ringing, kice baba babba har ya siyi wata, dan nasan ummi de bazata se miki waya ba tunda kudinta kaff suna karewa ne wurin se miki cosmetics, kuma nasan abba baze siyamiki waya ba ya fiso ki karatu besan shiririta "

Tace "a, a ba shi yasiyamin ba fa "

Daga can yace "to waye? "


Tadanyi shiru sannan tace "yaya su ummi da abba are planning to get me married"
Tai maganar kasa -kasa. 

yace "very soon haka  with whom? "

tace "wani ne sunanshi khalil dangidan kawarta "

Yace "to, what's in your mind did you like him "

Tai shiru 

Yace "faseelat are you with me? "

tace "yeah ,honestly yaya bana sonshi but I will marry him, as they wish"

Yayi shiru saboda problem da yaji daga wurinta can zuwa yace "will you... Se yayi shiru "faseelat zama da wanda baka so, will not give you a good and peaceful marriage life, akwai wani freind dina ya auri wadda bata sonshi at the end auren mutuwa yayi dan ko 5 months ba suyi ba, "

Tace "yaya tunda de ummi na so to zanyi hakuri in aure shi haka "

Ya fitar da iska "huuuuuuh, to naji Allah yasa haka shi yafi zama alheri all the best "

Tace "amin, ina su dije su hanne su fatouma su kawu "

Yace "actually i really don't know cos nayi Week  banje gidajen su ba "

Tace "kana nan wurinsu fadila sun rike ka "

Yace "bahaka bane fa, I'm very busy we are about to start exam ,karatu ne kurum ya hana .

tace "to Allah ya bada saa, agaida ammah da su fadila da husna ka fadamusu ina missing nasu "

Yace "OK bye "

Ya kashe kiran ta sauke ajiyar zuciya da ma ace kanwa na auren yaya da ya omer kawai zata aura, ji yadda yake magana gashi kyakkyawa ga daukar  wanka best dress dinta English dress, tace "gaskiya yaya matarka ta mo re wlh"


Abba bugawa baba babba waya yayi ya fadamasa abinda ake ciki, yace baya gari se next week ze dawo amma yanzu zeyi sqeesing ya dawo, saboda shine madaurin auren faseelat, 

Abba be yi kasa a gwiwaba ya fadawa abokinshi yace Dan Allah ya masa bincike akan khalil abokin nashi yace ba matsala, sannan ya wuce wurin kannenshi yafada masa shima yace ze bincika abokinnashi har unguwarsu khalil yaje ya tambayi manyan mutane gamedashi, hakan be isaba seda yaje yasamu principal din makarantar su ya mishi bayani shima, haka suka dage bincike. 


Bayan kwana hudu zuwan khalil gidansu faseelat ya ragu inyaje yau be zuwa gobe amma suna yin waya tunda ta samu lpya shikenan se hankalinshi ya kwanta amma fa duk zuwan da zeyi se ya ajiye mata bandir din 50 nera guda biyu da Alamu canzo kudi masu yawa yayi, in yabata bata amsa shiyasa yake ajiye mata kawai ya tafi. 

Bangaren faseelat ba wani improvement saboda har yanzu de ba sonshi take ba watarana in yan wulakancin na kai inyazo ko kallonshi batayi har yakara sa inda indarshi yatafi. 



bayan sati 

baba babba ya dawo shima yasa ammishi nashi binciken duk binciken da akeyi abu daya ne ke fitowa bakinsu cewa "mutum ne me kunya da ibada kuma me yawan ambaton Allah,  gaskiya khalil ya samu yabo wurin mutane, 

Hjy saratu ko tana nan ta zuba ido akan al'amuran khalil duk da de batason wainar da yake toyawa bayan idonta ba, 

yau ummi takira ta tafada mata zasu iya turowa jibi 

Hjy saratu taji dadi sosai alhaji yana dawowa tafada mishi shi kuma yafadawa wakilansa, 

Jibi nayi sitting room din baba babba ya cika da manyan mutane su 5, akai gaishe gaishe da ciye -ciye bayan sun gabatarda kansu, sannan suka bada nera dubu 100, 
Alhaji babba da yake dattijon mutum ne yace karsu kara kawo sisi duk radda suka shirya suka wo kayan sa rana, daya daga cikin wakalan yace su ko yanzu a shirye suke buga waya kawai zeyi akawo kayan sa rana, 
Baba babba da yake abba ya bashi labarin matsalar faseelat din ya amince ,akasa rana nan da wata ukku, ko minti 15 baaiba se ga kwalayen biscuits da huhun goro biyu manya manya ana shigowa dasu, dayake dama alhajinsu khalil yayi retire shine yabude babban supervision store da kudin retire nashi. 





da Faraa abba yashigo gida ummi na masa sannu da zuwa tace "wai lpy kake ta faraa "

Yayi dariya "surukanki har sunzo sun tafi "

Tace "eh se akai yaya? "

Yace "uban diya har yasaka rana nan da 3month ran Friday "

Ummi farin ciki ya lullubeta tace "to Allah yasa alheri "

faseelat na kitchen tanajin abinda suke fada lokaci daya cikinta ya juya ji Kake kululululu, ta tashi da sauri tatafi kewaye tafara fetsa zawo,
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *RAGGON MIJI* Gimbiya 0 5,661 06-28-2019, 10:40 PM
Last Post: Gimbiya



Users browsing this thread: 1 Guest(s)