The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/showthread.php 26 require_once
Warning [2] Undefined array key "mybb" - Line: 1952 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 1952 errorHandler->error
/inc/functions_indicators.php 41 my_set_array_cookie
/showthread.php 629 mark_thread_read
Warning [2] Undefined property: MyLanguage::$ratings_update_error - Line: 5 - File: showthread.php(732) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(732) : eval()'d code 5 errorHandler->error
/showthread.php 732 eval
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "additionalgroups" - Line: 7162 - File: inc/functions.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions.php 7162 errorHandler->error
/inc/functions_user.php 844 is_member
/inc/functions_post.php 406 purgespammer_show
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "profilefield" - Line: 6 - File: inc/functions_post.php(474) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php(474) : eval()'d code 6 errorHandler->error
/inc/functions_post.php 474 eval
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 741 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 741 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 746 - File: inc/functions_post.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/inc/functions_post.php 746 errorHandler->error
/showthread.php 1070 build_postbit
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "threadprefix" - Line: 4 - File: showthread.php(1168) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1168) : eval()'d code 4 errorHandler->error
/showthread.php 1168 eval
Warning [2] Undefined array key "invisible" - Line: 1506 - File: showthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php 1506 errorHandler->error
Warning [2] Undefined variable $threadnotesbox - Line: 30 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 30 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $addremovesubscription - Line: 79 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 79 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval
Warning [2] Undefined variable $forumjump - Line: 86 - File: showthread.php(1533) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/showthread.php(1533) : eval()'d code 86 errorHandler->error
/showthread.php 1533 eval




Thread Rating:
  • 0 Vote(s) - 0 Average
  • 1
  • 2
  • 3
  • 4
  • 5
*KASUWANCI NA* by ASMABAFFA
#1
KASUWANCI NA

6-10


Official


By
AsmaBaffa

AUTA kema wannan page Sadaukarwa ce gareki.


Tafiya nake ina tunani har na Isa bakin titi ina jiran na shiga Napep shuru shuru ba taxi ba Napep kowacce a cike suke,wata dalleliyar motace tayi parking a gabana tunanina Namiji ne irin samari yan iska masu ragewa mata hanya a nemesu nan take na kara tamke fuska na dauke kaina na kalli can gefen hanya,wani kamshi naji ya cika wajen sakamakon bude murfin motar dake Saitina da akayi sai lokacin na kalli me fitowar ba kowa bane face yan matan nan na gidan Saurayi Aayan wanda suka min dukan tsiya sune su biyu suka fito a zafafe kida na tashi a motarsu sunci uban kyau ko ina zasu je oho,ina cikin wannan tunani sai ji nayi an sharara min ruwa a jikina me sanyi,a firgice na kallesu da mamaki,nan suka sheke min da Dariya dayar ta fusgo min Hijab tare da shakeni,dayar ta duro min ashar tare da cewa ubanwa kika zaga har gidanmu?dama nace wlh duk ranar dana ganki sai kin San wa kika yiwa rashin kunya wato har iyayenmu ko?

     Dayar data shakeni ta tsandara min mari tace Wai ke face to face harda zagin ya Aayan ke din banza kucaka yar matsiyata kin San su waye ubanmu har zaki bude rubabben bakinki ki zagi kakarmu who are u me kwakwalwar dusa banza gaja.

  Wani bakin ciki da bacin rai ya taso min duk saurin kuka na haka na danne shi,dama cikin haushin masu kudi nake ga bacin ran halin da muke ciki,nan take na kasa hakuri nima nace kune dai gajoji yan iska tsinannu na shaki wacce ta shakeni nima na zuba mata Mari me lafiya,nan take ta shakeni tare da Dafe kuncinta, dayar ta taso a fusace kafin ta karaso na tsuguna tare da kwaso kafafunta ji kake Tim ta fadi gefen titi,na bita kuwa tare da jawo kafarta kaiiiii kowa yana kallo ina janta a kasa tana ihu,na hau kanta tare da Zama daram na rufeta da duka tako ina,wacce na mara kuwa da sauri tazo kaina itama ta hau dukana,muna ta faman yi,ga yara da mutane sun taru ana kokarin rabamu amma Sam munki Hakura yi kawai mukeyi,
    Wata motace dalleliya ta kara parking a gaban ta yan mata wata budurwa itace wacce muka samu tare suna rawa ranar da muka je gidan Polio da gudu ta taho tana yiwa yan Uwanta magana Ku kyale matsiyata Ku zo mu tafi pls wannan ba Class dinku bace Ladies pls,babu wanda ya kulata da takalminta me shegen tsini,gani tayi babu me hakura kawai ta daga waya ta kira Babansu tare da fada masa Address din inda muke,Nan take sai ga arnayen Motocin Aayan sunyi parking sun kai su bakwai da securities,yana zuwa ya fito cikin Takun mashahurin Namiji yau sanye yake cikin farar shadda dinkin fitted dai dai jikinsa ya dau matukar kyau ga wani arnen glass  Brown a fuskarsa ba karamin kyau yayi ba,ganinsa yana tahowa nayi matukar firgita kamar zanyi fitsari sabo da na tsorata bazan manta da dukan da yayi min ba,ban San sanda na hantsilar da dayar daga jikina ba na tashi daga kan dayar da nake zaune na gyara hijab dina na kwashe da uban gudu kamar zan tashi sama,ina danyin nesa dasu na tsaya ina maida Numfashi,shi kuwa baima tunani ba Sam bai gane ni ba amma ya tabbata ya sanni.
 
    Ina kallonsa ya karasa wajensu ya kama yan matan nan ya dinka kwada musu mari ba ji ba gani yana ball dasu sai da ya canja musu kamanni sannan ya fada mota yace Securities su kamo ni,banyi tunanin wajena zasu zo ba ina ta kokarin tare Napep amma babu,kawai sai motoci na gani sun zagayeni,kafin kace me Sojoji sun zagayeni ba hanyar guduwa.
    Saurayin ne ya fito cike da jin kai ya kalleni da kyawawan idonsa,kwarjininsa da haibarsa sun cika min zuciya nayi kasa da kaina har gabana ya matso tabbas nice ya gane nice naje har gida na zagesu da Iyayensu,nan take yace a sa masa ni a mota ko ta wanne Hali,Kuka na fashe dashi me karfi ina rokonsa wayyo uwata wlh ni ba yar uwarku bace baka da dalilin hukuntani,yana jina ko kallona baiyi ba nan take suka jefani a mota suka figi motocinsu dani a ciki,Su kuma yan matan da kyar suka shiga mota daya me jarabar son girma ta jasu sannan tayi waya aka zo tare da daukan motar tata da ta bari gefen titi,Hospital ta wuce dasu aka yi musu Dressing tare da magani sannan suka tafi gida.

      Ina cikin bayan wata mota Sanyin Ac sai kadani yake na dunkule waje daya ina ta faman Rusa kuka cewar an saceni za a yanke min kai,ta window naga mun shigo wani katafaren Building na gasken gasken komai glass ne fadin tsaruwar wannan building bata baki ne ashe wai Office din wannan hadadden saurayin ne,harda su Lifter, ko ina Flowers kamar wani Hotel don a Hotel din ma sai shahararre,ina kallo suka sa Lock tare da kulleni ni kadai a motar tun 9am suka shige ciki ina ta sa ran zasu fito gashi motar taki budewa,na rasa yanda zanyi,11am shuru,12pm tuni nayi bacci a cikin motar,3pm dai dai na farka daga baccin daya saceni a cikin motar tun 12 na fara baccin,yunwa taci har ta cinye amma banga Alamar zasu fito ba Sam,tun ina kuka har na hakura gashi banyi ko Sallah ba ni da bana kauna na hada Sallah sabo da gaskiya Allah yasa min son Addini sosai,ganin basu da niyyar fitowa kawai na fara karatun Qurani a hankali sai da nayi ya kai izu biyu sannan na koma tasbihi da sauran Zikhri dana iya,ina ta yin abina bilhakki da gaskiya ina adduar Allah ya kawo silar samun kudin asibiti na Ammah kuma Allah yasa ta warke,yunwa ta addabeni da kishirwa,5pm naga hadadde ya fito cikin shigar 3qtr fari da riga Armless red kamar ka saceshi ka gudu sabo da haduwa ta ko ina,kallonsa nake tayi ina tasbihi ga yanda ya zubawa wannan Saurayi baiwar kyau,sura, ga iya daukan wanka,uwa uba ga nutsuwa Kwarjini da haiba,Securities suna take masa baya yana gaba da robar ruwa a hannunsa,da sauri suka bude masa mota ya shiga ga yan Jarida suna binsu da gudu suna jefa masa tambayoyi amma ko bude baki baiyi ba bare ya basu amsa haka aka bude masa mota ya shiga sannan Securities suka shiga nasu harda motar da nake ciki suka figa muka bar wajen,ina ta mamaki ko ya manta dani gashi nasan Ammah da yan uwana yanzu sun shiga wani a kan rashin dawowata,

     Wata katafariyar Unguwa ta masu Hanu da shuni muka nufa ina mamaki nan kuma kamar a turai wacce GRA ce wannan haka?domin nasan Ba Unguwarsu bace wannan,Harga Allah wannan Saurayi wato Aayan ya manta dani a cikin mota,direct Gidansa wanda babu wanda yasan dashi nan ya nufa,gidan fadin haduwarsa da tsaruwarsa bata baki ne ya wuce duk inda ake tunani,gidane na fada wanda kafin a sami irinsa sai dai ko a turai ko Abuja watakil,sunayin parking a compound duk suka firfito aka bude masa ya kallesu tare da basu Umarnin su kwashe motocin su kaisu main Family House tunda yana da motoci iri iri a cikin wannan gidan kalarsu daban masu shegen kyau jibga jibga,daya daga ciki ne ya sanar dashi yarinyar fa? Sai lokacin ya tuna da ina ciki,tsaki yaja sannan yace a fito masa dani su kuma su tafi Gida.
    Nan take aka yo waje dani suka figi motoci suka bar gidan daga ni sai wannan Matashi Aayan me cikar zati da kwarjini.

    Shuru nayi tare da sunkiyar da kaina kasa ina wasa da yatsun hannuna jikina yana bari kamar mazari,Kallo daya yayi min wani na mugun wulakanci tare da rainin hankali yana yatsina fuska kamar yaga kashi,nayi mugun raina kaina domin bani da maraba da Almajira mara galibu,juyawa yayi cike da takama hannunsa cikin aljihun wandonsa daya hannun kuma yana latsa waya yace let's go,bana jin turanci amma na gane go din kawai nabi bayan sa kamar Munafuka burina kawai ya kyaleni na tafi gida abina.

    Code number ya danna nan take kofar ta bude ya shiga nima haka,Wow ai ciki Aljannar duniyace kawai komai na Alfarma abin ba a cewa komai domin shagala nayi wajen kallo ina mamakin kudin wannan matashin komai Allah ya bashi.
    Steps ya hau na bene,har na taka zan bishi ya daga min hannu alamar na tsaya tare da zabga min uwar Harara yana tsaki,a tsorace na kame a wajen,tunda ya shiga ya mugun dadewa har ana shirin Magrib sannan ya fito sanye da farar jallabiya fara fitted a jikinsa yana sheka uban kamshi,ina tsaye kamar gunki yazo ya wuce ni kamar Allah bai halacci dan Adam ba haka ya wuce ya fita daga palon sai karar mota naji da alama ya fita Ashe Sallah ya tafi masallaci,nan take naga tsaiwa baza ta kaini ba kawai na fara duba dakuna gaba daya dake cikin palon kasa Allah ya taimakeni ina bude wata kofa na hango makeken daki dauke da lafiyayyan gado da mudubi tare da sip na Alfarma komai milk and Brown color ne a dakin,kofa na gani a cikin Bedroom din nan take na Murda Handle din toilet ce ta yan gayun gaske ban taba ganin irinsu ba dan Allah yasa a birni muke da bazan iya gwada yanda ake kunna tap din ba,ina shiga wajen sink na nufa abin mamaki ina mika hannuna sai ruwa ya fara zuba shaaa idan na janye hannuna sai ruwan ya dauke haka shower ma kai abin kamar Aljanu,ban San lokaci ya ja ba na shagala na manta da kowa ina ta tabe tabena har na gaji nayi fitsari da tsarki sannan na daura Alwala na fito Palo da sauri dan kar mugun ya dawo ya isheni na shigar masa wani waje,ina fitowa na duba gabas na shimfida dankwali na sai na fara jero salloli,Magrib na fara yi sai la'asar da Azahar ina zaune ina azkhar na Mike na gabatar da Sallar Isha da kyar kasancewar yunwa taci karfina gaba daya a kasa a zaune ina adduoina.

     Motarsa naji da Alamar ya dawo lokacin ina yanda nayi Sallah ina adduo ina wanda ban san ma a fili nakeyi ba ina fadawa Allah ciwon Ammah da halin da muke ciki Allah ya yaye mana,kamshinsa naji alamar ya shigo  da mamaki ya kalleni da alama Sallah nayi karfa ko Bedroom na shigar masa,wata mahaukaciyar tsawa ya buga min da tasa nan take na saki kuka,Keeeee a ina kika samu Ruwan Alwala? Jiki na rawa na nuna masa Bedroom din dana shiga da yatsa na, tsaki yaja tare da cewa Allah ya taimakeki wata leda ya wurgo min a jikina sannan ya haura Sama da nasa a hannu.

    30 mnt ya fito da lemon gwangwani a hannunsa yana korawa nan ya fada saman kujera tare da nutsewa a ciki ya dauki remote yana kunna Tv ya kamo tashar wakokin turawa na yan Iska kusan ma kamar tsirara ake nuna su su Nicki Minaj etc.
     Da kyar na Mike na karasa kusa da kafafunsa a hankali cikin ladabi da kwantar da murya nace Sir....Shuru ya min kamar bai San ina magana ba,Nace Sirr.....shuru,Sirrrrrr.....da wani mugun Bala'i ya juyo ba tare da yace komai ba,nan dai na daure da kyar sabo da kwarjininsa nace Dan girman Allah kayi Hakuri ka barni na tafi gida dan Allah,Ammah ta tana gida bata da lfy da kannena yanzu suna cikin damuwa dan Darajar Allah Sir,idan ma baza ka barni na tafi ba to ka kira min su a waya ka hadani dasu na kwantar musu da hankali kafin Lokacin da zaka barni na tafi.

     Shuru naji yayi kamar ma ba dashi nake magana ba,na daure ina hawaye nace Sirrrr....sai lokacin ya juyo ya kalleni tare da dauke kai can yace me kike so kice? Wato duk maganar da nayi ma bai ji ba,wani bacin rai ya kamani cike da fushi na hayayyako masa nace ka barni na tafi idan baza ka barni ba ka kira min sis dina na fada mu......wani gigitaccen Mari naji a kumatu na,kafin na bude Ido ya kara min wani marin me masifar Radadi nan ba shiri na barke da kuka,mikewa naga yayi sai gashi ya fito da dalleliyar wuka a hannunsa,a wuyana yasa ta yace will u close tht ur dirty mouth or...kafin yayi Magana na hadiye kuka na sai shesheka duk da bana jin turanci amma na gane Close da mouth tunda Su Meenat suna koya min.

      Dan kinga ban miki komai ba shine zaki raina min hankali am I ur mate or what?,baki da tarbiya na gama ganewa dama ina nemanki ke gaki marar kunya ke har kin isa ko kalleni ki zageni har gida,kin San ko ni waye who do u think u r? Murmushin takaici yayi tare da cewa dama bari nayi naga karshen rashin kunyarki,har kina min fada ni zaki kalla ki min maganar banza bayan kina hannuna ko yankaki nayi na yanka banza, shi dama Aayan haushin mata yake ji har jira yake mace ta masa abu yaga ya ci mata mutunci domin mata sun masa abinda bazai manta ba.

      Ina gefe nayi mukus fuskata tayi jajir sai yatsunsa kwance a fuskata,wancen abincin ubanwa zai ci miki?da sauri na rarrafa na dauka na bude ledar jiki na mazari na bude Fried rice tasha hadi tare da kaza sai lemo,ruwa da Yogourt a ciki nan take na bude na kai lauma da bismilla kamar mayunwaciya haka nake afka abinci 5mnt kamar waccen ta zubar har na lashe abincin na shanye yogourt tare da lemon sannan na daga ruwan na shanye du,yana zaune mamaki ya rufeshi yana kallon ikon Allah ci kamar jaka,ya tabbata ko da yunwa ya kwana bazai iya cinye abincin ba,na gefensa ya kara jefo min a jikina nufinsa na cinye,ni ko dama ji nake kamar banci ba domin ba laifi akwai ci,haka na dauke na kara budewa yana bude baki da mamaki yaga na kara cinye nasan ruwan ne kawai ban Sha ba amma har yogourt din na shanye ta,da hannu ya min Alama na mike,zumbur na Mike tsaye,yace naje can bangon na dawo haka da sauri naje na dawo,yace yi tsalle na gani nayi tsalle ba shiri sabo da tsoronsa da nakeji,shi tunaninsa bazan iya tashi ba wannan uban abinci dana cinye amma sai yaga ras dani,a zuciyarsa yace bari ya kara gwadawa ya gani,nan ya Mike ya shiga kitchen ya fito dauke da fura tasha hadi a katuwar roba tare da Fruits a wani bowl,nan take yawuna ya tsinke naga dadi ban saba cin irinsa ba amma da shinkafa da wake ce ko plate daya bazan iya cinyewa ba,ko tuwo bazan sauraresu ba amma wannan kayan dadi haka ina zan barsu ko cikina zai fashe bare wannan dan abinci na take away kamar an roko gaba daya bazai plate daya ba,
    
    Furar ya miko min ya tamke fuska yace shanyeta,da mamakinsa yaga na dauke da sauri har ina murmushi don ina son Fura a duniya,kawai na fara Sha cikin nishadi har lumshe ido nake ina addua ga Allah ina inama Ammah na kusa,ina Sha ina Santi a raina gata tayi sanyi a raina nace ah lallai wannan yana so aci a koshi Ashe ma bai cika mugu ba yo ni badan su Ammah ba ai da na rokeshi ya dauki rikona a gidansa,ina ta santina sai gashi na shanye harda lashe spoon din,wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke abinfa ya daure masa kai karfa ko Aljana ce,Nan ya mika min Bowl din Fruits dama su nake kallo cike da kwadayi nan ma na karba harda godiya na koma gefe na fara lunkuma su kankana a baki nace kai Allah me iko na yini banci ba Ashe tanadi Allah ya min harda kara'i yana kallo yaga na tashi Fruits tsaf,karkuce abubuwan masu yawa ne basu da wani yawa kun San dai Harkar yan gayu komai kadan kadan ba dole na cinye ba.

     Yau kuwa yace sai ya kure yarinyar nan mayya,ya Mike ya koma kitchen sai gashi dauke da kaza tasha hadi tana tiriri da Alama warming dinta yayi ya turo min gabana,kamar nayi kuka sabo da dadi yaushe rabon naga kaza guda a gashe sabo da murna ban san sanda na kalleshi ba nace Dan Allah ka daukeni aiki ko share share da goge ne a gidan nan,wata uwar Harara ya zabgo min ban san sanda nace yi hakuri na fara yagar kazata ba ina aikata cikina,gani yayi fa da gaske zan iya cinyewa kawai yace karta je ta barke min da Zawo a gida kawai ya taso ya fisge plate din tare da cewa Mayya.

     Yana dawowa ya mika min faskekiyar wayarsa nufinsa wai nasa Number na kira gida,ban iya ba amma gudun laifi na karba haka nan take nayi kamar zan iya na zuba yatsuna guda biyu na fara birkita screen din,naga Sam ban gane ba nasa yatsuna guda hudu na fara dirzawa a fuskar wayar,na juyata na juya na dukufa kamar Idona zai zazzago sabo da yanda na zarosu ni a dole me danna waya,shi kanshi da ya kalla yayi tunanin wannan yarinyar Aljanu gareta ko mahaukaciya ce bai San tsabar rashin zaman aji ne da rashin shiga mutane daga siye sai siyarwa, gani yayi zan masa barna ya fisge abarsa tare da cewa fada min Number cikin hasala kamar zai dakeni,to mu dai a gidanmu babu waya dama akwai wani Shehu me Kanti idan wani abu ya faru shi Muke kira a waya sai ya kai gidanmu ayi magana don Number dinsa na kaina,na iya da turanci amma wai dan kar nayi mistake ya dakeni sai naji tsoro nace gwara na fada da hausa nan na fara cewa 

sifili takwas sifili...wait wait ths is bull shit ban san wannan abun ba,nan nace yi hakuri bari na Canja na firgita kawai maimakon na fada da turancin sai wai dan yafi ganewa sai nace..tayar mota.. takwas..tayar mota,wai gani nayi Zero (O) yana kama da tayar mota shine dan yafi ganewa nace haka,wani mugun dariya ce ta kamashi da ya gano me nake nufi da Zero ne Tayar mota lallai wannan yarinya dakikiyace amma sai ya daure fuska yace wlh zan kwada miki mari zan miki abinda baza ki manta ba,nan take nace 080 sannan na fada masa Numbers da turanci,yace amma ke dan Iskanci zaki raina min hankali kin iya fada dai dai nonsense tare da Jan tsaki yana dialing bugu daya aka daga ya mika min wayar nace Hello...Shehu Mufeeda ce,dan Allah dan kaiwa Ammah wayar mana minti daya,nan Shehu yace to Mufeeda ya fita da sauri yayi Sallama gidan tare da gaishe da su Ammah dasu Meenat suka gaisheshi suna cikin wani Hali sunyi jirim suna jimamin Ina Mufeeda ta shiga tun safe har dare hankalinsu ya tashi,Shehu yace gashi inji Mufeeda tace za kuyi magana ai da sauri Ammah ta karba jiki na bari,Mufeeda tace Ammahna kuna lfy? Ya jikin naki? Ammah tace ba ta wannan nake ba kina Ina Mufeeda lfy iceko,dariya ni Mufeeda na kakalo tare da cewa lfy lau Ammah kin ganni a gidan wannan kawar tawa wacce kika sani Naeema yar gidan me kudin nan kin San ai da sun tafi kasar waje to sun dawo shine muka hadu a kasuwa tace muje naga gidansu,
     shine ma mamanta take tambayata ke nake basu labarin cutarki da aikin da za ayi miki shine Maman tace mijinta yayi tafiya gobe ko jibi zai dawo na zauna kar na tafi na jira zai iya biya mana kudin aikin da za ayi miki,kinga ai bazan taho ba shine na zauna ina jira kuyi addua Allah sa a dace,nan take Ammah wani farin ciki ya lullubeta tace Mufeeda kin tabbatar haka zancen yake ba karya?nace tabbas Ammah ai kin San halina dai ko kin San kuma dalilin fita ta Allah watakil ya amshi adduar mu,Ammah kinga dadin da naci harda Kaza da Yogourt,kuyi addua amma yau Ni ina cikin daula ina su Meenat bani su,nan ma aka bawa Meenat suka Sha labari aka mikawa Maeeshah ma tana Anty jambaki pink ya kare ki siyo min wani,kuma takalmi na ya tsinke Sis nace to Maeeshah zan siyo bawa Ammah,nan nace Ammah aci gaba da kular min da Kasuwanci na dan Allah Meenat tayi komai,Ammah tace kin San basu iya kosan sosai ba,Nace Ammah suyi haka koma yane a tara min kudin in na dawo za muyi magana sai goben idan ya dawo me gidan zan sanar dake idan Bai dawo ba zan fada miki komai dai,Allah yasa a dace cewar Ammah ta mikawa Shehu wayarsa Mufeeda tayi masa godiya ta kashe shima ya musu sallama ya tafi,nan Ammah tace Meenat ta kulle musu gida ta rufe suka yi kwanciyarsu cikin farin ciki.

    Ni kuwa ina gamawa hankalina ya kwanta nan na saki ajiyar zuciya,shi kuwa da mamaki yake kallona yanda na iya fesa karya haka,lallai suna da matsala amma ina ruwansa,ni ko dama su Ammah nake ji kuma na gyara komai,idan na koma nasan karyar da zan kara shimfidawa, baki ya tabe nan take ya fisge wayarsa tare da wucewa samansa,ni kuwa yana tafiya na koma saman 3seater na kwanta a tsorace har bacci ya saceni, tunda ya shiga bedroom ya rasa wannan mugunta zai min wacce bazan manta ba ina cikin bacci naji ya harbo ni kasa daga saman sofa,a firgice na tashi, ba Imani yace sai nayi Kamun kunne,haka nayi na Dade ina yi har sai da na saki Kuka,sannan yace nayi kneel down sannan Hands up nan ma na fara ina tayi haka yayi tafiyarsa ya barni ina ta abinda ya sani har bacci ya kwasheni na bingire a wajen,ban farka ba sai da gari yayi haske na Mike a firgice tunawa da banyi Sallah ba yasa na Mike da sauri na fada bedroom din da nayi Alwala jiya,komai na kayan wanka da amfani a kwai a toilet din masu tsadar gaske,ba bata lokaci tube kayana na kai hannuna ruwa me dumi sosai yana zubowa gwanin dadi  ban san sanda na fara wanke kaina da shampoo me kamshi da tsada ba,ina gamawa na dauki liquid soap na sheka wanka sai kamshi ina ta washe baki,ina dubawa naga harda sababbin tooth brushes da toothpaste na dauka kuwa na wanke bakina tas abinka da abu me tsada hakorana suka kara haske da kyau Malam nayi wani Fresh dani,Towel nasa tare da goge jikina tas,sa nan na daura Towel na fito ina kara tsane gashina,mirror ba abinda babu na shafawa masu tsada,na dauki lotion na shafa a jikina,babu powder sai wata fara kawai na shafa abata na dauki lipgloss na shafa me kyau red,ban san jagirar waye ba na dauka na zizara a Idona sai gashi nayi kyau sosai.

    Gashi na wanda ya bushe na taje na shafe shi da Maya Mayan gashi yana sheki da kamshi dama gani Allah ya bani tsayin gashi,Daure abina nayi nan take nayi acuci da gashina sannan na shafa roll on tare da turaren jiki dana gani me arnen kamshi,kayana na kwaso na saka haka ina so na wanke pant dina amma ba dama kawai na maida abina sai lokacin na tuna banyi sallar Asuba ba da sauri nayi tare da Azkhar sannan na fito Palo cikin Jin dadi na zauna,ina jin motsi na sauka kasa tare da kneel down na daga hannu sama wai dan yace a haka na kwana inayi,kallo daya ya min yasan Lallai har wanka nayi,ko kallona baiyi ba ya fita,15mnt sai gashi ya dawo tare da take away leda hudu,ya zauna a saman Sofa tare da miko min leda uku da sauri na karba dama yunwa nake ji nan na zauna daram tare da bude ledar sai ga kwai da chips tare da gashashiyar Hantar rago, haba Malam nan na zaro harshe na lashe labbana na fara dagargazar Harka yi nake ba ji ba gani,nan na kau da Leda daya na bude daya na lashe na jawo ta Ukun na cinye komai tas tare da daukan ragowar ruwana na jiya na shanye tas nace Alhmdllh tare goge hannuna da tissue din dana gani ciki.

   Mamaki ya gama kashe Aayan har firgita yayi yana mamakin a ransa kuma cikinta baya lalacewa,yana kallon TV yace tashi ki gyara gidan nan kaf yayi maganar kamar bada ni yake ba,Zumbur na Mike na kayan aikin,kitchen ya nuna min da yatsa ina shiga na gansu a shirye na hado da kayan mopping,yace na biyo shi haka yasa na gyara samansa Kas Kas, ko ina yana kyalli har su toilet,abin ya bashi mamaki baiyi zaton zan iya gyara haka ba,muka dawo kasa ko ina na gyara har room din da nayi wanka da toilet,haka ya dinga nuna min wasu sashen har wajen motsa jikinsa sai da na gyara tsab,ta window na hango maza suna ta aikin gyaran compound flowers tare da goge windows ni kuma na gyara ciki, nayi matukar jigata nasha wahala,yace sai na shiga kitchen haka na shiga na wanke na goge na gyara komai neat har store,haka fridge ma ya fitar da abinda suka lalace yace na gyara ciki tare da bani wasu abin na gyaran Fridge haka na gyara fes na kara Mopping kitchen din na wanke komai na shanya su sannan na fito,ina fitowa yace naci gaba da Kamun kunne ba Hutu,inayi ina kuka,sai da na kai 1pm sannan yace naje nayi Sallah na bar masa gida,cike da Murna na Mike na gyara jikina tare da Alwala nayi Sallah ta saida na kara gyara fuskata gudun tuhuma wajen Ammah sannan na fito tare da yin hanyar waje,Keee naji muryarsa me sanyi,juyowa nayi a rude nan naga ya daga waya yana magana Hello Abbi ka tashi lfy,ta ciki naji Muryar Abbi yace zo ka bude min kofa ina son magana da kai gani a gidan ka wato ni zaka rainawa Hankali ko,nan take ya firgita amma dake namijin duniya ne sai ya maze bai kawo komai ba ya raba ta gefe na wani kamshi ya dakeni nan take jiki na ya mutu na lumshe ido,kofar ya bude kawai sai ga Abbi ya bayyana a gabana da sauri na tsorata tare da ja baya.

    Salati ya saki da salallalami yace dama nasan wlh ba abin kirki kake aikatawa a wannan gidan ba shi yasa nazo da kaina,ashe baka da kunya baka da mutunci ai jiya na tambaya ina ka kwana ance ba a sani ba nasan kana nan,ashe abinda kake aikatawa kenan munafiki ka nuna Sam kai baka kaunar mata Ashe abinda kake kenan,karuwai kake kawowa gidanka,ashe shi yasa baza ka iya zama da aure ba,wannan yaro kwai tsinanne in Allah ya yarda Cutar kanjamau ce ajalinka,baza ka jawo mana abin kunya ba wlh dole yau Hajja taji zancen nan kuma aure dole kayi zaka ga abinda zai biyo baya,nan Abbi ya min kallon Banza ya fice a fusace.

    Shi kuwa Aayan ko a jikinsa haka ya nuna amma yaji zafin sharrin da Abbi ya masa,ni kuwa tausayinsa naji sabo da na tuno maganganunsu farkon ganina dasu,Driver ya kira a waya sai gashi yazo  umarni ya bashi jeka wannan zata gwada maka gidansu ka,ka kaita can.Nace na gode wata uwar Harara ya balla min nan take nayi mukus tare da bin bayan Driver na shiga motar sai muka bar gidan ina jin dadi na rabu da jaraba.


11-15


Official


By
AsmaBaffa


Ths page is for u  MARCYCOOL.

ina matukar Godiya da jinjina fans masu Sharhi aci gaba da gashi kuna birgeni.

Allah ya taimakeni Driver na da kirki cikin mutunci ya kaini har kofar gidanmu wanda kaf mutanen unguwar mamaki sukeyi na wannan arniyar mota amma wai sai suka ga Ni Mufeeda yar Kasuwa yar talakawa fitik wai ni aka sauke a wannan mota, ai fa sai mutane suka fara guna guni ga zahiri ai karuwancina ya girmama ni kuwa Allah sarki ban san ma sunayi ba, wata kawata a makwaftan mu Nawwara itama dai Nawwara yar malam Shehu ce talakawa amma sun fimu rufin asiri ita kadai ce kawata sai kuma wata yar gidan masu kudi Na'eema amma ita yanzu sun koma Kasar waje da karatu har iyayenta suna kasar waje abinsu,

    A hanya Nawwara tace Mufeeda kece a wannan zundumemiyar mota haka duk da bana zarginki ki kiyaye ko sabo da sharrin yan Unguwa,Murmushi nayi tare da cewa Allah kadai nake tsoro ni,Allah yaga zuciyata.
    cike da farin ciki na shiga gida da Sallama dauke a bakina,da fara'a suna min Oyoyo sannan na wuce wajen Ammah tare da gaisar da ita,tace  Mufeeda kar ki kara yin irin wannan tafiyar kinji na fada miki,wannan ya Zama na karshe da zaki tafi wani gida ki kwana ba tare da Sanina ba sai dai ki bugo waya,bazan yarda da wannan shirmen ba,karki ga na yarda dake kice zakiyi abinda kika ga dama ko dan kina ci damu etc kice zaki juya ni baki isa ba,ni ba irin iyayen nan bace masu son abin duniya akan yara ne ke ci dasu sai su zauna yaran na juya su sai abinda suka ga dama zasu yi,ki nutsu wlh akan haka gwara mu daina karbar abin hannunki bana so neman Kudi ya kaiki ga halaka ko sabawa Allah,naji matukar ciwo da sai dare ma zaki bugo ki fada min ni har ga Allah ban yarda da zancenki ba kawai dan naji lafiya kike yasa na dan samu nutsuwa,nan Ammah ta dinga fada ba ji ba gani ina bata hakuri harda kuka na,nace bazan kara ba kiyi hakuri abinda na tsaya nema ma ba a dace ba domin me gidan yayi tafiya kasar waje nan ma na kara mako karya ta na fada,aiko nasha fada wajen Ammah,ni dai hakuri nake bayarwa har ta hakura.

     Bayan kwana biyu tsakani naga sana'ar tawa ta danyi kasa don haka na tattara ragowar kudin dake hannuna na siyo kajin Hausa da Akuya guda daya wai zan gwada yin kiwo ko za a samu suyi albarka,Kaji biyu yan budurwa na kawosu,akuya tana meee...mee na samu na daure ta can karshen gidanmu,lokacin wake beans yana araha kawai na auni kwano biyar na boye ina jira yayi tsada na siyar naci riba,sannan na dan siyowa su Meenat kayan kwalliya tare da kayan makaranta Uniform na dinka musu sabo idan an koma schl suma su sa sabo,haka na siyo mana Atamfa muka raba yadi biyu kala Uku akayi mana dinki me kyau na talauci domin rabi wasu yadi ne na adon Atamfa akayi mana kari dashi,sai suka ba da ma'ana,dama bamu da kudin dinka shadda daga atamfa sai materials sai kuma kayan gwanjo da muke sawa,suma dinkin atamfar na talauci duk bamu da riga da zani ko daya daga skert damamme sabo da yadinma bai isa ba bare tela ya maka mana dinki dole sai dan fitted,sai ko dogayen riguna baza ka gammu cikin Tsumma ba Sam sabo da ina yawan yi mana dinki tare da yan takalma na roba yan Dari hudu zuwa biyar muna dasu da yawa dasu muke too match,haka mayafai ma ina siya mana da hijabai zaka ga muna canja abinmu iri iri mata sai da gyara ai,bani da burin da ya wuce naga Ammah cikin farin ciki Tare da kannena duk kudin da nake nema sabo da su nake nema.
    
    Asalinmu
       Sunana Mufeeda Adam Fatima, Asalin Shuwa Arab ne Babanmu,a Borno state suke da Zama tare da Family dinsa gaba daya,Bashi da Ilmin Boko sosai sai kasuwanci da yake y,Babanmu Adam yana da dangi da yawan gaske wanda mu bamu San dasu ba Sam,Iyayensa sun Dade da rasuwa tun yana yaro domin shi kadai suka Haifa Allah ya musu rasuwa ya taso a maraya,shi yasa ma ya taso da neman Kudi har Allah ya kawoshi Kano state,yana shiga kauyuka saro kayan Noma ya kai kasuwa,Har ya shiga Kauyen Ammah wato Kauyen Rimin Gado can rigar Fulani,Nan yaga Ammah cikin halin rashin gata tana Shan wahala hannun matar uba sabo da bata da Uwa sai Uba,danginta kuma fulanin tashi ne basa Zama Sam kullum a yawon daji suke basa Zumunci,bayan Adam Abban mu ya auri Ammah  da shekara daya Allah ya dauki ran Baban Ammah wato Sulaiman,Haka Abba yaci gaba da kula da Ammah suna zamansu lfy a cikin birnin kano gwale,ko sunje kauyen ma ba wasu dangi sun tafi yawon Shanunsu har Ammah ta daina zuwa ma tunda duk yan Uwanta sai wanda suke uba daya kuma basa kulata sai ta kyalesu kawai amma duk da haka tana kaimu muna zuwa itama kafin lalura ta sameta tana zuwa musu.

     Mu kuwa ganin basa zuwa basu damu da mu ba ko tace muje sai muki zuwa idan munje ma basa ganinmu da daraja,Shekarar Ammah da Abba biyu da Aure ta Haifeni aka sa min suna Mufeeda kowa yana yabon kyauna,sai da na cika shekara biyu sannan aka kara haifar Meenat,itama After 3years sai aka Haifi Ma'eeshah,Lokacin Babanmu ya samu wadata sosai ya siyi gida kato cikin Rijiyar Zaki muka koma ciki yana Business sosai sannan ya zana waec da Neco ya koma makaranta yayi NCE ya gama,lokacin tuni ina zuwa Primary schl amma ta Gomnati sabo da ba masu kudi bane mu sai rufin asiri domin munfi karfin ci da Sha bare sutura,ina primary 3 aka saka Meenat da Ma'eesha suma muna zuwa nice Babba, Da yamma muje Islamiyya, ina kula dasu sosai domin tun ina yarinya Allah yasa min son iyayena da yan uwana fiye da kaina,mun taso cikin kulawa da tarbiya muna jin dadinmu har na kusa gama Primary 

sai kuma muka ga Abbanmu sam ya daina kula Ammah sai wulakantata yakeyi,ba irin wulakancin da Ammah bata gani ba a hannun Abba,idan suna fada har Kuka mukeyi,amma duk lokacin bamu da wayo bamu San akan me suke fadan ba,muna dai ji yana cewa idan ya gaji korarta zaiyi,tun abin baya damun mu har muke damuwa muna bashi hakuri,bamu San dalili ba dai sabo da Ammah bata bari mu San halin da suke ciki,sai dai muga tana kuka watarana Abbah yace zai fita wata state dake Kudu Abia state neman Kudi tun da Allah yasa ya tafi bamu kara Jin labarin Inda yake ba ko a waya.

