The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*AMANA TA BARMIN* by Zahra Muhammad Mahmud
#1
*AMANA TA BARMIN*
????????
 
Zahra Muhammad Mahmud
 
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

BISSMILLAHIRRAHMANIRRAHIM.

*BAN YARDA WANI KO WATA YAJUYA MIN LABARINBA,IN AKAYI NABAR MUTUM DA ALLAH*
*1-2*
 
Sauri yake zashi gurin,ayki,sabida yayi latti,dan haka hankalinshi nakan hanya.
 
Yazo danja,besaniba,saura kaɗan ya bigeta,dan har motar tafara,taɓa jikinta,da sauri yataka burki,ya fito yana kare mata kallo.
 
Ɗago da kanta tayi itama,ta haskeshi da fararen idanunta,tsintar kanshi yayi da sakin murmushi.
 
"yanmata kiyi hakuri don Allah wlh ban kula dake bane shiyasa"ya faɗi yana murmushi.
 
Itama murmushin tayi,sannan tace tana juya ido.
 
"lah karka damu,ay abun ma yazo da sauki tunda baka bugeni ba"
 
"ina kika nufa,inji ko hanyar mu daya na rage miki hanya?"
 
"kaida kace kana sauri,kaine kuma dason ragemin hanya,baka tsoron asaka a gurd room?"
 
Dariya yayi me bayyana kyanshi,sannan yagyara tsyuwar hularshi ta sojoji,yace.
 
"muda guardroom sede mukai wani,amman bamuba,kina cinye lokaci,ina kika nufane"
 
Murmushi,tayi,sannan tace.
 
"zani,yusuf dantsoho memorial hosital,ne"
 
"good hanyarmu daya,sede ni 44 zani,danhaka muje nasaukeki"
 
Ba musu tashiga motar,yaja suka tafi,ahanya yana janta da hira kamar haka.
 
"me zakije yi a asibitin?"
 
"ni nurse ce acan,shiyasa zanje"
 
"daga wacce anguwa kenanfa?"
 
"unguwar sarki"
 
"sunanki fa?"
 
"maryam"
 
daga haka sekuma sukayi shuru,zuwacan de yace mata.
 
"duk dade cewa shishshigi zanyi,amman hakan baze hanani faɗamiki sunanaba,am,captain farouk Ahmad,nigerian army,from unguwan dosa,kozan iya samun numberki?"
 
Dariya maryam tayi sannan tabashi numberta,yayi saving.
 
seda yakaita har cikin asibitin sannan,yajuya yakoma gurin nashi aykin,wato Asibitin 44.
 
yana,isa gurin ayki,ma'aikata,sojojin se sara masa sukeyi.
har ya isa office dinshi.
 
Jakar laptop dinshi ya ajiye yafice duba marasa lafiya.
 
Be baro asibitinba,se,karfe shida na yamma.
 
Tafe yake yana tunanin maryam wacce suka haɗu da safe,yarinyar ta burgeshi,game da saukin kanta,ba wulakanci ba komai,(abinda yanmatan zamani suke kira jan aji,hmmm yarinya ja aji ki tsufa gidanku).
 
Har ya isa gida yana tunaninta.
 
Yana shiga falon gidan yafara,cilli da kayan jikinshi,kamar ƙaramin yaro,ya wurga hula can,riga can,wando can,takalmi can,safa can,sannan ya zauna dagashi se singlet da gajeren wando.
 
Hajiya mahaifiyarshi ce tashigo falon,kamar kullum,da takalminshi tafara cin karo,tsayawa tayi riƙe da baki tace.
 
"Farouku wai se yaushene zaka girma,kayarda kuma ka girman?"
 
Tasowa yayi yana murmushi yace.
 
"Hajiyata Allah yajamin nisan kwananki da lafiya,matuƙar kina raye hajiyata,kullum ni yarone,ɗa duk girmansa baya girma agaban iyayensa"yaƙarasa maganar yana rungumeta.
 
Tureshi tayi sannan tafara tsince kayan nashi tace.
 
"ka kiyayeni,farouku,da daɗin bakinnan naka,wlh aure zanmaka,kajecan matarka taci gaba da kulawa dakai"
 
Dariya ya kwashe da ita,daga baya kuma ya haɗe fuska,irin shagwabarnan.yace.
 