    Mun shiga damuwa me tsanani,Amma taje har garinsu wajen danginsa tare da mu amma sukace suma basu da labarinsa,haka abokanansa na business da sauransu duk an nemesu shuru suma basu sani ba,munyi kuka munyi bakin ciki har aka kwashe shekara guda lokacin na gama primary,anyi cigiyar Abbah har gidan Radio amma ba labari haka Ammah ta fara Sana'ar kosan siyarwa da Awara tare da sauran kanana nan sana'a gida dasu take mana komai na rayuwa,har na shiga Jss1 na gama na shiga jss 2,Katsam lalura ta samu Ammah haka kawai bata iya motsa kafafunta daga Hips zuwa toes,munci kuka gashi nice Babba ga karancin Shekaru haka makwafta suka taimaka mana muka kai Ammah asibiti mafi sauki,da yan kudin da Ammah ke Tarawa muka sai mata magunguna sannan suka ce dole akwai wani aiki da za ayi mata nan gaba,tun da muka dawo Ammah ta dan samu sauki ni kuma dama duk sana'oin nata na iya su sai naci gaba da yi na daina zuwa schl nake biyawa su Ma'eesha suna zuwa,ni ke kula da Ammah da gidan baki daya,akan sana'ar ma sai na kara wasu da yawa ina yi iri iri komai siyarwa nakeyi ba sauki,har Allah yasa  Meenat na Ss1 Maeeshah na jss2 ga Islamiyya suna zuwa ni kuwa komai ya tsaya min sai neman kudin jaraba kamar zanyi sata.

har yau munyi munyi da Ammah ta fada mana fadan dake tsakaninta da Abba kafin ya bace amma taki fada mana sabo da haka muka kyaleta sannan muka kara tsanar Abba da ya gudu ya barmu,dan ni ko zancen wani Abba bana yi sam bama na so a ambaci Sunansa shi yasa a makaranta ma Sunana Mufeeda Adam Fatima sabo da sunan Ammah Fatima kawai nace ai bazan sa Kakanmu ba Ammah ta zan sa,haka Meenat Adam Fatima tare da Maeeshah Adam Fatima haka duk muke Amfani dashi da ace da halima sai dai nasa Mufeeda Fatima Adam to kawai dan da uba ake ado shi yasa ba kyau dole nake Sa Adam.
    Za muji nan gaba Ina Abbah ya boye oho,ko da gaske ya bata,ko yana raye,ko yan Mafiya ne,mene ya hadasu da Ammah suke fada,wacce lalurace a jikin Ammah haka? Oho dai.

     Ci gaban labari

 bayan kwanaki kadan na yanke hukuncin zan fara zuwa gidan yan siyasa tare da yan kasuwa da sauran masu kudi na fara neman taimako ko Allah zai sa a samu me Imani ya tallafa a biyawa Ammah kudin magani,bayan na gama kosan siyarwata tare da gyaran gidan haka nayi girkin rana na kwashe a cooler sannan na fara daka lallen da nake siyarwa ina daurawa a leda ina saidawa ashirin,lallen ma ban barshi ba sai dana yi masa Algus na hada da gayyen bishiyar sabara na daka ya kara yawa na daura na ajiye,idan mutum ya siya lalle sai yaga lallen yaki yi masa ja yadda yake so to anyi masa Algus da wasu gayyen,wanka nayi na shirya cikin skert dina dan gwanjo tare da T-shirt dita nayi kyau nasa Hijab dina me hannu sunsha wanki da guga,ban shafa ko Powder ba na yiwa Ammah Sallama nace na tafi kasuwa siyo kaya,tayi mun a dawo lfy,ban zarce ko ina ba sai gidan Chairman din local government dinmu,ban san gidan ba da tambaya aka nuna min ni da me Napep,bayan na sauka mutane damkam a kofar gidan har da yan Sanda masu gadi gida me kyan gaske,maza yan siyasa sai kallo na suke domin sunga baiwar kyau wajena,da gani kuma sun San ba yar siyasa bace ni kamilalliyace ni yar mutunci,salamu alaikum nayi musu sallama tare da gaishesu sannan nace Dan Allah yau Hon yana nan? Suka ce ae kinyi sa'a yana gida muma shi muke jira,amma tunda ke macece bari mu rokar miki masu gadi ki shiga kice wajen matar Hon kika zo,ai kuwa haka akayi nan take yan Sanda sunga kyau suka ce na shiga,

nayi godiya na fada gidan cikin nutsuwa,wata yar aiki ce ta nuna min kofar shiga ciki,nace tayi min jagora zuwa wajen Hajiya,har nan ta kaini sannan ta shiga tare da sanarwa Matar Hon,cikin Sa'a aka ce na shiga har ciki yar aiki tayi min iso,matar Hon yarinya baza ta wuce 24yrs da ganin irin kyau da Allah ya min yasa ta tsaneni kar na kwace mata miji,nan take naga ta canja fuska ta Mike tare da miko min Dubu biyu tace na tafi an sallameni,babu bakin magana jiki ba kwari na karba na dau hanyar fitowa kenan kicif sai ga Hon ya sakko daga sama da katon cikinsa yana shafa tumbinsa,ya kalleni nan take ya lashe bakinsa tare da yi min signa da Ido kamar kwarto,ni dai na fice da sauri daga palon.

    Matar Hon tana Alhaji ga abincinka amma tuni yace Hajiya na fita Office ana jirana ya fito da sauri yazo kusa dani a bakin gate,da sauri na durkusa na gaisar dashi sannan na fada masa abinda ya kawoni nan take yace ai karamar matsalace wannan ya bani card dinsa yace na samesa a guess house dinsa,na tsorata amma dai na karba nace sai nazo na fito daga gidan na tafi gida ina murna ta.

     Ban fadawa Ammah inda naje ba nasan fada zata min kawai nayi shuru,washe gari kuwa dama yace 5pm zanje gidan da yace,ba tsoro na shirya na tafi ba wahala na gane gidan na fita daga Napep,Naga gida rafkeke na kwankwasa sai ko ga me gadi ya bude yana ganin budurwa yasan irin matan da Hon ke Tarawa kullum ne da fara'a ya tarbeni yace shiga yana ciki,nan ya min iso har cikin palon Hon,sai lokacin tsoro ya kamani,lokacin na hango Hon daga shi sai Singlet da gajeren wando yana latsa waya,da fara'a yana washe baki yace zauna mana kyakyawa me kyan sura,Nace ba sai na zauna ba idan zaka taimakeni to ka bani dan Allah,dariya yayi yace zo mana ke ya kike abu kamar bagidajiya ina ganinki wayayya zo muji dadi mana sannan na baki kudin a wuce wajen kawai,tsorata na karayi na fara ja da baya nace ni ance ba kyau namiji ya rike ma mace  hannu nidai zan gudu,Hon yayi dariyar Kuruciyata yana lallabani yana hure min kunne amma naki matsawa ko kusa dashi,tasowa naga yayi ya taho jikina ya fara shafa min fuska yana kokarin cire min Hijab,yana sakin wani Gurnani ai da gudu na ja baya a rude na bude kofar na fice da gudin tsiya ko me gadi gani yayi kamar walkiya na bude kofa na fice wufff.

     Ina Haki na fito da matsiyacin gudu na cukwikwiye Hijab dina na tattara skert dina ba takalmi a kafata tuni na watsar dasu,Na samu gefen titi kawai na Mike na dinga tsinka uban gudu ka rantse yan Mafiya ko Zaki ne suke Bina,ga unguwar shuru irin ta masu kudi ba kowa ba a ganin ko mota a titin,can naji karar mota ta bayana tunanina Hon ne haba ai sai na kara karfin gudu na yi nake kamar numfashina zai fita,a hankali motar take tafiya a saitina sai lokaci ina gudu na dan kalli glass din window din an sauke glass din ana ta min magana ta ciki gudu nake iya karfina da karfi nace wlh bazan tsaya ba Hon tsinanne dan Iska ina ta zagin me motar ji nake Hon ne ashe Aayan ne yake ta Bina da motar yana sheka dariya yanda yaga ina uban gudu kamar na tashin kiyama,tsabar mugunta sai yaki yin magana kawai yake ta Bina da mota duk inda nasha kwana sai yasha da motar yana ta dariya har sai da karfina ya kare tas na fara kokarin tsayawa Ashe ban sani ba idan gudu ya cika yawa yakai wani limit mutum kasa tsayawa yake da kansa sai an rikeshi kawai zai ta gudu ne,ina so na tsaya ina kokarin tirjewa amma ina gudu kawai nake falfalawa na fashe da kuka kuma ina ta gudu na kamar masifa har dai da kyar na samu na rike wata bishiya sannan na zube a kasa wajen ina maida numfashi,Dai dai lokacin Saurayi Aayan yana ta dariya harda kwalla sannan ya take birki a inda nake Kuuuuu yana ta dariya yana rike ciki,sai da na Huta sosai da sosai sannan na tashi tsaye ina karkade jikina,sai lokacin na hangoshi cikin motarsa Ashe shine ba Hon ba,kawai nima abin ya bani dariya kamar sabuwar Kamu na dinga sheka dariya harda kwalla,a ransa yace lallai yarinyar nan da alama mahaukaciya ce ko Aljanu gareta,na kalleshi saitin window na daure fuska sannan na maka masa harara,ai ko ya fito a fusace na firgita ba damar guduwa dan na gaji ina ji ina gani ya fito ya zabga min Mari sannan ya jefar dani a kasa keee ya daka min tsawa ba a min ko kallon Banza mind ur fucking Business,bana jin turanci tunanina yasan Business dina dana keyi a gida kawai sai nace dama ai ni Kasuwanci na nakeyi ina ruwanka dani haka kawai sai ka dinga cin zalina dan kaga bamu da kudi,ai kudin naku bana tsoron Allah bane tunda ba a taimako sai yawo a mota ana zalinci,tsaki yaja me karfi cikin takama ya koma labebiyar motarsa fuuuuuuu ya figi abarsa.

   Ni kuwa na turo baki tare da cewa Allah ya isa wlh duk ranar daya mareni again Allah sai na rama za a gani ai,nan na gama Kuri na sannan na tafi gida abina.

     Washe gari ban tsorata ba na kara shiri na tafi gidan Vice Chairman neman taimako amma haka na yini ban samu ganinsa ba sai yaronsa,Nace dan Allah wajen Vice nazo idan baza ka damu ba ka min hanya na ganshi,cikin daure fuska kamar zai bigeni ya hayayyako min da masifa ke malama an fada miki ya tafi Umrah bazai dawo yanzu ba,irinku dama yan mata makaryata da Iyayenku sabo da son abin duniya sai ku fara karya kuna zuwa Maula daga nan a lalata Ku yan iskan yara,har nawa kike amma har kinsan yawon Maula,nan dai yaron Vice ya min tatas na baro kofar gidan da takaici.
    Ban dai kara hakura ba washe gari haka na kara shiryawa na nufi gidan wani Commissioner na Ilmi,a bakin gate kofar gidan na yini ina jira ko za bani dama na shiga ciki amma masu gadin ko kallona ba wanda yayi,har zan tafi sai ga wani ya taho da Jibgegiyar mota kida na tashi Malam nan take mukayi Ido hudu da wani Saurayi black Handsome dan gayu,sai kallona yake,ina tsaye aka bude masa gate,sai wani kallo yake Bina dashi kamar tsohon maye,nan take naga ya sauke glass yana murmushi tare da yafito ni da hannu wai naje,da sauri na karasa,sai kallo yake kare min tun daga sama har kasa yace yan mata wa kike nema?nace wajen Babanka nazo Commissioner na Ilmi da alama kai dansa ne ko?murmushi ya kara saki yana min kallon irin na yan duniya,yace ae dansa ne ni ya akayi?Nan na sanar masa taimakon da nake nema akan rashin lafiyar Ammah yace wannan ai karamar matsala ce Beauty,kawo na sa miki Number ta,nace ni bani da waya mu talakawa ne,baki ya tabe tare da dauke kai yana cewa ai kuna da amfani ta wani fannin,ban gane me yake nufi ba kawai naga ya miko min wata waya sabuwa dal a kwalinta amma karama ce Nokia me kyan gaske,yace kinci sa'a Baby na siyo wa yaron Mama waya karbi ki rike wannan ga sim card  sabo bari na sa miki zamu dinga magana ta waya kafin Abba ya dawo sai a kaita asibiti.

    Tunanina da gaske ne ba tunanin komai nace nidai ka bar wayarka amma ka bani Number dinka zan nemeka kaji,yace karbi karki damu kyauta na baki yan mata kamarki ba waya ai abin kunya ne,cike da tsoro dai na karba hannu na rawa garin zai miko min sai da ya shafi hannuna yana sani harda lumshe ido,da sauri na dauke hannuna ina godiya,da kansa ya hada min wayar da komai ya sa min Number dinsa ciki ya dauki number ta sannan ya miko min Dubu biyu wai na hau Napep,naki karba kawai sai ya zubar min da kudin a kasa yana shu'umin murmushi ya figi motarsa ya shimfida cikin wannan gida na alfarma,na dade a tsaye ina tunani kawai dai nace Allah gani gareka na kwashi kudin nayi gaba abina.

     Danaje gida Ammah dan kar ta hanani amfani da wayar sai nayi karya nace Ammah yau dai na karbi kudin adashina na gidan Haule kinga na siyo waya sabo da baza a ace a gidan nan bamu da waya ko daya ba,nan suka dinga murna da tsalle,Ammah harda sa albarka tana murna dama yaran Zamani badai zuba karya a kifar da iyaye a corner can.

     Next day ban hakura ba dai sabo da ina tsoro kar fa nazo ba a samu tallafi wajen Dan Commissioner ba kawai na shirya na Tafi gidan Dan Majalisa na tarayya da suke Zama Abuja,ni dai nasan ba lallai na sameshi da family dinsa ba domin wasu ma ba a Sanin inda gidansu yake buya suke su canja unguwa ko state dan kar a je musu Maula,ni kuwa tsabar jaraba sai da na kwakwulo gidan da tambaya tun daga unguwarmu nake bin gidajen manya ko wani ya sani,idan ance me zaki yi sai nace sako wasu zasu kai gidan da haka aka gwada min gidansa amma fa basu cika Zama a kano ba kawai dai zanje na gani ko me gadi na samu contact Dinsa ya min hanya, haka na fada Napep sai gidan Dan Majalisar tarayya Abuja,gidan kansa abin kallo ne sabo da ya hadu karshe.

     Securities ko ina a gidan harda mutane a kofar gidan Yan maula,haka na kutsa kai cikinsu tare da tambaya ko me gidan yana nan suka ce ai rabon da yazo kano ma yau Shekara biyu kenan.
   Baki na bude tare da mamaki wani ciki yace sai dansa Yarima Bobo da ake aikowa da sakon yan siyasa ana kawo musu,yanzu ma shi muke jira ya fito kin San shi a kwai gadara da wulakanci sai yaga dama yake fitowa ya bamu sakon Hon Rep,
    Nan take nace aiko sai na jira dan nasa dan Ubansa ko shi waye,ina nan tsaye na gaji da jira har 2pm a wajen nayi Sallah saman dankwalina wata me tallan Fura tana zaune a kusa nace ta dama min ta Hamsim,haka ta dama furar tasha Nono me kyau da sugar, nace juye min ita a leda ki kulle,haka ta bani katon Dauri a farar leda na Fura da nono na bata ,sannan na siyi yogourt yar hamsim a leda tayi kankara,ina fara sha sai ga wani dan sanda yace Yarima yace Ku shigo ya ganku zai wuce Flight dinsa ya kusa tashi,da sauri mazan suka fada gidan yuuuuu,ni kadai ce mace haka na danna kai ciki ina Shan furata a leda yanda nake zuka kamar jariri ya kama Nonon uwarsa haka na lumshe ido ina tsotsa Malam ba ruwana.

    Muna shiga ciki nan na hangame baki wajen kallon irin haduwa na gidan ba a magana,Saurayin muka hango chocolate dashi ya hadu sosai ga kyau ga iya wanka abin kallo yana kamshi yasha light blue shadda yana sheki ga motoci a gidan birjik,muka karasa gabansa yana zaune a wata farar kujera yana faman yanga da gadara,ido muka hada dashi yasha mamaki ganin harda yarinya haka,dan a wajensa bana Sahun yan mata
   Ya fara sauraron wasu kawai muka ga Securities sun wani gigice sun nutsu waje daya tare da bude gate jikinsu na rawa,sai ga wasu motoci dalla dalla sun shugo gidan sun kai biyar kamar nasan motocin,ashe kuwa shine domin Saurayi Aayan ne me tashen kyau da Naira.

     Gani mukayi Yarima ya fadada fara'arsa tare da mikewa ya tarbi Aayan da alama abokaine harda wani tafawa suna dariya,Yarima Bobo yace amma kai dan Iska ne Aayan tun safe kace zaka zo kasan yau zan koma Uk amma ka bata min time yanzu na daga flight dina sai 12am na dare,Murmushi Aayan ya saki cike da izza ya dage masa gira daya kana yace to ya akayi ne man sauri ka gama da mutanen nan naku kasan ban son jira,Yarima yace ai kai dan Iska ne ga sit can,kusa da mu ya zauna can nesa a wata kujera ta yan gayu,Juice aka kawo masa yana korawa,a raina nace Allah sarki talakawa mu ko ruwa babu me bamu.

    Yarima yana ta ganin mutane yana sallamarsu da kudi,sai yace pls Ku mazane kuyi hakuri na sallami yarinyar can tunda macece,a raina nace Ashe yana da kirki,nan yace ke zo naji na sallameki sai lokacin Aayan ya kalli inda nake muka hada Ido,da mamaki ya kalleni lallai yarinyar nan wato har maula take zuwa gidan masu kudi sabo da son kudi,ko dai bata da iyaye ne oho,yana gani na karaso gaban Yarima ba tsoro na durkusa gaban Yarima tare da cewa ina yini?yace lfy tashi tsaye ki fadi abinda ya kawoki sauri nake ina da bako,ina durkushe a gabansa kaina a kasa kuma ina ta zukar Fura ta kamar yarinyar yaye,idan nayi magana daya biyu na zuki furata,babu wanda baiyi dariyar abinda nake ba kowa yana ganin ai yarinya ce,shi kuwa Gogan Aayan a zuciyarsa yake Dariyar kwadayi na,kuma sabo da kuruciya a gaban kowa ina mace ko dai bani da hankali ne. na karanta masa ciwon Mahaifiya ta,yaji tausayina kuma lallai yaga mu abin taimako ne,sai yace jirani a gefe bari na sallami sauran,

  nan na Mike na koma gefe,Aayan ko kallona bai kara yi ba har Yarima ya gama da mutanen kaf suka tafi ya rage daga ni sai Aayan sai Yarima,yace zo ke,da sauri na karasa gabansu su biyu,yace ina babanki ko ya rasu? Bana so na fada a gaban Aayan wanda ke latsa waya,sai nace Sirri ne sai dai idan zamu koma gefe na fada ma,murmushi ya saki yace to ya Mike ya taso na kara kasa da murya da rada nace bacewa yayi ba a San inda yake ba,kawai ko guduwa yayi wa ya sani,dariya Yarima yayi yace to shike nan ki kawo takaddun asibitin naki mu gani,nace to ai naji ance zaka yi tafiya,no ki jira zamu fita da frnd dina sai mu saukeki ki dauko takardun,a tsorace nace tab wancan masifaffen ne zai yarda,kin sanshi ne?ya tambaya,nace ae na sanshi kullum sai ya mareni idan ya ganni,murmushi yayi yace to ki jira ai motata zaki shiga,murmushin da nayi shi ya tafi da Imaninsa ya tsaya yana kallona,sai can ya dawo hayyacinsa yace ina zuwa ya koma wajen Aayan dake ta faman cika yana batsewa,Yace kai Yarima kasan fa ban son jira wlh zan tafi ka tsaya kuyi hirar,ba class ba komai,Sorry let's go,Aayan da mamaki yaga na shiga Motar Yarima shima cike da takaici ya shiga nasa motar suka ja muka bar gidan cikin zugar motocinsu,sai da aka zo kusa da gidanmu suka tsaya,Yarima yace yarinya yisauri ki dakko mana na gani,ina fita na kwashe da gudu na karasa gida na fada daki na ebo kamar kiftawar Ido na fito da wani gudun kowa ya ganni sai ya tsorata ko wani abu ne ya biyoni,da gudu ina Haki na kawo masa takaddu ya sauke glass kasa ya karba ya gani tabbas da gaske nan ya miko min card dinsa yace ga Number ta na Nigeria dana waje ki kirani kiji,da sauri na daga kai sama,ya zaro Dubu goma ya bani yace gashi ki siyawa marar lfy ko ruwane,godiya nayi na karba, Yarima yace ki daina gudu kinji yarinya ba kyau mace tana gudu,da ladabi nace to na daina ai tsoro naji kar Ku tafi sannan na juya na dau hanyar shiga gidanmu,sai da naje bakin kofar gidanmu zan shiga na juyo baya sai naga Motar Yarima sunyi gaba sai Na Aayan yana kallon inda zan shiga kamar Munafuki muna hada Ido suka figi motarsu fiii suka kara gaba abinsu nima na shige gida.
   Still ban gamsu da taimakon Yarima ba sabo da yan siyasa basu da tabbas ayi maka karya ka dauka gaske ne kayi ta jira ana ja ma rai,don haka kwana nayi ina tunanin cewar wanne gida kuma zanje nan take na tuno da wani dan kasuwa Hamshakin me kudi a GRA unguwar su Aayan,har matsuwa nayi gari ya waye na tafi,ga kuma gidan wata Mata nan ma Naji ance tana taimakon Talakawa.
   Sannan Zan biya sakateriya ta unguwarmu wajen Kansila Adamu me tallafi ko Allah zai sa ya shigar da sunana cikin masu karbar tallafin Manoma na Gomnati.
    Kuma duk a gobe zanje wani Training shima ko zan samu a dauki sunana cikin masu koyon sana'a idan ka gama a baka jari.gaskiya gobe ina da tsare tsare da yawa,don haka kosai ma kadan na soya na barwa su Meenat komai tare da shiryawa yau ba Hijab nasa ba mayafi na yafa nayi kyau yau doguwar rigar material nasa red and green mayafinta green da takalmin robata baki,Ammah nayiwa Sallama ta zuba min addua sannan na fita da addua a bakina.


AsmaBaffa
Reply
#2
16-20


Official


By
AsmaBaffa


JIDDER ZARIA ina godiya kema ga page dinki.

    Masu Sharhi kuna kasheni da dadi Allah dai ya saka.


Napep kawai na shiga 8am dai dai ina kofar gidan dan kasuwar nan me kudi dake Unguwar Su Aayan,abin takaici ba irin buga kofar da banyi ba amma ba wanda ya bude min hasalima me gadin ne yazo yace ai sun Dade da tafiya Kasar waje basa rayuwa a nan sai jefi jefi,haka na juya da Niyyar tafiya  katsam sai ga yan matan gidan su Aayan su uku sun fito a cikin mota da Alama schl ko wani waje zasu je sunsha wanka da kyau,suna Shan kida,da sauri suka fito daga motar suka zo ba bata lokaci suka fara dukana,ina ihu nima ina ramawa Amma sunfi Karfina,nan take daya ta cire takalminta me tsini ta kwala min a kaina a akasi nan take na zube a Sume wajen na fitar da jini,ba Imani suka koma cikin mota suna murna sun rama abinda nayi musu suka shige mota,ina yashe a kasa ban san inda kaina yake ba,sai 10am Aayan ya fito yau a mota daya zai fita shi ke Driving ma,kawai ya hangoni a kofar gidansu cikin mawuyacin Hali,mamaki ya lullubeshi me ya kawo ni nan da sassafe ko dai Aljana ce ni,a tsorace ya tsaya tare da bude motar ya fito da ruwan roba ya watsa min,nan take na ja numfashi na Mike zaune a firgice ina Dafe goshina wajen da jini ya fita,mikewa tsaye nayi ina Jiri kamar zan fadi na dauki gyalena da kudin Napep dina,na fara tafiya ina Kuka gwanin tausayi,amma marar Imanin ko a jikinsa sai ma tsawa daya buga min yace me ya kawoki nan again da safe,ko kulashi banyi ba naci gaba da kuka na ina tafiya,shuru yayi tare da cewa Yau sai naga inda zata kara zuwa,ya shiga mota.

    Yana gani na shiga Napep yana Bina a boye ban sani ba,tuna ninsa gida zanje amma ina sai yaga me Napep ya Parker a gate din wani makeken gida,na biya Napep ya tafi na shiga kwankwasa gida,Aayan dai yana mota yana Shan kallon ikon Allah mutum jini na zuba a jikinsa amma bata lafiyarsa yake ba ta neman Kudi yake.
    Security ne yazo yana turanci where are u From? To ni dai Na gane me yake nufi amma bazan iya juya yaren ba sai nace na kakalo karya nace ni yar gudun Hijirace  daga wajen Nijar nake,wajen Hajiya nazo a tallafa min Mahaifiyata bata da lfy,lokacin da nace haka Ashe Aayan yana bayana yaji komai harda yiwa Gate man signa yayi shuru,ni kuma ban san yana wajen ba sai nayi karya a akasi,abinda nacewa Frnd dinsa Yarima Bobo daban abinda na fada anan daban,sabo da bana so nayi ta tona sirrin gidanmu shi yasa ni a ganina idan nace yar gudun hijirace mahaifiyata ba lfy Zanfi samun tallafi kuma Ashe Munafuki yazo jin gulma.

     Tuni gate man yaja tsaki tare da banke kofa ya rufe,ina juyowa muka hada Ido da Aayan yana mun mugun kallon tsana alamar yaji komai,karya ba kyau yan Uwa mu guji karya kanayi watarana sai asiri ya tonu duk da akwai dalilina na karyar amma ya dace kayi gaskiya a komai idan za a baka a baka don Allah. bai ce komai ba yana gani goshi na yana jini amma yayi tafiyarsa ya shiga mota,nima na siyi pure water na wanke Raunin tare da fuskata sannan na sa gefen gyalena na danne gaban goshin nawa Ina duba agogon robar dake hannuna,
lokacin Training yayi nan na nufi sakateriya inda za ayi,mun taru da uban yawa amma sai me hanya da gata shi ake dauka mu da bamu da hanya sai muka koma yan kallo muna zare Ido,

    Ina duba lokaci na shiga wani part can cikin sakateriya nan na fara neman Kansila Adamu me tallafi aiko yana nan na sameshi a Office dinsu na kansiloli,masu son mata suna lashe baki ana kallona wanda kuma basu damu ba kallo ma ban ishesu ba haka na karasa wajen Adamu Kansila wanda yana daga cikin masu son mata,Adamu ko kudin Hotel zaka biya masa shi da mace to ba abinda bazai yi maka ba,kullum rayuwarsa a hotel take da mata,aikinsa kenan a kai mata hotel,ko so kake ka yaudari Adamu Kansila to ka biya masa Hotel ya kai mace ciki.

   Ni dai ban sani ba muna ta hira da Adamu ana kallona a karuwarsa har muka jero tare da ketowa ta cikin mutanen dake sakateriyar har bakin titi ya rakoni yana cewa ki kwantar da hankalinki ai tallafi kamar kin samu ki kyale wannan na sana'ar aikin banza ne zan sa ki a me tsoka,ina murna still hannuna yana kan goshina na danne ciwon,Adamu yace me ya sameki nace bigewa nayi wajen shiga mota,yace sannu muje na kaiki Chemist ayi miki dressing,muka jera tare da Adamu Kansila muna hira yana ta murna ya samu Damar hure min kunne,yana wani taku da iyayi shi a dole Kansila me kudi,haka muke tafiya muna ta murmushi kamar saurayi da budurwa ga Adamu akwai wankan shadda gashi matashi dan kyakyawa dashi ba laifi dai,sai kallonmu akeyi,abinda ban sani ba Aayan yana can side din da mota yana tafiya a hankali yana kallon komai nawa da nakeyi don yace sai ya kure karyata bai yarda dani ba.

    Yana kallo Adamu ya kaini chemist akayi min Dressing muka fito tare Adamu na kokarin rike min hannu na matsa gefe da sauri shi kuma yana borin kunya,amma duk da haka Adamu yace yaushe zamu hadu,nace ban gane ba,yace akwai maganganu da nake so muyi amma a Hotel zamu fi samun sirri ko? Nan take nace ban gane ba,yace au da nufin ki a banza zan saki a tallafin?ai ban gishiri na baka Manda,nan take bakin ciki ya mamayeni wato duniya baza a taimakeka don Allah ba,yan Iska sunyi yawa kowa sai ya nemi lalata ma rayuwa,ban san sanda naji haushin bata lokacina danayi a wajensa ba na fara masifa shi kanshi Adamu bai San bani da mutunci bani da kunya ba sai yau da nayi masa tatas daga karshe nace Algungumi a haka kamar mutum Ashe mata kake yiwa ciki to baka isa ba in dai hannu ne bazan bari ka taba ba bare kayi min ciki,ni tunanina ai kawai hannu ake rikewa ana yiwa mace ciki,nan na kara boye hannayena cikin mayafi tare da gallawa Adamu Kansila harara nayi gaba abina ina tafiyata a hankali,duk abinda nakeyi Aayan na kallona ban sani ba.Napep na shiga na koma gida nace na fawwalawa Allah na daina fita neman taimakon kowa Allah ya kawo min hhh naji wuya.

     Kasuwancina na rike bilhakki da gaskiya domin yanzu har funkaso da miya nakeyi da yamma,shima na kan danyi masa Algus yanda za aci riba me yawa nifa komai nawa sai anyi cuwa cuwa.
     Ammah kwana biyu da alama ciwonta kara karfi yakeyi sai addua muyi kuka mu gaji ina ta kiran wayar Yarima bata shiga idan kuma ta shiga ba a dagawa.
   Haka na kira dan gidan Commissioner da gudu ya dauka sabo da yayi saving number,dama kwadayinsa ya tashi yana ta neman Number ta amma bata shiga har yana masifa cewar yayi asarar kudinsa ya bani waya Bai Mori kudinsa ba,shima muna fara waya naji yana kawo min maganar iskanci,Hello Baby ya kike?nace lfy idan na kawo maganar maganin Ammah sai naji yace za ayi yan mata karki damu sai ya dauko maganar iskanci me kikeyi yanzu?wanne kaya ne a jikinki? Ai da zan aureki kullum sai na miki sucking sau biyar,ni ba wani ganewa nakeyi ba da na gaji na gano lallai dan iska ne kawai sai na kashe wayar tare da cire layinsa na ballashi sannan na siyi sabo na sa a wayar da ya bani nace naci banza yaro nasa mata kudi naci gaba da neman Yarima Bobo.hh

     Ina ta nema amma ba a dagawa sai na tuna abokinsa Aayan ne nan take na shirya da yamma wurin 5 lis na rubuta yar takarda na tafi har gidan su Aayan nasan ba lallai a barni na shiga ba kawai na mikawa wani security nace ya bawa Aayan,yace ai yana gida ma jira ya kai masa abinda yace sai na fada miki,nan ya tafi ciki ni kuma ina daga wajen gate ina faman jira cike da tsoro kar yan matan nan su dakeni ko Aayan ya wulakantani.
    15mnt sai gashi ya dawo yace wai ki shiga yan mata,yace ayi miki iso,a tsorace na bi bayan Mutumin mukayi tafiya me uban Nisan gaske kamar zamuje wata unguwar yan aiki kawai muke wucewa har muka isa wani part wanda ban san dashi a cikin gidan ba ya kai karshe wajen tsaruwa har Palo aka shigar dani sanyi da kamshi ya daki hancina har wani bacci nake ji.
    Daga shi sai dogon wando ya fito jikinsa ba riga wow...wow Innalillahi ko wace sai taso ta kwanta a kirjin Aayan sabo da tsananin kyansa wayyo,nidai nayi kasa da kai ina jin kunya,cike da Izza ga masifa yace karki kara zuwa gidan nan da zummar kina nemana wajensa kika je can da matsalarku,ni da kika ganni dana taimaka miki gwara na zubar da kudin,kuma sai na baki punishment na aiko min da takarda da kikayi wai na fadawa Yarima Number kaza ta kirasa ya kiraki back ni zaki aika? Look at u Nonsense yaja tsaki a gabana ya zura farar riga ko kunya babu yace follow me,haka na bishi kamar Rakuma,abin haushin duk kusan mutanen gidan kowa ya fito a wannan lokaci duk part in muka zo sai mun iske mutane mata da maza dattijai duk yan uwan Aayan,kowa baki bude yake kallonmu yana gaba ina baya,shi kuwa Gogan ko kallonsu baiyi ba bare su sa ran yasan da zamansu kayi masa magana bashi da mutunci dole sukayi shuru sai kallo da mamaki kucaka kusa da Aayan kuma a part dinsa to karuwa ce? Nan take yan matan da suka dakeni suka ce Mommy wlh akan wannan yarinyar ya dakemu rannan kamar zai kashe mu karuwarsa ce,Abbi dake fitowa shima yace haka zancenku yake yaran nan.
   Hajja kakarsu Tsohuwa me ji da kai da kudi tuni labari ya kai kunnenta cewar maganar Abbi gaskiyace cewar Aayan mata yake bi na banza don haka ya Zama dole a dauki mataki a kansa tsatsaura,ranta ya baci amma tace zata yi maganinsa.

     Ni dai a tsorace nake har muka karasa wajen mota yace get in the car,ba shiri na fada ciki sabo da na matsu na bar gidan a tsorace nake,Driver ne yaja ina baya,Aayan yana wata motar daban wannan gidan nasa muka shiga,da sauri ya fito nima na fito ina murna Allah yasa ya bani irin abincin ranar nan,ban San me yasa Bana Jin tsoron komai idan ina tare da wannan masifaffen Aayan ba.

    A baya na bishi har ciki yace Oya fara gyara gidan nan,da sauri na fara aikin sai da na gyara komai yana sheki duk da cewar dama ba wani dirty kawai mugunta ce,sai da na gama ya sani kneel down hands up na Sha wahala sannan ko ruwa bai bani ba ina kallo yana ta cin abun dadi da lemo haka yace na tashi na bar masa gida,ba shiri na Mike da sauri domin magrib ta kusa ina tsoron Ammah,har zan fita sai na dawo gabansa yana daukan wani abu kamar hanta yana ci yana kora lemo na faki idonsa na dauke ledar zan kwashe da gudu ya sa min kafa nayi muguwar faduwa a kasa,a fusace yayi kaina nasan duka zanci kawai na fara kuka amma ko tausayi yana huci zai mareni sai kuma ya fasa hannuna yaja tare da jefani waje ya banke kofarsa,sai da na ci kuka na sannan na Mike tare da karkabe jiki na,zan fita kenan wani cikin yan aiki yace kiyi hakuri kinji ki daina shiga sabgar Oga wlh baya kaunar mata ki kiyaye ba abinda bazai miki ba kuma bazai taba nadama ba,ke naga yana daga miki kafa ma wlh da wasu ne ko hanyar da yabi basu isa sun bi ta ba,amma ke har yana kyaleki ki shiga gidansa har ya saki aiki,a raina nace ni ina ruwana da zai taimakawa Ammah ai da na yarda ko kullum yankar naman jikina zaiyi ba matsala,haka na fita na bar gidan na koma gida, my
  Ammah sai fada take min ta gaji da yawon da nake ranar ta sa min doka tace bazan kara fita ba sai bayan sati biyu ko me za a siyo Meenat ta karba taje ta siyo.

   Tun daga Ranar ban kara fita ba ko kofar gida Ammah ta hana,ina zaune da wayata ina game Ma'eesha na kallo Meenat ta tafi cefane kawai sai ga kiran Yarima,jiki na rawa na daga muka gaisa yace gobe na kai Ammah Hospital din an gama biyan komai da komai,sabo da murna ban san sanda Hawaye suka kwararo min ba,na dinga godiya ina masa addua yace ba komai ko mene ake ciki na kirashi a waya,nan take na sanarwa dasu Ammah kowa murna haka ma Meenat da ta dawo harda Rawa,ranar har Nafeela mukayi na godiya ga Allah.
   Washe gari da wuri muka shirya tare da daukan Ammah a napep muka tafi asibitin Murtala.
    Ba bata lokaci akace Doctor mu yake jira an biya komai da komai yau za ayi wa Ammah gashin kashi tare da sauran aikin da za ayi mata,muna ta addua aka shiga da ita.
   Abin da ya bamu mamaki shine abinci lafiyayye na resturant take away tare da ruwan roba carton biyu,tare da lemuka iriri sai fruits da kayan hada tea duk aka dinga shigowa dasu wai inji Boss dinMufeeda,ni kuma  tunanina ya bani dama Yarima ne,kuma ina tunanin so na yake.
    Haka harda su flask na tea dana abinci da cups tare da spoons sai plates wai duk inji Yarima,abin ya bamu mamaki muka dinga murna,na koma gida domin kwaso kayan jinya,mota wata sabuwa naga tasha gaba na,Aayan na gani kawai sai na karasa jikin motar tare da cewa ina kwana?ko saurarata baiyi ba yace shiga mota,ban so ba amma ya zanyi haka na shiga gaba na zauna ina jira ya kaini inda zai kaini,sai naji muryarsa me sanyi da dadi kamar na suma haka naji,yace  karbi waya Yarima zaiyi magana dake,waya na karba a tsorace muka gaisa yace Mufeeda kike ko?

nace ae yace to gaskiya zan fada miki duk kudin aikin nan da komai bani na biya ba Aayan ne ya biya abokina,yanzu haka an fede Ummanki amma baza a dinke ta ba sai anyi deal dake akwai sharadi idan kin yarda sai a karasa mata aikinta ta tashi idan baki yarda ba kuma a barta haka ta mutu,a firgice tare da fara kuka nace mene sharadin?yace Aure za a daura muku da Aayan na kasuwanci domin shima a gida ance dole ya kawo mata ko a bashi wata akwai abinda yake so ya nunawa yan gidansu kin gane zai miki bayani idan kin yarda,nan take nace abu me sauki muje a daura indai Ammah ta zata tashi,yace Amma dole sai da danginki nace ba komai muje suna Borno da wasu a kauye nan kano,y ace za kuje a jirgi ai sharp sharp.

     Waya nayi da Meenat basu San halin da ake ciki ba nace su kula da komai sai gobe da safe zan dawo,Guess house din Aayan muka je dashi ba tare da ya ko kalleni ba nima haka ina mamakin duniya babu na Allah,muna zuwa ya mika min wasu kaya a kwali yace je kiyi wanka sosai ki sa,da sauri na fada bedroom dake palon nayi wanka da Sallah na shafa lotion da komai kwalliya ce kawai na kasa yi sabo da halin da nake ciki na sa kayan na shafa turaruka yanda nayi kyau abin ba a cewa komai kamar yasan size dina doguwar rigar Arab ce fitted me shegen kyau da ado kamar wata Amaryar Larabawa haka ba dawo da mayafinta,black da adon sky blue nasa takalmin da na gani sky, harda wata jaka itama sky,na fito sai dai kirjinsa babu Nonon kirki yan kana na ne dasu kowa yaganni yaga yarinya danya danma ina da tsayi kuma ba kiba ba ramammiya bace,normal nake yar cakwas dani. wayyo shi kanshi yasan na hadu amma sai ya dauke kai yana yatsina fuska,ya shirya cikin sky blue yard me shara shara kamar Amarya da Ango lallai zamu kwashi yan kallo,amma gaba daya zuciyoyinmu ba dadi,ni haushinsa ma nake ji,shima haka,

muje naji yace tare da cewa bani da lokacin yi miki bayanin dalilin aurenki da nace zanyi,amma ina da dalili,ki nutsu Rayuwar gidanmu da zaki shiga daban take,da kanki zaki gane me yasa na aureki idan kin shiga gidan,bazan cuceki ba karki sa rai ina sonki, ko zan faranta miki,ko zaki ji dadi no Kasuwanci ne deal ne,zan biya ki kudin da zaki kula da yan uwanki kuji dadin duniya tare da Ummanki zan biya mata kudin hospital da komai,ko mene kike so a duniya zan baki,ni kuma zaki aureni ki zauna cikin kunci dan baza ki so Zama dani ba baza kiji dadi ko da minti daya ba,sannan ga matsalar family na sai kinbi a sannu zaki gane matsalarsu ko kiyi Nasara a Kansu ko suyi a taki wannan ya rage naki,ko da ace ina Sonki na aureki to fa ni bana haihuwa, kuma an auna lafiya nake amma nayi aure har sau Uku ban taba yiwa wata ciki ba,ba asibitin da banje ba,sannan zaki ji ance ina da Hawan jini ina da Diabetes wannan karya ne lafiya kalau Alhmdllh kawai fada nayi dan na samu sauki wajen family ta wani ban garen,bance ki dagawa kowa kafa ba a dangina sabo da ni kike aure ba su ba,amma banda rashin kunya karki soma raina min yan Uwa thts all,idan kin kiyaye zaki samu kudi da jin dadi,sauran yaki ya rage naki,ni dai ina da manufata da burina na aurenki wanda a yau zaki fara ganin daya.lets go,bana bukatar kiyi wani abu dan ki faranta min rai sabo da na tsani mata kaf banda uwata yayi gaba abinsa.