"hajiya wacce,macece zata ɗauki ɗawainiyata,bayan ke dakike uwata kullum,cikin ƙorafi kike dani?".
 
"oho maka,kaika sani,duk inda ma zaka nemota kanemo,nide nagaji wlh,ace ƙato kamarka,baze iya adana,kayanshi ba,kullum nice zan adana maka,ruwan wanka bazaka haɗawa kanka ba kuma bazaka yarda me ayki ta haɗa maka ba dole seni,tsurfa kalakala ka iyata,gurin zaɓar abincin dazakaci,shine zanci gaba da zama dakai haka,mutumin dako takalmin ka na ayki baka iya sawaba,baka,iya sa belt ɗinka ba dukafa ninake maka farouku katausayamin kayi aure don Allah,kaji me sunan manya"
 
Dariya ya kwashe daita sannan,yafice da gudu yabarta tsaye tana bin bayanshi da kallo.
 
Ɗakinshi yanufa,kamar kullum,mahaifiyarshi,ta gyara mishi shi,sosai yayi kyau se kamshi ke tashi.
 
Wanka yashiga,yajima kamin yafito,ɗaure da alwala,ya zura doguwar riga,yafice zuwa masallaci,domin gabatar da sallar magrib.
 
Muje zuwa.
 
*AMANA TA BARMIN*
????????
  
Zahra Surbajo
 
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
 
*3-4*
 
Be dawo ba se bayan sallar isha,kai tsaye ɗakin mahaifiyarshi,yanufa.
 
Akan abun sallah yasameta zaune tana lazimi.
 
Guri yasamu yazauna,harta kammala,sannan ya matso ya kwantar da kanshi akan cinyarta,yace a shagwaɓe.
 
"Hajiya me kika dafamin yunwa nakeji"
 
"tuwon dawa akayi da miyar kuɓewa ɗanya da busasshen kifi"tabashi amsa.
 
Miƙewa yayi yanufi dinning,yacika tumbinsa,ya leƙa ɗakin hajiya yamata seda safe sannan ya haura sama ɗakinshi.
 
Koda yaje bacci tunanin maryam yahanashi sukuni,hakanne yasa ya ɗauko wayarshi yakirata,bugu biyu ana ukun ta ɗaga cikin zazzaƙar muryarta tace.
 
"salamu alaikum"
 
Shuru yayi muryar tagama ratsashi tukuna sannan yace.
 
"waalaikumussalam yanmata ykk"
 
Tund yafara magana tagano muryarshi,dan itama wuni tayi tunaninshi,cike da faraa tace.
 
"au captain ne ashe,lafiya lau nake,kaifa?"
 
Dogon fasali yaja sannan yace.
 
"kinji daɗinki niko gani kwance banida lafiya"
 
aruɗe maryam ta furta.
 
"hasbunallahu waniimal wakeel me ya sameka,captain?"
 
Murmushi yayi sannan yace.
 
"ciwon sonki maryam,tunda naganki,kin hanani sukuni,pls karkice bakya sona,kisa na hana hajiya bacci yau"yaƙarasa maganar cikin shagwaɓa,nida nake gefe nace su farouk anyiwa hajiyama mara dalili,bare wannan me dalili ce.
 
Jikin maryam gaba ɗaya yamutu da salon na farouk,rasa abunyi tayi,murna zatayi kome.
 
shi yakatseta da cewa.
 
"pls kibani amsa don Allah,karkice zakimin wulaƙancin da yanmatan zamaninnan sukewa samari da sunan jan,aji,inkinasona kawai ki faɗamin base kin wahal daniba"
 
murmushi maryam tayi danta lura farouk rigimammene na ajin farko,intace zata ja lokaci bata bashi amsa ba,ze iya samata kuka.dan haka cikin salon siye zuciya,ta furta.
 
"nima ina sonka farouk,Allah yasanya akhairi atarayyarmu dakai"
 
wata ajiyar zuciya yasaki sannan yace.
 
"Ameen my wish"
 
daga haka hira yaɗan jata daita,se da dare yafarayi sukayi sallama kowa yakwanta cike da farincikin sabuwar soyayya.
 
Washegari dawuri yatashi yatafi masallaci yana dawowa yatarar hajiya ta haɗa mishi ruwan wanka,dan haka wanka yashiga,yana fitowa ya zura kakin shi,ya ɗauki takalmin da belt a hannu yasauka kasa gurin hajiya yakaimata tasa mishi.
 
Ayko tana sawa tana mushi mitar yayi aure ita tagaji,shiko se dariya yake mata,har tagama shiryashi,yaje yaci abinci,yafice yanufi gurin ayki.
 
*********
 
Farouk Ahmad sunan shi,haifaffen garin kaduna ne,saurayine ɗan kimanin shekaru talatin da haihuwa.
 
Mahaifin farouk,Alhaji Ahmd babban soja ne,inda yake da tarin dukiya me yawa,tunda suka haifi farouk basu sake haihuwa ba abunka da ƴan boko daga uwa har uba se basu damuba suka ci gaba da kulawa da ɗansu.
 
Farouk nada shekaru goma shabiyar mahaifinshi yarasu,kamin rasuwar mahaifinshi,yadamƙawa mahaifitarshi amanar farouk,tare da roƙonta tariƙe masa amana,karta bar farouk yayi kukan maraicinshi.
 
Wannan shine maƙasudin da hajiya saude mahaifiyar farouk ta ɗauki so da ƙaunar duniya ta ɗora masa,duk da kulawar datake bashi batayi wasa da ɓangaren tarbiyyarshiba,tana bashi tarbiyya dede gwargwado.
 
Tun tasowar farouk yake da shaawar zama likita,dan haka yana gama secondry school yatafi ƙasar egypt ɗomin karantar likitanci.
 
shekarunshi bakwai acan yadawo da shaidar kammala karatunshi,bayan daeowarshine kuma yaji yana shaawar,yazama soja kamar mahaifinshi,hajiya bata hanashiba fatan alkhairi taimasa.
 
Ayko yashiga gidan soja da ƙafar dama,yana shiga yayta samun ƙarin girma har zuwa yanzu dayake riƙe da muƙamin captain,yana kuma ayki a Asibitin 44 a matsayin babban likita.
 
farouk mutumne me tarbiyya,ko kaɗan baya aykata abun Allah wadai,ƴanmata da yawa nasonshi,amman shi ba abinda yadameshi dasu.
 
Farouk kyakkyawane ajin farko,namijine shi me cikar zati,shiyasa yake da kwarjini da haiba,a idon duk wani me kallonshi.
 
wannan kenan.
 
yana isa asibitin be jimaba,yafice zuwa nasu maryam.
 
Akunyace,tazo suka fan taba hira sannan yakoma bakin aykinshi.
 
koda maryam ta tashi agurin nata aykin,shi yazo ya ɗauketa yakaita har gida sannan yadawo bakin nashi aykin.
 
*******
 
Kimanin watanni biyar kenan farouk da maryam suna soyayya,hatta iyayenta sunsan dashi,hakanne yasa mahaifita faɗawa farouk yaturo magabatanshi,inda yamusu alƙawarin zuwansu cikin satin.
 
duk abinda akeyi ko kaɗan be bari hajiya tasaniba dan so yake yabata mamaki.
 
Gurin ƙannen mahaifinshi yaje yashaida musu,kuma ya roƙesu karsu bari hajiya taji,ba musu suka amince dan suma sun ƙosa farouk ɗin yayi aure.
 
cikin satin sukaje nemawa farouk auren maryam,inda basu baro gidanba seda aka tsaida ranar aure,watanni biyu masu zuwa.
 
murna gurin farouk da maryam kamarme,duk sun ƙosa ranar tayi.
 
Yau saura wata guda bikin,su farouk tuni har ankai lefe gidan su maryam batare da hajiya tasaniba,itade kullum cikin yimasa gorin yayi aure,take,sede yayi dariya yace,
 
"hajiyata kenan insha Allahu,sena baki mamaki,wato zanyi aure batare dakin saniba se ranar da aka kawo miki amarya kisa mata albarka"
 
Wata guɗa hajiya tasaki tace.
 
"da ko inkamin haka har in mutu bazan dena samaka albarka ba zanyi farinciki fiye da tunaninka,rawar dazan taka kuwa,seka riƙeni"
 
Kullum haka yake shaida mata,ita kuma tabashi amsa da haka.
 