   Ni ko a raina ban dauka serious ba tunda bani da wayo yarinya ce ni ga karancin ilmi,ai sai nace tunda zan samu kudin kula dasu Meenat da lafiyar Ammah kawai a daura banyi tunanin komai ba,duk na rude har na matsu a daura domin a mayar da Ammah a dinketa ta samu Lfy burina kenan,abinda ban sani ba tuni ma har anyi aikin an gama komai Ashe wayo suka yi mini dan ba yarda da wuri.
    Gidan make up ya kaini da kansa yace na shiga ina shiga naga ana ta karramani Ashe sun San da zuwana,nan fa aka gyara min gashi da kwalliya yar sama sama,na fito shi kanshi saida ya kalleni ya kara kallona,amma sai ya tabe baki na shiga yaja muka tafi sai gidansu dake GRA,a cikin motar yace karki tunanin auren zan sakeki da wuri tunda kema dan kudi kikayi ni aurena ba saki sai da dalili,ni kuwa kudi nake nema dama kawai nace karka damu ni ma dan kudi nayi ai kasuwanci ne kawai nima idan kudin sun isheni zan nemi saki  sabo da na auri wanda nake so ni insha'allah kamar yanda nake yar sunna sai nayi auren so da kauna na sunna.

   Baki ya tabe ba tare da yace komai ba har muka shiga cikin gidan kafin na fito yace kiyi kamar muna son juna a gaban iya Family na,kudi da Ammah kawai nake hangowa nace to an gama, fitowa yayi nima na fito muka jera kamar masoyann gaske abin birgewa muna tafiya can wani part sai ga yan matan nan da samari birjiki muna hangosu kowa da abinda yakeyi na nishadi,a hankali yace action nan take na tuno kudi da Ammah ta kawai na kakalo murmushi lafiyayye na saki ina masa wani kallo da kowa zai ce Masoyina ne mun shaku da juna.
    A hankali yace Good job Ashe lallai Yarima bincikensa yayi gaskiya kina son kudi,murmushi nayi nace na gaske ma kuwa ai na shaku da kudi a duniya bani da burin da ya wuce kudi,Muna tafiya muna magana tunanin mutane ai duk soyayya ce da kallo kawai ake binmu, muryarsa naji yace karki gaisar da kowa nasan ke village girl ce,nace an gama in dai da kudi baza ka samu matsala dani ba,wani kallo ya min yana yatsina fuska muna tafiya,yan matan nan suna ta mamaki yar iska nan Ya Aayan zai aura tab ai kuwa zata ci duka,nan take kishi ya turnike su zai auri wata ba su ba ga mata kyawawa a gidansu yan Uwa,nan take suka ci Alwashin ganin bayana,dan haka daya a ciki ta taso cike da kishi tace ya Aayan badai kazamar nan zaka aura ba,dama itace kace zaka kawota bayan gamu a gidan ka Zaba mana,kallo ma bata ishe mu ba harda ni ,aiko ta fusata tare da jawo gyalena ke yar matsiyata,na rigada na gama rainasu nan take na fisge mayafina tare da cewa kinci sa'a ina da muhimmin Uzuri banda lokacinku amma da kin San yau kin rike gyale me daraja nayi gaba abina,dan ta kara Jin haushi ma kawai nayi ta maza na rike hannun Aayan a karo na farko,yayi matukar mamaki nan take ya canja fuska,nace Business ne ka bari a gama lfy na fika Sanin dokokinsa muje kawai nima ina da dalilina na yin hakan a sannu zaka gane. mamaki 
Ya cika shi a fili yace lallai Yarima yayi bincike me kyau,nace ba karya indai akan kudine shirka da kisa ne kawai bazanyi ba.
     Muna wuce wajen yan matan na saki hannunsa ya juyo tare da gasa min harara karki kuma taba min jiki,nace an gama sai da dalili duk cikin kudinka,har muka shiga part din tsohuwar nan wato Hajja,tana takama da isa na durkusa har kasa na gaisa ta tsabar tsufa bata gane nice nazo polio ba,cike da wulakanci ta amshe ni,sai ga wasu dattijawa yan gayu su Hudu mata sun shigo nan ma kaina kasa cike da ladabi har kasa na gaisar dasu suma dai a wulakancen suka amsa,sai ga maza manya su Uku sun shigo ciki har da Abbi duk suna kama da Alama brothers ne,suma haka na gaisa su Abbi ya gane ni murmushin mugunta ya saki ya kalli Aayan tare da cewa karuwar taka zaka aura kenan,lallai bariki tayi dadi,dayan cikin su yace ke bafa ya haihuwa ba lafiyayye bane amma kin bamu mamaki da zaki aureshi to mudai baza mu rufe miki cutarsa ba idan kudi kike nema ma ki shafawa kanki ruwa idan kuma tuna ninki aure na gaskiya to kece a wahale,mamaki ya kamani amma na tuno Ammah kawai nace ina sonsa haka sabo da Allah zan aureshi,Abbi yace a ina danginki suke? dangina na uba suna Maiduguri,na kalli Aayan cike da fara'a nace ai munje da kai rannan kasan ko ina ka basu address suje,ido na kifta masa,mamaki ya kamasu karfa da gaske soyayya muke da Aayan gashi ma yasan dangina.

     Yace muje na saukeki a gida ko,Abbi yace no Ku tsaya dole da ita za a tafi gaban iyayenta muka sani ko karya take,nace ba damuwa,muna zaune aka shirya tafiya maiduguri a jirgi abinka da Naira,Manyan mata su biyu su Abbi su Uku sai Aayan da ni kuma,ina kusa dashi babu wanda ke kula kowa,wai abinka da masu kudi sai gani a jirgi ina tsoro dai haka na maze,mintina kadan sai gamu a Maiduguri Allah yasa muna zuwa watarana,nasan ko ina,motoci aka kawo musu yan gaske nayi jagora har gidan su Abbanmu,nanfa yan uwansa Allah sarki suka dinga murna cewar Ammah dani mun girmamasu mun basu hakkinsu za ayi min aure amma su aka barwa komai a matsayin su na dangin uba,haba shi Kanshi Aayan yayi mamakin irin mutunci da karramawa da aka musu duk da cewa ba masu kudi bane amma an mutunta su matuka,matan ne kadai suke ta yatsina fuska suna tabe baki kun san dama mata sunfi maza kasa danne abu.

     Nan take abin mamaki sukace a daura Aure domin su Abbi su gama shirya mugunta a kaina.
   Dangin Abbana sai da suka tabbatar ina so da yarda ta sannan kawai suka tara mutane a masallaci shi kanshi Aayan baiyi tunanin Abbi zai ce yanzu za a daura ba,shi Sam bai ma kawo nan kusa za a daura auren ba,nan take dana sani da nadama suka lullubeshi.

    Nima haka har kuka a boye yar yarinya dani yanzu na shiga 17yrs ace za ayi min aure,tunowa nayi Ammah na can rai a hannun Allah,ina zaune naji ana guda kamar wasa wai an daura Sadaki Dubu Dari Uku,ina jin yanda nayi tsada a sadaki na sai gashi ina murna naji kudi domin ni in dai kudi ne an gama kawai,har wani yanga na fara yi daga jin sadakina Dubu Dari uku,Aayan kamar ance an masa mutuwa ya kasa boye fushinsa,nan na karbi Numbers na dangin mu na basu tawa muka musu Sallama zamu dawo Kano,har kudi na dan basu kadan cikin na sadakina da kyar ma suka karba domin Aayan ya basu kudi masu yawa.

    Bamu zarce ko ina ba sai kano a jirgi,muna sauka sai kauyen Rimin Gado dangin Ammah mun samu kadan daga ciki na nuna musu kaf dangina an karbemu a mutunce sai dai nace Ammah tace a gaishesu bata da lafiya ne,kamar yanda na fadawa Dangin Abba, sunji ba dadi har wasu sunce zasu zo dubata.
    Sharp sharp muka gama komai suma sunsha kudi wajen Aayan amma kowa yasan wannan Ango bashi da fara'a kamar ba auren so ba haka muke dashi sosai yake fushi a fili.

  Su Abbi sai kus kus sukeyi ana shirya mugunta.
      A ranar muka dawo cikin garin Kano bani da burin da ya wuce naje naga Ammah ta samu sauki,daga ni sai Aayan a mota,yana Driving, cike da zumudi nace kayi waya naji an gama aikin tunda na yarda an daura auren,kallo na yayi a matukar hasale yace an dade da Gama mata aiki tuni anyi komai je ki gani,a hospital din ya saukeni ya figi motarsa ya barni tsaye baki bude da jakata a rataye,nace oho dai ni tunda zan samu kudi shike nan,ya kaga Ammah ta samu Lfy?gashi nayi auren da take buri nayi,na cikawa Ammah burinta gashi nayi auren da takeso,da sauri na shiga dakin da su Ma'eesha ke ciki special room aka bamu sabo da Naira.

     Ina shiga gabana yaba da dum ganin su Meenat suna Rusa uban kuka,ga mutum nan a lullube da alama gawa ce,lokacin dare yayi jakata na jefar a kasa a tsorace na karasa tare da bude gawar Innalillahi na maimaita domin Ammah ce tabbas ta rasu.
    Zubewa nayi kasa sumammiyya,nan likita suka shigo aka mai Dani gadon tare da rufuwa a kaina da kyar na farfado ina uban gunjin kuka,sai hakuri ake bamu su Meenat suna rungume a jikina,kwana mukayi kuka ni tunanina laifin Aayan ne mugu su suka kashe min Ammah ta gashi ya zalunceni na yarda an daura min Aure dashi amma sunyi ganganci da Rayuwar Ammah ta rasu wayyo Allah,yau ina Algus da nakeyi sabo da maganin Ammah duk sabo da kar ta mutu tasha wahala nake tsoro,kullum yawon neman Kudi na tsallake risk da dama don kawai na samo kudin magani.

   Ba tare da Sanin uwata ba naje nayi auren kasuwanci don sabo da kar ta mutu ayi mata magani ta warke,nayi duk abinda zanyi amma kash baiyi amfani ba,sai ma gani nake ina zargin kaina cewar da hannuna na kashe Ammah domin nice na damu sai an mata aiki duk da cewa an fada mana cewar aiki biyu za ayi mata da na kafafu sai kuma wani a cikin Mahaifarta shine me matsalar ba lallai ta tashi ba,amma na dage sai anyi gani nake zata warke,dana sani da nadama nake ta faman yi,Ammah na zaune lfy na damu gashi ashe ta hanyar aikin da kudin da komai amma sai lokacin ta rasu,burina bai cika ba domin bani da burin da ya wuce nayi kudi Ammah taji dadin duniya tare da kannena sannan nayi aure Ammah taga mijina da jikokinta amma kash babu ko daya da ta gani domin wannan auren ma na Kasuwanci ne.
     Iya karfina na kwalla kara da ihu,kowa sai ya tausaya mana,kuka muke ba ji ba gani tare da tumami harda birgima tare da shure shure abin sai wanda ya gani,sai da muka kwana cir muna abu daya,gari ya waye ma muka daura. lokacin akace Muzo mu nemo yan uwanmu maza a dauki gawa.
    Nan take nayi waya dangin Ammah kaf da Dangin Abbah da sauran makwafta da abokan arziki tuni zancen ya watsu Ammah ta rasu,Allah ya taimakeni dangin uba na ne suka daura min Aure,haka dangin uwata da saninsu.h ar mamakin auren nakeyi sabo da kudi wai nan a rana daya anyi an gama komai gaskiya kudi sunyi a rayuwa.


21-25


Official

By
AsmaBaffa

CHOICE ths page is for u...?❤
 
ASYCOOL ina kika boye ne?


Fans masu sharhi ta ko ina ina matukar Godiya da kulawa ina jin dadi yanda kuke kokarin yin Sharhi abin ba a cewa komai sai godiya Masoya ta ko ina,Allah ya bar zumunci ya biya muku bukatunku na alkhairi,tsakanina daku sai godiya,insha'Allah kowacce da page dinta masu sharhi,shine farin cikina da zan baku na yanda kuke sharhi.loves u all.????❤❤


Gaskiya duk Wanda ya San Ammah mutuniyar kirki ya girgiza da mutuwar nan,nan take asibitin ya samu halartar dangin Ammah maza da mata da yake mutuwa ce har sunzo mana.da taimakonsu aka bamu gawar muka tafi da ita dan  gidanmu na talauci,nan fa dangin Abba ma na Maiduguri sun samu Damar zuwa da yawa,ga yan unguwa harda kawata Nawwara,su Shehu me waya sune kan gaba,Adamu Kansila ma yazo haka aka hada gawa tare da sallatarta aka kaita gidanta na gaskiya,Kuka mukeyi sosai musamman ni da Meenat,Maeesha ba hankali sosai Sam bata ma damu ba sosai har ta daina kukan,mu kuwa sai nasiha ake mana da Wa'azi ana bamu hakuri, washe gari kuwa da safe ana ta kawo mana abinci daga makwafta,ga wani dangin Ammah sun dafa,

     Ma'eesha tasha baccinta ta tashi ba hankali ta fara bude abincin iri iri sai ta rufe ta dawo gefe na tare da nuna min da yatsanta tana Sis ni wancan nake so cike da shagwaba tace ni me tiririn  can nake so,saida ta bawa mutane dariya,da rana kuwa tana cin tuwon shinkafa tace Sis wai kamar ana biki? Muci tuwon mu musha Kokonmu Ammah ta tafi Rimin Gado kafin ta dawo. haka muke ta amsar gaisuwa,har akayi sadakar uku dangin nesa duk wasu sun tafi sai iya na Ammah mata da wasu mazan su uku wanda suke uba daya da Ammah,makwafta suna kawo mana abinci iri iri kullum,da kudin sadakina nake yin komai na kashe kudi sosai domin mutuwa yanzu kamar biki haka take,Meenat sunji ana ta ce min Amarya Allah sarki jiya aka daura mata aure sabo da har yan unguwar mu sun San anyi auren domin munzo da Aayan tare dasu Abbi sunga gidanmu na asali da muke rayuwa,haka kuma na hada su da wasu manyan dake makwaftan mu tunda mu bamu da yan Uwa a cikin kano sai abokan arziki,gashi Ammah na asibiti kuma Bai dace ace anyi aure ba wasu shedu ba babu Sanin mutane ai babu dadi a ganina bai dace ba,shi yasa nace dole Muzo sharp sharp su gani su San inda muke da zama duk da cewa dangin Aayan sun min kallon wulakanci ganin inda muke da zama har dariya suka yi masa dama sun San ai sai talaka ce zata iya aurensa.

    Ni dai ko a jikina tunda kudi zan samu gani nake kudi sune maganin komai,sai gashi tun ba aje ko ina ba an saukar min da Aya,Meenat ce ta jani gefe tace Sis ya naji ana ce miki Amarya?ki Bari baki su tafi zan sanar daku komai,da gaske kinyi aure? No ki Bari idan mun nutsu zaki ji.Bayan anyi sadakar Bakwai muna zaune Dangin Ammah suka samu a tsakiya cewar zasu dauki Meenat da Ma'eesha su tafi dasu kauye ni kuma tunda nayi aure na zauna dakin mijina duk da cewa abin ya daure musu kai rashin ganin angon nawa a wajen janaizar Ammah,amma sai nace dasu baya kasar yayi tafiya kasar waje,cikin ladabi nace Ni bance karku tafi dasu ba dama Ku ya dace Ku rike mu,amma sabo da karatunsu kuma kauye ba schl baya ga haka basu saba da rayuwa acan ba,kuma nima zan shiga damuwa na rashinsu ga rashin Ammah me zai hana a bar min su mijina zai rike su ba matsala zai musu komai sai mu zauna tare,Dangin Ammah dama kadan suke jira nan suka fara masifa to ai gaki gasu in dai rikon dadi gareshi,sannu yan Birni Ku yan boko ko to dama dan mu fita hakkinku mukace zamu tafi daku amma tunda haka kuka Zaba shike nan, a cikin matan ma daya tace a'a haba a bisu a hankali ai yara ne ga rashin Uwa sunyi amma har ita Mufeeda kanta nawa take kuruciya ce kawai,nayi mamaki a birni guda amma kamar Mufeeda wai Fatima ta yarda tayi aure tana yar Sha bakwai a shekaru,duba fa yan Birni da sai su kai shekara talatin yarinya na yawo a titi wai karatu take.
   Daya cikin maza kanin Ammah yace to Alhmdllh ai mijinta me kudi ne da alama zai iya rikesu da Amana na tabbata amma ya dace ace munje munga gidan mijin naki,gumi ne ya keto min nan take na rude.

   Karya na kakalo nace ai ba yanzu zan tare ba,dazu munyi waya dashi jibi zai dawo daga turai sannan zasu sa ranar da zan tare sai na fada muku a waya ko nazo har gida na kawo kati sai kuzo ayi komai da Ku,ganin mijin nawa me kudi ne tunda sun ganshi tare da danginsa ba karya gashi sunsha kyautar kudi kawai sai suka washe baki tare da cewa to Allah ya kaimu ki tabbatar kin yo mana waya,da sauri nace Insha'allah,to yanzu abinci fa da sauransu wa zai baku kuma Bai dace Ku zauna Ku kadai ba a wannan gidan ba,nace ai masu gadi zai kawo mana yace suna kan hanya ma sojoji ne,da mamaki sukace lallai kunyi dacen me kudi ke ko yar nan kin huta a duniya dan Allah a dinga tunawa damu dangi kar a samu a manta damu,nace haba dai ai daku za a ci komai,nan dai suka yi ta kauyancinsu na Fulani daga nan suka tattara gaba daya suka mana Sallama zasu tafi,har kudin mota na basu muka rakasu har tasha sabo da bamu saba dasu ba ko kuka bamuyi ba sabo da sun ishemu dama sai bata mana gida sukeyi suna samu aiki.
    Suna tafiya mu Ukun muka tsaya a wani gidan yan haya,gidan haya ne Babba,daki daki ake bada hayar kowa da dakinsa sunfi mutum ashirin a gidan kuma toilet daya garesu,Meenat tace me zamu yi a nan? Ko magana banyi ba nace suzo muje,muna shiga muka gaisa dasu suna ta mana ta'aziyya,dakin wata Dattijuwa Uwaliya na shiga tana zaune gefe tana Shan kunu,Uwaliya bata taba haihuwa a duniya ba,danginta duk suna kauye sana'ar aikatau wanke wanke da shara ce ta kawota birni,bata yi dacen gidan da take aiki ba kuma bata son zaman kauye sabo da babu sana'ar kirki a can,sai ta kama hayar daki a birni tana zuwa gidan aikin haka da safe ta dawo da yamma kullum,da fara'a ta tarbeni muna gaisawa nace  Uwaliya idan baza ki damu ba ki dawo gidanmu da zama mana kyauta na baki daki daya mu kuma sai mu dauki daki biyun,dama gidanmu daki Uku ne sai dan kitchen da toilet ammafa bashi da wani kyau gidan gidane na talaka amma nasan yafi wanda Uwaliya ke haya a ciki,da murna Uwaliya ta dinga godiya,haka mutane suka tayata murnar daina biyan kudin haya zata zauna kyauta a gidanmu,wasu suka dinga mamaki wai duniya ta juya min baya duk son kudin Mufeeda yarinyar da komai nata na kudi ne yau gashi taji uwar bari kar a hauro ayi musu fyade har roko take a zauna musu kyauta a gida lallai duniya tun ba a je ko ina ba kenan.

     Uwaliya ta kwaso kayanta kaf tare da sanarwa me gidanta ta dawo gidanmu sabo da gida ba Babban gida bane gashi mijin kasuwancin nawa ya kashe min Uwa ya gudu ban kara ganin sa ba,ya barni da igiyar aure mara amfani a kaina,idan bai nemeni ba ya zanyi wayyo neman kudi ya jawo min.

    Dare yayi Uwaliya tana dakinta ta gama cin abincin da na siyo mana har ita na bawa tana ta godiya sabo da Uwaliya mutuniyar kirki ce ba ruwanta da kowa ba gulma ba sa ido.
   Na tasa kannena a gaba Meenat da Ma'eesha nace dole suci abinci naga duk sun rame,duk da cewa na fisu ramewa sosai,Bani da karfin gwiwar da zan mana girki duk cikin kudin Sadakina nake cinyewa,Meenat tace sis kici mana idan baza kici ba mu taya zamu iya ci,duk kin rame dan Allah ki kara hakuri kullum fa sai kinyi kuka cikin dare muna jinki,Maeesha tace kuma ance ba kyau ana yiwa wanda ya mutu kuka yanzu Ammah kina kara mata azaba fa,wani hawayen tausayin kanmu ne ya zubo min na share ina kakalo Murmushin dole tare da sa hannuna a abincin muka fara ci badan muna so ba,kawai tunanin Ammah nake da kanmu tare da igiyar dake kaina,miji bai San me nake ciki ba,kaico na nikam na tafka kuskure dana sani nakeyi da nadama,ganin basa ci da yawa na shiga basu da kaina ina ciyar dasu suma suna bani abin haushin na fisu saurin kuka kawai hawaye nake ina ci har sai da na karya musu zuciya suma suka fara,Maeesha tace Wai Ammah baza ta dawo bane? Wai Sis ba a dawowa? Nace baza ta dawo ba ina shesheka na kara fashewa da kuka babu me lallashi,muna ta tuno Rayuwar da mukayi da Ammah me dadi tun tasowar mu,dan ma Allah yasa gaba daya kayan Ammah na sawa na kwashe na bawa Danginta dan kar ma na gansu bakin ciki na damuna da yawan kuka,sai pics Namu da nata amma komai nata na kwashe na bayar,masu amfani kawai na ajiye tunanina ko da kuwa Allah zai bayyana mana Abbanmu watarana.
    Uwaliyace ta shigo ta zauna kusa damu ta fara yi mana nasiha tana lallashi tare da kwantar mana da hankali har mukayi shuru,sai ta fara yi mana labaran tatsuniya na abin dariya muka dinga ta faman dariya kamar ba mune dazu muke kuka ba,mun dade sosai sannan nace muyi bacci ta tafi dakinta,nima na kulle mana daki,muna kwance mun cure waje daya,cike da nutsuwa nace Meenat Ku tashi muyi magana,da sauri suka Mike zaune a saman katifar domin ko arzikin gado bamu dashi.

     Rungumesu nayi a jikina sannan na kwantar da Ma'eesha saman cinyata ina shafa kanta,Meenat ma tana jikina ta jingina,nace Meenat nasan kinfi Ma'eesha hankali zan baku labari akan zancen da kuke ji nayi aure,ba wai bane tabbas da gaske Meenat nayi aure nan na kwashe labarin duk yanda akayi tun daga fitar da nake nemo kudin maganin Ammah har haduwata da Aayan,Yarima tare da Aurena kaf na basu Labari Ma'eesha nasan duk da ta fahimci komai amma baza ta kai Meenat fuskanta ba,gani nayi Meenat tana ta murna tana dariya,nace mene haka ke kuma? Sis wlh kin cikawa Ammah burinta shi yasa,kuma Alhmdllh kin samu me kudi Allah yasa na gari ne sis ya tallafa mana,kawai ni shawara mu dage da addua kamar yanda muka saba sai kiga Allah ya canja masa zuciya from bad to good,kuma am serious bashi ya kashe Ammah ba domin kina fita aka fito da Ammah lfy an mata aiki tuni kinga lokacin ma baki je wajensa ba bare yace miki baza a hada ta ba sai kin aureshi kawai wayo sukayi miki, naji dadin zancen Meenat sosai da ta ganar dani amma da haushin Aayan nakeji cewar shi ya kashe Ammah amma duk da hakan ban wani yarda ba kawai shi ya kashe min Uwa.

    Meenat tace lokacin da Ammah ta farfado Sis tana ta nemanki bakya nan,sai tace mana naji a jikina wani abin Alkhairi zai samu yata Abin alfaharina Mufeedata yau Alkhairi zata hadu dashi,naso ace zanga wannan lokaci da Idona amma kash,sai muka ga tayi shuru,ta kara rike hannuna tace Meenat kuyiwa yar uwarku biyayya idan kuka saba mata bazan yafe muku ba,ku hada kanku  karku taba rabuwa sai aure,Mufeeda zata rike min Ku da Amana kamar ina raye,ta Zama madadina,sai tayi tari taci gaba kuce ina son Mufeedata Allah ya bata miji na gari me kaunarta wanda zata huta taji dadi a hannunsa,sannan Ku fada mata nace duk Wanda ta aura ko waye tayi masa biyayya,ta kara hakuri sannan ta kula dashi da rayuwarsa tare da komai nasa da ya shafeshi,karta bari a take mata yanci duk Rintsi ta kwace yancinta,Mufeedata nasan ba me tsoro bace dan haka kar taji tsoron fadan gaskiya a duk inda take,taji tsoron Allah a duk inda take,tabi Allah,ta kula da ibada,ta tsare mutuncinta na ya mace,sannan tabi mijinta ta kula da iyayensa,ku rike addua, kuyi Zumunci dangina dana babanku baku da kamarsu, ba da iya Mufeeda nake ba,gaba dayanku yarana wannan shine abinda zan bar muku,shine a matsayin gadonku tunda ban bar muku komai ba,karshe Ku fadawa Mufeeda idan Allah ya bayyana babanku kuce masa duk abinda ya min na yafe masa baki daya,ni nasan ban zalinceshi ba amma shima ya yafe min,naso ace na aaaabaku labari akan zamana da babanku har zuwa sabanin da muka samu,da dalilin sabaninmu amma idan ya bayyana nasan zai sanar da......Nan mukaga Ammah tayi shuru Sis sai ga Doctor ya shigo yayi aune aune sai muka ga ya lullubeta suna magana da turanci da wasu nurses nan take mukaji ashe mutuwa Ammah tayi,gaba dayanmu kafin Meenat ta gama bamu labari mun jige rigarmu da hawaye..Nan Ma'eesha tace Sis Meenat kin manta tace mu fadawa Mufeeda wai tayi aure shine burinta sannan idan tayi aure ta fadawa mijinta Ammah na gaisheshi kuma ga Amana nan ta yarta Mufeeda abin sonta me share mata hawaye,ya daya tamkar da Dubu,mace me kamar maza ya riketa Amana ya bawa mufeedanta farin ciki shine bukatar Amman Mufeeda,nan take da jin zancen Ma'eesha sai muka koma muna dariya muna hawaye kamar Ammah ce ke maganar,dama Ma'eesha akwai iya bada labari gashi bata mantawa yanda ka fadi abu haka zata bada labari. Haka mukayi ta hirar Ammah har dai na sa Ma'eesha a tsakiyarmu muka kwanta abinmu har bacci me nauyi ya kwashe mu.

    Sati biyu da rasuwar Ammah cikin kudin Sadakina na kara jarin sana'oina,cikin Sadakin na canjawa su Meenat makarantar Kudi aka yi musu transfer a secondary schl me Saukin kudi sunfi na Gomnati karatu ni kuma bani da burin da ya wuce suyi karatu,Komai har su Uniform nayi musu har kala Hudu hudu su schl bags littatafai etc,haka nayi mana sababbin dunkuna masu dan kyau,na kara siya mana abincin gida domin tuni na cire rai da auren da nayi na gama tabbatarwa cutata Aayan yayi sabo da haka kawai nayi watsi da wani aure,na manta ma ina da igiyar aurensa sam duk da cewa abin na raina amma na hakura na rungumi rayuwarmu ace anfi sati biyu da daura aure amma kamar wanda ya auri karya ai idan da gaskiya sai yazo ya biya ni kudin kasuwancina dana yarda na aureshi bisa sharadi.

     Haka na kwashe wata guda da aure amma babu labarin Aayan abin takaicin kuma duk na karar da kudin sadakina,gashi kuma sana'ar tawa yanzu Sam bata tafiya ba kudi a hannun mutane,sai a yini guda ba a zo ance za a siyi ko Wake ba,duk na shiga damuwa ina tunani idan komai ya kare mana ya zamuyi ina zan sa kaina,abinda ya Dameni shine nayi Nadamar Halayena na Algus a sana'a ta tuni yanzu tsakani da Allah nake yinta bana kara komai marar kyau,kuma Istigifari nakeyi Allah ya yafe min,Amma Kuma dana gyara halina sai ma na daina ciniki,komai ya tabarbare,ba riba,lokacin kuma da bana yin ingantacciya komai tafiya yake min dai dai ina samun ciniki da riba,ikon Allah kenan yanzu Kusan duk sun karye ma,idan ya kare sai dai na iba a cikin Sadakina na kara dama duk kudin ma sun kare sabo da nayi mana abubuwa ciki da dama.
   Sai da nayi dana Sanin canjawa su Meenat makarantar Kudi yanzu da uban me zan biya musu idan shekara ta kare,nidai haka nake ta yawon saro kaya da siyarwa ina sana'ata tunda ba labarin angon,ni kuma bazan je gidansu ba,ga rasuwar Ammah kullum sabuwa ce a wajenmu ko yaushe muna kuka muna tunaninta.

   Yau juma'a na kai wata daya da sati daya da Aure kuma haka da rasuwar Ammah,tun safe na sallami su Meenat suka tafi schl,Uwaliya ma ta tafi gidan da take aiki,ni kadai ce a gidan sai da na gyara ko ina dake gidan fes fes tare da kunna turaren wuta,na kunna turaren wuta har Toilet sannan na dawo tsakar gida jikin Rijiyar gidanmu ina wanke mana kayan sawarmu ina shanyawa ga girki ina yi jullof din shinkafa taji kayan hadi harda kifi sabo da bamu da yawa shi yasa girkinmu ke dadi,sai dana cika igiya da kayanmu kana na shanya tare da kara wanke wajen,kwashe abincin nayi a wani foodflask me dan kyau sabo dana siya mana shi set biyu.

    Lokaci na kalla naga bani da abinda zanyi kawai na kwashe yan kudin da suka rage min na zuba cikin Aljihun tight wando na na ciki,sabo da ni duk tight din dana ke sawa cikin kaya to sai na kaiwa wata tela ta dinka min aljihu da zip a jikinsa sabo da ko ina zanje a duniya da kudi a jikina kaf nake tafiya tun Ammah Nada rai,bare yanzu da nake tsoro kar na barsu a gida wani cikin yan iskan gari su shiga su yashemu tas mu rasa inda za muyi shi yasa kamar me aikin Hajji kudina na jikina wanda zanyi amfani dasu kawai nake rikewa a hannuna,kulle gidan nayi tare da tafiya gidan kawata Nawwara sabo da tana ta zuwa ni bana zuwa,da Sallama na shiga muka gaisa da Ummanta tare da Yayanta Hammad,tunda na shiga Hammad yake ta kallo na har kunya naji,Umma tace shiga ciki mana Mufeeda mutuniyar taki yanzu zata dawo ai,ina Zaune sai ga Nawwara ta dawo dama Salat aka aiketa ta siyo,Da gudu ta fado palon tare da miko min hannu muka tafa,tace shegiyar gari sai yau zaki zo, nace ke dai bari ba lokaci wlh yanzu ma dan kar na karya alkawari nazo miki sauri nake na koma kafin su Meenat su dawo kin San yau Friday,Nawwara tace hakane uwar mata,Wlh ina tausaya muku musamman ke da kike komai it's not easy ace kamarki ke kula da gida just 17yrs,ni abinda ma ya Dameni Mufeeda auren nan naki kinji yanda ake gulmar a unguwa dan abin ya shafeku ne ba za ayi a gabanku ba,wasu sunce karya ne dama,wasu kuma sunce ai auren kudi kika yi sabo da son abin duniya gashi wai ya gudu yaki zuwa ko kallonki baya yi,wasu ma sunce bature kika aura,wasu kuwa wai ciki yayi miki shine aka zubar dan kar a gane shine akace ya aureki,wasu kuma sukace ai ana daurawa ya samu ya kwanta dake shine ya fece,ke kowa da abinda zaice,murmushin takaici nayi nasan ni na jawowa kaina sai nace can da matsalarsu zasu gani ai watarana gaskiya zatayi halinta,yanzu gulma ba kauye ba birni kowa yinta yake.

    Ita kanta Nawwara karya take tace tasan sirrina ni dama can ban damu da kawaye ba bare duk sirrina na kwaso na fada musu a dinga gulmata sabo da mutum mugun ice wani jira yake yaji sirrinka yaje yayi ta yadawa a duniya shi yasa ni bana so wata ta fada min sirrin rayuwarta kuma nima bazan fada miki nawa ba kawai ayi hirar duniya,duk inda mutum ya kai da gulmarsa bazaice ya San sirrin gidanmu ba,shi yasa ko ita Nawwara tayi tayi taji gaskiyar Aurena da halin da nake ciki amma naki yarda ma Sam ta sani daga ni sai yan uwana suma kuma haka Ammah ta tarbiyar damu,sirrinmu iya mu kawai family,share zancen Nawwara nayi na saki wata hirar can ta duniya daban,daga nan na Mike nace yan makaranta sun kusa dawowa ni zan wuce,Hammad yana  Jin haka ya mike tare da fitowa waje,saida ta rako ni har waje muka yi Sallama,ina cikin tafiya Sai ga Hammad yana cewa Mufeeda na amsa a mutunce,Yace wai da gaske kina da aure dan Allah? Nace ae,da gaske ko wasa ni fa ban yarda ba na dawo daga service naji labari,murmushi nayi nace wlh yaya Hammad da gaske ne, bata rai naga yayi tare da cewa to gaskiya wannan ba mijin kirki bane kisa ya sake ki kawai ai gwara ki zauna ba aure,nace to idan ya sakeni wa zan aura?Ni ina son mijina bazan iya rabuwa dashi ba,komai shi yake daukan nauyinmu,Hammad yayi wani dariya kamar Boss yace sannu yar karya da ba a San Asalin balbela ba da sai ace daga masar take,ance me kudi ne ya akayi kike sana'a?kina ci da kanki,wa ya taba ganinsa yazo wajenki?makaryaciya rufa miki asiri zanyi kisa ya sakeki na lallaba Na aureki Ku ba gata ba,ba yayan uban kowa ba sai shegen iyayi wai ku  kyan da kuke dashi ne yake rudarku ko? 

Nima fa bani da hakuri watarana nace ina ganin mutuncinka Hammad karka bari na yaga ma mutunci a unguwar nan,ka gyara kalamanka,ni yanzu me daraja ce da tsada domin ina da aure kuma da ace kasan wa nake aure da sai ka raina kanka tare da yin nadamar kalamanka,ni nafi karfinka wlh ko ace bani da aure hankalinka da nutsuwarka sun min kadan a matsayin mijina,ina fadar haka na juya cike da Raunin zuciya ina son fara Kuka... dum gabana yayi mugun faduwa ganin motocin Aayan sun kai su Bakwai a jere kofar gidanmu,juyowa nayi na kalli Hammad kana nace ga dan Halak can, zo ga mijin nawa sai ka mutu na juya ina tafiya,na barshi nan tsaye,kusa da inda suka yi parking akwai me salat ba ruwana na tsaya na siya mana salat da tumatir sannan na rike ledar zan shiga gida,muryar su Meenat naji da fara'a suna sis mun dawo ina kika je?da sauri suka karaso tare da rungumeni ina musu Kiss a goshi domin mun saba da hakan ma,Ma'eesha ce ta karbi ledar salat dake hannuna ni kuma na karbi jakankunan makarantarsu muka nufi shiga gidanmu,ko kallon motocinsa banyi ba,yana ciki duk abinda mukeyi yana kallonmu,yasha mamakin ganin ko kallon motocin banyi ba kuma yasan na gane shine saima gida yaga mun shige,ni kuma cike da bakin ciki na banko kofarmu da karfi da niyyar na rufe dan Ubansa tunda baida mutunci nima zan nuna masa abin haushi da kunya kawai sai kofar ta balle baras ta fadi kasa rigijif ai ko har securities dinsa sai da suka barke da dariya yanda na shiga gidan cikin fushi da hasala tare da mako kofar kuma sai ta balle.

     Aayan ma sai da ya dara duk kuwa da kuncinsa,muna shiga na taimaka musu suka cire kayansu,nace suje suyi wanka muyi sallah sai muci abinci, shi kuwa Aayan ganin masallaci za a fara sallar Juma'a sai yace suje suyi sallah sai su dawo,a nan masallacin unguwarmu sukayi Sallar, kafin su fito na gyara salat na yanka mana,Bayan munyi sallah na zuba mana a tire kato kun San dai akwai ci ni kam,a tsakar gida saman tabarma na wani baje cinyoyina,sanye nake da Vest red,sai skert din atamfata yayi mugun Dameni gani da hips tare da da tudun Mazaune kamar babbar mace,haka nayi wani cas dani ga skin dina jajir da ita fara,ko dankwali ban daura ba sabo da ni dama a gida bai Dameni ba,jelar gashina har yaso wuce tsakiyar baya na,sajena da gashin gaban goshina sun kwanta luf,ina ta bawa su Meenat abinci a baki kamar wasu yara nima ina ci suma suna bani muna hira.

    Wani yaro ne ya shigo da Sallama wai Mufeeda tazo sauri yake zai tafi,nasan bazai wuce Aayan ba cike da masifa nace kace bata da lokacinsa,yaro ya je ya fada sai ga yaron ya dawo yace wai idan ya iskeki sai kin gwammace kida da karatu,Mufeeda tace kace nace yazo din koma mene yayi idan zai iya,yaro yace ni dai tsoro nake ji bazan iya fada masa ba,Mufeeda tace to dan uwarka nice sa'arka zaka zo ka fada min fice min a gida,yaro ya fice da sauri yana kuka Mufeeda ta zageshi,can sai ga Oga Aayan da kansa ya shigo gidan cike da bacin rai yana huci,kamar ance wani ya mutu yanda yake kunci,yanda ya hadu yau ba a cewa komai,yayi masifar kyan da ban taba gani ba,cikin kana nan kaya yake hadaddu duk gidanmu ya gauraye da kamshinsa.