Duk wata hanya da hajiya zata samu labari farouk yatosheta,dan gaba ɗaya hidimar bikin gidan kawunshi dake hayin banki aka koma yi,kuma kowa ya gargaɗi iyalinshi akan kar abari hajiya taji.
 
Da yake farouk yana da gida acikin malali GRA,gyarashi yayi yamasa sabon fenti,acan akaje akayi jeren kayan amarya,nandanan gida yafito yayi kyau,se fatan Allah yakawo amarya da angon cikinsa lafiya.
 
***********
 
Rana bata ƙarya,yau aka ɗaura auran farouk da maryam,bisa jagorancin kawunnanshi.
 
Murna da farincikin da farouk da maryam suke ciki baya misaltuwa.
 
ƙarfe biyar na yamma,motocin ɗaukar amarya,sukaje suka ɗauko amarya,haka aka ɗaukota cikin rakiyar danginta se kuka takeyi.
 
baa zame ko ina da ita ba se gidan hajiya domin tasa mata albarka. 
 
muje zuwa
 
*AMANA TA BARMIN*
⛩⛩⛩⛩⛩⛩⛩⛩
 
Zahra Muhammad Mahmud
 
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
 
*5-6*
 
Hajiya na zaune a falo tanashan fruitsalad taji ƙarar buɗe get,a zatonta farouk ne amman guɗa da hayaniyar data dunga jiyowane yasa tamiƙe ta leƙa ta window.
 
Jamaa birjik a tsakar gidan sun nufo falonta,da sauri ta koma ta zauna tana zaman jiran tsammani har mutane suka shigo falon da sallamarsu.
 
Ganin matan kawunnan farouk riƙe da wata wacce ta rufe fuskarta da mayafi ne yafiba hajiya mamaki.
 
Bayan kowa ya natsu hajiya tace.
 
"da dana ganku naɗauka ɓatan kai kukayi,amman ganin idon sani acikinku yasa na fahimci ba ɓatan kai kukayiba,to don Allah kusanar dani abinda ke tafe daku,wlh duk na ruɗe"
 
Guɗa gaba ɗaya matan sukasa,sannan wata me suna sadiya acikin matan kawunnan farouk ta kama hannun maryam takaita gaban hajiya,ta kamo hannun hajiya tasaka na maryam aciki sannan tace.
 
"Ɗanmu kaifi ɗaya ne inde ya furta zeyi to seyayi,farouk yabaki mamakin daya jima yana shaida miki ze baki,to gatanan yace akawo miki kisa mata albarka,amaryarshi kenan,da kawunnanshi suka amso masa auranta yau a unguwar sarki"
 
Ido kawai hajiya take warewa jitake kamar a mafarki,wai yau itace riƙe da hannun matar farouk,zuwacan ta fashe da kuka ta jawo maryam ta rungume,tana samata albarka,gaba ɗaya falon ya kaure da murna.
 
Zuwacan hajiya tace.
 
"Tabbas farouk yasani fsrincikin dabansan iyakarsa ba mamaki ko tabbas yabani shi,dan haka nima zancika alkawarin dana masa"tana kaiwa nan tamiƙe tafara cashewa tana yin waƙoƙin da mutanan da sukeyi tana rausayawa,kowa se dariya yake,anyi anyi ta dakata amman fafur taki,tace se farouk ne ze riƙeta ta daina kamar yadda itama tasha alwashi.
 
Ayko ba shiri sadiya takira farouk awaya ta faɗamasa,da sauri yanufo gidan,haka yayta ratsa mutane ya iso filin da hajiya ke dansewa .
 
Ruƙota yayi yana dariya yace.
 
"hajiyata kema kincika alƙawarinki dan haka na riƙeki seki daina"
 
Rungumeshi tayi tasa kuka,tana fadin.
 
"farouku baka taɓa sani farinciki irin wannan ba Allah yamaka albarka kaida iyalinka gava ɗaya,wlh ina alfahari da samun ɗa guda ɗaya tamkar da dubu kamarka,dama da taron yuyuyu gwara guda ɗaya ƙwaƙƙwara"
 
Farouk yaso tafiya dan abokansho na jiranshi amman fafur hajiya riƙeshi tayi,sannan ta sallami yan kai amarya da kuɗi dubu ɗari biyar.
 
koda suka bukaci tabasu amaryar sukaita gidanta fafur hajiya tayi tsalle ta dire akan bazata bayarba,wai ay albarka aka kawota tasa mata to bata gama sawar ba,harda juyawa gurin maryam dake takure akusa da ita tace.
 