    Wani Kwarjini ya min tsoronsa ya kamani na fara da na Sanin maganar dana fada masa,Ma'eesha sarkin Surutu tace sis gashi nan ya shugo ko shine mijin naki? Meenat ta kalleshi ta kalleni haka take yi sannan sukace ina yini? Da kyar ya iya bude baki yace am fine tare da kare min kallo ta kasan ido,

ni dai naci gaba da basu abinci a baki ina cewa kuci abinci akwai Islamiyya kun sani, ganin su Meenat a ransa yace har kanne gareta Ashe,muryarsa naji yace ina Mum naki,cike da zafin rai nace taje inda ka aiketa, ba wannan ne ya kawo ni ba ina da aikin yi,kizo muyi magana dake,Meenat tace Sis kije mana,sai da na ebi abinci a hannuna sannan na Mike da abina ina ci kamar mayya,ya kalleni yana mamakin jarabar ci na ko micijin ciki ne da ita oho,hannuna da shinkafa a ciki na dunkuleshi nace shigo wannan dakin,ya wani yatsina fuska yana tabe baki haka dai ya shiga yana wani makale jikinsa irin zai kwashi dirty,

     Ji nayi yace ba a gidanmu zaki zauna ba yanzu,wani gidan za a kaiki daban,kiyi fixing Date da kike so su Abbi sunce ba yanzu zaki shiga family house ba sai nan gaba,so gidan dana kaiki rannan kike gyarawa nan zaki shiga,ki sanarwa Mum naki,wani farin ciki ya kamani kamar na taka rawa wannan hadadden gida ga kayan dadi zanci na koshi, ban san sanda na fashe da murmushi ba tare da cewa wannan gidan me kayan dadi? sai kuma wani bakin ciki ya tsaya min wato bai ma San Ammah ta rasu ba,kuma ko irin yace min ya me jiki ko ta warke Sam,nace aiko ya me jiki kace min ko? Au bata warke ba?kamar na mareshi haka naji,nace ta rasu,Allah yaji kanta ya furta irin ko a jikinsa,nace daga ni sai kannena mu uku,yace then? kuma ni yanzu na fasa auren ka sakeni kawai yafi min bashi da amfani sam,murmushi yayi yana daga tsaye yace kin makaro kinci Sadaki,kuma na biya kudin Magani na cika alkawari dole ki cika min nawa,don haka sai ki biyani ko ki karbi aure zabi daya,Hawaye ya zubo min da muryar kuka nace mugu ka kashe mana Ammah zaka ce na biyaka kudi,ai kaine ya dace ka biyani kudin diyyar Ammah kai ka jawo ta rasu,da tuni muna nan da uwarmu,Kuma haka ake Business din idan banda sadaki me ka bani,bayan kai kace zamu ji dadin duniya da kudin,zaka yiwa kannena komai na rayuwa zanyi abinda nake so da kudi yanzu me kayi daga ciki,haka ake Deal din,ai sai na fara gani a kasa tukun,Oya na mika masa hannu nace miko kudin fara harkoki da jin dadi first mu fara murmurewa muma muji dadin duniya sai na yarda nima a kaini gidanka,kuma dole ka sai min injin Markade na dinga yiwa mutane ina samun kudi domin makociyar mu da kudin Markade taje Makkah, tare da keken saka kayan sanyi, bai sanda yayi dariya ba matar dake neman jin dadin duniya kuma wai itace da Markade a inji, ita nufinta duk cikin Jin dadi ne bata saba da dadin ba to,nace kuma sai ka sai min irin abin rannan me dadi,ka bani kudin kashewa,yace nawa zan baki?Na gama tunanina na shirya masa mugunta zanci kudinsa da yawa nan take na sosa kaina nace Dubu bakwai duk wata daya,kacal?yace, Na hangame baki nufinsa basu da yawa nace Dubu goma Sha daya to,ya juya tare da cewa get ready Next wk Driver zaizo ya daukeku.

  nace to haka za a kai maka Amaryar taka kai ba dangi?ba kwalliya?ba gyaran jiki?ko haka kaga anayi ko kuma son kudi da tsumulmula ce tayi ma yawa,mene Tsumulmula? Nace gashi nan haka wai ake kasuwancin zaka tafi ko sisi baza ka bani ba cikin kudina na business,abinci ya kare hakkinka ne,bani da Vaseline,ina so zan yi kitso ai sai ka kawo kudin ko? Ni tunanina ai nayi ne dan na tatseshi kudi na hada masa mugunta zan cinye masa kudi su kare,ya kalleni tare da daure fuska yana dariya a ransa yace nawa ne kudin?Na shirya karya na ninka kudin nace Dubu biyu,wata dariya ta kamashi amma ya maze ya zaro Dubu biyu sababbi kar yace gashi,na karba nace tsaya na irga domin kudi suna da doka tare da ka'ida,na dankwali yawu kamar me irga wasu milliyoyi na irga nace sun cika,yayi hanyar fita daga gidan, wai duk cikin Jin haushinsa dan na kona masa rai nace amma wlh girma ya fadi,an fadi kasa ba nauyi,ka bani kunya kuma ka bada guys ashe ma duk bogi ne da ake kurin ana da kudi sai dai a kwashi motoci ana yawo a gari,a tambayi Dubu biyu ba kari ba komai ina laifin ka bani Dubu uku ko ka kankaro girma da mutuncinka,amma yanda na fada haka ka bani a haka kamar gaske,ana tafiya kamar dan sarki aji tsoron Allah wlh azara'ilu ko yaushe zai iya zuwa, ficewa yayi da sauri sabo da dariya taci karfinsa bai so kuma taga hakorinsa yana dariya, haka ya shiga mota yana dariya,su Kansu escort din nasa mamaki sukeyi Aayan kamarsa duk jarabarsa wata na sashi dariya.







AsmaBaffa
Reply
#3
26-30


Official

By
AsmaBaffa


MAMAN MEENAT ina godiya da Sharhi,taku ta manya ce kunfi karfin kowa sai dai mu kwashi gaisuwa. page na yara ne?HAFCYCY this page is for u Sweety.

    QUEENMERMU tamu dubun gaisuwa???❤❤❤❤ 
MAMAN WALEEDA kin boye Allah yasa lfy.

Masu Sharhi yan albarka 
ASMABAFFA FANS CLUB
TASKAR SURAYYARMS
TASKAR FIDDAUSI SODANGI
HAUSE OF HAUSA NOVEL tare da sauran Gps ina matukar jinjina muku da godewa.masu min magana ta Pc tare da masu kira ina rangado muku gaisuwa me yawa Allah ya kara kauna.


     Koda ya fita basu zarce ko ina ba sai gidan Yarima Bobo abokinsa wanda suke shirya komai tare,ni kuwa mamaki nakeyi kamarsa duk kudinsa wai yanda na tambayi kudin ba kara ba komai iya 2k din ya bani,nan nace bari ya dawo sai na gwadashi nace ya bani Naira Dari kacal na gani iya 100 zai bani,Meenat ce tace Sis mijinki me kyau dan gayu wlh kinyi sa'a wannan irin kyau amma dai dan kasar waje ne ko? Kyan banza ne dashi Meenat sai fadan masifa,Hmm to Allah yasa ya canja ya koma Sonki Sis ai idan munje gidansa kwalliya zaki dinga yi ta jan hankali ki sace masa zuciya da wuri,idan mun ganshi a gidan ko?ai ba gida daya zamu zauna dashi ba main gidansu daban inda za a kaini daban kuma ni ai ba sonsa nake ba ina ruwana da har zanyi kwalliya sabo dashi,sis ke har yau da sauranki Allah ana gabas kina yamma irin wannan ai abin a so ne,baki na tabe tare da cewa ke karki Dameni me zanyi dashi auren Kasuwanci nayi ba abinda ya Dameni ya dauki nauyin mu komai da komai muji dadi shike nan buri na,kallo na Meenat tayi tare da cewa Sis ke bakya sha'awar maza ne kamar wacce wanzami ya cirewa Budurci?ko dai ba a sani ba Ammah tasa wanzami ya yanke miki Belin ki? Dariya nayi domin Mufeeda ta fini Sanin duniya tana zuwa schl,nace baki da kunya Meenat ai ni bana son wani Namiji me zanci dashi tir Allah kiyaye,Meenat ta dinga dariya tare da cewa Sis yanzu ko yar Runguma kuyi bacci ba kya so ga dan Kiss ma? Baki na rike ina kallonta nace ke wanne kiss wanda nake gani a film? Wlh bai isa ba idan yace ma zai min za a kwashi Bala'i da yan kallo ke nifa duk irin harkar nan bata damuna gwara kudi kawai,Meenat tace ni kuwa da nice na Samu me kyau haka ga kamshi,kudi komai ya hada ai da anga kwasar duniya,ke Meenat yarinya dake kike irin wannan zance,da nawa kika girmeni wai ma ki zauna kamar ba yar cikin birni ba gaki a cikin Birni amma kamar kina kauye, ae naji tunda Ku zaku Zama yan birnin ba komai zan muku ko mene abinda nake so kawai na koma makaranta idan ya Amince amma ni me ya Dameni da wani love.

      Muna rayuwarmu bayan kwana uku su Meenat suna zaune suna ta faman game a wayata Nokia a tsakar gida,ni kuma sanye nake cikin wando tight 3qrt blue sai rigata iya rabin cinya me gajeren hannu pink kaina ba dankwali jelar na lilo  ina kusa da Rijiya na ebo wanki ina ta wanke mana kayan sawa kusan ko yaushe sai nayi wanki haka nake bana son kazanta.
    Sallamar mutum muka ji kawai a cikin gidanmu kamshinsa ya gauraye ko ina nan take muka gane Aayan ne yazo yaji lokacin da na Zaba a kaini gidansa matsayin matar Aure,mamakina shine rannan a waje ya ganni ina yawo amma Bai ko tambaya me yasa na fita bada saninsa ba,kaina na bawa amsa ai ba Sonki yake ba ina ruwansa ko ma ina zaki je.
     Ganin su Meenat suna wajen yasa na amsa Sallamarsa tare da mikewa ina goge hannu na,gabansa na karasa tare da cewa sannu da zuwa wani Kwarjini da tsoronsa yasa na dan duka nace Ina yini,ko amsawa baiyi ba,na Mike na kawo masa wata kujerar roba fara tare da kara goge masa kujerar da wata duster,sai lokacin ya zauna kamar wani sarki yasha kana nan kaya yau ma wandon kansa abin a kalla ne ya hadu pencil dashi,Meenat ga Uncle yazo nace sabo da shishigina shi kanshi sai da ya tabe baki wai Uncle,da sauri suka zo suma tare da durkusawa a gabansa suna gaisheshi to su dai sun fini samun matsayi sabo da ya amsa musu sau daya da lfy bai kara ko ce musu komai ba suka koma inda suke suna ta game dinsu,Yau wacce rana ya ganni bana cin komai, bai gama tunaninsa ba yana zaune yaga na shige dan kitchen dinmu na fito da pure water a plate guda biyu na ajiye masa,ko kallon plate din baiyi ba sai faman chat yake a waya yana wani murmushi,kara komawa kitchen nayi na dauko Ayaba guda wajen biyar na mikawa Meenat da Ma'eesha guda biyu,tuna ninsa shi zan bawa ragowar sai yaga na koma inda nake wankina na bare guda daya gutsira biyu na cinye gudan Ayaba,na dan ci gaba da wankina na kara bare guda itama gutsira biyu na cinye duk yana kallona ba tare da na gane hakan ba,guda daya na rage na koma wajensa tare da dora masa saman ruwan dana kawo nace gashi nan Kaci sabo da Ido guba ne shi yasa,komawa kitchen nayi tare da zubowa su Meenat tuwon shinkafa miyar ganye tun daga Ido zaka San akwai dadi,Nace kuzo Ku kara abincin yamma kar yunwa ta kama min Ku,dama indai ba schl to dole muna kara cin abinci da yamma,ni kuwa a rana sau hudu sau biyar nake cin abinci,shi yasa kannena ma haka nake dura musu ko basa so sai nace sai sunci kadan.

   Ma'eesha tace nidai sis na koshi har sau nawa za muci tuwon nan gashi da dare ma kice sai munci,Na bata rai tare da cewa kin san tunda na zuba sai an cinyeshi ko Amai zakuyi sai kunci,Meenat cike da shagwaba tace pls Sis mun koshi Allah,nace to Ku kuzo muci tare nima zanci na zauna wajensu na fara ci ina dura musu ta dole suna yatsina fuska sun koshi,sai da muka cinye dole sannan na wanke plate din na maida kitchen,nace Ku ajiye wayar nan kuzo Ku karasa wankin nan da sauri suka taho tare da karba sunayi,ni kuma na koma kusa da Angona Aayan na zauna saman tabarma na kalleshi tare da cewa Angon Business,ba tare da ya kalleni ba yace wacce rana kike so? Nace to wai dangina baza suzo a dauki Amarya ba? Ni bana son mutane a harkar nan Business ne mene amfanin sanin mutane,ba auren so ba mene sai an sani wani auren kirki ne wannan da har zan nemi mutane,Allah baka hakuri zabi date da kanka idan ma yau kake so muje,amma kuma da mun tafi tare da Uwaliya da take gidan nan ko? Wani kallo me cike da masifa ya wurgo min tare da cewa wannan gidanku ne ko na haya? Namu ne na kanmu cewa ta,yace to bana son kwashe kwashe ku din ma dole ce zata sa Ku shigar min gida bare wata Uwaliya ko me,ku Uku nan zan iya rikewa wannan gidan kusa yan haya ko Ku bar matar a ciki ko Ku siyar da gidan ni ba matsala ta bace.

     Burina kawai muje hadadden gidan nan ace yau gamu a ciki zamu zauna wayyooo dadi gashi nasan ma zai dinga siyo mana kayan dadi ai nan take nace azo gobe a dauke mu,mikewa yayi zai fita,wata dabara ta fado min na Mike da sauri tare da dauko Hijab na saka nabi bayansa da sauri sabo da so nake wasu yan unguwa masu sa ido su ganni tare dashi su tabbatar da gaske ne aure na a daina zagina a gari,sai da nayi sauri na jera dashi har waje,ya kalleni tare da cewa ina zaki je,nace uhmmm makwafta zanje tunanina zaice kar naje ai ina da aure sai naga ko a jikinsa,muka fita har waje tare ina ta faman Mannewa kusa dashi sabo da yan unguwa suga fa ae ga zahiri ga sheda,na rasa me zance nace wai ka tsaya mana banfa gama magana ba,ina jinki ai,sabo da na jashi da zance har mutane su ganmu da yawa nace haka ake Business din kuma ni me zansa idan anzo daukan Amarya? Banza ya min,nace sannan ina son Naira Dari zan sa kati a wayata na kira Family,da mamakina sai naga ya tsaya a jikin motarsa ya zaro Dubu guda sabuwa ya kira Almajiri ya mika masa tare da cewa dan Allah samo min canji ka ce a hada ma da yan 100.

    Muna tsaye mutanen Layinmu yan sa ido yau sunga zahiri da idonsu motoci sunfi 8 a kofar gidanmu,sunga da gaske ne me kudinma na gaske ga kyau,muna tsaye dan mutane suce auren soyayya ne sai wani murmushi nakeyi ina washe baki,shi kuwa tunani yake anya lafiya ta kalau kuwa ko dai ina da tabin kwakwalwa mutum shi kadai ya dinga dariya yana murmushi haka,wasu maza ne matasa duk na sansu mugayen yan sa ido ne a unguwarmu hango su nayi sun taho wajen mu da alama ball zasu je duk sunyi shigar Jersey ina ganin haka na kara matsawa jikinsa kamar zan shiga cikinsa,kamshinsa yana ratsani ba zato yaji na saka hannuna a cikin nasa na rike kam kam kamar za a kwace shi,dama tuni na gano ba ta rike hannu ake yin ciki ba Meenat ta fayyace min komai,hannunsa yaja yayi yayi ya fisge amma sai dai ya girgiza da jikina gaba daya na rike hannun kam,idonsa yayi ja sabo da bacin rai da ace ba mutane yau da naci ubana a hannunsa dan Zane ni zaiyi kawai,Sake min hannu mana are u mad? Cewarsa ina murmushi tare da tamke lips dina ina mamularsa nace uhm uhm ni bazan saki ba kawai ka tafi baka bani kudin ba,su kuma mutane na layin yan sa ido ana wlh da gaske ne yana sonta sosai kalli soyayya,matasa suna cewa tayi dace Allah ya bata,wasu matan da suka sanni cewa suke ina ma sune wayyo dadi suna sha'awata,haka Nawwara ma ta fito ta hango mu nan ta tabbatar da wannan soyayya ce me karfi rike juna har a bainan nasi,Haka almajirin ya kawo canji still ina rike dashi ya hakura ya kyaleni ya karba abin al'ajabi sai ya cire Naira Darin dana tambaya ya mika min yace jeka da sauran Dari taran na bar maka kyauta,yaro ya tafi yana ta tsalle da murna,ni kuma ya bani Naira Darin,Nace ka rike albarka bana so tunda Ka iya bawa Almajiri Dari tara ni ko Dari,hannunsa ya fisge tare da maida Naira Darin aljihunsa ya shiga mota escort suka ja motoci suka kara gaba,ni ma nace Alhmdllh an samu shedu a unguwa na koma cikin gida abina.

   Uwaliya tana dawowa na sanar mata cewar gobe Mijina zai turo a dauke mu zamu koma can da zama ita kuma ta nemi wata suci gaba da Zama a gidanmu suna gyara mana shi,ta dinga godiya sosai,nace danma mijina bai yarda bane da tare zamu tafi dake,Uwaliya tace hakan ma na gode ai kun gama min komai akwai wata kawata Kaltume zan nemota mu zauna tare,nace to ba matsala ga kayan kitchen da komai kuyi amfani dashi mu iya kayan sawarmu kawai zamu Eba. A daren muka hada kayanmu tas marasa kyau muka zubar domin babu wanda zamu bawa sun lalace da yawa.
 Gidan mu kuma so nake na samu kudi na gyara shi na zuba yan haya a ciki shi yasa nace su Uwaliya su zauna kafin na samu kudi.

    Washe gari 5pm Driver da katuwar mota ya Parker yace mu fito inji Oga,muka zuba kayanmu a boot Uwaliya munyi Sallama tuni ta tafi wajen aiki,munsha kyau domin duk jaraba sai da na  dinka mana Atamfa me kyau ko wacce kalar tata daban,tasha dinki me masifar kyau riga da skert,da mayafi me kyau tare da takalmi me dan tudu me kyau,muka je saloon,sannan akayi mana lalle me arnen kyau har su Ma'eesha akayi komai.
    Bayan munyi wanka Meenat ta tsantsara kwalliya tare da dauri me kyau dama ta iya watarana Amare marasa kudi suna kiranta tayi musu kwalliya da daurin gogoro sabo da tana da basira a nan sai ka rantse make up kaje aka yi ma,Haka tayiwa Ma'eesha ma kamar ka sacesu haka suka koma.
      Amarya kizo na miki kwalliya kar mijinki ya raina ki yana kallonki a bagidajiya,da kyar na yarda Meenat ta zauna ta fara sheka min kwalliya tare da dauri me masifar kyau,ni kaina ji nayi kamar na lashe kaina sabo da tsananin kyan da nayi,kowa ya kalleni sai ya kara,sai kuwa ga Driver yace mu fito,Maeesha ce ta dinga kai kayanmu Driver ya zuba a boot dama ba wasu masu yawa bane,muka yafa gyalenmu kamar yan mata zamu party,Hips dina kamar zai fado tsabar tudu da fadinsa a skert, muna fitowa Driver sai wani girmamani yake,muka shiga mota nace Baba zaka kaimu makwafta muyi musu sallama,samun waje ga baki ga hanci amma haka nace Driver ya dinga kaimu gida gidan da muke mutunci sosai harda Nawwara mukayi musu Sallama cewar zamu dawo sai mu basu address na gidan mijina.sai kallo da gulma anga uwar motar da muke ciki makwafta ma sai an kaimu a mota,wasu suka ce Allah ne yasan manufar Jaki shi yasa bai Yoshi da kaho ba.
    Bayan mun gama nace wa Driver muje ya kaimu gidan mun gama,ya fige mu muna dan kamshinmu har gidan Aayan dama na rigada na San gidan,Driver na parking muka ga wasu sunzo sun dauki kayanmu tare da shigar mana dashi ciki suka fito tare da cewa Oga yana ciki Ku shiga yace.

   A raina nace ai ko bai ce ba zamu shiga kunji fa,muna zuwa kofa na danna Door bell ya bude muka shiga sanyi da kamshi ya ratsamu,yana jikin kofar ya bimu da kallon mamaki yanda yaga munsha kyau kamar yayan Larabawa zasu je Party musamman ni ba a magana,a ransa yace ashe dai suna da kyau,sai kuma a fili ya tabe baki yace kuje ciki mana kun zura min Ido,a hankali muka shiga tare da Zama a saman kujera,yana zuwa yace ba a Zama min a kujera,ya kalli Ma'eesha yace wannan ce kadai zata dinga Zama a kujera amma Ku banda Ku,shuru mukayi muka ji ya kuma cewa Bedroom guda daya gashi nan shi zaku dinga Zama bana so ana fitowa Palo ana takura min,bana son Surutu a gidana,akwai komai a kitchen na girki,dan ma bana so a bata min gida da hayaki ne amma da itace zan siyo muku yanda kuka saba kuyi girki dashi a Compound amma kunci Sa'a zaku iya amfani da Gas,wani dadi da murna ya kamani zan dinga dafa mana kayan dadi dama nasan gidan nan akwai harkar dadi.

    Je ki duba kitchen abinda babu ki dawo ki fada min,da sauri na Mike ko kunya irin zan ga harkar dadi,ina shiga na tsaya turus ganin buhun dawa,gero,masara,wake,shinkafa yar hausa harda ta tuwo fara, sai maggi kala biyu Rak fari ajino motor da star,harda kanwa,Flower,kukar miya etc duk dai wani abu na cimar talaka futuk shine cikin kitchen,haka kayan cin abinci ma komai ya siyo na roba kar mu taba masa nasa na glass,komai irin cimar mu ta talaka ya kawo,haka fridge ba komai a ciki ko ruwan roba wai musha na pampo alhalin ko a gida pure water muke Sha duk talaucinmi.

   Jiki a sanyaye na fito cike da jin haushinsa,nace Meenat kuje Bedroom,ba tare da nace komai ba na zauna a kasa tunda yace kar wacce ta hau masa Kujera,ko kallo na baiyi ba yana ta kallon News abinsa,nima ina kallo ne kawai don bana jin me suke cewa sai dai dai nake tsinta,sai satar kallonsa nake yana ta Shan juice lafiyayye da gani zaiyi dadi,yasha rabin kwalin sai naga ya ajiye glass cup din ya Mike tare da haurawa samansa,sai da na tabbatar ya shiga sannan na daga kwalin na kafa a baki na tare da shanyewa du na lashe bakina sai na fada kitchen na ebo ruwa a tap nazo na dura a cikin kwalin dai dai yanda ya bar lemonsa na maida cup din tare da dawowa kamar da na zauna na wani langabe kai irin Allah sarki din nan.

     Kamar jira yake sai gashi ya fito sanye da shadda yar gaske yana sheka kamshi da alama fita zaiyi,yana zuwa sai aka yi sa'a ya bude kwalin lemon da niyyar ya tsiyaya yasha Sam bai zata nice zan yi haka ba,yaga maimakon yaga lemo sai yaga ruwa na tsiyayowa da sauri ya jefar da kwalin tare da yin gefe ya firgita ko Aljanune,tunani ya shiga sai ko ya kalli bakin kwalin ya hango jambaki na a jikin abun,nan take ya gano nice na shanye na zuba masa ruwa,ni kuwa tuni na Mike tsaye cikina ya Duri ruwa jikina ya fara bari,yasan guduwa zanyi don yaga har na tattare skert sai naga kawai yayi hanyar fita waje,nan na sauke ajiyar zuciya,ashe Duk bedrooms da kitchen tare da sauran kofofi ya kulle ta yanda bazan iya guduwa ba, tuni Idona ya kawo Ruwa nasan yau sai dai gawata,saman 3 seater ya koma ya zauna tare da nutsewa a ciki yayi dai dai cike da isa yace zo,nace ni?yace no ni,da sauri na karasa tare da durkusawa a gabansa yace bude bakinki na gani,ba shiri na bude ya kuwa ganshi wani fes dashi,ruwan dana dura a kwalin ya dauko ya fara dure min shi a baki ina kwat kwat har ya kare  ,jefar da kwalin yayi tare da barin gidan gaba daya.

    Yana fita nace su Meenat su fito mu shiga kitchen,kayan abincinmu na talakawa muka shirya a store sannan na ebo dawa muka gyara ta na wanke na shanya ta a kwandon ta bushe,haka masara ma,na ebi gero cup 4 na jika shi zan kai markade sabo da kokon safe,waken da zan soya mana kosai ma haka na ebo komai dai muka gyara komai abinmu,Na fito wajen masu gadi nace dan Allah a ina za a kai min nika da Markade? Wani cikinsu yace Hajiya unguwar masu kudi irin wannan sai ansha tafiya me nisa,nace ni dai a gwada min,ai ko ya gwada min,nasa Meenat ta dauki Dawa a cikin Leda Viva,nima na dauki masara duk sun kai kwano uku uku,sai geron dana jika na Koko a cikin dan botiki dan kadan Ma'eesha ta dauka,muka fito tare da tafiya me uban nisa muna tambaya har sai da muka bar layin sannan muka samu gidan wata mata me Markade wani namiji kuma da injinan nika,na bada kudi nan take akayi mana komai da komai muka dawo gidan tare da tankade garin muka adana abinmu,Nasa hijab na kara fita yan su Curry da sauran abubuwan girki na bada kudi na siyo mana harda su kayan kamshi,kayan hada lemo,da zobo da sauransu,ina dawowa a gate na bawa gate man kudin pure water nace ya siyo mana manyan Leda biyar mu dinga Shan abinmu, na dawo su Kubewa bushashiya na bawa su Meenat dama akwai turmi dan karami a kitchen din suka daka mana muka tankade da yawa duk sai da muka shirya kayan abincinmu komai na marasa karfi na shirya kitchen tsaf muka gyara shi tas,pure water kuma na shirya wasu a fridge wasu kuma a can gefe na ajiye idan mun shanye sai mu dinga zubawa ciki,a hakan ma sai murna mukeyi abinci available zamu ci mu koshi a kan lokaci ba sauran wahala da babu kaza babu kaza,shi abinci ko garau garau ne kake ci in dai ba yankewa kuma akan lokaci to Shar za a ganka.
   Bare har da su shinkafa ga ta tuwo ma,mangyada manja ai shike nan mu,shi yasa dana fita ma sabo da yau jira nake Allah ya kawo Aayan da dare na nuna masa cewar ina da zuciya.
   Shi ko Aayan jira yake yazo gidanmu da wuri yaga wanne girki zamu kwaba tunda yasan ko kayan miya bai ce asiyo mana ba,ba nama bare kifi bai San na siyo mana kayan miya harda naman rago na Dari uku tare da danyar Kubewa zamu zabga girki.

       Meenat tace sis mu wlh ai indai zamu dinga samun wannan ai Alhmdllh a gida ina muke samun haka kullum sai dai fa muyi girki tazarce,Nace Ku canja kaya kuzo muyi sauri mu kara gyara gidan nan sabo da idan yaga dirty daya to jaraba zai mana,nan take muka kara gyara gidan ya dau kamshi,ni kuwa ina kitchen sai girki nakeyi kamshi na tashi,Magrib nayi mukayi Sallah lokacin na gama miya tuwon danyar shinkafar nake karasawa,ina gamawa mukayi wanka da Sallar Isha tare da canja kaya marasa nauyi, Ma'eesha tasha 3qtr dinta dan me kyau da nake siya musu tare da yar vest na sa mata, Meenat kuma riga da skert tasa suma English wears na gwanjo amma masu kyau kalar yan gayu, ni kuwa doguwar rigar material nasa fitted nayi kyau amma ba kwalliya a fuskata.

     A katon wani tire na roba na zubo mana miyar Kubewa danya da naman mu kowa yanka uku,Sai tuwon a leda har guda hudu manya,ga pure water shima na zubo a wata roba kalar ta Almajirai duk cikin kayan da Aayan yace a ciki zamu dinga cin abinci ne.
     Na dakko mana komai muka zauna tsakiyar center Carpet na tattare rigata zuwa wajen hips gaba daya cinyata a waje take fara sal da Ita mul mul da su,Meenat ta fara dariya wai Sis ke baza ki taba cin abinci a hankali ba kuma sai rufe dankwali kin wani kwaye cinya jiba ana hango short wandonki,to mu da waye a cikin gidan daga ni sai ku,zamu fara ci kenan muka ji karar bude kofa kamshinsa ne yasa muka san shine ya shigo,Sallama yayi muka amsa na fara basu abinci a baki,tsabar sa ido shine yazo ya wani baje saman 3seater yana kallonmu a nutse,yanda yaga na kwaye cinya dankwali yayi kasa duk sabo da abinci,Maeesha tace Sis ki san masa abincin mana nayi banza da ita muna cin abinmu,ni na manta ma yana wajen Sam ina ci har cinyata nake dana da duka sabo da dadin girkin,idan na ci Loma daya sai na sosa kunne sai soshe soshe nakeyi kamar me kwarkwata ko cutar karzuwa sabo da ni idan da abinci a gabana mantawa nake da uban kowa,Meenat su Kansu dariya sukeyi tace sis ya dai wai abincin nan ko yafi Nama dadi ne,Ina lashe hannu tare da tsotse yatsu na ina tande baki nace ke Wannan gonar da aka shuka kubewar nan daban ce maybe kasar kalarta daban kinji har zaki zaki haka,wajen mutumin nan zan dinga siyowa,suka sheke da dariya shi dai Na'im yana kallo ina ta side plate din,Maeesha tace Sis ki kyale kwanon haka mana nace baki San ba kyau cin abinci ba tare da an side kwano ba ai sai Abar albarkar abincin a kwanon.

  Aayan yana kwance yana ta faman kallon ikon Allah cike da alajabin abin nawa,muna gama nace muje a wanke hannu Muzo asha karatu,yana zaune yaga na Mike ina uban nishi tare da jansu muka je muka wanke hannu da baki sai ko muka kwaso jakan makarantarsu muka dawo palon kusa da shi yana kwance kai ka rantse nice shugaban masu ilmin boko na duniya yanda na faffake ina bude littatafai,Aayan yana jira yaji yanda zan fara koyawa kannena karatu.

      Ga mamakinsa sai yaji Meenat ta bude wani English book tace fada min words din jiya naji,Bai san sanda ya bude baki ba wanda bamu San ma yana yi ba,Na fara cewa Singular and plural,Abu me guda daya da abu me biyu,Examples like Mango-Mangoes,Orange-Oranges,Bag-Bags,Lady-Ladies ina fada ina rubutawa a littafi har na gama,Maimakon nasa Ladies sai nasa Ladys nan take Ma'eesha yar karama taci gyarana tare da kwace biro tace sau nawa za ace miki haka ake rubutawa ladies wai yau kusan wata daya kenan kullum sai kin manta,Meenat tace to Saura mu fara  present tense and past tense amma yanzu a koma baya muji,mene Noun? Nace Noun? Noun... to ....Noun.. dai shi sai na fada tunani tare da kallon sama kamar a nan zan samo amsa,nace to shi dai Noun... shine dai,nan take Aayan bai San sanda ya kwashe da dariya ba sai da muka kalle shi yanda dariya ke masa mugun kyau,Meenat tace Sis what is a Noun? Shine dai me? Na kara kallon sama tare da zura biro a bakina nace shi dai Noun is a name of....of.....yawwa shi dai Noun is a Name of Yawwa uhmmm....yes Animal dabbobi irin su Damusa, Kunkuru,zaki,kuma dai shi dai Noun is a  Name of place like harda yanga irin na gano gaskiya harda daga yatsa kamar malama na kwalla da karfi nace like capital city of Nageria Abuja,na kara karfin muryata nace also kasar Masar,na daga kai sama nace yes Habasha,idan muka dawo gida Nigeria zan iya ce muku Rimin Gado,Kura,Kasuwar Rimi,yan Kura and also kofar wambai  market,Aayan Dariya ta mugun kamashi duk uban labarin nan wai a Noun akeyinsa.

    Meenat tace yes muna jinki sis,Nace kuma dai shi Noun is a Name of person na saki murmushi irin shegiyar nan nace like ni Mufeeda,Ammah Allah yaji kanta duk da ta riga mu gidan gaskiya amma zan sa da sunanta Fatima,Abba wanda ya arce,Maeesha kema kina cikin Noun,Meenat ma ta shiga ciki,Aayan ma gashi nan a kwance,Maeesha suka sheke da dariya, nace ah to dana fadi wasu banza na waje ai gwara na gida.

     Na kara daga murya kamar me koyar wa a class nace Kai Noun shege ne wato shi ya hada komai harda Things kinga Bag,pencil,biro,spoon duk suna karkashin Noun.Meenat suka dinga dariya sosai suka ce kinyi dai dai amma labarin ai yayi yawa,nace wai me yasa Noun bai hado da abinci masu dadi a ciki ba aikin banza,ai kamata yayi ace akwai su Hen,su Ram,kabewar miya,Danwake,Taliya,Apple.
    Aayan yana ta boye dariyarsa,Ma'eesha tace Saura Verb, nace Verb gaskiya ita bata dadi is an action word or a doing work, ni Verb bata birgeni sam,kamar yanzu munyi aiki yawwa Cooking,jumping,running,washing,kuji wani iskanci wai harda kallo watching ace yana cikin aiki,eating ma ai ba aiki bane amma a ce harda shi ciki,haka dai suka dinga tambayata ina bada amsa amma sai nayi dogon bayani da Hausa na cinye lokaci.
   Ma'eesha tace daga yau an daina hausa sis duk bayanin da zakiyi sai dai kiyi mana da turanci kaf,na zaro Ido tare da cewa dan Allah kuyi hakuri ni dai me zance,Meenat tace wlh ba hausa gobe ki shirya naga Alama indai ba haka ba baza ki iya ba.
   
  Sabon karatu sukayi min present tense an past tense,sannan sukayi nasu na manyan kwari tare da assignment ina kallonsu,sai kuma muka koma Islamiyya,anan kuwa nasan komai Qur'ani suke kara min da wasu littafan amma duk na iya tunda na iya karanta larabci da rubutu kuma ni nafi kokari a fannin Arabic sosai ko Aayan ya sheda daga jin yanda nake karatu ina cin gyaran su Meenat.har muka gama abinmu sannan Ma'eesha ta mayar da komai Bedroom ta dawo still Aayan yana kwance abinsa yana danna waya, nace su tashi muje su kwanta bai kula mu ba muma haka,amma yayi mamakin ganin yanda muka yi girki lafiyayye haka gamu yara kuma yasan fita nayi na siyo wasu abun amma abincin ya birgeshi sabo da shi yafi son abincin zallan hausawa fiye dana turawa.

    Sai da ya dade sannan muka ji karar mota tare da bude gate wato mu kadai zamu dinga kwana a gidan,munyi addua na kara yi na tofa mana baki daya muka haye saman lafiyayyen bed din da bamu taba ganin irinsa ba muka fara bacci sosai,can cikin dare wurin 12:30 naji motoci sun shigowa gidan na farka tare da mikewa na daga labile na leka ta window Aayan na hango da ledojin take away dinsa a hannu ya dawo.A zuciyata nace dama yana kwana a nan? Na tabe baki tare da komawa na kwanta,shi kuwa yana shigowa sama ya haura yaci kayan dadinsa ya fesa wanka tare da shirin bacci yayi addua ya kwanta sai bacci.

   Washe gari na tashe su mukayi sallar asubah tare da azkhar sannan nayi wanka suma suka yi tare da shirin makaranta ni kuma nasa kaya Atamfa riga da skert me kyau harda shafa powder tare da lipgloss,wake na gyara da sauri na fice tun gari baiyi wani haske ba na taka har inda ake markade sabo da Blender bata yin laushi yanda ake so,dan markade kadan nayi na dawo da sauri na daura ruwan dama Koko,sai na fara soya kosai yasha kayan miya kamshi ka rantse wani nama ake soyawa,Aayan yana jin motsinmu tare da kamshi yana tunanin wai ina muke samun abun girki me kamshin dadi haka, ruwa na tafasa na dama Koko me dadi da lfy,na ebi nawa a cup ina cin kosai ina kora Koko Malam,Meenat ma suka shigo sanye da uniform dinsu na zuba musu suka ebi kosai a plate da sugar suka fito Palo suna Shan abinsu,sai ga Aayan ya fito sanye da Jallabiya fara,suka ce ina kwana ya amsa ba yabo ba fallasa da lfy Alhmdllh,Ya kalli abinda suke ta ci bilhakki da gaskiya ganin yana kallonsu Ma'eesha tace Yaya gashi in zaka ci,baki ya tabe tare da cewa ban iya ci ba,d a dadi fa,yace am Ok,Meenat a tsorace tace ka dandana,a ransa yace wannan jagwalgwalon zanci ganin bana wajen ya mikawa Ma'eeshah hannu wai ta bashi ya gwada,da Sauri ta mika masa kosai daya yaci yaji shegen dadi,dama kosai yana dadi haka? Abinda ya ayyana a ransa kenan,Meenat tace a karo? Ba tare da yace komai ba ya mika hannu a karo masa,ta dauki plate din suka koma gabansa gaba daya Yana sama suna kasa zaune,Yana Sa hannu ya dauka yaci suma suna ci suna shan kokonsu,Maeesha tace Yaya a kawo ma kokon da dadi fa,karon farko kenan da ya kalli Ma'eeshah ya gansu kyawawa gwanin sha'awa ga tsafta,yace sai dai ki bani naki nasha,ta mika masa ba kunya ya karba yana sha da kosan,dan rashin Imani bai ce tazo a kara mata wani ba dan shi sam bai iya kula da mutum ba,ba ruwansa da wani caring ko kina cikin yanayi na Kaza yace je kiyi Kaza sam bai san wannan ba,yaci ya sha abinsa ya mike bai ce ko a dawo lfy ba yana uban takama da gadara ya koma sama abinsa,a haka na fito suka bani lbr nayi mamaki da ya iya ci,na Sa Hijab na rakasu a kafa har Babban titi tare da sasu cikin Napep suka tafi schl nace idan an tashi kar su taho su jirani zanzo na daukesu a schl tunda baza su gane gidan ba.komawa nayi gida lokacin yayi shiri zai fita an kawo motoci wasu kalar,ni na manta ma ina da aure Sabo da ba abinda na fasa yi ko ina fita nake yi,shima bai ce min ina naje ba ko mene ma nayi ina ruwansa ko kallo ban isheshi ba haka ya shiga mota aka jashi nima nayi ciki tare da fara gyara gidan ko ina.


31-35


Official


By
AsmaBaffa


SAMEERAN GAYA yar ALBARKA ga page naki.

HAFSAT KHAIRAN   Tare da MAMAN SAMHA ina gaisuwa.

JANNAT jinjina gareki me tarin yawa.


  Dan Allah masu Sharhi kuci gaba da yi ina gani,kwana biyu Net yana bani prob zaku ga reply baya zuwa da wuri ina matukar damuwa wlh,fans kun san dai AsmaBaffa ba haka take ba,ina kokarin Yiwa kowa reply sai daí idan ban gani ba,dan Allah ayi min uzuri ko da wata tayi magana taji ban mata reply ba to wlh ban gani ba ko matsalar networkc.sai masu yi min magana ta pc kuma indai anga ba reply da wuri to net ne kwana nan matsala yake yi,kuma ko wacce nayi reply back sai yaki Tafiya sai da kyar,dan Allah ina kara baku hakuri za a gyara kuma ayi min sharhi na ina gani Sabo da nayi typing me kyau.