"ƴata kina jina dasu ko ke har albarkar tawa ta isheki haka nabasu ke ku tafi?"
 
A kunyace maryam ta girgiza kai.
 
gaba ɗaya matan sukasa shewa,hakade hajiya ta korasu dukansu batare data bada maryam ɗinba.
 
Shiko farouk ganin hukuncin na hajiya ne ya ɓata masa rai,dan yaga sotake ta ɓata mishi bojet,shida yasha alwashin barje guminsa a daren yau,dan haka turo baki gaba yayi.
 
Me aykice ta shigo ɗauke da tsintsiya zata tattara falon.
 
Hajiya ko se nan nan take da maryam,farouk rai aɓace yace.
 
"ammande hajiya ay ba wannan a alƙawarin da kikayi,dan haka nibanga amfanin hanasu tafiya da ita ba"
 
zabori hajiya ta cira agurin me aykin,ta bi farouk da gudu,dan dama yana ganin tafara ƙoƙarin cirowa yasan shi zata doka .
 
Haka sukaita zagaya kujeru tana faɗin.
 
"ɗan kusun uwa me kan buta,daka tsaya yau dako kaci gidanku a gurina"
 
Maryam duk yadda taso hana dariyarta fitowa seda ta fito,sabida lura da tayi daga uwar har ɗan tamkar tom and jerry suka koma,to inba tom and jerry ba,taya ƙato kamar farouk zaace zaa dokeshi da zabori kuma shi dan shegantaka harda guduw.
 
Hajiya ganin baze kamu bane yasa tasamu guri ta zauna tana haki.
 
Maryam se dariya take,daga inda farouk yake ya miƙa hannu ya dungure kan maryam din yace.
 
"ay dole kiyi dariya mana yanzu tunda kinga ƙeta,sekace ba ita bace aka ɗauko ɗazu tana kuka"
 
murmushi maryam tayi,tasake matsawa jikin hajiya dan kar yakuma dungureta.
 
dariya hajiya tayi sannan tace " ƙyaleshi,haushin na riƙeki yakeji"
 
Haka de sukaita hirar su gwanin ban dariya.
 
farouk ficewa yayi yaje ya sanar da abokansa abinda hajiya taimasa.
 
Ayko nan sukai ta masa dariya,suna tsokanarsa,ji yayi kamar yaje ya sato maryam ɗin.
 
Se goman dare ya koma gidan,lokacin hajiya da maryam nakan gadon hajiyan suna bacci,koda ya shiga ɗakin yagansu a haka,shima ta gefen da maryam take yaje yayi kwanciyarshi abunshi.
 
Hadarine agarin hakan yasa garin yayi sanyi maryam sanyi takeji hakanne yasa ta sake shigewa jikin farouk azatonta hajiya ce,shiko dama baccin yakasa ɗaukarshi musamman jin maryam dayakeyi ajikinshi,hakan ya ɗaga mishi hankali,shima rungumeta yayi sosai ajikinshi,sannan yaja bargo ya rufesu har hajiya dakecan gefen gado tana shirgar baccinta.
 
 
Koda Asuba tayi,hajiyace tafara tashi dan haka bargon ta yaye da niyyar tashin maryam,abunda ta gani ba ƙaramin mamaki ya bata ba,maryam kwance a kirjin farouk,shikuma ya rungumeta suna shan baccinsu.
 
Saɗaf saɗaf hajiya tamiƙe ta fice daga ɗakin,cike da jin kunyar abunda farouk yayi,"dana sani nabashi matarshi sun tafi gidansu su ƙarata"hajiya ta furta sanda ta ke ƙoƙarin,shiga ɗayan ɗakinta.
 
muje zuwa 
 
*AMANA TA BARMIN*
⛩⛩⛩⛩⛩⛩⛩⛩
 
Zahra Muhammad Mahmud
 
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
 
*Sadaukarwa ga duka members na groups ɗina,sonku ajinina yake,kuna sani nishaɗi,Allah ya karemin ku acikin kariyar sa,seda ku surbajo ke haskawa dan haka,kune kashin bayan zahra,Allah yasadamu a Aljannarsa Ameen*
 
*7-8*
 
Maryam ce tafara farkawa,jinta ajikin mutum ne yasa tayi saurin buɗe idonta,
 
Ganin farouk rungume da ita ba ƙaramin tada hankalinta yayiba,da sauri takai dubanta inda hajiya ke kwance wayam batanan.
 