   Sai kuma typing error ayi hakuri dashi,sai kuma kuskure na Dan Adam dole zaku ga abinda bai muku a ciki ba,har kullum ina so kusan cewa Sako ake isarwa,idan mutum shine star bazai yuwu ace baya kuskure a rayuwa ba,dole sai yayi abubuwa shima na kuskure tunda ana so a koyi darasi da shi ne,baza ace star shi ya Zama halaye 100% ba,so ayi hakuri aci gaba da karatu da Sharhi Insha'allah Novel zai tafi dai dai.
   I really love my fans wlh sosai Sabo da so nake na dage ko wacce Insha'allah masu Sharhi sai na baku page Insha'allah sai daí mantuwa,wadda bajintarta tayi yawa har 2 ko 3 page ma zan bata suna nan kuma ina ta ganinsu AUTA, FlOWER ma suna ciki etc Bazan fadi sauran ba yan kuri ne zasu cika min Gp?.


       Ko da na shiga gidan kawai aikina nayi ta faman yi sai da na gyara ko ina har Bedroom din Aayan ko ina sannan nayi mana miyar jajjage na siyo kifi na Sa mata,tayi dadi sosai,na dafa farar taliya na gama ,a gurguje nayi wanka na shirya tsaf sannan na maka Katon Hijab na tafi dakko su Ma'eeshah,ina zuwa suna fitowa da Sauri suka karaso inda nake tare da frnds dinsu wai zasu gaishe da Sis din frnd,harda gaisheni da turanci kawai na amsa tunda nima na dan iya a raina nace da kunyi hausarku Yara nafi karfi a nan wai su a dole yan private,shi kanshi me Napep yayi mamakin shegen gidan daya sauke mu,yace kamar wannan gidan ace za hau Napep ga yan mata zuka zuka haka,Me Napep tunaninsa ko yan aiki ne tunda yaga bamuyi kalar masu kudin ba,kawai sai ya fito daga Napep zai gwada sa'arsa a wajena ko zai dace da ya more ko yar masu kudi ce ai zaiyi auren jari.

    Yashe baki yayi tare da cewa yan mata ku bar kudinku ai kyauta na kawoku ni,kamarki Hajiya ai kin wuce a karbi kudinki,na daure fuska tare da cewa kaga Malam karbi kudin ka ban son kinibibi ina da aure ni koma meke Ranka ka Adana kalamanka,yace yar yarinya dake yana dariya yace sake magana yan mata ido ba mudu ba ai yasan kima,tsaki Naja nace karbi da Allah kar mijina ya ganni a nan,yaki karba yana kallo na,muna haka sai ga motar su Abbi ta shugo tare da mata ciki manya biyu da yan matan nan dai abokan fada na su Uku, tare da dattijai su Abbi su biyu suma.

   Cikina ne ya wani kulu kulu Sabo da tsoro nan take gumi ya keto min,na cillawa me Napep kudi Naja hannun su Meenat muka bi su ciki domin tuni sun shige da motocin su ciki,gashi basu san Code din kofar ba,nima ban sani ba Ma'eeshah ya rubutawa a paper jiya yace ta bani,dole suna jikin kofa suna jirana,a hankali na taho,suna bina da wani banzan kallo wanda saura kadan na fara Kuka,wata a Cikin manyan matan ta ja tsaki tare da cewa an kawo mana irin jaraba kuma dangin matsiyata sai abinda muka gani,Abbi yace taki yin Sauri ma kamar gidan ubanta,Yan mata a ciki daya tace zaku gaji da kallo indai wannan Villager din ce bata da kunya wlh zaku ce ni na fada muku,Dayan Babban yace wa zata Yiwa ai ko masa a saketa dan ubanta,cikin manyan matan wacce batayi magana ba tace dallah ki Sauri ki bude mana ko gidan uwarki ne wannan dole a maida ita Family house ko dan ta koyi Ladabi,nan take Abbi yace a'a ba yanzu ba tukun na gama planning idan lokaci yayi zakuji.

   Ni kuma jin matar nan tace ba gidan Uwata bane jin za a zagi Ammah ta yasa zuciya tazo min wuya,haushi ya kamani gani dama da saurin fushi ni ban fiye jure a fada min magana a gabana kuma ace na danne ba zai wahala,ana fada min nake tunzura nima sai idona ya rufe ko za a kasheni sai na rama.
   Ina zuwa gabansu na bata rai nasa hannu zan bude matar nan ta dungure min kai dan ubanki baza kiyi Sauri ba,a fusace na juyo tare da maka mata uwar harara ba ruwana ko uwar Aayance ni ban sani ba kawai kasa dannewa nayi,aiko yan matan nan da kadan suke jira suka fara salati suna zuga tare da cewa kun gani ko ai mun fada muku to wlh nan gaba ko marinta kukayi sai ta rama,Abbi yace Dan ban tan ubanki baza ki bude ba,aiko na kara harzuka kawai na fasa budewa Naja hannun su Meenat na juya inda na fito ina Tafiya a hankali cike da gadara ta nima,maganar duniya sukayi ko ehem basu ji muryata ba,ina ji suna lalalala lallai dole a dauki mataki ba karamar yar iska bace wannan magana ma tafi karfin tayi,shima dayan yace wannan tantagararriyar yar iskar tsagera ce,bata da kunya bata da mutunci kamar mu ta iya yi mana haka,ka duba Nafisa da Bilkisu babu abinda ba a musu ba Amma yaran nan basa iya daga mana ko yatsa,ka duba Shema'u zagi duka duk taci a gidan nan Amma ko daga ido bata taba yi mana ba sai wannan yar matsiyata,talakawa ma sauran kuwa daya aura daya ke yayan masu kudi ne dama su basu gaji tsiya ba,Abbi yace bar shegiya zata shigo gidan ne sai tafi kowa wahala da kanta zata bar gidan,nan take suka kira Aayan yayi Sauri yazo,minti 10 sai gashi a mota daya shike Driving,yana shigowa ya hango mu can gefe a zaune,gashi dama kuma Business din namu yace a gaban danginsa a nuna soyayya,ni kuwa na manta ma tunda ban gani a kasa ba,ba a biyani kudin ba,banci na ta da kai ba,nan take ya canja fuska ya koma nishadi da farin ciki ko kulasu baiyi ba sai wajena da ya taho yana wani murmushi muna hada ido sai ya maka min harara,yana zuwa kusa dani ji nayi kawai ya riko hannuna,na fisge hannuna yace  film za ayi gasu nan zasu gane, nace can da matsalarku abinda ba sanin darajar business kayi ba ina ruwana ni, zan mareki kin san Halina wlh idan kika bari suka gane sai na yagalgalaki na koreki kuma,ni kuwa nasan zai iya mun samu rufin asiri ai ba shiri na mike,ina murmushin yake ya dauki Ma'eeshah a kafadarsa kamar yarsa yana mata wasa wai dan ace ana soyewa da mata kannenta ma ai kamar kannensa,Meenat tace a ranta kaga makirin Namiji a fili kuwa ya jawota kusa dashi itama ni kuma hannuna na cikin nasa,Maeesha an samu sake har wasa take da gashinsa a ransa yana ta jin haushinta tana lalata masa gashinsa me kyau yasha gyara.

     Muna zuwa yace ur welcome, Abbi karami barka da yini,Aunty ya kuka tsaya a nan,My life bude musu mana,Abbi ya fara masifa wannan har kake kira da ur life yarinyar da ta zage mu taci mana mutunci yar Iska,Aayan ya bata rai a ransa fa Amma don yasan Halina ba tin yau ba bana iya hakura idan anmin abu,yasan tabbas zan rama indai sun min tunda yasan halin danginsa,a fili yace ko baki ganesu bane Dear,nayi shuru ya mintsini hannuna na saki murmushi tare da cewa ban ganesu ba naga suna fada ne tunanina kar suzo har gidan mijina suyi min sata,aiko nan take suka yo kaina ubanki zamu sata,yan matan nan sunfi kowa,Abbi yace Kafura da fuska kamar ta mage,na faki ido na Galla masa harara,yace wlh wlh sai nayi maganinki,na kara fakar ido na Galla masa harara tare da juya idona sannan na murguda baki,karaf a idon Aayan,a gabansu bai nuna ya gani ba,sai da muka shiga ciki na zame hannuna Meenat ta rada min ki kirashi da Babyna,nan nace Babyna kawo min Ma'eeshah taje ta huta nasan kasha nauyi,ya miko min ita tare da zama kusa da su Abbi,ni kuwa ko ta kansu banbi ba nayi Bedroom abina har suka gama fada da jaraba wa Aayan ina jinsu wai ya auro gadon rashin mutunci bani da tarbiya,shi kuma yana basu hakuri suka dai gama mitarsu suka bar gidan cikin bacin rai dama wai a haka ganin Amarya suka zo za ayi gulma.

     Suna Tafiya ya haura Samansa yayi wanka da komai tare da cin take Away dinsa har Bedroom dinmu ya leko yace zo ke,lokacin wayata kawai nake dannawa ina game,su Meenat sun Tafi Islamiyya.
    Na mike na bi bayansa har palo,yana zaune na durkusa a gabansa ya dauki dogon lokaci sannan yace ke baki da kunya ko? Ana tausayinki ba kya jin tausayin kanki,baki na turo gaba,yace ko nima zagina zakiyi,baki da hankali ai ko ba komai sun girmeki,kuma kina Matata ko darajata ai baza ki raina min dangi ba,nan gaba ke zaki sha wahala awajensu ni ba ruwana iya kaci idan sunce na rabu dake nayi musu abinda suka ce,kamar Abbi zaki kalla ki harara Kanin mahaifina ne fa kamar mahaifina ne.
   Bazan hanaki yi ba tunda ke zasuyi ma ba ni ba,kinga ba ruwana,baki na kara turowa Hawaye yana zuraro min sannan nace haka kawai shike nan ni bani da yanci,ni mene baka Yiwa Kannena ba ashe da dadi kenan yanzu nayiwa naka kaji Haushi,sannan su zagar min iyaye sai nayi shuru Sabo da bani da zuciya ina...... wlh zuciyata bata mutu ba,babu wanda zai zagar min Uwa na kyaleshi ko shi waye,kai ko ni wlh Bazan dauki zagi da Duka ba sam bazai yuwu ba,bari kaji ko kai da bana so aka zaga Bazan kyale ba tunda yanzu kaine kake ciyar damu ko dan darajar wannan idan naga me cima mutunci sai inda karfina ya kare,sannan da kake cewa ana tausaya mana ai dai banzo gidanku nace ka taimakamin da sisinka ba bare kace taimako nazo nema,hasalima ni kake zalinta,tunda duk Aure ai aure ne ba banbanci,da kudinka Allah ya hore ma ka hana iyalinka sai daí ka bawa na waje ina zaka ci gaba ai baza suyi albarka ba kuma baza kaga dai dai a komai naka ba,tunda kana da Halin siya min Nama ka makale kudinka,ko kwai dan kwai ma babu,bare su madara me kwakwa ba daya bare kanwar biyu,sabo da son kudinka ko tsire baka siyo ba dan ka kyautatawa iyalinka,sai kudina na ma da suke hannunka tunda har yau Banga an fara bani kudin auren Business ba,ai in kana so nayiwa danginka biyayya to ka tabbatar sai ka karbi aurenka kace ba na kasuwanci bane tunda kai kace ba aure bane to mene hadina da wasu danginka da zan girmamasu,dadinka nake ji da zan mutunta su? kuma ko ba komai suma ai basu mutuntamu ba ko mu ba mutane bane bamu da daraja sai ku Sabo da kuna da kudi,Deal ne tsakaninmu zancen mutunci bai taso ba,a fara biyana kudi ayi a gama auren,idan kuma ka soke kasuwanci ka zabi daya ciki sai ka min komai da Allah yace miji ya sauke a kan matarsa nima zan sauke nawa,amma sai kazo kwata kwata ana abu ba akan dokar Allah ba mun tsara tamu dokar kace zaka zo da wani zance wlh kama zo da da bidi'a ....kau.....nake jin maruka ta ko ina a fuskata inba a lokacin sai da na dena gani kaf bana jin magana, yayi niyyar ya dinga ball dani kawai ya kyaleni da iya marukan da ban san adadinsu ba,na mike kuwa ko Hawaye babu na karkade jikina irin na gama kangarewa din nan nace Bazan fasa fada ba idan kana so na bisu wlh sai daí ka soke kasuwanci muddin kasuwanci za ayi wlh basu Isa ba ko su waye a danginka in dai sun min sai na take su nima,ni so nake ma ka kaini can Sabo da mufi goge raini,,na tattare skert zan Arce ya biyoni na kwalla kara nayi saman Bene da gudu,ya biyo ni a ransa yace yau sai ya hallaka yarin nan yana magana tana yi,ya auri mata manya manya ma magana basa iya yi masa sai wannan yarinyar, Ina gudu ina hakki nace dan Allah kayi hakuri karya nakeyi Bazan iya ba zan bisu sau da kafa,wayar chager naga ya fisgo ai na koma kasa da gudu garin gudu na fadi yazo kuwa cike da bala'i ya juya daukan wayarsa data fadi na mike idan guduwa zanyi kamani zaiyi,kawai ya sunkuya zai dauki waya na Arce ,nasan ina tsayawa zai ci Ubana, ina shiga su Meenat suka firgita suma sun dauka wani abu ne, jikin kofar yazo yace zaki fito ne,nace ni dai na fada ko gobe suka zo sai nayi musu,kwanan nan zan fara taka kowa, zaki fito ne sai na yankaki,nace ae idan anyi zuciya a biyani kudina,yace ko ina bayarwa ma Bazan taba baki ba,da na baki gwara na zubar kuma ko ina Tafiya ina taka kudi Bazan baki ba,shuru nayi masa Sabo da ina tsoro kar ko yar dubu daya ya hanani da me zanyi Cefane ko kudin Napep na schl din su Meenat.

    Meenat ta kalli fuskata tare da cewa Sis dama ke ai akwai jure duka, shawara kawai mu daina fita ko palo sai in baya nan,Nace baki da hankali ai gwara ana damawa damu idan ya gano tsoronsa muke ji raina mana hankali zaiyi,ni yanzu da kike gani na Salo Salo zan dinga rikida ina canjawa tunda naga ba kudin nan za a samu ba bare idan na samu nace ya sakeni kinga gwara kawai mu samu na lallabashi mu samu kudin siyen kayan daukan wanka muci mu sha mu baza gayu,idan ya maidamu Family house a haka mun gama yawo kalli bamu da kayan sawa na kirki,

 Meenat tace ni tsoro nake ji Sis bazan iya ko daga musu yatsa ba wannan uban kudi da suke dashi haka, tsoro ma nake ji kar a sakeki,nace ke ki daina min fatan saki yanzu gidan nan shine rufin asirinmu,ni ina son aurena wlh rike abina zanyi da daraja,gwara kawai nayi dan samun lada tunda kudin nan naga Alama ba sune komai ba, Meenat ta dinga dariya tace kowa ya tuba dan wuya ba lada Sis.

   Ke na hakura da kudin na koma kama mutuncina ni kam harkar auren nan zan dawo na gaskiya,Idan ma ya sakeni Allah yagani,Meenat tace Good yanzu za a fara zaman aure kenan? Nace ae,tace to ai kin batawa mijinki rai sai ki fara zuwa ki bashi hakuri,haka ne miko min Katon hijab din can na Ammah nafi daraja a idonsa,hhhh Meenat tace yo wacce daraja zakiyi kinje wajen miji da Hijab ai kamata yayi ki dau wankan sugar,baki da hankali Meenat cewa zaiyi sonsa nake,ni kuwa ba sonsa nake ba bautar aure zanyi,so kike ya rainani ba class yana kallon tsaraici na,kin manta jiya da kika bude cinya kina lashe lashe a gabansa fa,to ai ni mantawa nayi dashi kuma in Allah ya yarda daga yau na koma yar gayu nima,ko kayan dadi ne sai nayi yanga zanci,kuma bazai kara ganin jiki na ba,Meenat ma ba hankali tace kin san kuwa Maza ba kunya garesu ba zaneki zaiyi kuma ta kalle miki jiki,nima nace ai yanzu zan fara bawa jikina tsaro.

     Sadaf sadaf na fito da shirgegen Hijab dina,ba kowa a palo na tafi ina taku na  nutsuwa irin nayi hankali fa,baya palo nayi ta Maza na haura samansa,har hadadden Bedroom dinsa na kwankwasa tare da Sallama na leka kaina ciki,na hango abinci lafiyayye da abubuwan dadi iri iri a gefensa yana ci yana aiki a system,Na murda handle na shiga,da mamaki ya kalleni yanda yasan tsorona na iya fitowa yanzu duk rashin kunyar da na masa,Har gabansa naje na durkusa tare da cewa sannu Aayan dan ni ba ruwana da wani yaya ko waye waye kawai Aayan tunda ba Masoya bane akan me zan boye suna.nace dan Allah kayi hakuri kaji wlh wasa nakeyi zanyi musu biyayya Bazan kara ba ni dai mu zauna lfy,da mamaki naji yace kin kyautawa kanki idan ma baki ba ke zaki sha wahala,ki nutsu ki san me kike abinda Family dinmu sukeyi bana wasa bane,har yau baki san dalilin auren Ki da na yi ba,kiyi abinda nace zan biyaki kudinki ko wani kike so ki fada min muna gamawa sai na warware aurenmu na aura miki wancan a ranar tare da kudade,nace to Alhmdllh ai ta kwana gidan sauki,amma da ni nufina zanyi bautar aurena tsakani da Allah,no..no..no Need kawai kowa yayi rayuwarsa cewar Aayan,nifa ba wai nufina aure kayi min wani abu na mata da miji ba ai na rigada nasan baza ka iya Yin komai ba,baka da lfy, a firgice naga ya dago tare da cewa a ina kika sani?nace ranar dana fara ganinka tare da Abbi time din da ka fadi nazo taimako ka min duka duk naji me kuke cewa,oh shine kika zo ki fada min kenan? karki jawo na goge miki hadda yanzu ki gani zan iya ko Bazan iya ba,nace ni ba haka nake nufi ba ina magana hankalina baya jikina sam yana ledar dana ga kayan tande tande a ciki har dogon wuya nakeyi haka nake ni Allah ya zuba min kwadayi a rayuwata tun ina karama Ammah bata yawo dani Sabo da babu dama naga me talla sai na mika hannu a bani,ko kuma nayi ta kuka sai an siya min,ko gidan biki idan akaje dani to fa kowa sai yasan kwadayi na,Ammah watarana sai dai ta goyani a baya tasa Zani ta daure ni har hannaye tam,sai dai nayi ta kuka a baya ina kallon masu tallan kayan ciye ciye.

    Yana satar kallona yanda nake kallon abin ledar sai yace bari ya gwadani,Muryarsa naji yace ko zaki ci ne? Da Sauri nace a'a na gode ni bama na ci,murmushi yayi kana yace to shike nan dama na koshi zubarwa zanyi dasu,da Sauri nace kawo na zubar ma,a'a kyale idan zan fita zan zubar da kaina,Nace da dai ka kawo na hutar da kai kamarka dan gayu ka tsaya zubar da shara ai bai dace ba wannan sai irinmu,gaskiya ne dauki to kije dustbin kasa ki zubar,da Sauri na dauka tare da cewa sai da safe,yana ta jinjina kwadayi na don yasan ba zubarwa zanyi ba,kuma dama shi din yaga damar bani ne ganin yanda nake shi yasa yace na kallon abun shine tace a zubar,ni kuma tunanina wayo nayi masa na fita ina dariyar mugunta irin na cuceshi.

   Ina shiga Bedroom na bawa su Meenat labari suka ce lallai Sister kin iya wayo,muka sha ice cream,Nama,lemo da wani chips yasha hadi.
   Tun daga wannan Rana bamu kara ganin Aayan ba ko kamshinsa har muka kwashe sati biyu mu kadai muke rayuwa a gidan kuma sisi bai bar mana ba haka ya tafi,a bakin masu gadi naji wai yana Abuja,nima ban damu ba sam tunda Allah yasa ina dan boye kudi a hannuna kuma na saba da irin wannan ni dama tun ina yarinya a wahala na taso da tunanin ya zamu kare.

     Sati daya shuru,biyu shuru,kudina duk sun kare gobe ma su Meenat basu da na zuwa schl nayi Cefane dana hannuna,muna zaune a palo na gama gyarawa Ma'eeshah kai na fara Yiwa Meenat kitso itama, door Bell muka ji, nace Ma'eesha je ki bude ta mike da gudu tare da bude kofar gani mukayi an mako kofar tare da ture Ma'eesha ta fadi gefe bakinta ya fashe,ba kowa bane face yan matan nan na gidan su Aayan su Uku har yau ban san sunansu ba, da sauri na mike tare da daukan Ma'eeshah ina mata sannu tare da goge mata baki da tissue,saman kujera na kwantar da ita ko kallonsu banyi ba naci gaba da Yiwa Meenat kitso,muna kallonsu suna ta jan tsaki ana yanga tare da taku dai dai muna kallo suka haura saman Aayan,da Sauri na mike tare da bin bayansu suna yanga na sha gabansu kafin su karasa bedroom din na riga su shiga ciki tare da zaro key din dake jikin kofar na rufe kofar da key na zare key din zan bar wajen suka tareni a palo dole sai na basu key dakin dan uwansu ne dole suyi abinda suka ga dama.

 Kallonsu nayi sama da kasa sannan nace Bazan baku ba,a saman nan 2 palo ne ga Bedrooms har Uku kasa ma haka ku shiga duk inda kuka ga dama Amma banda dakin mijina.
   Bazai yuwu ku dauki abu ya dawo yaga babu ba ni zai tambaya,hakki nane kula da kayan me gida tare da dukiyarsa,sannan dakin nan sirrinmu ne na ma'aurata bazai yuwu dan kuna danginsa ku shigar mana dakin bacci ba salon a ga gadon kwananmu, kaina sukayo gaba daya zasu dakeni na zame tare da guduwa muka shige Bedroom muka danna key suna nan tsaye cike da mamakin kalamai na tare da rashin kunya ta Amma ba komai zasu gyara ni Allah kawo ni Family house.

    Nan take suka kira Aayan wai sunzo na zagi iyayensu,Yace su jirashi gashi nan ya dawo daga Abuja yanzu flight nasa ya sauka yama kusa da gida, 15 mnt muka ji motoci lokacin na fito daga wanka daure da towel na Sa Katon Hijab dina har kasa na fito don tunanina matan nan sun tafi sai na gansu a palo suna ta faman kallon kida a TV, dariya suka kwashe min da ita tare da cewa kaga yar kauye wai miji ya dawo Amma jibeta yanda ta Fito suna ta faman yi,ni dai ban kulasu ba na bude kofar da naji kara,wow yanda ya wani mugun kyau ba a cewa komai kamshinsa na tashi,Kallonsa na tsaya yi sai da yace Madam ya akayi ne yana murmushi ganin idon danginsa a wajen Amma nasan da basa nan ko kallona bazai yi ba,sai kallonmu sukeyi ganin idonsu yace ko Hug babu ya miko hannu zai rungumeni da Sauri Naja baya tare da cewa nayi fushi ai ka bata min,nan kuwa kawai ban so ya taba min jiki a wani auren business,Baki ya tabe sannan yace ni ko?yanda ya dage girar ya masa kyau,muryarsu muka ji sunce ur wlcm ya Aayan, tnx kawai yace musu yayi sama abinsa na dauki jakar nabi bayansa sama,su kuma suna ta tabe baki,ni na mika masa key ya bude dakin,Yana shiga Bedroom na ajiye masa jakar zan juyo naji yace me ya hada ku? Bakya jin magana wato ke ko? Duk abinda zakuyi karki sake kuyi min kokawa a gida tunda nasan kun saba,nace ni hauka nake na hada jiki dasu ai yanzu na girma Antynsu ce ni ai yanzu,zuwa sukayi tare da make min Ma'eesha harda fasa mata baki daga ta bude musu kofa,suka shigo har sama zasu shigar ma daki ni kuma naga bai dace ba ai nice matar gidan in banda an raina ni taya za a wuce dakin mijin mace kawai wai zasu dauki abu shine na kulle kofar na fada musu bai dace ba,ko ba komai idan wani abu ya bata ai ni za ace,Murmushi ya saki tare da cewa ashe kina da hankali,ina dashi mana ai kaine dan baka sanni ba kake tuna nin yarinya ce ni,ko magana bai kara yi ba ya wani shige toilet abinsa nima nayi waje,suna jiransa ya fito ya dauki mataki a kaina,amma shuru yama manta dasu gaba daya yana bacci abinsa.
    Suna komawa gida suka fadi karya da gaskiya wurin kakarsu Hajja nan take tayi masa waya lallai ya dawo damu Family House a yau ba sai gobe ba.

    Kawai ji mukayi yace mu hado kayanmu Driver zai maida mu can gidansu zamu koma da zama, haka muka shirya har kuka nayi a boye dan nasan shike nan mu kuma,Har part din Aayan na gidan Driver ya kaimu,dama na taba zuwa sau daya lokacin dana kai masa takarda ya nemo min Yarima abokinsa akan Aikin Ammah,part din ya tsaru harda na masifa,sama da kasa kasa 2bedroom da palo sama ma haka sai kitchen da store ya hadu iya karshe don yafi gidan da muka bari kyau da komai a kasa still muka zabi daki daya abinmu mu Uku,na duba kitchen da store wayam ba komai sai Indomie,kayan tea dana Coffee sai kayan sha dana gwangwani shirye cikin Fridge.

   Yanzu za a fara rayuwar fa.



AsmaBaffa
Reply
#4
36-40


Official


By AsmaBaffa


ZAINAB ATIKU SALAMA and MRS Hamza wannan page din sadaukarwa ce gareku.

   Jinjina gareku 
HEENDU
RAMCY MAKE UP
MOMMYN ZAHRA
HAJIYA ABOU
AUNTY SUMEE
HUMAIRA 
ZULAIHAT
SAFEEYA AHMAD
   Ina muku fatan Alkhairi tare da godiya da Sharhi.

     Masu Sharhi na ko wanne Gp da wanda kuka min magana ta pc ina gani kuma zaku ganni Online wlh Simcard dina ne yake da matsala sai kun min Uzuri kafin na gyara,sako yana shigowa ina gani Amma ni Idan nayi reply baza su zo da wuri ba,kuyi min Sharhi ina gani kuma zan bawa ko wacce amsa Fatana kuyi min Afwa da Uzuri.

Kamar an sanar a gidan Radio haka muka dinga ganin yan gidan suna shigowa mata da Maza wasu na taba ganin su wasu kuma ban sansu ba,Kowa da kallon wulakancin da suke mana,ni kuwa ko magana banyi ba ko ina wuni bance da kowa ba nima kuma na cewa su Meenat karsu kula kowa,kaf yan gidan nan sai da suka sheda bani da mutunci bare kunya Sabo da zaman kawai da nayi a kujera ya isheka amsa, manyan ne kawai suke min kallon Banza ina kyalesu Amma indai mutum matashi ne ko budurwa yaro ko yarinya indai suka min sai na mayar musu da matartani ina daga zaune abina nima kuma basu Isa na gaishesu ba bare su Sa rai da mutunci na shigo.
   Wasu manyan samari ne su Uku za suyi basu kai Aayan shekaru ba sunji labari ance musu Amaryar Aayan kyakyawace ta karshen gaske sai dai bata da kunya ko kadan,gata kuma kalar kauye ce duk iyayin Aayan ya kare a yarinya karama kamata kuma ba yar gayu ba,da sallama suka shigo bayan Sallar Isha Sabo da su Maza ne kuma suna da dan hankali,kallo daya na musu na dauke kai tare da amsawa a hankali,Ganin basuyi min kallon Banza ba yasa na saki fuska tare da cewa ina wuninku,suka ce lfy sannu Amarya ya gajiya nace Alhmdllh babu wanda ya kara magana,Sai kare min kallo sukeyi musamman wani a cikinsu kallo kamar maye hakan ma da Hijab dina,Sai ko naji yace Amarya ya kamata a mana girki muci mu ji,nace sai dai ku shiga kitchen da kanku ni yanzu sai na huta nasha gajiyar hanya daga wancan gidan zuwa wannan na jigata a Cikin mota Driver ya jijjigani da yawa a hanya na fada ina yatsina,mamaki ya kashe su abinda sun san gidan ba wani nisa da wannan unguwar Amma wannan yar rainin hankali ce wai mu shiga kitchen ma,

tasan ko mu su waye,kaji yar talakawa cewar daya a cikinsu ya fada a hankali bai san naji ba,daya kuma yace min kannen Aayan ne mu ni sunana Khaleel,ga Ameer sai wannan Mujaheed, nace good bari na shiga daga ciki,wanda ke yawan kallo na wato Ameer kenan yace a haba ko hira ba ayi ba,zama nayi kawai nayi shuru suma suna zaune sun dade sosai har wurin 8:30pm

   Sai ga Aayan ya shigo rai a bace kamar zai daki mutane kadan yake jira,suna ganinsa suka min sallama suka fita,ni kuma na kalleshi yanda ya wuce da Sauri yana bin steps,Saman bed ya fada tare da kwantawa ruf da ciki ko me yake tunani oho ko wani abu akayi masa ban sani ba ni dai,nasan dai bazai wuce matsalar yan gidansu bace ni kuma ban san mene dalili ba bare nayi wani abu a kai,shi baya kulani bare nasan matsalarsu,ban ma san ko tarihin gidansu ba sai wanda na tsinta ranar ganina dasu na farko sai kuma abinda na fara gani yanzu a gidan kamar dai shi Aayan kadai shi suke warewa basa so Amma dai ban san komai ba,duk da haka sai naji tausayinsa,naji ba dadi me ciyar da kai ace yana cikin wani Hali dole ai kaji ba dadi sai kawai na wuce kitchen,Sharp sharp na dafa Indomie da kwai kar ma yazo yasa a kwashe su ya kawo mana su garin danwake shi yasa nace bari muci rabonmu,na bawa su Meenat na zuba wata a plate na nufi dakinsa can sama a nan na sha kallon haduwa.

   Saman Bed na hangoshi a kwance ban san me yake yi ba bacci ko tunani,Aayan...Aayan na fada a hankali,a hankali ya bude idonsa tare da cewa Lfy? Abinci idan zakaci Indomie naga ka dawo daga Abuja baka ci komai ba,ko kaci? Kansa ya dago a hankali tare da kallo na ya dauke kai yace ni bana cin Indomie yanda ya fada kamar dan yaron goye a shagwabe,nace to me kake ci? Ai nasan baza ki dafa min ba bakya jin magana,fada zan dafa ma ai nayi hankali na daina, yaushe kikayi hankalin? Na daga kai ina tunani sannan nace an dade fa tun shekaran jiya, murmushin da bai shirya ba yayi kana yace Kosai nake so da kunun gyada sai danwake,nace to ai nan babu kayan yi a wancan gidan ne akwai,Waya naga ya dauka nan take naji yace a kwaso kayan dake kitchen da store na abinci a kawo masa part dinsa,wani bakin ciki ya dirar min shike nan mu baza muci abincin zamani ba,kamar yasan me nace sai naji yace shi kuka saba ci ai a gidanku idan na baku na yan gayu baza ku iya ci ba,nace mu dai zamu iya dan Allah,yace to ba yanzu ba sai watarana idan naga dama, cike da takaici nace shike nan ai,su Meenat basu da kudin Napep na zuwa schl,sannan nima dan Allah ka sani a schl,budar bakinsa sai yace ni bani da time idan kina da wani zan baki kudi ki zabi schl me araha private ya kaiki zan biya ni Bazan iya biya miki private me tsada ba,sabo da na raina basirarki, nace wai mene amfanin kudinka? Kallona yayi tare da Sa Headphone a kunnensa irin na takura masa haka na fita na kyaleshi cike da tunanin to wai me yasa ya aureni yana kallo ko kayan sawar kirki bamu da Amma ko Ya siya mana wasu to bai bamu abincin kirki ba ma sai wasu kayan sawa kawai dai raini ne ya jawo mana a danginsa.

    Ina zaune a palo sai gashi an kawo komai na girkinmu irin na can gidan su dawa gero masara etc,Kitchen na shiga na fara shirin hada gyada da danyar shinkafa tare da lemon tsami na kunun gyada,ina cikin aikina sai ga samarin nan Ameer me kallon tsiya,khaleel da Mujaheed har kitchen suka ce Amarya girki ake shirya mana nasan ganin kwakwaf suka zo kuma sun gani su masara dasu geron,dan masifa suka ki fita daga kitchen din sai suka ce wai sai sun taya ni,nace a'a bana so kannena zasu tayani,sai ga Meenat ta shigo kitchen cikin English wears riga da skert tayi kyau Sabo da wanka tayi tare da fesa kwalliyarta da ta saba,aiko suka bi ta da kallo sunga me kyau da diri,ni kuwa a hijab nake baza su gane komai ba sai fuskata da take da tsananin kyau,Meenat tace Sis kawo na hada waken muna ta aikinmu tare suna kallo don zama sukayi a kitchen din wai sai an fara girkin sunci sunji,Ina tsoron tambayarsu gidan da ake markade na hakura mukayi a blender sai suka ga kosai mukeyi da kunun gyada,basa cin kosai su Amma suna shan kunun gyada,Aayan ne ya fito daga dakinsa Ya taho kitchen da niyyar daukan ruwa abin ya daure masa kai ganinmu gaba daya da rida ridan kannensa a kitchen muna yar hira jefi jefi sai tambaye tambaye suke mana akan girkin nan,ina tunanin zanga ya bata rai ko yaji haushinsu ko Ya musu magana su fita Maza bai dace su dinga shigewa mace me aure ba Amma sai naga ko a jikinsa ruwansa ya dauka tare da ficewa.

  Muna gamawa naga sun zaro cups zasu fara eba,nace ku tsaya mijina fa? nasa ne dole sai na fara ebar masa,Ameer yayi murmushi tare da cewa Amarya ai ko nasan ne muna da yancin shigowa mu eba ko shi bai Isa yace kar mu eba ba,Kallonsa nayi nace to ni na Isa dan shi yasa ni nayi masa sai na ebar masa,Na gano ba so suke su sha ba takura min suka zo yi don kamar ma turo su akayi su Sa min ido.

    Sai da na dauki wani jug me kamar flask na zuba ma Aayan, meenat bata ce mana komai Sabo da na hanasu magana akan dangin Aayan kosanta take soyawa,naje na ebarwa Aayan na ebar mana namu tare da kai mana Bedroom,na dawo lokacin Meenat ta gama soya kosai muka gyara kitchen sannan nace to zaku iya eba dan bakar jaraba suna palo sai da suka shigo kowa ya eba a cup suna sha duk wanda nayi suka shanye ba ruwansu da tambaya,Khaleel ma da yafi su rashin kunya Na Aayan yazo wai zai kara a ciki ya masa dadi, nan take na dauke komai tare da jerawa a wani tire me kyau sannan nace bazai yuwu ba kunsha rabonku nayi gaba na Barsu a palon,sama Na haura tare da knocking sannan na shiga yana zaune saman Sallaya yana addua na ajiye masa zan fita naji yace wait,ina tsaye ina jiransa ya gama tare da shafawa sannan naji muryarsa yace Zauna,can gefe na durkusa yace me suka ce miki su Ameer? Na bashi labari har abinda nace musu,yace to daga yau ko me suka ce ki musu kiyi musu ko nawa ne ki basu,nace ni Allah Bazan basu ba,nasha wahala kace na basu,to ba nawa bane nace ki basu,to me ya hanasu suyi auren su ko su tafi wajen iyayensu ni na haifesu da zan dinga wahala suna raina min Hankali,ina matarka tunda kannenka ne ai kamata yayi su dinga girmamani kuma sai suzo kitchen su tsaya min a kai ai duk kai kake basu kofa,kamar wanda ke jin tsoronsu ni ban gane maka ba,kace rannan na dinga ramawa yanzu kace na daina na bari kenan su takani ko? Shuru yayi bai ce komai ba,sai can yace nima  kinga ban san me ke damuna ba ths month ina jin bani da lfy ni ban san ma meke damuna ba gaba daya,ina ke maka ciwo? Yace babu a jikina nake jin kawai da matsala bani da lfy ban san ya zan iya fada miki ba,tunanina mutuwa zaiyi sai na fara hawaye nace ni dai karka mutu dan Allah irin Ammah yanzu wa zai bamu abinci gashi muna ci muna koshi,kallona yayi da mamaki shi da yake bamu abincin talakawa Amma har dadi nake ji a haka ina fata kar ya mutu Sabo da wannan.

    Miko min abincin,mika masa nayi sannan na zuba masa da Sauri wai dan kar ciwo ya kamashi ya mutu,ya karba a hankali yana cije lips ni tunanina ko jikin ne yake jin bazai iya karba ba,sai nace tsaya tsaya na karbi cup din nasa spoon a ciki ina juya sugar din sannan na rike masa a hannuna nace to bari na rike ma a haka kai kuma sai ka dinga sha ko na baka yanda nake wa su Meenat tunda baka da lfy? Banza ya min tare da bata rai yana ta fushi kuma yanzu kamar yaron da aka Zane,Sai ji nayi yace rike abinki ki sha,na fasa, yi hakuri gashi rike abinka Allah Sarki sha abinka kaji,ni kar na baka? Yace ae bana son naki, nace to gashi nan ni na tafi ma,na mike tare da bar masa dakinsa,na rigada na saba da Yiwa su Ma'eesha irin abun Yara idan zan basu abinci ko ina basu sai na dinga ta lallabasu shi yasa,ko ina basu ta dole. 