Motsintane ya farkar dashi,sake jawota yayi,duka takaimishi sannan tafara da cewa.
 
"haba don girman Allah me ka jawo min kenan,?wannan sam bedace ba ay se kasa hajiya tayi zaton damacan mu ƴan iskane"
 
Dariya yayi yamiƙe zaune sannan yace.
 
"Hajiyata ba irin hajiyoyin da kika saba gani bane,ita tadabance,dan haka ki adana kalamanki,ayni mijinkine dan haka babu komai aciki danna kwana jikinki,bari ma kigani"hannu yasa ze kamota da sauri ta miƙe ta sauka agadon,
 
Dariya farouk yayi sannan yace.
 
"wlh ba wanda yakai amare gulma,jita don Allah sekace ba ita bace tagama shan baccinta ajikina ba,wai amman yanzu zatamin borin kunya"ya ƙarasa maganar yana dariya.
 
maryam durƙushewa tayi agurin tana kukan kunyar haɗuwa da hajiya,shiko ko ajikinshi se tsokanarta yakeyi.
 
Toilet yashige ya ɗauro alwala yazo yayi sallah,yana idarwa yafice yabar maryam dake tashan kukanta.
 
da kyar tamiƙe tashiga toilet tayo alwala tazo tayi sallah.
 
Shiko yana fita, ɗakin hajiya yashiga,wacce ke zaune abun duniya ya isheta,da sallamarshi yashiga yana sosa ƙeya.
 
jikinta yaje ya kwanta yana dariya yace.
 
"Hajiyata shine kika tashi mu baki tashemu munyi sallah ba ko"
 
Duka takaimishi sannan tace.
 
"farouku kafita daga idona,rashin kunyarka ta isheni wlh,yanzu shine kabiyomu ɗaki ka kwana tare damu to wlh katashi yanzu ka kwasheta ku tafi gidanku dan wlh ko abincina bazan bakuba"
 
Dariya farouk yakeyi harda tuntsirawa,sannan yace.
 
"hajiyata kenan,da banje na kwanta ba nasan se kinjamin rai kamin kibani matata,yanzu kuwa base anjima ba zamu tafi"
 
Da gudu yabar dakin yanufi wanda maryam ke ciki,yana zuwa yace.
 
"to kinji daɗi ay gashinan kin janyo hajiya tace mubar mata gidanta,ni wlh bakimin adalciba,ina zaman zamana kika kwanta ajikina,gashi kinja tace ko abinci bazata bamu ba"
 
maryam kara tsananta kukanta tayi,dan ɗauka tayi hajiya tayi fushi dasune,shiko se tsokanarta yakeyi.
 
Fafur taƙi miƙewa su tafi dan haka sungumarta yayi yafice da ita,se dukanshi take akan ya sauketa amnan fafur yaƙi,har yakai bakin falo ya tuno beyiwa hajiya sallamah ba dan haka juyawa yayi yanufi ɗakin nata ɗauke da maryam a hannunshi,kuka take masa akan yataimaka ya ajiyeta amman ko ajikinshi,
 
haka yatura ƙofar ɗakin hajiya hashiga ɗauke da ita,hajiya na ganinsu,filo ta ɗauka ta biyo shi da gudu,ayko juyawa yayi da gudu yana faɗin.
 
"dama sallamah mukazo yimiki"
 
"wlh farouku kabari na kamaka jikinka se ya fada maka,mara kunya kawai"cewar hajiya dake biye dasu da filo a hannu zata daki farouk.
 
shiko ɗauke da maryam se gudu yake tirƙa,yana dariya,hajiya bata kyalesuba seda suka fice daga falon,ta maida ƙofar ta kulle.
 
jingina tayi da ƙofar tana dariya,tana godewa Allah daya bata suruka me kunya,gamida yima Allah godiya daya bata farouk amatsayin ɗanta.
 
Adduar samun zaman lafiya,da zuria ta gari tayi musu sannan ta wuce kitchen tana dariyar dramer tasu da faroukun nata
 
shiko seda ya dangana maryam da mota sannan ya sauketa aciki,zagawa yayi yatada motar suka fice daga gidan,maryam se rusa kuka takeyi,yayinda gefe ɗaya kuma dariyar biyosu da fulon da hajiya tayi takeyi.
 
shiko farouk se tsokanarta yakeyi ahaka har suka is gidansu.
 
muje zuwa
 
 
Surbajo for life.

*AMANA TA BARMIN*
????????
 
Zahra Surbajo.
 
DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION
 
*Sanya d'an'uwanka musulmi farinciki da nishad'i sadaka ne,sadaka kuma tana maganin masifa da bala'i,hakan tasa nasha alwashin ci gaba dayin sadaka,koda kuwa idan na d'ago idona acikin na Abubakar shek'au zan sauke*
 
*9-10*
 
Koda suka isa gidansu maryam bata dena yimasa kuka ba,
  
Shi kuma bedena yimata dariya ba,dan kukan nata dariya yake bashi.
 
A falo ya sauketa shikuma ya nufi dakinshi yayi wanka,ya shirya,sannan yafito falon,
  
Still tana zaune  a inda ya barta,zama serious yayi sannan yanufeta,
 
Tsugunnawa yayi agabanta ya ɗora hannunsa akan cinyarta yasoma magana.
 
"haba baby na,yanzu shikenan kin dawwama kuka kenan akan abunda bana kuka ba,?hajiyata fa ba irin surukar da kika sani bace,dan ita bataki kuyi wasan guje guje kamar yadda kike ganin tanayi dani,bata da damuwa ko ta kwabo,don Allah karkisa nafara zargin kaina da sanya babyna damuwa pls"ya fadi yana me kwantar da kanshi akan cinyarta.
 
Tausayinshine yakamata,dena kukan tayi ta kwantar da nata kan akan nashi,ahaka take fadin.
 
"baby karka damu kanka kunyace tasani kuka ba komai ba,amman tunda hajiya me fahimtace nadena damuwa,don Allah ka kwantar da hankalinka"ta ƙarasa zancan tana shafa gashin kanshi.
 
Suna haka suka tsinkayi sallamar megadi abakin falon.
 
Farouk ne yaje dan ganin abinda yakawoshi,yana buɗe kofar yaganshi ɗauke da basket din abinci.
 
"ya akayi baba?"cewar farouk.
 
"direban hajiyane ya kawo wannan yanzu wai inji hajiya tace akawo muku"cewar megadi.
 
Murmushi farouk yayi ya amshi basket din ya koma ciki.
 
Maryam na ganin shi da basket din tamike taje ta amsa,suka kai dinning,sannan ta ce tana kallon shi.
 
"Baby ina kasamo mana gara har haka?"
 
Jawota yayi jikinshi yana dan shinshinata ya raɗa mata akunne.
 
"Hajiyar da kika dauka fushi tayi damuce ta ayko mana dashi"
 
sunne kai maryam tayi,dan zamewa tayi zata haura sama,da sauri,farouk ya janyota ta dawo jikinshi,
 
Haduwar jikinsu awannan lokacin ya haifarmusu da bakon yanayi,hannunshi ya dora akan mazaunanta,yayin da ita kuma,hannunta daya na kan kirjinshi,ɗayan kuma yana ta bayanshi,ta kwantar da kanta akan kirjin,
 
rankwafowa yayi dede setin kunnenta yace.
 
"ina zaki tafi kibarni?"
 
Cike da shagwaɓa tace.
 
"wankafa nima zani nayi"
 
"inzo in tayaki?"
 
noƙe kafaɗa tayi sannan tace.
 
"A a nide banaso"
 
"to in ni kuma ina so fa?"
 
"kai baby don Allah kadena wannan maganar ni wlh kunya kake bani"
 
Dariya yayi gami da daukanta cak suka nufi ɗakin ta.
 
Akan gado ya ajiyeta yazauna shima yana haki.kallonshi tayi adan kaikaice tace.
 
"lafiya kake wannan hakin sekace kaɗauko katon dutse?"
 
murmushi yayi yana shafo mazaunanta yace yana daga mata gira.
 