     10pm muna daki muna karatunmu ya shigo Bedroom dinmu tare da cewa zo,Maeesha tace Hi Uncle,murmushi ya mata tare da daga mata hannu,Meenat ma ta gaisheshi ya amsa da sakin fuska kadan,Hijab dina na Sa tare da binsa a baya har Bedroom dinsa yana Saman Bed ina kasa a tsugune yana ta faman cika yana batsewa ga jarabar takama,yace  gobe ki shirya 8am kuje ku gaisar da Hajja kakarmu ko me zata ce karki mayar mata da martani kiyi biyayya,nace to Insha'allah,yace muje yanzu wajen Abbana,nace au kana da Baba mahaifi? Yace of Course ai ni dan gata ne Umarninsa nake bi,murmushi nayi nace kuna kama? Yace mene kika tambaya? Idan kuna kama to nasan Babanka ma me kyau ne ko Ummanka ka biyo?ke dadina dake shirme,Ummanka ta rasu ita? Ya daga kai tare da cewa kuma nafi son Abbana ba tun farko,Nace tab ni kuwa nafi son Ammah,Abbanka yana Sonka kenan da yawa gani nayi yana ta farin ciki kawai akan nayi zancen Abbansa lallai yana sonshi,fuskarsa na leka nace Dan Abba zan dinga ce ma yanzu,muje na ganshi ma zan dinga kai masa abinci,yace ai ba komai yake iya ci ba,bashi da lfy ya fada kwalla kamar zata zubo masa,nace eyya ai Insha'allah zai warke ne,lets go kawai yace min,nabi bayansa falau falau da hijab muna ta sheka uban tafiya yana gaba ina bayansa har muka je wani building a Cikin gidan katafaren me kyau,ciki muka shiga kafin ma mu Isa inda zamu hau steps duniya ce guda ko ina kuma Securities ne masu tsaron Daddyn Aayan, sannan muka haura sama can wani Bedroom shima nan duk sune suke tsaro har cikin dakin,saman Bed na hango shi dattijo kyakyawa irin Aayan suna kama sosai sai daí Aayan ya fishi farar fata,sallama mukayi masa da mamakina naji ya amsa yana murmushi tare da cewa My Son kazo ke nan,Aayan ya karasa jikin Bed din tare da rike hannunsa yace Daddy ya jikin? Alhmdllh Son yanda kasan jikin kullum haka yake ina so na taka kamar kowa Amma bazai yuwu ba,kana gani komai sai dai ayi min haka nake ba inda ke motsi a jikina sai baki na,addua kawai itace Mafita tunda ba inda ba aje ba ciwo yaki ci yaki cinyewa,to hakanma mun godewa Allah.

   Ina mamaki yanda yake fes haka cikin koshin lfy ace wai baida lfy komai nasa baya motsi gashi shar dashi muryarsa ras haka,a hankali naga Aayan ya rada masa magana a kunne nan take ya fara murmushi tare da cewa Yata matso kusa ya kika tsaya nesa,Da Sauri na karasa gaban gadon tare da durkusawa har kasa nace Ina yini ya jikin?Yace Alhmdllh,nace Allah kara lfy,Ameen yata Gashi nan sai kinyi hakuri kin ganshi baya jin magana na dade da cewa ya kawo min ke sai ya dinga min hanya hanya,Murmushi nayi ina jin kunya nace ai yanzu ya kawoni kuma kullum zanzo ba sai ya kawo ni ba yanzu tunda na gane hanya,Murmushi yayi tare da cewa na gode Allah ya muku Albarka,ya albarkanci aurenku ya baku zuria ta gari,Ya sunan yar tawa nace Mufeeda,Alhmdllh naji ance da kannenki ko?nace ae yace to Allah rayasu ya musu Albarka nace Ameen,Allah yaji kan mahaifiyarku nace Ameen Daddy, ki kara hakuri kinji,zaman gidan nan sai hakuri,wannan dan nawa baya ji kin ganshi ina fama dashi sai kinyi da gaske saurin fushi gareshi ga zurfin ciki,ki rike min shi da Amana yata kinji,nace Daddy ai shine sai ya dinga fada yana fushi, Dariya yayi sannan yace to zan masa fada,nace to Daddy,Harara Aayan ya zabga min nayi shuru dani,Mun dan dade a dakin Aayan suna ta hira sannan yayiwa Daddy sallama muka dawo part dinmu,na wuce dakinmu shima yayi samansa.

    Cikin dare 2am na farka da ciwon Mara sosai naji kamar abu ya zubo min a pant,mikewa nayi da Sauri na shiga toilet,sai naga period nima na fara dan ban taba yi ba sai yanzu,Meenat kanwata kuwa ita tun tana Jss 2 ta fara dama ta fini kiba, fitowa nayi tare da tashin Meenat nace Meenat tashi ki bani pad nima na fara period,cikin magagin bacci tace Sis ta kare tun last month wacce kika siyo min na karar da ita,To fa yanzu ya zanyi kenan,ki Sa tsumma kafin gobe,ke da rushing na fara fa wlh tsumma bazai daukeni ba kinji yanda yake tsiyayowa kuwa,to yanzu ya za ayi kenan,nace bani dankwalin tsohuwar a tamfar nan taki na Sa naje Wajen Aayan ya san ya zaiyi dani,Meenat tace baki jin kunya? Kuma kin san bazai je ba sai dai yasa me gadi,a'a zai iya karbo min ko wajen yan matan gidan nan ne kema kin san Bazan iya kwanciya haka ba gashi dare yayi dole tunda lalura ce kuma yasan mata sunayi ai dole gunsa zan je.
   Haka ne kam jeki to muji,nan na karbi karamin dankwalin na koma toilet tare da gyara jikina don nasan kafin naje sama Na dawo na bata kayana ko ma ya dinga saukowa saman tiles.

   Cike da tsoro na masa knocking shuru har sai da nayi yafi sau goma sha sannan naji yace Am coming yana jan tsaki ya bude min kofar daga shi sai wani dan tight short karami ko riga babu a jikinsa,daki ya koma nabi bayansa Sabo da ya kunna light din haske ya gauraye dakin,lfy ciki dare? Na fara ina ina uhm...uhmm..na juya baya tare da tamke idona kawai na maze kamar bani na fada ba nace ehmmm wai..Wai,yace to fitar min tunda baki da abin fada,da Sauri nace period na fara kuma bamu da pad gashi dare yayi ko zaka karbo min wajen kannenka na karasa tare da matse idona kam na juya masa baya.

    Tsaki yaja tare da cewa sai ki bari sai gobe kya siya ni me ya shafeni a nan fitar min a daki na zata wani abu ne,Marairaicewa nayi ina rokonsa dan Allah Dan Abbansa ka amso min pls haba Na Daddy,kallona ya tsaya yi yanda nake shagwaba kamar yarinyar yaye, hannu ya daga min hey..hey Hold it thr ban son shirme see u ko kunya baki ji kina min shagwaba ya fice fuuu ya barni,murmushi nayi tare da cewa oho dai ni dai ka karbo min shike nan.
     Yana fita na fada saman Bed dinsa nace sai na more naji dadinsa yau dai na dinga birgima a kai ina tunanin zaman da zamuyi wanne Hali zan aro na daurawa kaina dan naga karshen yan iskan gidan nan,tsawa naji keee...Ban san sanda na fado kasa ba dan na manta a Bed dinsa nake,yace Iskancin naki har ya kai Bed dina nan take ya bude wardrop tare da dauko sabon bedsheet ya jefo min tare da cewa cire min wannan kazantar zaki shafa min a Bed shimfida min new, ban bata ma bafa kalla ba komai a kai fa,i wl slap u,ba shiri na cire wancan na shimfida masa wanda ya bani tare da dame masa yayi kyau,wani turare ya miko min ungo fesa a saman Bed din,haka na fesa,yace to jeki da wannan ki wanke min gobe ki dawo min da Abuna Kazama,nace haba Ranka ya dade ka rage irin wannan ni fa matarka ce Amma kwata kwata baka kyautata min,ko Auren business ai ka bari dai mu rabu lfy Amma ba komai bani abun na tafi,naje sunyi bacci ban samo ba,To su manyan matan su Abbi fa? Ko lokacinsu ya cika basa yi su? Baki ya tabe tare da cewa bama shiri taya zanje nace su bani sun san ke zan bawa baza su bani ba,kuma dare yayi bare a siyo,sun tsofe ma wanne period zasuyi ai sai yayansu, nace to ni yanzu ya zanyi na fada kamar zanyi kuka ina doka kafafu,tafi ki san me zaki Sa sai gobe,ni Bazan tafi ba ya kake so nayi dan Allah,tunda farko ne ai bazai miki da yawa ba kije kawai,nace to ni nawa ba haka yake ba kana ta sani ina fadar badala da rashin kunya a baki na,baka san yanda nake ji ba idan ina ambata irin wannan lafazi na Badala a gabanka, murmushin da bai shirya ba ya saki,oh nan kunyata kike ji kenan,wlh da kyar nake iya magana lalura ce ta kawo ni dan Allah a san yanda za ayi dani Na Daddy Allah dai yaji kan Mommynka  ya dauraka akan makiyanka,jin nayiwa iyayensa Addua sai naga ya saki ransa kamar wanda aka Yiwa Bushara da Aljanna yace to yanzu ya za ayi kenan? A raina nace na gano lagonka,nace babu 24hrs ne a Kano?Yace da dai Abuja ne sai a samu kuma kinga 2am ba kyau fita ko fitsari tsakar dare nace haka ne,amma muje mana wajen yan matan ka rakani ni zan san yanda dole ma su bani.yace to muje a Cikin wardrop ta jikin Bed suke ajiyewa,nace an gama muje.

   Tiryan tiryan muka je har kofar dakin daya,yace wannan dakin Hanifa ne,ai ko na dinga knocking kamar dakina ta bude sai ta ganni tare da Aayan da har zata min masifa ganinsa yasa tayi mukus don tsoronsa suke ji,ni kuma da tsokana kawai nayi ciki da ita tare da tureta na banka cikin dakin,direct na bude wardrop Aiko na gansu a jere na dauko sinki daya na bude na kwashi guda uku sannan na watsar da ragowar a kasa nazo zan wuce na bata rai,tace wlh baki Isa ba ni zakiyiwa wulakanci har Bedroom,na kalleta sama da kasa nayi irin gwanar nan nace How Dear u zaki na min magana any how duk wanda yaji zaice na gama kwarewa da Turanci,taki Sakina kuwa,na kira Aayan Babyna da Sauri ta sakeni tana hararata na fito  nace masa muje to,muna Tafiya a hanya nace nayi fashi da makami kaga abinda baza ka iya ba,kai kullum sai ka dinga zura musu ido kamar wanda suka Yiwa asiri danma suna jin tsoronka ai da tuni ina ga kowa ma taka ka zaiyi.

   Ki shirya gobe zasu zo daukan fansa wlh harda iyayensu,nace dan Allah ina son muyi magana da kai Na Daddy Allah ya karawa Daddy lfy da nisan kwana, ina binsa a baya da Katon Hijab dina har Bedroom dinsa,ya fada saman Bed dama yasa jallabiyarsa,a hankali na zauna a gefen Bed din ina jin tsoro,ina jiran naji tsawa sai naji shuru,ina zama ina cewa Fatana Allah ya bawa Daddy lfy wlh a gidan nan,da anga yanda zaifi kowa Sonka ai da kafi karfin kula mu ma Sabo da ka zama Gold,yanda  naga Daddy na Sonka abin sai wanda ya gani inama Abban mu haka yake irin naka na furta tare da kwanciya na mike sambal a gefensa,tunanina wayo zan masa shi kuwa tuni ya san me nake nufi Amma sai ya shareni ya gama ganin iya wayon nawa me nake nufi.

    Dan Daddy wai ya maganar schl din tawa,yace anzo wajen,nace dan Allah Oga kwata kwata ka kaini schl,yace hmm yana dariya a ransa wai shi yar wannan Jaririyar zata Yiwa wayo,yace dama Arabic da boko kika shiga a hade tunda naga kinfi kokari a Arabic sai ki hada biyu abinki,nace ah gaskiya a'a nima nafi son na zama yar boko sosai,to ki zabi wacce kike so sai na biya miki,Nace to, Amma ai sai dai wani ya kaiki,bani da time ki samu wani a yan uwanki ko frnds su kaiki zan baki kudin,nace to zanje Amma dan Allah kasa a kaini a mota kaga raina ni za ayi a gidan nan,yace an gama,duk tunanina da gaske yakeyi sai murna nake yi nayi masa wayo,nace saura kayan sawa zamuje shopping Sabo da goge raini,yace nawa ne zai Isa a goge rainin?nace ko dubu goma sun isa,ya kyalkyale da dariya ku Uku dubu goma to kaya kala nawa zaku dinka kenan nace kala Uku Uku ko hudu,yace lallai dasu zaku goge rainin kenan? Nace to ni ban san kaya ba tunda ai kasan ba siya muke sosai ba.kawai biye min yake yaga iya wayon nawa.

    Dan ya nuna min na masa wayon sai yace bude can,naje na bude wata Wardrop,nan take na kusa sumewa kudi ne a jere a jere bundles da yawa na Dubu dubu da dollers,yace ebi yanda zai isheku,nan take gumi ya keto min na rude na rasa yanda zanyi jikina yana rawa na ja baya tare da cewa ni dai sai dai ka bani da kanka, ba yanda baiyi dani ba kan na dauka Amma na kasa sai ma shagwabewa danayi zanyi Kuka kudin sun tsoratani,mikewa yayi tare da kwaso Bundles goma yan dubu dubu ya zube min a gabana yace jeki dasu ai sai na fashe da kuka nace bana so ni,kamar naga wani Dodo na dinga ja da baya,yana dariya a ransa a fili yace kefa kike son kudi,nace ni ba irin wannan nake so ba,tunda kace sai na Eba da yawa to bani dubu ashirin sun ishemu komai da Komai,yace naga ai an baki kudin Sadaki har dubu dari Uku ya kikayi dasu?lokacin ai bana cikin hankalina Sabo da rashin lfyar Ammah da rasuwarta duk a nan suka kare.

    Bundle guda ya bani na yan dubu da kyar na karba na tsaya ina tunani,kafaduna biyu ya rike tare da bude kofa ya jefa ni waje tare da rufe kofarsa,Bedroom dinmu naje da murna na nunawa Meenat tace gaskiya Sis tsakani da Allah kin damemu a wannan tsakiyar dare 3am ta wuce kinki bacci sai labarin mijinki kike mana ki kwanta mana ki huta,ni dama idan labari na Cina to komai dare sai na tashi mutum na fada masa,bayan na shirya kaina duk sun koma bacci har na kwanta nima na tuna ban fadawa Meenat labarin Daddy Baban Aayan ba.

    Tashinta na fara yi Meenat Meenat ku tashi kuji banza suka min nace wai ina magana kun rainani ko,muna ji ki fada mu wlh bacci muke ji ke bakiyi ba kin hana kowa yi,ina basu labari suna uhm..eh...to...har bacci ya kwashe mu,kafin asuba wayata tayi kara ta tasheni ban dauka ba Amma sai na tashi Meenat,kawai sai ta fashe da kuka  wai na hanata bacci,nace to yi shuru kwanta jaraba bakwa jin maganar Ammah tace kuyi min biyayya Amma bakwa yi,Maeesha ta farka itama tayo fitsari muka koma bacci,ni dai banyi wani baccin kirki ba sai na dinga tunanin   Mijin Kasuwanci na.
    
   Washe gari da Safe lafiyayye tea na hada mana Sai kwai na hadashi murtuk dashi naga banza ta fadi irin muci rabonmu kafin yasa a kwashe mu koma Koko,sun sha Uniform dinsu ni kuma doguwar riga da dan hijab karami,tun Safe yan gidan suke ta buga mana kofa ina ji naki budewa,bugun duniya naki budewa sai ma kara Sa lock da nayi,Ina jin Abbi yana zunduma mana ashar akan naki budewa yaransa kofa,wai nice ma zan musu breakfast kuma abinda suke so haka kowa zai fada na dafa musu,ai kuwa bugun duniya muka ki bude kofa gashi suna jin motsinmu,Abbi na gani ta jikin window ya leko yace sai kun bar gidan nan wlh tunda ba yar arziki bace ke,yar Iska,guntuwar shegiya haka ya dinga zagina ta window,na kalleshi ido da ido tare da Galla masa harara na murguda masa baki,yace zaki ci ubanki wlh sai naga waye ubanki a kasar nan,tafi nayi da hannuna na kara Harararsa ina gatsina masa goshi da gira,ni dai bance komai ba,yana ta zagina,ke yarinya ki shiga hankalinki,a nan nayi magana nace Yarinya tana bayan Uwarta ni dama haka nake idan naji haushi bani da mutunci ba kowa nake iya dagawa kafa ba ko za a kasheni,Meenat tana ta dariya Abbi ya kara kulewa,ya bar wajen a fusace yana baza babbar riga.

    Aayan ne yake saukowa yasha wankan gaske cikin kana nan kaya,kamshi na tashi,Meenat tace ina kwana suka gaisa,Maeesha ya rikewa hannu tare da cewa ba gaisuwa yau?tace ina kwana tana dariya,tace kayi kyau Yaya,tnx yace sannan ya kalleni tare da cewa Abincina fa? Ai ban san zaka ci ba bari na hada ma tea,yace a'a Kunun gyada nake so ko Koko ni,idan babu kuma sai ki bani Tea,ai dole nayi maka,yo Allah na tuba ko ba gasara ai dole a nemota kamar Dan Daddy guda yana so akanta ba sai ayi yaki ba a gidan nan,Dariya na bashi sosai yanda nake maganar cike da girmamawa kamar Ina gaban Sarki,kun san wasu mazan akwai son a yabesu ko a girmamasu,wasu kuma suna so a daraja musu iyaye ya dace mata su dinga fahimtar mazajensu.

    Shi Aayan a ransa yace zan gama kure wayonki yarinya har yaushe aka haifeki,Kitchen na shiga dama jiya na tace mana markaden koko,sharp sharp nayi masa tare da soya masa Chips tunda ba time din yi masa kosai,a Dining na ajiye masa sannan na dawo palo wajensa nace Ranka ya dade an gama,a ransa yace zanyi maganinki soon wai ke me wayo.

    Ni na zuba masa da kaina,yana shan abinsa yayi nisa nace da sha nace Dan Allah ina neman wata Alfarma idan da hali ba damuwa kuma ban takura maka ba,yace ina jinki,nace so nake ka bani Driver daya da mota za a kaini unguwa zanje shopping sannan zamu je schl din da zan shiga,waya naga ya dauka tare da danna kira Malam Garba shugo ina son ganinka,minti kadan sai ga Malam Garba Driver yazo,Key din mota ya miko min na karba,yace gasu nan daga yau in zasu je unguwa zasu dinga kiranka kana kaisu inda suke so,ga key din mota nan a hannunta idan zaku fita ka karba idan kun dawo ka bata key din a hannunta,har schl zaka na kaisu,Malam Garba yace an gama Alhaji,nace ga key din ka kaimin su Meenat schl da yamma kuma zamu fita na fada ina wani  mazewa irin matar Alhaji,Aayan yana kallona duk abinda nakeyi.
 Yana gamawa ya mike tare da kara ajiye min Bundle guda na yan dubu yace gashi ki biya kudin schl din ragowar ku kara a shopping karki dawo da kwandala gidan nan duk ki tabbatar kin karar dasu a shopping,nace da gaske mu kashe duka zaka kara mana na cefane?Yace yes.

   Yana fita na dinga tsalle da ihu tare da su Meenat,nace ai na fada muku ni ba a ja dani duk jarabarka sai na ma wayo,gashi dai kwana biyu har na samu abinda nake so,Meenat tace to bari mu dawo muje shopping wlh za a buga damu har mota ya bayar ana kaimu unguwa fa,Meenat tace Sis yau sai munje tsohuwar Unguwarmu a motar munyi musu birga,nace ke banza ce ba yanzu ba sai mun siyi kaya masu tsada mun koma yan gayu sai muje a gaisa ayi zumunci 
   Muje na rakaku mota daga nan mu ganta,gaba daya muka fita har inda Aayan ke ajiye Cars nasa,Malam Garba muka hango a wata shegiyar Benz yar gaske sabuwa dal wai itace zamu dinga hawa,su Meenat suka gaisheshi ya amsa yana me fara'a don gidan kaf babu wanda ke Saurarar dan aiki bare a gaisar dashi komai girmanka.

    Meenat suka kame a gidan Baya,sai ga yan matan nan sun fito zasu tafi schl suma ina ganinsu nace pls Baba Driver ka kular min da motata ,ido suka zaro yaushe na samu matsayi har Aayan ya bani mota.da Sauri naga Hanifa ta koma ciki tana zuwa ta zayyanewa kakarsu dasu Abbi.
   Ina ciki ina aiki naji bugun kofa na leka ta yar kafa na hango su Aiko naki budewa bugun duniya naki aikina kawai nakeyi.
   Aayan na gani ya dawo yace na bude ina budewa Hajja kakarsu ta wankeni da Mari,ga hannunta kamar jikin bishiya Sabo da fatar duk ta tsofe ta bushe.
  Zata kara min na goce,nayi niyyar magana haka nayi shuru ganin Aayan na kusa.

   Abbi da Maza da mata sun kai su goma kowa da kalar zagin da yake min,Aayan na gefe ya kalleni na kalleshi,matar Abbi tace ke har kin Isa matsiyaciya daga kawoki cin arziki,na kalleta idona a bushe nace yo ai bake kika auroni ba,kema ai ba gidanku bane aure ne ya kawoki,kuma wlh Bazan ragawa kowa ba tunda ba aurenku nakeyi ba,Hajja tace iyye au Iskancin naki ya girma haka ina magana kina magana kin san dawa kike magana,nima ai baku san wace ba,Aayan ta kalla tace kai saketa yanzu na bada Umarni,maza rubuta mata saki,nace ku kuke tsoron saki idan an sakeni sai me rayuwa zan fasa ko me,Kaka tsohuwa Hajja ta rike baki dan tunda take babu wanda ya taba mata ko musu Amma gashi ni tana fada ina fada,tace saketa nace,Aayan yace baku kuka Sa na aureta ba ni ne naga dama kuma da dalilina Bazan saketa ba ya juya yayi ficewarsa tare da cewa idan kin gama ki kira Malam Garba a waya na ajiye miki Number dinsa a Dining,nace to Ranka ya dade a dawo lfy Allah ya tsare min kai,yace Ameen,nace Million dayar daka bani sunyi kadan Yanlabai,yace kin san inda suke kije ki kara yanda zasuyi,na Gode Allah ya kara budi,yayi gaba na kalli Matar Abbi Hajiya Karima nace kiji dan Allah Baby bashi da dama wlh common shopping a baka yafi million ga kyautar gida ga mota yau da Safe,tsaki naji sunja Hajja tace a sannu zan shayar dake mamaki wlh sai na canja miki kamanni ba a takani da yarana a zauna lfy.

    Na kalleta nace aiki ya ganki ga tsufa ga shiga rayuwar wani Allah ya taimaka,wlh dan ina ganin girmanki ne ko ba komai zaki ci darajar tsufa da kuma matsayinki na Mahaifiyar surikina kakar Mijina idan da mutunci ke kakata ce Amma baku san haka ba,ku tambayi wace Mufeeda a Unguwarmu kowa yasan yarinyar kirki ce kuma ta wanni fannin bani da mutunci wlh da ace haka kawai ne da kun san wace ni Amma kunci darajar Mijina,ba tabani a zauna lfy dan ma ba akan kudi bane,bana yarda a taba lafiyar hanyar cin Abincina akan wannan bana dagawa kowa kafa.

    Matar Abbi ce ta fisgoni suka hadu da Sauran matan suka fara dukana,sai da suka fasa min gefen bakina kadan hakan ma dan na gudu ne da Allah yasan irin Illar da zasuyi min.

   Daki na fada na kulle nayi Kukana boye a fili nace wlh kun jawowa kanku dan ni indai ba lallabani akayi ba to kara lalacewa nakeyi, musamman akan kasuwancina dan yanzu auren nan ta hanyarsa muke ci muna sha shine kasuwancina kuma kowa yasanni akan Business ba mutunci zan iya ja da kowa.


41-45


Official


By
AsmaBaffa


MMN BASMA,SALMAT BASHEER,SUBYUSMAN ga page na baku Sabo da kauna ina Godiya.

Gaisuwa cikin Trailer zuwa ga
HAFSAT KHAIRAN
OUM FAROUG
MUM SUHAIL
MAMAN HAIDAR
HAJIYA JAMILA
MAIMOUNA MATER ta NIGER.

    Kuna Raina
MEENAL SIDI
YA SALAM
DJU LUV
NANA KHADIJAH
OUM SALM@
  Ina jinjina muku da Sharhi na gode.


    Bayan na gama gyara gidan kaf ko ina yana sheki da kamshi,tuwon danyar shinkafa nayi tare da miyar egusi harda naman Kaza Sabo da a kwai a fridge,a dining na shirya mana komai cikin Food flask masu shegen kyau,wanka nayi na shirya cikin material cotton riga da skert nayi kyau sai ka rantse me tsada ne,dan Mayafi kawai na Sa a saman kaina wanda yasha gyara,1:30pm Sabo da a motar gida ne ba bata lokaci sai ga su Meenat sun dawo suna kwala min kira,Ku karaso mana ina ciki kuma sai kirana kukeyi,Sis yanzu muka ga Yaya Aayan a Compound su Abbi sun sashi a tsakiya tare da tsohuwar nan kakarsu sai masifa suke masa,ko saurararsu baiyi ba kawai jinsu yakeyi,Baki na tabe nace saji dashi can kuje kuyi shirin Islamiyya ga abinci nan a Dining,Bari na kira Malam Garba ya karbi abinci yaci sai muje unguwa, a waya na kirashi ya shugo na bashi abinci a flask dama na ware masa nasa daban Aiko yaji dadi sai murna da godiya yakeyi don ba a basu abincin gidan yan aiki suke burkuta musu ko wanne kwamacala ko dadi babu,fita yayi yaci ya koshi sannan ya kawo min flask din,nace in ba damuwa mu fita ka kaini unguwa,yace ai ba matsala,kudi na zuba a jakata na yafa gyale na me dan girma kalar kayana,can na hango dandazon Family ana meeting akaina irin yanda za a dauki mataki a kaina,Aayan yana zaune gefe yana latsa waya,kamar ance ya dago muka hada ido dashi, hannu kawai na daga masa irin na fita,baki ya tabe irin ina ruwansa,bayan tsadajjiyar motarmu na shiga na wani lafe a kujera ina game da yar Nokia ta wacce dan gidan Comissionar ya bani ,wata Aisha  College nace ya kaini kana na Yiwa Malam Garba bayanin ya Zama wakilina a matsayin Babana ya kawo ni schl nan na tsara masa komai,yace ba damuwa yata.

    Schl din 2 to 5 pm ce yare biyu akeyi Arabic da boko,Kafin ka gamata ka kware wajen Turanci da larabci tare da Sauran karatun addini dana boko,tana da kyau sosai,bayan munje wajen Pc mun masa bayani yace kinci Sa'a saura kwana Uku mu rufe daukan student na wannan shekarar,da kansa Yamin tambayoyi a lokacin na nutsu na Bada amsar wasu wasu na fadi,yace Ss1 zai sani nace to na gode,haka na biya 15k kudin schl fees,na Bada kudin Uniform har kala Hudu,sai kudin littatafai,nace Ina da aure ayi min Hijab me dan girma,haka aka gwada Size dina da komai na mikawa Malam Garba kudin ya biya a matsayin shine Ubana,aka Sa min sunana Mufeeda Adam Fatima yanda muke amfani dashi.

   Bamu zarce ko ina ba sai inda ake siyar da schl bags da su Sandals na siya kala Hudu hudu suma tare da Sauran kayan karatu da komai,komai me kyau me tsada na siya,muna Tafiya a mota naga masu saida Glass na fuska,nace ya tsaya na siya,haka na zabi maka makan glass na yan gayu na gwada sunmin masifar kyau,da baki,da Brown sai farare biyu wanda ake yayi na zamani latest,yanda suka min kyau ba a magana,tun a motar na kara gyara fuskata na sa bakin nan faskeke kowa ya kalleni sai ya kara ya min kyau gashi kuma No respect.

    Yanda na fita na barsu haka na dawo na samesu ana ta maganganu an hana kowa tafiya tsohuwar banza tana ta isa da Mulki ita ke magana har da wata jaka ta yan mata a gabanta wai itama fa bata tsufa ba,ganin suna wajen koda mukayi parking ban fito da wuri ba sai da na dauki lokaci yanda naga Aayan yana yi,sannan na zuro kafa daya da sabon cokeken takalmina me tsada dana siyo a wajen masu takalma na ganshi ya birgeni Dubu Bakwai na siya da jakarsa me kyau,irin zanen dake jikin material din Golden,ba wani iya tafiya nayi da me tsini ba amma karfin Hali yasa nace ai dole a je damu muma,ina fitowa sai da kowa ya Bini da kallon kurilla,yanda naci uban acuci da gashina kuma ba dankwali na daura ba kawai gyalen me dan girma da dan kaurinsa na mutunci na yafa a kaina sannan ga glass dina,Malam Garba ne ya kwaso min kayan a ledojin store din dana je,karba nayi nace na gode kaje kawai Baba sai zuwa bayan Magrib zamu fita again sabo da zamuje shopping da kannena na,yace ba matsala Allah ya kaimu,nace Ameen sannan na bashi Dubu Dubu biyu nace a saiwa iyali Alawa,ya dinga godiya nace No Need Baba Ai ba komai.
   
   Su kuma dangin Aayan tunaninsu wasu kudi Aayan ya fara sakar min yanzu,nan take bakin ciki ya rufe su,musamman yan matan nan yau daya sunga na fara komawa wata Baturiya, Aayan yana ganin irin tafiyar da nakeyi ni ga yan mata,kwas kwas na cuno lips gaba irin yar gayun nan,nazo ta gabansu na makale Murya tare da Sallama ba wanda ya amsa nima ban damu ba dama na sani,na matsa kusa da Aayan yana zaune na sunkuya tare da rada masa taso Kaci abinci tuwo ne nasan kana ci ko? Yace zanzo kije yanzu magana akeyi min na Family,nace wanne family? anan tashi mu tafi ni dan Allah wannan har wasu dangin kirki ne,Yana so ya Harareni ko ya min rashin mutunci amma ba Hali sabo da Idan ya min haka zasu gano gaskiya sannan zasu kara wulakanta mu.ganin yaki tashi still ina tsugunne a gabansa nace ko tsoro kakeji? Naga Alama wlh tsoronsu kakeji muje ni zan tare ma fadan ko me za suyi ma zan amshe ma,tsaki yaja kadan tare da mikewa yace muje naga kin fara rainani dan kinga ina sakar miki fuska,ko kallonsu baiyi ba suka ga na janyeshi munyi tafiyarmu,Hajja makirar Tsohuwa tace kar kowa ya masa magana Ku kyaleshi ai Ubansa ya isa dashi zan yi maganinsu,kowa yaje yasha sha'aninsa zan nemeku,

   Haneefa tace wannan kwai tsinanniyar Yarinya wlh,Allah ya dau ran shegiya a huta da yar Iska,Dayar a ciki tace shike nan na kasa cika burina sai da nace wa Abbi yasa Aayan ya Aureni yace baya so naje na fada sonsa na kasa cika masa burinsa,Sauran yan matan suka ce ke dai bari ai Allah ya yarda sai an saki yarinyar nan shegiya ko Nono bata dashi bata fi 16yrs ba fa,Ameer yace 17yrs take amma wlh ta iya girki dan baku jiba ne gata me kyau da tsafta inama ni na aureta,ai ni wannan ko Haihuwa nawa tayi burina Aayan ya saketa ko ta halin yaya sai na aureta,Dariya sukayi dukkansu suka tafa da yan matan,Khaleel yace mayen mata yaga kayan Dadi kana jin Aayan zai kyale yarinyar nan ko Sufi ne shi? Ameer yace ina ai wlh ko abarshi bata motsi indai bata motsa akan yarinyar nan ba to ina tabbatar ma har abada babu kuma macen da zata gani ta motsa a kanta,Dariya suka kara shekewa da ita su Haneefa harda shewa,Mujaheed yace ka manta Aayan din yanzu ne fa dan bashi da lfy ya rage amma sha'awarsa ta kai karshe,jarababbe ne na karshe kullum cikin chargi yake baya Free dan bura uba ai yanzu ya gama da wannan yarinyar fitsararriya sai shegen baki kamar gidan tsutsa,Ameer yace ai zaiyi dadi ne lips din,Haneefa tace Ameer da Alama ka kyasa fa,yace tuni ni wlh sabo da ita nake shiga part dinsa so nake ko hannunta ne watarana dole na shafa dole sai mun raba jikin nan nata da Aayan,Mujaheed ya jinjina kai to ka dai bi a hankali kasan halinsa wlh kana ganin kamar baya damuwa ana abu kasan ba a taba masa mata ko zai shekara dubu bai taba abarsa ba indai wani ya taba masa mata wlh yaki kawai za ayi gidan nan,dan kasan shegen akwai kare mutuncin iyali,za kaga kamar bai damu ba yana sani kai kasan yanda Khaleel sukayi akan matarsa Bilkisu wacce Daddynsa ya fara aura masa Sabo da karfin sha'awarsa aka masa aure da wuri tun bai gama Degree ba,kuma duk da haka bai ko taba jikin Amaryar ba ya gano cewar da yarinyarka ce tun tana waje kuma kun sheke da ita,ya akayi farko sanda kake zuwa har Bedroom dinta kuna shoshalewa ya sani Amma ya muku banza kalli dai irin yanda ya gasa mata aya a hannu ga na Family sannan kuma ya mata saki mafi muni,sai a lokacin muka san ko yatsanta bai taba rikewa ba,hmm kai dai bari ashe matsiyacin ya sani tuni,Ameer yace ai ni so nake ma na kulla mata sharrin da zai saketa ni kuma na koma wajenta,ina nan ina hada mission dina.

    Ni kuwa tare muka jera muka shiga ciki ba wanda yayiwa wani magana ya wuce Bedroom a matukar gajiye,nima na samu su Meenat basu dawo daga Islamiyya ba,a gurguje na cire mayafin da glass dina tare da takalmin,na dauki kayan gaba daya nayi saman Aayan dasu,sai da na shiga naji karar ruwa yana wanka,ajiye ledojin nayi na koma tare da kawo masa abincin na ajiye,ina Zaune ya fito daure da dan Towel yana goge jikinsa da wani karami a hannunsa,kaina na dukar kasa ina wasa da yatsuna ban dago ba,shi kuwa ko a jikinsa har ya gama shirinsa sai kamshi naji yana tashi,ina dagowa naganshi Sanye da 3qrt da t-shirt yasha kyau yana jikin Mirror yana gyara gashinsa,na kalli Namiji yanda yake ta shafa man gashi masu tsada kala kala yana tajewa, sabo da bana gani na kyale nace to ai ya isa haka wannan ai sai ka karar dashi da wuri kunfi so kuyi ta asarar kudi amma wannan shanana mayuka da kake haka ko Mace albarka,naga ya bude wani kala yana fesawa shuuuu,na Mike nace dan Allah ka barshi haka yanzu idan kasa kadan ka adana abinka gobe ma ai sai ka dauka ka sa amma rana daya ka kusa karar dasu a dinga tausayawa kudin mana.

   Kawo na karasa ma,ya fisge abinsa,nace nafa iya naka ma da yake na maza da wuri zan gyara ma shi kuma wlh ko fita kayi sai an San kana da mata,kasan shi gwauro idan ya fita tun daga shigarsa ake ganewa sabo da babu me nuna masa inda aka samu matsala,wani sai kaga gashi a wuyan rigarsa ya zuba,murmushi yayi Bai ce komai sai yace ai bakinki ne Gwauron gashi nan yi min naga iyawar taki kuma karki min da zafi,Ina murna nace ai nasan har kyauta yau sai kayi min,sunkuyawa yayi tare da miko min kan,nace zan gaji da wuri a haka,na zauna Saman Bed shi kuma na shimfida masa Sallaya  nace zauna ka gani ni da nake me kitso,Kamar bazai Zauna ba sai kuma ya zauna,na ware cinyoyi kamar zanwa wata kitso dai yace ke hade wannan cinyar taki kina period,nace sai na fasa ma dan zan maka shine zaka fada min magana.

    A hankali na dinga taje masa ina fesa masa abun gashin,sai wani lumshe ido yakeyi zaiyi bacci,nace kudi biyu zaka biya ga na gyaran gashi ga kuma na hannun mace yana taba ma kai kasan hannun mace daban ne sai an biya,wannan hannun naki kamar Dutse gwara na maza dashi,ni kaina ba wani yi nake ba kawai tajewa nakeyi ina wasa da gashin dama karya nake ban iya ba,bacci ne ya fara kwashe shi har na gama,nace na gama tashi ga abincin can,yana son yayi bacci na mika masa,yace Hannuna da Mai ban son tashi kisa spoon ki bani naci,ba da wani abu ya fada ba nima haka nasa spoon ina bashi har yaci ya koshi nace lemo zaka Sha?yace Ruwa ni ban fiye Shan lemo na kwali ba nafison fruits ko ruwa,ruwa na mika masa yasha,na kwashe komai na maida,su Meenat suna dawowa nace su shirya muje shopping,wanka muka Sha nasa doguwar rigar da Aayan ya bani nasa lokacin da ya kawoni wajen Family dinsa shiri mukayi sosai Meenat ce tayi mana kwalliya mun Sha kyau,mun fito nace suje jikin motar Driver yana can bari na fadawa Aayan.

   Knocking nayi masa sannan nayi Sallama na shiga yana zaune yau magazine yake karantawa,nace zamu fita Shopping,hannu kawai ya daga min irin muje kawai,katon store muka je munsha siyayya sosai da sosai,Cosmetics,shoes,bags,mayafai,jelweries,Night wears,sai atamfofi kala biyar biyar,shadda kala Uku uku,sai materials tare da laces suma,Ready made dogayen riguna da riga da skert,mayafai dasu Inner wears duka masu kyau yan tsakiya dan yan tsakiya za ace baza ace masu tsada na karshe ba kudin baza su kai ba,wajen telanmu muka wuce duk Wanda za a dinka muka bayar,lokacin har dare yayi kusan ma 8:30pm,nace yau ba girkin dare nace Baba Driver dan kaimu Yahooza suya sai murna su Meenat sukeyi,mukaje na fita na siya mana muka zauna inda aka tanada don Zama ga masu son ci a wajen,muka ci abinmu muka koshi tare da ice cream,na siyowa Aayan ma nasa harda kilishin da suke siyarwa, Malam Garba ma na bashi nasa harda shi na siyawa,ya dinga godiya da addua,

  Wasu sai kaga suna cin abu ma a gaban yan aikinsu wai baza a iya bashi yaci ba,bare aje dashi waje shima a dan siya masa ko kadan ne babu me kulasu Sabo da son kai su tunda talakawa ne suci irin nasu, 
     sai 9pm muka dawo gidan,a gurguje nayi wanka nasa rigar baccina kamar T-shirt take amma yar doguwa iya rabin cinya tsayinta,powder na murza nasa lipgloss  sai dan turare na Amtek na shafa na dauki Take away na Aayan na wuce Samansa.

     Da Sallama na shiga Yau ma yana saman Sallaya Sanye da Jallabiya yana karatun Qurani,ina zaune gefen Bed dinsa ya gama adduoin nasa sai lokacin ya juyo ya kalleni tare da cewa ya akayi? Ko ka tambaya mun dawo lfy? Gashi to na mika masa take Away,ledar ya bi da kallo sannan ya kalleni da baki ya nuna ledar tare da cewa bude na gani,da sauri na sakko kasa yace to Ustaziyya gyara Hijab din kina samun a fuska,Dariya nayi  kawai na tsuguna tare da bude masa ledar duk kamshinsa ya cika min hanci me dadi ji nake kamar na fada jikinsa na shako kamshin da yawa,na  bude yaga package na kilishi,daya ledar kuma Kazace da yawa tasha hadi,sai Fura da ruwa harda yoghurt,son jin dadi na da kwadayi na ya jinjina a ransa duk wata hanyar cin dadi na Santa har na iya na siyo masa wannan.

   Muryarsa naji yace ina naku?nace ai mu a wajen muka zauna muka ci Namu kawai sabo da nafi so muna dawowa yaran nan suyi bacci su kyaleni na huta,Murmushin da bai shirya ba ya saki gaba daya ya tafi da Imanina don idan yayi murmushi wani masifar kyau yake karawa na musamman,ke ba yaranki ba amma feeling kikeyi kamar yaranki ne kika haifa sai son girma,

    Fari nayi da Ido wanda ban san nayi ba nace ai ko Ammah na da rai nice kamar uwarsu,rufe wannan ledar bari na gyara farce na,nace au baka zuwa a yanke ma farce?yace a'a basa min yanda nake so ne a Abuja nakeyi ko kuma lokacin dana zauna a London,amma nan garin Sam nasu bai min ba tsoro ma nakeji kar su samin cuta,na kalleshi nace iyye kaji Manya Ashe har a London ka zauna uhm lallai dole kayi yanga,kallo na kawai yayi ya mike tare da dakko abun da yake yanke farcensa kalarsu ma daban ne, kawo na yanke ma kaji na iya sosai,Ba musu ya mika min na gyara Zama a gabansa, nace to fa sai ka koya min yanda ake amfani da kalar Nail cutter en nan ban gane ta ba, 

gwada min yayi tare da cewa indai kika lalata min Nails sai kin biyani farce na in dai bai min kyau ba,ae naji kawo kafar to, kafarsa na jawo wani mugun laushi ba duk mace ba, na daura saman cinyata da na rufe da hijab, na mika masa take Away din tare da cewa to ci mana, naman ya fara ci ni kuma na dukufa ina yanke masa Farce,yana ci yana latsa waya yana murmushi ko chat yakeyi oho, ji nayi yana dariya nace mu gani me kake gani na dariya haka,ba komai kawai yace, da na dan shigar da zafi zai ce karfa ki yanke min precious skin dina, wannan kayan da kika cike min Bedroom dasu fa,nace au na manta ne na schl ne na kawo ma ka gani na bashi Labarin komai gobe ma zan fara zuwa,ba sai na gani ba kawai ki kwashe abinki,nace to ba damuwa.

    Ina gama yanke masa na kafa ya gama cin abincin nasa,hannu ya goge da tissu ya miko min yatsun hannu masu shegen kyau dasu,na fara gyara masa farce ina cewa Dazu mun siyo kayan mun kai wasu dinki,du na karar da kudin Dubu  uku ce kawai ta rage.

    Ok yace ke kika bawa Malam Garba Abinci? Nace ae har ba dare ma,ya min waya yana ta godiya Ashe kina da hankali dai? Murmushi nayi nace Kai wai nufinka bani da hankali?to ba karamin Hankali da wayo ne dani ba,yace sai dai kiyi wa wani wayon na ki,harda kai ma zan mawa,Sau nawa nayi ma wayo kaine dai baza ka gane ba,a ransa yace lallai yarinya zan nuna miki baki da wayo soon,ina gama masa ya kalli yatsun tare da cewa uhm ba laifi,toilet ya fada yayi Brush dama yayi wanka kaya ya canja zuwa na bacci,yana fitowa yaga na kwashe kayan dana kawo du na tafi dasu,light ya kashe ya kwanta abinsa tare da Addua.

    Washe gari ina gama aikace aikace na shiri nayi cikin riga da skert English wear nayi kyau na yafa mayafi na fita na tafi har part din Daddyn Aayan,securities basu barni na shiga ba sai da suka sanar masa matar Aayan ce yace daga yau indai itace a barta ta shigo kawai.
    a saman Bed dinsa na ganshi an canja masa kaya yana kwance abinsa,cike da ladabi na durkusa har kasa na gaida shi ya amsa da fara'a,daga nan yace zauna ya ta,a gefen gadon na zauna,nace Daddy da har zan kawo ma abinci na tuna Ya Aayan yace ba komai kake ci ba,murmushi yayi tare da cewa ae ni abu me ruwa nake ci sai kuma vegetables sai ko snacks amma duk sauran abinci basu Dameni ba,tun farko haka nake ni dama abincinmu na Hausawa basu Dameni ba sai Fura da Kunu kawai amma na turawa nake ci,me girki na ma daban take yata,nace Daddy shi kuma Aayan ko yana  yaro amma na Hausawa gargajiya yafi so,yace ai wannan kyaleshi kawai Uwarsa ya gado ta nan.

   Kuna zaune lfy dai ko?ae Daddy lfy Alhmdllh,to idan ya miki wani abu kizo ki fada min kinji,nace to,idan kin samu lokaci kizo watarana zan baki labarin tarihin gidan nan namu kaf sabo da ki koyi Zama dasu,ranar da bani da schl zanzo,Allah ya kaimu,na mike nace na tafi zanje makaranta,yace na gode Mufeeda Allah ya taimaka,na fito a hanyar dawowa part dinmu na hadu da Ameer a hanya yana kallona zan wuce amma yaki matsawa sai ma hanyata da ya kara tarewa,na kasa gane masa kawai na matsa can na wuce abina tare da ja masa tsaki,a ransa yace zanyi maganinki.

    1:30pm ina bedroom na fara shirin zuwa schl ina cikin sa sabon Uniform dina sai naji knocking ba zato,da sauri na zura hijab dina na fito da tunanin ko Aayan ne ya dawo to in ba shi ba waye zai min knocking a Bedroom,ina fitowa naga Dan iskan nan Ameer, ina ina ya fara ahm...ahm...abinci zaki bani,harara na maka masa nace banyi da kai ba don ba auro ni akayi dan na dafa ma abinci ba,na koma Bedroom tare da sa key,abin nasa ya fara tsoratani tun daga irin kallon da yake Bina dashi.

    Cikin Uniform na fito ba karamin kyau nayi ba black and white komai nawa har jaka da takalmi kowa ya kalleni a uniform din sai ya kara nayi matukar kyau,Sallamar su Meenat naji Ma'eesha tana Faman Kuka,lfy Ma'eesha ina Meenat din na ganki ke daya,Sis wannan matan ne suka Mareni kuma ga Meenat can a Compound wai shoe  maker ya tareta wai sonta yakeyi,wanne kuma me wankin talkami, wannan su Haneefa yake wankewa takalmin schl baki ganshi ba cikinsa kato hannunsa da jikinsa siriri kamar tsinke cikinsa kuwa katon gaske kamar zai fashe,sunce wai Meenat sai ta kulashi dole.

    To shine kike mana kuka haka,to ai marina wannan Haneefa din tayi akan nace Meenat tazo mu tafi,ok wuce kiyi wanka ga abinci nan a Dining na tafi schl ni daga can zanga Meenat,maza Ku fara shirin Islamiyya,Bye Sis nace Bye, na fita rataye da jakata,saida nayi tafiya kadan sannan na Iske Meenat Tsaye tare da wannan mutumin me gyaran takalmi,ni tunda na ganshi ma dariya ta kamani don cikinsa girmansa ya isa ga jikinsa siriri kamar a bushe shi ya fadi,su Haneefa suna zaune suna faman latsa waya.

   A fusace na karasa wajensu nace Malam mene haka lfy kazo ka tare min yarinya anan ko kunya baka ji idan kudin magani kake nema ai sai kayi magana a baka kaje Hospital,Meenat tace ba ke bace Sis nace ki bamu dama amma kince kar mu kula su ko me zasuyi mana dole kece zakiyi kawai,Yan matan nan ne suka taso kanmu,ke wace da zamuce ayi abu kice zaki hana wannan ya gani yana so kuma dole ta kulashi in dai tana gidan nan,sabo da shine dai dai ita,Haneefa tace au Ku nan har kunfi karfin wannan kuna yayan talakawa,dama kadan nake jira Mari lafiyayye na zabgawa Haneefa dama kin Marar min kanwa wlh ba wanda ya isa ya taba mana lfy ya kwana lfy,nasan in suka hadu zaneni zasuyi Marin ma da kyar nayi ta maza na shammaceta na fesa mata shi, Cikinsu Sukace KWAJA jeka ka dawo gobe dole sai ka auri wannan suka nuna Meenat,Meenat tayi dariya tare da cewa au dama sunanka KWAJA? Lallai Kaci sunanka ta kara sakin dariya,nace wuce to ciki yar iska idan kika kara tsayawa dashi wlh zan miki rashin mutunci,to ba ke kikace kar na dau mataki Kansu ba,motocin Aayan ne suka shigo ya hango Su Haneefa sun rike min Hijab gashi nayi kyau, har gabanmu yazo yace sake min mata yana gyara wayar Usb da ya Ciro a motarsa,Haneefa ya damko ya dinga tsula mata wayar tana kuka da ihu,su kuwa sauran tuni sun Arce,wlh duk ranar da kuka kara taba jikin matana sai na kusa kasheku a gidan nan kuma kinsan ba abinda zai faru,nasan kin san da haka,kallona yayi tare da takowa wajena zai damko ni nima na kwashe da gudu,ya biyo ni taku biyu ya damko ni Ransa a bace ya kalleni ido da ido sai yayi murmushi matsoraciya yi mata dariya zance shine kika gudu,aiko Nace Haneefa tana Kallona  na kyalkyale da dariya nace wooo ayi mata gwalo,Aayan yace fara frog jump dan ubanki kafin nazo nan na halaka ki,da Sauri ta fara yi,yace yi mata dariya ke kuma Aiko na dinga yi ina wooo harda tsalle,muna Haka sai ga Hajja kakarsu ta fito kamar zata make mutane,Aayan yace jeki schl tana cewa tsaya dan ubanki Karuwa Amma ko kallonta banyi ba na shige mota abina Malam Garba yaja,ta glass tana Kallona ina kallonta na mata gwalo,Aayan ya daga min hannu bye,tana zuwa ta daga hannu da niyyar sharawa Aayan Mari ya rike hannun caraf tare da matsar da ita gefe ya wuce ya bata waje bai ce kala ba,Kuka da kara tare da ihu ta fara yi a gaban yan aiki,Sai ga Abbi yana huci an taba Uwarsa.

    Tunda na fara zuwa schl yau Sati guda kenan lfy nake zuwa ina dawowa abina cikin jin dadi,haka su Meenat ma,Aayan kuwa tun daga ranar da ya Zane Haneefa ban kara ganin Sa a gidan ba,ashe wai ya tafi Umrah Saudiya bamu sani ba sam,koda kudina suka kare Bedroom dinsa na shiga na duba inda yake ajiye kudi na ebi dubu biyar idan ya dawo sai na fada masa.
  A schl dinmu har kawa nayi yar gayu wayayya MARYAM ga hankali ga sanin ya kamata,kullim tunda taji ina da aure take fada min yanda ake Tafiya da Imanin me gida,nace ai ni kullum da Hijab nake zama a gida idan zanje unguwa ne nake Sa mayafi watarana,aiko ta dinga dariya tana wayar dani ni kuwa dan kar ma Aayan yace Dan shi nakeyi nace ko Ya dawo bazanyi ba.

    Yau da yamma su Meenat sun dawo kenan daga Islamiyya KWAJA me gyaran takalmi ya biyota tun daga wajen gate,dama su Haneefa sun fadawa Securities in dai Kwaja ne a barshi ya dinga shigowa yana da budurwa a gidan bayan haka ma yana goge musu takalmin schl.
    Direct Kwaja ya shigo yana wargaje baki da wata falkekiyar T-shirt,hannun rigar Sabo da ramarsa kamar skert hannu tsilili a ciki, kansa har wasu jijiyoyine ke tashi kamar me kwoshokwo, wuyansa kamar mirkin laima,dan kirjinsa kuwa kamar Allo,hakoransa guda biyu manya a waje na gaba,bakinsa yake dargajewa shi tunaninsa ai dole ma ya auri Meenat tunda yayyenta sunce sun bashi ita.
     ta window din sama Na hangosu yana tsaida Meenat yana Meenatu Meenatu yan mata dan Allah ki tsaya,haba Meenatu so kike sonki ya kashe ni? Meenat ta ja tsaki tare da hararsa Malam Kaja mituncinka mun san darajar Dan Adam shi yasa nake daga ma kafa Amma tunda kaki ji zaka ga abinda zanma.
    Kwaja yace ko me zaki min ni Bazan ji haushiba tunda ina sonki,da wlh ba da gaske nake ba Amma na yaba da hankalinki da nutsuwarki,gaki kyakyawa ni yanzu ba zancen yayyanki nake bi ba wannan da gaske ne daga makwallaton zuciyata a daina maganar wasa, to bana sonka kaja Life dinka ka kara gaba Malam cewar Meenat,Murmushi yayi yace yan mata bani da Lifan ni bana karya dan a soni,karki kiyi tunanin Ina da Lifan kice Naja Lifan dina na tafi wlh Allah ko Keke bani dashi idan zaki soni ki soni dan Allah nasan ku manya ne kun wuce ayi muku karya,Takaici ya kama Meenat tace ina ruwana da karyarka ka ja rayuwarka kayi Out a gidan nan,Haushi KWAJA yaji yace na fuskanci Ku kunfi son dan karya azo ana muku birga da mota kullum idan nazo zance na baki Dubu daya ko Dubu daya da Dari biyar koma fiye da haka,to ni ba haka nake ba gaskiya da gaskiya nakeyi wlh da zaki aureni kullum sai na dinga siyo miki kifin gona kina soya mana,watarana ma Miyar zabo zaki dinga yi mana,Taliyarmu  guda da macaroni da wake gongoni guda ya ishemu na na kwana hudu zuwa biyar, tsaki Meenat taja tayi gaba ta barshi nan,ina jikin Window  ta sama ina ta dariya gaskiya Su Haneefa yan Iska ne,Meenat ta shigo na dinga mata dariya,nace Allah sarki kanwata duk iya kwalliyar nan kuma taki sai ki kare a KWAJA tumburarre,Dariya tayi itama tare da cewa ai Allah ya tsinewa su Haneefa yanzu idan nayi wani Saurayin yazo ya ganni da wannan ai wlh rainani kawai zaiyi ya daina zuwa,ina ta dariya harda kwalla Meenat tace dan Allah ki daina,har dare muka kwanta ko farkawa nayi sai nace ta KWAJA tashi na baku lbr,banza tayi min tace wlh sai na fadawa mijinki idan ya dawo tunda haka kike min.

     Yau nayi shiri tsab ba schl zanje wurin Daddyn Aayan ya bani labarin gidan nan da yace zai bani,koda naje  Sallah ya idar daga kwancen,yana murmushi muka gaisa,nace Daddy yau na shirya a bani Tarihin naku. Yace to yata bude kunnuwanki kiji.

      
     Next page is very Important readers ku tsaya ku karanta da kyau shine zamu san waye Aayan.


AsmaBaffa
Reply
#5
46-50

Official


By
AsmaBaffa


Page naku ne MADINA ALEEYU
MAMAN SAMHA
NAJA'ATU ALIYU

Jinjina gareku na wajena
MOMMY ARFAT
AYFA
MARYERM MUHD
HAJARANCY
HAULATU KAMBA
QUEEN KK


Zaune nake na nutsu Daddy ya fara bani labari,
 Mu yan Asalin Kasar Algeria ne sabo Dama kasar suna da yawan farare duk kusan larabawa jar fata,har yau muna da ragowar dangi acan kawai zumunci ne da yayi karanci yanzu bama yi dasu suma haka,Babana Mahaifi kakan  Aayan shine Jabeer Muhd Jabeer tunda suke dama su masu kudi ne sun gaji dukiya me tarin yawa,a tarihinsa kaf  ba aji talaka a jininsu ba tun zamani me tsawo,komai sun hada ilmin boko da kasuwanci,Jabeer Muhd Jabeer Allah ya Yoshi me son yawon zaga duniya har Allah ya kawoshi Nigeria can cikin wani dajin Fulani dake Taraba sunje yawon bude ido a rugar fulanin Allah ya hada shi da Mahaifiyarmu Hajja kenan wacce kike gani a gidan nan tana zuba mulki sunanta Karimatu,Karimatu Hajja basu gaji arziki ba don a rugar ma su talakawa na karshe,Allah yayo su da son kai tare da son abin duniya ga tsafi da bin Malamai,Sau daya suka hadu da Jabeer taga yana da dukiya dama bata da burin da ya wuce ta auri me kudi wanda zai kaita kasar waje su zauna,tun daga tambayarta ina ne gidan me gari shike nan ta koma gida ta sanarwa Babarta cewa taga wani tana so Bature ne,sunansa Jabeer,nan Babarta Larai ta shirya sai gidan bokanta,Lokacin Jabeer ya bar kasar nan ma Nigeria yana Ghana,yaji son Karimatu ya shigeshi babu bata lokaci ya dawo a gigice sabo da tsafin da suka masa,yana zuwa da maganar Aure Larai da mijinta Usmanu Baban Hajja suka amince sabo da son abin duniya.

    Ko dangin Jabeer babu sai wakili aka yi masa a kauyen aka daura Auren Karimatu Hajja da Jabeer,sabo da aikin bokanci ya tafi da ita Algeria sunyi shekara daya ya dauketa suka koma London inda a nan aka samu Cikina ta Haifeni naci sunan kakana Muhd,ana kirana Muhd Jabeer Jabeer, a London na taso cikin Jin dadi gata tare da kwanciyar hankali,ga ilmi sosai na zamani dana Islama,sabo da Babana akwai son Musulunci,y anda ta mallake Babana yasa take masa abinda taga dama,wulakanci iri iri da cin mutunci,tana ta sace masa dukiya da kadarori amma duk da haka arzikinsa karuwa yake,ita kuma tana ta sace wasu tana adanawa.

    Bayan na kwashe shekaru biyar a duniya asirin da Babata Karimatu Hajja tayiwa Jabeer Babana ya karye,nan fa Jabeer yace Bai San zance ba baya son Hajja,ya dinga wulakantata,gashi sabo da kudi bata so su rabu tana kasar waje tana cin daula,haka take jure wulakancinsa sabo da kudi har ya kara Aure ya auri Masoyiyarsa Hafsat Balarabiyar kasar Jordan,mata ta gari suna zamansu lfy tana sonsa tsakani da Allah ba irin mahaifiyata ba da son kudine kawai,a haka take zaune har ma abin yaci tura ya saketa saki har uku,sabo da ta Saci kudi da yawa yasa ta san yanda zata yi dan kar ma a gano ta sai tattara ta gudo Nigeria da dunbin dukiya a wancan zamanin.

       Ni kuma ina wajen Babana hannun Hafsat Balarabiyar matarsa ta Jordan tana rikeni Amana da gaskiya,tun kuma daga kaina Babana bai sake haihuwa ba har aure ya kara amma Bai kuma haihuwa ba a duniya,bayan shekara Uku da sakin Karimatu ta samu wani mutum da take matukar Kauna da gaske amma bashi da ko sisi can cikin wani kauye yake shima a Taraba state Fulani ne sosai,sabo da tana sonsa ta gina katafaren gida na more rayuwa a cikin birnin Taraba,ta aure shi suke zaune tare da shi.

       Dama ni bata son Babana sai don kudinsa,bare da asiri ya karye ya wulakantata sai ta kara tsanarsa bata da makiyi sama dashi sabo da kudin basu isheta ba tafi so ta yashe shi tas, sabo da wannan har ni da ta Haifa ta tsaneni kiyayyar Mahaifi ce ta shafeni nima bata kaunata da abinda ya shafeni, shekara biyu da auren Yusuf ta Haifi danta dashi Namiji Mustapha shine da kike ji ana ce Masa Abbi a gidan nan, bayan 2yrs ta kara Haifar kaninsa Sani shine zaki ji ana ce Masa Abbin Ameer, sai dan Autanta Awwal  shine Abbin Khaleel  tare da kannensu. tana ta juya dukiyarta amma basa wani karuwa sosai sai rufin asiri,Katsam Mijinta sai ya rasu Baban su Abbi kenan,ita ta Sha wahala dasu ta dauki nauyin karatunsu har iya Secondary da komai sabo da tana masifar sonsu kamar ranta sabo da yanda take kaunar Mahaifinsu,ni kuwa Abbin London kenan ko waiwayenmu bata kara yi ba,har dai iyayenta suka rasu sai dangi,haka Iyayen Babana ma sai dangi ana ta karewa.
     Na gama Degree da Masters dina duk muna London,Babana yana ji dani sabo ni kadai gareshi,Har ya hadani Aure da wata budurwa Balarabiya yar Jordan cikin yan uwan matarsa Hafsat lokacin ya Damka min dukiyarsa baki daya da komai ga kuma aikina ina yi,na zama hamshakin me kudin da nayi suna a duniya kaf a wancan lokaci,Muna zaune lfy da Matata Asiya Wacce ta Haifar min Dan Albarka na Da daya tamkar da dubu Aayan kenan,dukkanmu a london muke rayuwa,har Aayan ya gama Primary lokacin kuma Su Abbi su Uku suma da matansu sun Haifi yaransu Maza,Abbi Mustapha mijin Hajiya Saratu Mami shine Baban Mujaheed,Haneefa,Sajeeda,da kuma Minal karamar yarinya,Awwal mijin Hajiya Zarah Ummi suna da Yara su kuma Biyar Khaleel,Farida mate din su Haneefa shegu Uku,Maryam,Nura sai dan Auta yaro mate din Minal wato Ahmad. Sani mijin Hajiya Haleema Anty yaransu uku Ameer fitinanne, Zahraddeen dan Wiwi,sai Yusrah.

     Yanda iyayensu suke da hadin kai haka suma yaransu suke da hadin kai ba a jin kansu, Sabo da Hajja ko yaro taga yana bijire mata sai ta tafi gidan boka ta kai sunansa cewar Danta wane baya jin maganarta ayi masa magani ya koma sai yanda tayi dashi,haka Matan yayanta ta gama dasu sai abinda tace,jikokinta ma haka, ni ne kadai da Dana muka gagareta, kuma a halin yanzu hausawa haka suka koma,wai ko dane sai iyaye suyi masa asiri su mallake abinsu sai abinda suka ce,sai kaji ana in ka zauna yanzu zaki haifawa wata ta gaje miki da,ko shaye shaye,ko dai wani banza idan yana yi maimakon ayi masa addua wai sai a tafi gidan malam,dana wane ko Ya ta na rasa yanda zanyi tana Kaza a canja mata ra'ayi,ko miji ne bata son auren sai iyaye su kai sunanta kaga kawai ta koma sonsa,yana karyewa kuma shike nan Allah kyauta.

kin san yaro tarbiyyar daka dorashi da ita zai tashi,ni da Dana da basa sonmu har yayansu basa sonmu,shi yasa ko yaro yana ma kallon Banza maybe sunji iyayen su sunce wani abu a kanka,wasu ma in kaga suna daraja ka to iyayensu ke yabonka gabansu a kula iyaye,daga kun samu matsala da yan uwanki ki kwashe ki fadawa Yara wane dan uwana ko yar uwata tayi min Kaza sai kiga har abada baza su sota ba,ko kin dawo kin gyara bazai gyaru ba,a guji gulma da zagin yan Uwa da mutane gaban Yara.har Matan su Abbi basa kaunarmu kuma nine nake musu komai na rayuwa har daukan Nauyin karatun yaransu da komai na duniya har yau har gobe har yanzu da aka kawoki gidan nan yata.
    Lokacin da Aayan yana secondary ya gama lokacin Allah ya karbi rayuwar Jabeer Babana tare da matarsa Hafsat sunyi Hatsari a jirgin sama.

    Muna zamanmu da Dana har ya shiga University lokacin Nazo Nigeria neman Mahaifiyata Hajja don Babana ya bani Address kafin ya rasu,bata yi wani farin ciki ba Amma ganin nine yanzu me kudin sai ta saki kuka tace dole sai mun dawo Nigeria da iyalina ko ta tsine min nabi duniya,ba yanda zanyi da dukiyata da komai nawa na dawo Nigeria tare da Gina katafaren gidaje har Biyu a  Abuja nace daya na dana Aayan daya nawa,ga motoci na Alfarma,har karatun Sojoji nayi shi yasa kike ganinmu da Securities a gidan nan harda jiniya in ta kama Sabo da nayi aikin soja na shekara Uku a kasar nan da Babban matsayi Sabo da tun ina yaro soja nake so shi yasa nayi aikin.

     Ni da Matata Asiya mun dawo Nigeria dasu Hajja tare da kannena su Abbi duk na kwashe mu muka koma katafaren gidana dake Abuja,kudin Hajja data sata sun kare dama,ni na dauki nauyin su Abbi duk da sun girma suma da iyalansu sai da na Sa su sukayi Degree,na basu aiki a Company na nake biyansu albashi me tsoka,na siya musu motoci still ban fasa daukan nauyin iyalansu ba,amma sam ko me nayi musu basa taba Cemin ko an gode hasali ma sai daí su nuna bana musu komai a duniya,ko yaushe burinsu suga na tsiyace na talauce,burinsu ace a cikinsu ne daya yake da wannan arziki,haka Hajja ma komai nine me laifi su basa taba yin laifi Sabo su take so,abu kadan in nayi zata fara zagina,tana min baki,amma su ko me zasuyi baza ta musu Fada ba,kullum burinsu su ganni cikin halin bala'i, ba irin asirin da basuyi min ba Sabo da na talauce su gaje dukiyata Amma Sabo da karfin addua tare da tsoron Allah da kyakyawar zuciya,bana nufin kowa da sharri,bana shirka sai Allah ya kareni duk abinda zasuyi a banza,tunda na gane halinsu na dage da addua,ita kanta Hajja bata so ace nine me kudi ba cikin yaranta ta fi so ace Awwal,Sani ko Mustapha sune masu kudin ba ni ba,sabo da dama bata so na da ubana kuma bugu da kari ba ita ta raineni ba, sam babu wannan shakuwar ta raino tsakanin Uwa da Danta,nima ban damu da ita ba nafi son matar Babana Hafsat data rasu nafi Jinta a raina Sabo da mun shaku ta rikeni da Amana.

    Makirci kulla tsiya ba wacce basa min,har Hajja ke Goya musu baya ana bin malamai akan dukiyata ta koma wajensu,kawai dai Hajja bata yarda ayi min asiri na cutar da lfy ta ba,tace duk da haka ni Danta ne na cikinta ko bayan ranta idan suka cutar da lfy ta ko raina bata yafe ba,duk abinda zasuyi na karbe dukiyata sunyi Amma ba abinda ya faru,su kuma Sabo da ita tasha wahalarsu suna jin maganarta amma shedan yafi karfin zuciyarsu don  ko taya ma so suke suga bayana,hassada suke min ta gaske,ni kuma da yake dama a goge nake na waye nasan me nakeyi bana kulasu duk wata hanya na tosheta wacce zasu iya samun dukiyar tawa ko kadan ne sai daí in ni na basu da kaina, Aayan yaro ne me hakuri da kawaici tare da danne bacin rai Amma ta wani fannin yana da zafin zuciya,tun yana secondary na fuskanci yana da karfin sha'awa har cuta yake kwanciya a asibiti Sabo da sha'awa.

    Saura shekara daya ya gama Degree a London mu muna Nigeria lokacin Hajja su Abbi sun zugata dole tace sai na dawo da Aayan Nigeria nayi masa aure mun zauna gaba daya Sabo da suna bakin ciki shi yana waje yaransu basa kasar waje bayan har saudiya da Dubai na kai yaransu sosai baki daya,da kudinsu ma suna fita kasashe suke duk ta silar arzikina, Asiya Matata kullum cikin kuntata mata suke tana ta hakuri har Mari tasha a wajen Su Abbi ban taba ce musu komai ba,wahala ba wacce bata gani ba,duk aikin gidan nan na abinci ita ke dafawa shi yasa ta iya girkin hausawa sosai,Hajja ta wahalar da ita sosai  tare da matan su Abbi suka hade mata kai kamar zasu kasheta kullum kalar abinda zasuyi mata daban.

    Ganin matsalar Aayan ta sha'awa gashi kyakyawan gaske kuma tana turai ina tsoro kar ya lalace sai na yarda nace ya fito da mata zan aura masa idan ya karasa Degree ya dawo Nigeria,ya kawo min wata musluma yar turkysh yana so,Amma Sai Hajja tace ban isa ba idan har na aura masa ita bata yafe min ba,nayi masa bayani ban boye ba,da yake Aayan akwai biyayya sai yace ya hakura to kar mamana tayi fushi da ubansa.

   Su Abbi ne suka zuga idan Aayan ya auri Jar fata zamu kara yin kudi mufi haka arziki,dan danan suka nemo wata budurwa kyakyawa Bilkisu yar gidan Minister itama budurwar Khaleel ce,suka hada baki dasu Abbi domin a aurawa Aayan sai ta san yanda zatayi ta yashe mu tas,koda suka ce ga mata sun samowa Aayan sai da na bincinka na tabbatar ba yarinyar kirki bace Amma Hajja tace sai an aura masa ko ta tsine min,haka na hakura aka daura auren Bilkisu da Aayan yana London nace Hajja tayi hakuri Bilkisu tabi mijinta ya gama karatu sai su dawo tare,kafin Bilkisu ta tafi sai da suka gama tsafeta a gidan boka yanda zata mallake Aayan ta samo musu kudi,to na rigada na sani ina Yiwa dana addua shima kuma akwai addini yana yi na kara ja masa kunne kan rike addua,koda Bilkisu taje baiji yana sonta ba,ya kasa kusantarta,har ya gama Degree lokacin ya dawo Nigeria kullum da sha'awarsa muna hanyar asibiti ga na Hausa muna yi,kuma ya kasa kusantarta,har ya gano cewar tana fasikanci tare da khaleel,bai sake ta da wuri ba sai da ya tabbatar da ita ta gane kurenta,su kuma su Abbi ganin bata samo kudin ba ta kasa komai sai suka tsaneta suka koma azabtar da ita,duka zagi ba abinda basuyi mata ba har Aayan yaga zalunci yayi yawa ya bata hakuri tare da kudi me yawa suka rabu,yanzu haka ta dade da aure harda yaranta biyu.

   Lokacin kuma Asiya Matata bakin ciki yayi mata yawa,lokacin kuma Hajja da kanta taje gidan boka ta samu nasara wajen Yiwa Asiya asiri tace dole sai na saketa,naki yarda don ina sonta,rigima mukeyi sosai,ta daina kula Aayan sam ta tsani Danta,tace indai ban saketa ba sai ta kasheni haka Aayan na rokarta tayi hakuri yana kuka nima haka na saketa saki daya ta ta koma kasarsu,bayan asirin ya karye na maida ita ba tare da kowa ya sani ba har Aayan,Shine ma dalilin da yasa yake jin haushin mahaifiyarsa har yau,na fada masa gaskiya Amma yaki fahimta yata,muna tare shekara daya da dawowarta  ta samu ciki wajen haihuwa ta rasu Allah ya karbi abarsa,munyi kuka ni da Aayan sosai haka muka hakura.

    Daga nan Hajja da kanta tace ta samowa Aayan matar aure Nafisa ita kuma yar talakawa ce Amma bata da tarbiya ni kaina tasha zagina a gabana,lokacin Aayan ya hakura bai sonta Amma dole ya bata hakkinta na matarsa,a lokacin kuma su Abbi sun masa asiri kwata kwata ya daina sha'awar mata ko kadan dan kar ma ya haihu a duniya zuriarmu ta yadu mu kara arziki,ba asibitin da bamuje ba,akace lfy yake,har na Hausa da addua anyi Amma sam,ganin haka yasa Nafisa ta bude bakin rashin mutunci wanda akan Aayan take saukeshi ya kasa Control dinta zagi da komai ba wanda bata yi,su Abbi na zugata dan a bangarensu take,lokacin Hajja ta matsa min ita Kano take so mu koma da zama Abuja ba dadi,haka na zabi unguwa mafi kyau na tsantsara mana wannan gidan da muke ciki wanda duk shekara sai an canja masa fasali, Sabo da bacin Rai Aayan ya tafi yin karatun masters dinsa na Electrical engeneering,Nafisa tana nan tana sheka rashin mutunci har da ni,yana gama Masters a london ya dawo ya mata mugun duka ya saketa sakamakon zagina da yaji tayi.

    Suka kara nemo masa mata wata Rukayya ana ce mata Ruky lokacin Aayan bai warke ba na dage masa da addua Allah ya taimake mu ya warke don baya boye min komai nima bana boye masa yace min yanzu yana jin Sha'awa, Ruky da Farko tazo da mutunci tasha wahala hannun Hajja duk cikin Matan da suka aurawa Aayan Hajja bata son Ruky Sabo da taga kamar tana Son Aayan,shi kuma Aayan bai son Ruky ya dade da ganowa Ruky Makaryaciya ce gata kawai sha'awarsa takeyi dama tuni tasan Maza tun a waje,amma duk da haka nace yayi hakuri ya bata hakkinta,yaje mata da niyya kawai sai kuma ya kasa aikata komai gashi yana sha'awa Normal Amma ya kasa aikata komai,Ruky dai taga no way itama tace a saketa,wannan da yake Hajja bata sonta sai da tasa wasu suka Zane Ruky tas wai ta ci kudinsu a banza bata yi zaman aure ba,Da kanta Ruky tace a saketa,na bata hakuri Amma tace ina sam Allah ya karta baza ta zauna ba,Aayan yace taje itama,daga sannan kawai yace wa su Abbi bashi da lfy bazai taba haihuwa ba,an gwada shi hasali ma bazai iya Yiwa mace komai ba,sannnan ya kara daurawa kansa cuta yace ai ciwon sugar da Hawan jini ne dashi wai duk dan su kyaleshi haka ya huta don ya rantse bazai kara auren matar da zasu zabo masa ba ko me za ayi.
     
   Muna rayuwa haka kullum kiyayyarsu Karuwa takeyi akanmu musamman Aayan sunfi takura masa har Hajja cikin jikokinta bata son Aayan,Shi kuma baya shiga harkarsu baiyi rayuwa dasu bama bai taso dasu ba sam basu saba da juna ba,Sabo da basa sona da Dana nace Abbi ko kannensa su bawa Aayan auren Yarsu daya ayi yar gida sukace sam basu yarda ba Sabo da a zuciyarsu suna da manufa a kanmu.
   Muna ta rayuwa kwatsam Aayan ya birkice min shi Barin kasar zaiyi bai son gidan nan,aikinsa ma Shi bari zaiyi ya daina komai,na rude muna ta addua watarana ya fita shike nan bai dawo ba,Kowa har Securities basu ganshi ba,sati daya,biyu,uku,wata daya har wata Uku,babu nema cigiya har kasashe ba a ganshi ba,addua sosai har masallatai na raba,ana ta yi sai aka ganshi can wani kauye a gindin bishiya ya dawo hayyacinsa,ashe su Abbi ne suka masa kucciya,ganin haka nace dole mu Barsu,ai kuwa Hajja tace idan na tafi bata yafe ba ta tsine min,Aayan yace mu zauna kawai Amma shi zai koma Abuja da zama shine Aayan ya koma rayuwa a Abuja lafiya yana min aikace aikace na Business tare da fita kasashe,yana yawan zuwa Umrah Sabo da addua ko yaushe zaki ji ya tafi idan ya Zama less busy.

    To Daddy wannan cutar taka fa? Ai yau kimanin shekara daya da rabi kenan ina haka har na saba ma,shima sati daya ina dan jin jikina ba dadi nazo wucewa Naji yan uwana su Abbi suna shawarar yanda zasu kashe Aayan mijinki Sabo da su gaji dukiyata su da yaransu,har yanzu a wannan kudirin suke,kuma duk yaransu sun san da wannan,dalilin haka na yanke jiki na fadi shike nan komai ya daina motsi shima ba kasar da ba aje ba har na gargajiya da addini anyi,masu irin cutata da yawa suna tashi suna warkewa Amma ni tun muna yi har mun gaji ma na hakura na barwa Allah.
  Aayan yace bai hakura ba na hanashi har haushina yake ji yaki zuwa gaisheni Sabo da naki yarda mu ci gaba da neman magani,kin san mijin naki ba dama.
   To Daddy ni kuma me yasa ya aureni? Nine nasa aka auroki yata ke zabina ce,watarana kafin kuyi aure yazo nan yana ta fushi da masifa wai daga ya kwanta a kasa wata tazo ta haye masa jiki Kazama,watarana ya kara zuwa yana fushi wai wannan ce ta zageshi wlh sai ya halakata,da kyar na lallashe shi,watarana kuma yazo yana dariya yace min kece dai ya kara ganin ki son kudi ya kaiki wani gida ko wani ya biyoki ko me kina dai ta sheka gudu kika kasa tsayawa da kanki sai da kika bigi bishiya,wata rana kuma yazo nan yace min Daddy naga mayyar nan nace wace mayya yace me son kudi taje Maula gidan Yarima tana ta shan fura a leda a gaban Maza.
    Shine na bashi Umarni nace lallai lallai dole ne yaje ya aureki,sabo da ina so ko Allah zai sa yayi dacen mata ko ma ya samu haihuwa ya tara zuri'a.idona na rufe gaban Daddy sabo da kunya,yace min ke yarinya ce,nace ae a hakan,ba fushin da baiyi ba shi baya Sonki bazai aureki ba nace dole ya aureki duk yanda zaiyi ma ya aureki amma nace zai iya aurenki na Kasuwanci zuwa dan wani lokaci sai ku rabu idan zaman bai yuwu ba,bana son a cuci wani,lokacin yace indai dan na wani lokaci ne ya yarda zai biyaki kudi ya aureki tunda ina son yayi aure,ko yaushe kike so kasuwancinku ya kare ki fada masa zai rabu dake yata baza a cuceki ba,bazan miki dole ba,nasan aure a haka bazai yuwu ba,shima na fada masa.

  Ya akayi su Abbi suka yarda? Sai da muka biyasu kudi me yawa sannan suka sa Hajja ta yarda suma suka yarda suka Zama maneman aurenki,kudi aka biyasu in ba haka ba sai sun zuga Hajja tazo tace bata yarda ba, ko auren da basu zuga Hajja tayi masa ba shima Contract sukayi Deal aka biyasu kudi suka kyale zancen,sun san kuma zamu iya kwace kudinmu tunda a tafin hannunmu suke,sabo da sun San baza su iya sawa a sakeki ba an rigada an biya shi yasa suka zuga Hajja tace ki dawo gidan nan da Zama,wannan securities din ma duk Aayan ne yasa suke tsaro na sabo da makircinsu,to Daddy dukiyar taka fa? Tana hannun dana Aayan na bar masa komai tuntuni shine me kudin shi yake komai kawai taimaka masa nake da shawara,mijinki young millonier ne da an San abinda yake dashi a duniya to da duk duniya sun San da zamansa,amma duk da haka da dama sun sani kasashe nayi suna shima haka.