"ba gwanda katon dutseba,wannan taragon dana ɗauko ayshi kaɗaima ya isheni inyi haki"ya karasa zancan yana dariya.
 
batun kunya yaba maryam,da gudu tamiƙe ta shige toilet,ta kullo ƙofar,ta fara wankanta tana dariya.
 
Shima kwanciya yayi akan gadon yana dariya.
 
ta jima kamin ta fito ɗaure da tawul,yayinda ta rufo wani akanta,tana ɗan ɓoye fuskarta aciki,alamun kunya.
 
Ganin hakane yasa farouk miƙewa yafice daga ɗakin yana dariya yanufi falo.
 
Se alokacin tasake ta shirya,cikin sabuwar atamfarta riga da siket dinkin zamani.
 
Tayi kyau sosai,sannan ta feshe jikinta da turare,ta nufi falon cikin tafiyar kasaita.
 
farouk yana hangota yataso yazo ya tarbeta,suka nufi dinning,se yaba kwalliyarta yakeyi.
 
Akan cinyarshi ya ɗorata,ahaka suka ci abincin suka gama.
 
Fita yayi yakaiwa megadi nashi sannan ya ce mishi,koda wani yazo kar abarshi yashigo.
 
Dawow yayi yasamu maryam harta gyara gurin,tana kitchen tana so tayi wanke wanke,shiga kitchen din yayi,se jitayi ya sureta sunyi dakin sa.
 
Sun shiga be ajiyeta ako inaba se toilet,yasa ta dauro alwala shima yayi,suka fito yajasu,sallah raka biyu.
 
Bayan sun idar,tambayoyi yamata game da addinin ta tabashi amsa daidai gwargwado.
 
Daganan labarin yafara canjawa.
 
Daukarta yayi ya aza bisa kan gado,rokonshi maryam tashigayi akan ya kyaleta se dare,shiko ko ajikinshi yashiga rabata da kayan jikinta.
 
Maryam ganin ba kyaleta zeyi bane yasa ta hakura ta mika wuya,yaci gaba da sarrafata son ranshi.
 
Seda ya dirji sadakin shi da kyau sannan ya hakura ya kyaleta,shima badan ya gajiba sedan tusaya mata dayayi.
 
ita ko hawayene kawai kebin fuskarta,sabida iya azaba tashata,sede dauriya kawai datayi.
 
Duk tausayinta yagama kamashi,rungumota yayi jikinshi yana samata albarka,gamida bata hakuri,
 
murmushi tayi,ta ɗora hannunta akan lips dinshi tace.
 
"dan ka rarrasheni bakayi laifiba sabida na cancanci ka rarrashenin,amman batun bani hakuri wannan laifine,sabida ba laifi kayiminba,kayankane kuma ka karba ba zancan ban hakuri"
 
Wani daɗine ya ziyarci zuciyar farouk gamida zazzafar kaunar maryam,dake bin duk wata gaba ta jikinshi.
 
Dakanshi yamata wanka,sannan yabarta tayi na tsarki da kanta,ya naɗota a tawul kamar jaririya yazo ya kwantar da ita,sannan shima yashiga yayi,yafito kan gadon ya hayw yajawota jikinshi,suka shiga baccin safe.
 
muje zuwa.
 
surbajo for life.
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 2 36,320 09-14-2018, 12:13 PM
Last Post: Gimbiya
  *KANO TO JIDDAH* by Zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 9 111,928 09-05-2018, 06:57 PM
Last Post: Gimbiya
  *Y'ar Bautar K'asa* A Youth Corper*by Zahra Surbajo Gimbiya 1 17,110 08-10-2018, 01:58 PM
Last Post: Gimbiya
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 0 18,162 07-26-2018, 12:53 PM
Last Post: Gimbiya
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 0 33,643 07-16-2018, 03:44 PM
Last Post: Gimbiya
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 0 13,366 06-26-2018, 01:07 PM
Last Post: Gimbiya
  *KARAN BANA* by zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 0 15,622 06-19-2018, 01:08 PM
Last Post: Gimbiya
  *KANO TO JIDDAH* by Zahra Muhammad Mahmud Gimbiya 1 73,766 12-07-2017, 03:17 PM
Last Post: Gimbiya



Users browsing this thread: 1 Guest(s)