   Yarima Bobo fa Daddy?shi kadai ne abokinsa dan Nigeria da sukayi karatu tare kuma ya yarda dashi sun aminta da juna,ranar danaga ya Zane su Haneefa fa? Waya tayiwa Abbi kuma yasan ba mai iya taka musu birki sai shi shi yasa yace yaje ya Zane masa su.babu wanda suka tsana yanzu sama da mijinki da kuma wanda suke tare da shi,suna nan akan bakansu karki ga suna miki dariya ko sunyi luf kice sun shiryu wlh wani kullin suke kullawa,da bana raye da tuni Aayan ya bar kasar nan tunda ko tayi masa baki bazai bishi ba to amma ina raye ni zata yiwa kinga akwai matsala,ki nutsu yata shi yasa na baki labari ki san yanda zaki zauna dasu da basira tare da gogewa,fada da zage zage ko duka ba shi bane use ur Upper ki kwaci yancinki da na mijinki, idan kuma Kun shirya rabuwa baku da matsala Ku kuke zaune sa juna ba ni ba,yanda kukayi dai dai ne,a takaice na baki labari dan na yaba da tarbiyarki,nasan Aayan bazai fada miki ba shi yasa na sanar dake,idan kin zabi business za a biyaki ko nawa ne karki damu tashi kije a sannu kuma zaki ci gaba da gano halayensu daya bayan daya,abinda da ma ban sanar dake ba duk zaki gane nan gaba,a takaice na sanar dake. 

   a raina naji tausayinsu sosai har kwalla nayi sannan sai naji tausayin kaina da yan uwana,garin neman gira zan rasa ido,haka kawai son kudin jaraba ya kawoni inda za a ruguza mana rayuwa,yanzu ya zanyi?Me zanyi,lallai fada da masifa ba shine kadai zai kwace mu ba,ashe Aayan yana da gaskiya da baya saurarsu yake cewa na sharesu kawai,irin wannan kiyayya haka wacce zuciya ce dasu,ba a saduda ba dana sani tun tuni kayi ta abu daya akan wani,har Aayan suka batar dashi lallai,to tunda suka Yiwa yan Uwa haka ai nasan ma wajen Kudus zasu cilla ni shike nan zan bace ko a halakani,a raina nace ni na fasa auren na hakura da Kasuwancin kawai bari ya dawo ya sake ni kawai mu tafi,bazan iya wannan rayuwa ba wannan gidan ai sai su ni kam yafi karfi na.

   Muryar Daddy naji yace tunanin Me kikeyi yata?nace ba komai kawai mamaki nake yanda kuka iya Hausa haka bayan ba anan kuke ba,yace lokacin Hajja bata wani jin turanci da Hausa muke magana har na kai 5yrs daga nan ina son yaren akwai wani bahaushe abokinsa yaci gaba da koyamin na iya sosai,Aayan ma na koyawa Mamansa duk da bata wani iya ba haka muke masa Hausa ya tashi da yare biyu,da ya dawo nan kuma sai ya kara gogewa da yaren.
   
    Me kike so kiyi da kudi yata idan kin samu da har kika amince da wannan aure ba tare da bincike ba duk da cewa Aayan ya min bayanin halin da kuke ciki? Daddy Sabo da muyi Karatu Meenat ta zama Likita,Maeesha ta zama lauya,sannan nayi mana gida me kyau,mu dinga cin kayan dadi,sannan idan munyi aure mu dankara kayan daki masu kyau shike nan,Murmushi yayi yace to wannan tunanine me kyau,me yasa kike son Kanwarki tayi likitanci ke kuma fa? Nace ni abinda yake birgeni da Likita Daddy naga sun gwalewa mutum ido sai ayi zuruuu ana kallo sai ace yana da cuta Kaza hhhh na karashe ina dariya shi kanshi Daddy yaji kuruciyar tayi yawa sai dariya yakeyi.

   Yace Allah me iko to Lauya fa? Shi Lauya Daddy Allah hular nan da suke sawa wata tum tum kamar gashin tinkiya itace take bani dariya,kuma da glass dinsu yana birgeni,sannan idan suka tsaya suna zuba karya gaban alkali sai ka rantse gaske ne,shine suke birgeni sun iya sheko ta,Daddy yayi dariya to ai ba kowa ke yin karyar ba a cikinsu,amma dai sunayi ga shedar zuuur a karbi kudin mutum,Yace Allah ya shirya su,ke kuma fa me kike so ki zama ?nace  ai ni nawa yafi nasu dadi malamar Makarantar primary na dinga shiga aji gaba daya a mike ace Good morning Aunty,nace morning student How are u,suce we are fine thnk u Ma,sannnan ni kuma ina bata rai ina yanga tare da tsawa nace Sit down,kuma na dinga koya musu A babba a karama,Baba ya tafi Gona,malam yana karatu,Inna tana Girki.Daddy ya dinga dariya yace ah lallai naki yafi dadi,tashi ki tafi Yata gashi 4pm tayi Sallah zanyi, 8pm Aayan zai dawo yau daga Umrah,cikin Kasuwancin naku da kukeyi ki dafa masa abincin gargajiya yana son wainar shinkafa da miya.

   Na mike nayi masa sallama zan tafi yace Yata yau kin sani nishadin da na dade ban samu ba shekarunki nawa ne haka? Tunda kaine Daddy na gaskiya zan fada ma 16 nake saura wata biyu na shiga 17yrs Amma karka fadawa kowa Sabo da har Aayan 17 nace masa bana so a dinga min kallon yar yarinya.
   To Bazan fada ba sai kin sake zuwa yata nace to Daddy Allah kara lfy na fito  na dawo part dinmu.

   Sallah nayi na fada kitchen na fara  hadin wainar shinkafa da Miya,Su Meenat sun tafi karbo mana dinkunan da muka kai wurin tela, bani na gama Wainar ba sai wurin 7:30, ina kitchen su Meenat sun dawo tare da Driver duk na zuba musu sunci har Driver,Ni kuwa ina kitchen a kaskon ma naci na koshi da naga na soya wata tayi min kyau sai nace wannan tawa ce ni zan cinye ta,saai na jefata a plate na zuba Miyar taushen na cinye ina yarfe hannu,ga zafi ga Dadi,miyar tayi dadi harda naman Rago,ina gamawa na masa kunun gyada,na yanka masa Fruits a wani glass Bowl me kyan gaske nasa a fridge,Meenat da Ma'eesha ne suka wanke abubuwan dana bata tare da gyara kitchen fes bayan sun gyara ko ina na gidan sosai yana kyalli ko ina kamshi ke tashi,Dakin Aayan na kara gyarawa duk da cewa sun gyara sai da na kara tisawa na kunna Ac ga sanyi ga kamshi,na kulle,nayi Sauri na shiga wanka,na fito yau Salo zan canja a gidan nan.

   Meenat ce ta gyara min gashi da mayuka,na shafa lotion me kyau da kamshi,dama gashi na kara haske abinka da fara dama ta samu waje, yar kiba da kyau nayi Sabo da ina ci ina koshi a kan lokaci,Cikin dinkunan na zabi wani Lace me kyau pupple and Brown riga da skert nasa,yanda na fito a dinkin ba a cewa komai,mazaune sun cika fam dinkin das a jikina,Meenat ta shafa min powder sama sama ban son kwalliyar nan me yawa ni,maroon jambaki ta sa min sai kwalli tare da samin eyeliner a saman ido harda nayi tsananin kyau,gira kuwa na hana tayi min da brush na taje na gyarata ba tare da na kara komai ba Sabo da girarta baka ga yawa,tace saura sarka aka Sa min wata yar karama pupple da dankunnenta,nasa agogo na wani me kyau na yan gayu da muka siyo Brown,Meenat tace sai na Sa zobe ma yana kara kyau a hannu,haka nasa wani me kyau,ta zauna ta tsantsara min dauri tare da sakin gashina ta baya kyau ba a magana ni kaina sai yanzu na kara son kaina,naji kamar na lashe kaina Sabo da yanda na hadu,nace kai ashe nakai haka kyau,Meenat tace bakya fito da kyan naki ne ai ke kullum ke kike maida kanki baya.

    Nace a haka dai duk kwalliyar taki aka hadu da Kwaja kuma,Dukana tayi a baya da wasa muna dariya,tace Allah sai na kai kararki,nace yawwa gobe zan kaiku ku gaisar da Baban Aayan,Allah ya kaimu.
    Nace bari nasa takalmi ko?tace ae kisa me tsini ki Bada mamaki yau,ai ko na dakko cikin sabbabinmi wani Brown me tsini wow wow na gama birgewa yau ko uban waye ya ganni yau sai yawunsa ya tsinke indai Namiji ne.

    Ina cikin gwada yanda zanyi Tafiya Meenat tana gyara mana dakin muka ji Karar motoci,nan take na zaro Hijab Meenat ta fisge ke wai mene haka bayan kin gama kwaye cinya ya gani dan Allah muje palo,duk sunyi kwalliya Meenat cikin Doguwar rigar arab,Maeesha English wear tasa riga da Wando suma sababbi sun sha kyau,mun baza turaruka,ni kuwa kamshin nawa daban ne da nasu.
    Knocking muka ji nace wayyo kunya nakeji gashi nan zai ce sonsa nake,Meenat taja tsaki tace tonawa kanki asiri ki huta,Maeesha ce ta bude kofa ni kuma na hakimce a kujera na maze ina danna yar nokia ta ka rantse wata shegiyar waya ce nake chat ko wani abu.
    
    Wow wani Balarabe ne ya shigo Aayan sanye da farar fitted jallabiya yasha kyau kamar me don ya canja style din gyaran gashi na ala tsine uwar me karya.

    Kamshi ya cika gidan,cikin Securities wani ya taho zai shigo masa da akwatuna sai muka ga ya juya da Sauri ya bude kofar yace jeka daga nan ma is ok,da kansa ya shigo da akwatuna har Uku masu kyau na gaske.
    Sallama muka amsa Meenat ta kifta min ido na mike jin karar takalmina ya kalleni muka hada ido,na tafi da shi Amma sai muka ga ya tamke fuska,naje har gabansa na makale murya can kasa nace sannu da zuwa Aayan.

    Bina yayi da kallo yanda na sheka kyau ba a cewa komai,akwati daya na karba,Meenat ma tazo tace Sannu da zuwa yaya,da fara'a ya amsawa Meenat yace ya gida ya schl,tace lfy,Maeesha kuwa hannu ya bata suka tafa har suna dariya,tace yaya dama tuntuni Meenat take nemanka zata kawo ma karar Sis Mufee wani me Katon ciki ne  cikinsa kamar Randar Ammah yake zuwa wajen Meenat wuyansa Allah kamar bulalar malaminmu,shine Sis take ta tsokanarta tana mata dariya.da gaske ya tambaya yana kallon Meenat da yake duk yarane da Sauri Meenat tace ae wlh tun rannan kullum sai ta min dariya har da dare dan Allah yaya ka koreshi in yazo,ba damuwa in yazo ki fada min yace tare da Haurawa Sama,daya bayan daya na dinga kai masa akwatunan har Bedroom,ya shiga wanka lokacin na sakko kasa naji ana buga mana kofa nasan bazai wuce jarabar yan gidan ba,ina lekawa na hangosu kuwa mata da maza manya da yara na bude tare da cewa lfy? Basu gane ni ba sabo da kyau,Ke dalla matsa gidan ubanki ne? Juyawa nayi dan su kara ganin yanda na hadu,gaba dayansu da kyar suka gane ai nice, da mamaki sukace wajen dan Uwanmu muka zo ko kina da gado ne a gidan nan? Na yatsina fuska nace ku koma sai gobe da Safe a halin yanzu Bazan iya Barin me gidana yaga kowa ba dan karma a bata mana Mood, yanzu na boye abina na Adana mijina,na killaceshi baza kuzo ku Sa masa tention ba aikin banza sai roko da san abin duniya duk abinda ake muku bakwa gani sai kun shiga hakkin iyali ba dama mu gabatar da Sunna cikin kwanciyar hankali Naja tsaki kafin suce komai na banke kofa na kulle nasa lock nayi tafiyata.



51-55


Official

By
AsmaBaffa

Ina matukar baku hakuri fans na rashin posting dina jiya ayi min Afwa bana nan unguwa naje,yau kuma baki nayi shi yasa ban samu dama ba.

Wannan page dina ne AsmaBaffa???nima na bawa kaina da kaina.


Meenat suna ta karatunsu na wucesu na shiga kitchen tare da shiryo abincin Aayan na kai har Bedroom dinsa yana wanka bai fito ba dama wankansa dade wa yake sosai,ina zaune Saman Bed dinsa sai gashi ya fito daga shi sai dan gutun towel a kugu karami a wuyansa,jikinsa abin kallo ne ya hadu da yawa ko kai waye sai ka kalleshi sabo da kyau,dan kar yace ina kallonsa kawai sai na sa yatsana na tsakiya a baki ina ta tsotseshi na sadda kaina kasa,har ga Allah ban san ma na sa Yatsan a bakina ba, ina ta yi ya juya baya yana ta shirinsa don bazai iya kallon tsotsar yatsan nan da nake ba bilhakki abin so childish.

    Tunawa nayi da salona na wayo da zan masa tunda na Canja taku na,sai na Mike a hankali na taka har gabansa dama na cire takalmin dana sa Already,kunya da tsoro suka taso min sai na dake na matso lotion din da yake tsafawa na murza a hannuna cikin wata murya da ban san na iya ba nace kawo na tayaka baka iya bama sam kawai ban jira amsar sa ba na daura hannuna a kirjinsa tare da cewa mutum kato bai iya kula da kansa ba,suman tsaye yayi amma kuma sai naga yaja baya da sauri ya matsa tare da cewa kee mene haka,na nuna ban gane ba nace da akayi me? Ka tsaya mana na kara matsawa da sauri yaja baya again kamar yaga dodo, na bishi zan kara damkoshi sai naga ya ja da baya da gudu,na fara dariya ina binsa yana guduwa,na bishi muka fara zaga dakin da gudu dan sosai yake guduna kamar kamar yaga wani zaki ko Damusa,ina ta binsa ina dariya shi kanshi dariyarsa yake kunshewa yana yin kadan yana ke wai mene haka bana so, nace Allah sai na shafa ma,muka zaga ta bayan sofa ya daga kafa zai haura ta saman Sofa lokacin na kamo Damtsensa da hannu biyu sai ya fada saman Sofa  nima na bishi muka fada kai gaba daya ba shiri ya saki dariyarsa,nima haka na cikwikwiyeshi yana so ya cireni a jikinsa amma na rikeshi kam gaba daya a jikinsa na Dafe,da kyar dai ya kwace ya Mike ya gudu Saman Bed gaba daya ya shige blanket,sai kansa a waje,nace dan Allah ka tsaya mana wai mene? Yace ke tsaya a nan karki matso nan,Na tsaya a hankali nace shike nan tunda baka so bari na zauna a gefen Bed din naka,yace no sai dai in baza ki taba min jiki ba to ki zauna,ai nace na fasa Zama kawai zanyi.

    Ka tashi ka karasa shirinka Kaci abinci sai kayi baccinka,kaje wurin Daddy? Harara ya mako min ke wai nan nufinki wata mace ce har wani sani abu kikeyi kina tambayata abu kanki tsaye,ni da Daddy na me ya shafeki a ciki ki daina min shishigi tam.

    Allah ya baka hakuri dama tuna ma nayi,sakkowa yayi daga saman Bed din ya karasa shirinsa cikin kayan bacci masu kyau na maza ruwan toka,s aman carpet ya zaune dake dan gefen bed din,yana bude flask din yaga Waina da miya nan take ya dinga zuba murmushi maimakon ya min godiya kawai sai yace dan sunkuyo zatona wani abu zai ce kawai sai na ji rankwashi a kaina kwasss Gift ne wa ya fada miki ina son wannan? Anyway tnx da sauri na Dafe wajen nace ouchhhh ina turo baki cike da shagwaba nace da zafi Allah yanzu da kai na yiwa haka da tuni ka fara fada,abincinsa ya fara ci bai ce min komai ba,har ya gama yayi Brush ya fito tare da yin Nafeela raka'a biyu,lokacin na kwashe kwanikan na maida tare da gyara wajen,lokacin yana shafa addua ya idar.

    Saman Bed ya haura bai ce min komai ba dan ni Jarida nake ta buduwa ina kallon hotunan labarai,tunawa nayi ban fadi me ya kawoni ba,nace dazu mun dade da Daddy Muna ta hira,gaskiya Daddy yana da kirki sosai,kayi sa'ar uba Allah yaja kwana ya kara masa lfy me amfani,sabo da na yabi Daddy tare da masa addua sai naji yace dawo nan ki bani labari me yace miki ya furta yana nuna min gefensa da Hannu,naso naki zuwa amma kwarjininsa baza su bari na masa musu ba Sam,haka na Mike naje tare da hawa saman Bed din sosai har tsakiya kusa da jikinsa,kawai naji yanayina yana canjawa sai na tsinci kaina da son kwanciya a jikinsa musamman da naji laushin fatarsa dazu ga kamshi,du sai na diririce abinda nazo da niyyar na fada cewar a sakeni na fasa auren sai na kasa na manta ma da zancen Sam,sai naji kuma shagwaba ta motsa ba abinda nake so irin nayi abata na samu me biye min amma ba dama,a raina nace ke kina yar yarinya haka,muryarsa ce ta katsemin tunani da cewa ina jinki, kawai sai na susuce na rude abinda ya rambayeni daban abinda nake bashi amsa daban na riga da na zauce sabo da ya hadu da yawa.
    Na jingina da jikin Bed din nace hmm dama Ashe Umrah kaje bamu sani ba? Yace ae mana,me kika yi wa Daddy? Nace kudina ya kare nazo nan na dauki 5k ciki ka irga abinka kar kaga babu kace nice shima ba yanda zanyi su Meenat zasu je schl,yace Ok  Daddy yace miki wani abu? Ni dai ko jinsa bana yi wani iri nake jin jikina nace uhm...uhm...turarenka ma jiya nazo na fesa maka,amma kadan na fesa kar kaga ya kare kace nice, kalau kike kuwa ko aljanun sun motsa, kamshinsa ya gama gigita min rayuwata sam na kasa gane kaina,duk Ac da ke wajem gumi na fara yi,a hankali jiki ba karfi na zame dankwalina gashina me uban tsayi ya watsu ya kara wani kyau, bai kawo komai a ransa ba tunda yasan shirmena kuma kallon yarinya yake min har na Isa ma wani feeling,a hankali ya juyo kamar me rada yace ko baki da lfy?, Nace ni ina zan sani  lfy nake ko kalau bazan iya ganewa wanne yanayi ake ba,sanyi ne ko Zafi,zamewa nayi tare da kwanciya a saman bed din tare da lumshe ido nayi shuru ban kara magana ba nayi shuru,tasar min a bed ki tafi to tunda ke ba a abin hankali da ke,shuru bance komai ba,ya matsa na bar masa bed ni kuwa tuni jikina yayi weak da yawa bana son ko nayi motsi ina daga kwance nace kawai labarin gidan nan fa Daddy ya bani, to shine kike min shirme abinda na tambayeki daban amsarki daban? Banza nayi dashi,shima bai sake magana ba ya juya min baya tare da kashe light ina jinsa yace tunda baza ki tashi ba sai ki shekara a bed din,shuru na masa har ban san bacci ya kwasheni ba shima haka.

    Karfe daya na dare na farka na tuna maganar da zan fada masa ni ko dama komai dare idan na tuna zan fadi magana ban fada ba indai mutum na kusa dani sai na tashe shi,ba bata lokaci na kai hannu saman gashinsa na ja da dan karfi firgit ya tashi da masifa,hannu na kai  da niyyar nace Aayan zan dan bigeshi,caraf ya rike min hannu tare da juyowa daf dani muna facing din juna har muna jin numfashin juna,a hankali yayi magana ki daina taba min jiki,kinzo kin dameni menene,sai na kara mantawa da maganar da zan fada ta a sakeni,yanda naji hannunsa cikin nawa me laushi ga kamshinsa dake kashe min jiki sai nace ruwa zan sha,Ke haka kike dama kamar yar 4yrs ki hana mutum sakewa kuma haka kike kwanciya da kayan jikinki ke? Nace a'a yaune kawai,haka kawai kizo ki takura min ya Mike tare da kunna light ya miko min robar ruwa daya,ba shiri na bude na Sha ta dole,akwatin da yazo dasu daga Saudiyya ya bude tare da Zaro min wata sabuwar rigar bacci hadaddiya amma fa tayi tsaraici  gata fara wata silk ce yar guntuwa me hannun bra,in kasa komai sai an gani duk wani tudu da gangare,ina gani nace zan tafi Dakinmu ni,Murmushi yayi tare da komawa jikin kofa na dauka bude min zaiyi na tafi sai naga yasa lock ya dawo yace ungo tashi maza ki cire kayan nan,a ransa yace zaki takura min gwara nayi maganinki.

    Hade rai yayi kamar baya dariya ba yanda na sanshi tun farko,na tsorata yace get up ko yanzu nazo na fara ball dake tunowa nayi da yanda ya taba min farkon ganina dashi,da sauri na Mike na karba na kasa cire kayan na tsaya kawai,a hankali ya matso tare da rungumoni na kwanta a jikinsa ina ta salati a raina don wani zirrrr nakeji tun daga kaina zuwa kafa ta,zip din rigata ya zuge na kwace jikina da sauri na ja da baya zan tsere da zafin nama ya biyo ni tare da jawo rigita na dawo baya ina dariya shima haka,har mamaki nake dama yana dariya,ido muka hada sai naga idonsa kamar ruwa a ciki yayi dan red,ganin ina kallonsa kawai sai ya dauke kai tare da juya min baya yace na baki 2mnt ki canja idan kika sake na juyo wlh sai na miki sintir.

    Da sauri na cire kayana daga ni sai pant nace kar juyo na kusa da sauri na zura rigar a jikina dukiyar Fulani na yan matasa ana kallonsu da adadin girmansu,Na ninke kayan dana cire harda bude Sip side daya na adana abina kun San ni akwai tattali sabo da an saba da babu don wata tsaftar ma akwai babu a cikinta.
 
    Juyowa yayi yaga yanda nayi mugun kyau a ciki yace cire min a bata na fasa dama lefen wacce nake so zan aura na fara hadawa shine na baki daya sai naga ma bata miki kyau ba Ciro min a bata ba size naki bane nata ne, wani bakin ciki ya kamani tun ba ayi nisa da business ba za a ce aure za a kara,sai na tuno dama fa yayi aure ba sau daya ba yana saki,a raina nace me auri saki ne nima Sakina za ayi,da kyar na daure bacin raina na kakalo murmushi nace Allah ya sanya alkhairi kace zamu Sha biki ai ranar za a ga yanda zan kwashi rawa,kai amma naji dadi sosai kaga an samu me Kula da kai wacce rake sonka kake sonta haba ai Alhmdllh naji dadin wannan magana ka kuma birgeni da sauri da sauri nake maganar ina murmushi harda yar dariya kamar na zare, muryarsa naji yace tnx lallai kina da hankali na yaba da hankalinki kwarai ba ruwanki baki dauki duniya da zafi ba,sai ki dinga min abin cin gargajiya tunda nan kika kware ita kuma dama tafi iya na bature,cikin bacin rai da fusata na hayayyako masa da masifa dake ni tsinanniyace ko? Sama na zaga ko me? Kanwa na kawo? Wlh bazan kara kulaka ba bare har nama girki,auren Kasuwanci mukayi dan haka duk kudina ka tattarosu ka biyani gaba daya na kara gaba,kawai ka sakeni na gaji dama sai kawai na fashe da kuka sosai,da mamaki ya kalleni,cikin kuka nace bani takadda ta,wannan gidan naku bakin gida du ba na gari a ciki sai Daddy kawai gaba daya bakin Uwa ne a gidan banda Daddy,dariya ce ta kamashi ya dinga yi ni kuwa ina ta jin haushinsa,yace to kwanta gobe Insha'allah zan baki komai da kike so har sabon gida sai ku koma can da zama sannan na baki takarda abinda kike bukata yanzu,k karki damu kwantar da hankalinki indai wannan ne baki da damuwa,tunowa nayi da maganar Daddy cewar duk Wanda ke son rabuwa ba matsala za a rabu,naji wani mugun bacin rai ni rabuwar bata Dameni ba sai da naji yace wai aure zaiyi.

    Hannuna ya jawo zuwa saman Bed tare da cewa kwanta ki huta kiyi baccin karshe a gidan nan gobe zaku tafi,bazan huta din ba nace cikin fushi, kwanciya yayi a gefe na tare da kwantowa a samana yace tsaya kiji ina da nauyi? Nan take naji wani shock na gaske a dukkan jikina,nayi luf ya kwanta flat a samana kirjinsa saman nawa,wasu tsutsotsi naji yam yam a jikina ko nauyin nasa banji ba duk da cewa Bai sakar min nauyinsa ba, hannayena na zuro ta bayansa tare da sakalesu na rungumeshi nace baka da nauyi wai wayo nayi kar ma yace dadi naji gaskiya kuma abinda nakeji ne yasa na kasa daurewa sai da na dangana da rungumeshi.
    Gashina ya kalla me kyau da kamshi ya shafa a hankali yace ba laushi ma kamar ganyen bishiyar Dabino,murmushi nayi nasan ba gaskiya bane,na nutsa hannuna a cikin gashinsa me matukar santsi da laushi na kalleshi nace ina Sam taka Sumar kamar ta gyartai me gyaran tukunya da karfe,ni a raina dama so nake na taba Sumar shine na samu hanyar nayi masa wayo, hancinki yayi fadi da yawa duk bana ganewa me yake nufi ai nice kawai nake masa wayo,naja dogon hancinsa nace ai nawa yafi naka,yana karewa Lips dina kallo yace ke a tsorace na kalleshi yace ai bakinki yayi girma da yawa sai kace kofar gari,lips dina na turo tare da shegiyar Shagwabar da na zuke masa jini nace ai gwara nawa Allah,kalla na bude masa ka gani dan karamine wa zai ce spoon zai shiga nan? Ba wani nan cewarsa,ido na juya masa yana kallo na idonsa kamar ruwa ruwa ciki,ido muka hada da sauri yayi sama da kansa dan kar na gane yanayin da yake ciki,Aayan mene?na tambaya a hankali,murmushi yayi da saurin yana goge idonsa yace nothing me kika gani? ba komai I just ask never mind ok na furta irin naje schl fa,murmushi yayi tare da cewa kin san me yasa kike bani mamaki? Nace a'a duk wannan abun da muke yana samana a kwance,yace karfin halinki ne yake bani mamaki yana maganar yana kallon lips dina,a hankali ya gangare gefe daban yana cewa Good night ga key nan ki bude idan zaki tafi.

   Ban so ya koma ya kwanta ba sabo da ina jin dadin hakan banki mu dawwama a haka ba, munyi shuru kowa da abinda yake tunani,muka ji ruwa me karfi ya tsuge kamar da bakin kwarya,mikewa yayi tare da bude duka windows din nan take sanyin ruwan da ake da iska ya ka dakin gaba daya,Ac ya kashe da light,walkiyya fal fal tare da tsawa taratsatsa ake ta yi ba tsayawa,na tsorata dan ban son walkiya da tsawa ga window a bude muna hango komai,blanket ya jawo ya rufa mana gaba daya harda ni,ina ji ana tamfatsa tsawa,da aka saki wata ban san sanda nayi sauri na matsa kusa da jikinsa ba daf  dashi kamar zan shige masa amma sai ban ko taba jikinsa ba,bai san na matso ba ya juyo zai tatsileni duk girmana yar karama nake tashi a gabansa,kaina ya koma sam kirjinsa,kamashinsa ya bigeni, tsawa aka kara rankatawa me karfi na shige jikinsa sosai tare da kankameshi,duk dauriyarsa kasawa. Yayi sai da yayi hugging dina back,fuskata a saitin tasa a hankali na tsinci muryarsa yace tsoro?nace yeah wai ni baturiya,kina so ki daina Ji? Kai kawai na daga dan yanayin da nake ci bazan iya magana ba.

    Tafin kafarsa yasa a nawa kafar yana gogawa a hankali,cinyarsa ma tana gugar tawa,laushi da laushi sun hadu sai wani lumus kake ji,gashin jikinsa me santsi yana min wasu rubutu me lankwasar dadi? dadin ma Kun San har da me Lankwasa
     Ni ba gane me yake nakeyi ba dan nauka tsoron da nake ji na tsawa yake min maganinsa har ga Allah na manta ana wani abu idan anyi aure,kuma bayan haka ma ai nasan shi ance bashi da lafiyar da zaiwa mace wani abu,shi yasa na kara samun nutsuwa bana tunanin komai, fuskarsa ya daura saman tawa yana goga hancinsa a nawa,da kyar naji yace baki da hanci Ashe, kasa magana nayi sai da kyar nima na kara goga masa nawa back nace wannan kaine gashi me tsayi,bakinsa naji kawai cikin nawa sai da numfashina ya dauke yanda naji abinda yake min me tafiya da nutsuwar dan Adam,tuni ni na manta ma ana wani tsawa da ruwa tana ta rugiginta ni kuma muna rugurguzar juna,bakina yake tsotsa kamar zai cinyeshi,gaba daya na susuce shima haka,a hankali yace a barshi haka kin daina Jin tsoron? Nima naji dadi bana so a daina sai na shirya masa wayona shine da shagwaba nace ni dai tsoro nake ji zan iya suma gaskiya kuma har yanzu ina ji, dariya kawai yayi a ransa tare da Hamdala yace kai duk wannan abun amma kike jin tsoro gani a kusa,ni har na ma gaji amma dai shike nan bani tongue dinki, like how? Na tambaya,Ya ake mikawa mutum hannu ko wani abu,zaro tongue din kadan nace uhmm,Hhh dariya yayi yace sai kace miciji ya zaro harshe, karba yayi yaci gaba da gudanar da kiss dinsa sosai har lumshe ido nake ban san sanda na fara taimaka masa ba, wuyana yake shafawa tare da Sakkowa saman kirjina,nan take ya birkice ya koma wani iri,Nima haka nayi mukus dani ina ji yana murzasu ba da yawa ba naji kwakwalwata baza ta dauka ba sai na janye jikina da sauri nace na daina Jin tsoron,dake Ya kai karshe a duniyanci sai yayi murmushi tare da cewa har kin daina Jin tsoron? mace ae ni dai bacci zanyi,bai kara ce min komai ba ya juya ya fara addua ban san sanda bacci ya kwashe mu ba. 

    Washe gari muna yin Sallar Asuba na tuna akwai schl yana Azkhar nima nayi nawa na Mike tare da maida kayana da sauri ina ka tashi ,yace Alhmdllh nayi waje abina Kitchen na shiga,sharp sharp na soya mana chips da egg sai ruwan tea na shirya komai a Dining,sai ga su Meenat sun fito cikin shirin schl dinsu,Sis ina kwana? Cewar Meenat kun tashi lfy? Sukace lfy Alhmdllh.
   Ma'eesha tace a Palo kika kwana sis jiya bamu ganki ba,Kunya ce ta kamani nace ae a Palo bacci ya kwasheni,Meenat tace a fadi gaskiya dai sis a kunne ta rada min ya akayi ne daga cewa kin canja salo sai ki dawowa har palo na  fito bakya nan,Dariya nayi nace hmm ai ke dai bari Meenat ai na fada miki so nake mu bar gidan nan,zuwa nayi na takura masa kwana nayi ina masifa sai ya bani takarda ta, fada mukayi sosai,Meenat ta dauka da gaske ne tunda tasan Mufeeda bata musu karya,nan take gabanta ya fadi kamar zatayi kuka tace haba dan Allah Mufee kamar baki da ilmi wannan ai tsarin addini bane bai dace ba,dan Allah karki tozarta mu muna rufin asiri samun miji kamar Aayan sai an tona,ki tuna da shawarar Ammah sis,Maeesha ma tace dan Allah sister karki bari mu bar gidan nan,ni kuwa bata rai nayi kamar gaske nace karku dameni na gaji duk ma yanda za ayi ni bazan zauna dashi ba,shi yasa jiya ban bari mun kwana lfy ba
    Meenat ce ta fara hawaye tace bakiyi halacci ba wlh.kuyi sauri Kuci Ku tafi schl,sai suka ce mun koshi su wai sunyi fushi baza suci ba,ku zauna to bari na fito,zama sukayi ni kuma na shiga wanka da sauri na shirya kaina cikin doguwar riga ta Atamfa dama na iya dauri yanzu wajen Meenat na kafa shi na zuba kyau,ina fitowa kamar mun hada baki sai gashi shima ya fito cikin shadda milk color ya Sha kyau kyau kamar a saceshi,agogon dake hannunsa ya kalla yana sakkowa daga steps,Dining ya nufo kamar bai sanni ba,kallona bai yi ba,abin ya bani mamaki mutumin da jiya muka kwana lfy,Su Meenat kawai yake kulawa suna magana yana cin abincinsa,Meenat ganin hakan da yayi y nuna sai ta tabbatar da gaske jiya rashin  mutunci nayi masa,nan take taji tausayinsa tare da jin haushina, ina lallashinsa suci abinci amma suka ce baza suci ba har haushinsu ya kamani nace Ku tafi ai cikinku ne kuma sai dai ku tafi a motar haya yau ko napep hukincinku kenan na bijirewa maganata,Hararata Meenat tayi ina kallonta Shima Aayan ya gani yasan suna min biyayya suna da tarbiya tunaninsa ko wani abu nayi musu, nace Meenat me kikayi ba dai ni kika harara ba? Kunkuni tayi,nace I saw u now zaki san ni kika yiwa rashin kunya ke kina ganin kin girma ko nawa kike har ina miki magana kice zaki harareni sabo da ina wasa daku,nifa ba hararki nayi ba,tsawa na daka mata ni irin Babba din nan dalla jeki stupid Girl,Maeesha tace amma kin San munyi late zamu makara da yawa,shi dai yana Shan tea yana jinmu, baiyi nisa da fara sha ba ya Mike shima tare da cewa ga tea dinki nan nima bana sha muje na saukeku a schl Meenat.

    Ina tsaye suka tafi ni kuwa dadi naji yana kula yan uwana ko bai kulani ba in dai ya kula yan uwana Alhmdllh,akan ya wulakanta min yan Uwa gwara ni yayi min ko mene,sabo da wasu kai kadai suke so duk Wanda ya shafeka basa saurarsu bare su taimaka musu sai iya matarsu ko budurwarsu,Meenat suna fita suka hango Kwaja yana wankewa su Sajida takalmin schl,da Sauri Meenat tace Yaya Aayan ka ganshi to dan iskan da suke hadani dashi shegen ciki kamar an kifa kwarya.

   Koda Aayan ya kalli Kwaja bai San sanda ya saki dariya ba tare da cewa lallai an cuceki am so sorry su Hanifa yan iska ne,kamar ya sani sai ga Kwaja ya dago kansa wanda ke dauke da keya me shegen tsini goshi rafkeke ya bude baki hakoran gaba cako yana sakin murmushi yasha uban askin kwal kwal jijiyoyi a kansa rada rada ya dago sirisiri hannunsa saitin Meenat yana kifta mata Ido kamar na Kwado, Kuka Meenat tasa sabo da takaici,Aayan da kansa ya kira Kwaja ya masa warning kar ya kara ganinsa ya kalli ko fuskar Meenat,kuma ko gidansu ya daina shigowa ya dinga tsayawa bakin gate,a gigice Kwaja ya dinga bada hakuri kan ba zai sake ba.

    Bayan na gama komai nawa dana saba na gida shirin schl nayi 1:30pm Driver ya kaini schl tare da kawata muka hadu Sayyah,Muna hira Sayyah tace tunda kina da aure ki dinga zuwa gidanmu ana miki gyaran jiki,Maman Mu tanayi har shagon gyaran jiki ne da ita,idan kika je a gida ma zata miki naki,kuma gaki best frnd dina naga ke yarinya ce baki ma san auren ba,zata koya miki komai ta dinga tsumaki Oganki yaji zam zam,yanda kike me kyau fara idan ta gyara miki jiki sai Oga ya zauce wlh.

   Baki na tabe tare da cewa ke ni bazan yi ba Natural wanda Allah min ya isheni yanzun ma a haka kinga yanda yake bani wahala ina ga na kara wani abu,Karya nayiwa Sayyah dan karma taji sirrin aurena amma sai ta dage wai dole na samu time a dinga yi min ko duk wata sau daya ne,sannan a bani na tsumi nasha,a raina nace hauka nake na Sha tsumi me gida baya ko kallona kuma ko yaushe zai iya Sakina mu rabu,jiya ne ma kadai muka taba hada makwancin shima hakan nice na je tsautsayi yasa kuma ban fadi maganar data kaini ba na bige da kwana a can,a fili nace Sayyah kenan zanzo to amma sai na sanar  masa,kirashi a waya ki fada masa yanzu muji,sai yanzu na tuna bani da Number sa shima baida tawa amma sai nace yana Office yanzu he is busy sai na koma gida,tace to shike nan zan fadawa Umma ,nace ba matsala Insha'allah.

   Muna cikin class 4pm Saura 1hr a tashemu sai naji wani malami ya leko ta window wace Mufeeda Adam Fatima?nace Sir tare da daka yatsa sama,yace zo kinyi bako,Mamaki ya kamani bako kuma ni to wa na sani,Haka dai na daure muka Mike ni da kawata Sayyah cike da tsoro na fito motocin Aayan na hango mamaki da tsoro ya kamani ina ta Addua a raina nace Allah yasa lfy dai,Sayyah tace waye wannan haka wani hamshaki? Mijina ne,Sayyah tace kut dama kece matar Aayan Muhd Jabeer ta yanzu? Nace ae mana kin sanshi ne? Tace a labarai muke ganinsa a TV kuma akwai wata yar kawar Umma yar gidan Minister of finance ta Dade tana binsa tana sonsa sosai ta dinga kiransa duk inda yake sai ta nemeshi amma Sam ya dinga Wulakantata baya sonta,har yanzu bata hakura ba wlh sonsa takeyi,akwai ke yan mata da yawan gaske da na sani suna bibiyarsa don kawai ya kulasu amma ko sauraransu baya yi,nan take gabana ya fadi, bakin ciki ya taso min na fara masifa wlh idan ma kin Santa ki fada mata kar ta kara kiran wani da namiji a waya,aikin banza amma wannan kwai jaka, dabba, Akuya, tinkinya inba tsinanniya ba mene na bin mijin wasu a waya asararriya wacce ta rako mata duniya.

   Sayyah shuru tayi tana kallon yanda na dage nake ta zazzaga masifa da zage zage,tace lallai kishinki yayi yawa,nace ai ba kishi nake ba kawai haushi ta bani mace na bin maza tana zubar da ajinta,Dariya kawai Sayyah tayi tace to nidai na koma class tunda mijinki ne bye ta juya abinta,a hankali naci gaba da tafiya kafin na karasa motarsa kawai ya fito ya tako har inda nake tare da kamo hannuna ya jani ya sani cikin mota ya shiga Suka ja motoci muka bar schl din gaba daya.

     Nace lfy?bafa mu tashi ba,yace ae ni na tashi daga Office yau kuma abinci nake so kiyi min 5pm Yarima Bobo zaizo, shuru nayi ina gefensa a baya nayi shuru har muka karasa gida muka fito da sauri ya rike hannuna yana Jana fiiii,har cikin part dinmu,Hijab ya zare min ya kaini har kitchen yace fara masa Abinci me kyau yana son Founded yam da miyar kwai,nace to da sauri na fara aikin shi kuma ya fita,nan danan na shirya lafiyayyan Sakwara da miyar kwai tasha nama da alayyahu tayi dadi sosai,na hada lemuka kala biyu na zallan fruits me dadi yayi Sanyi,na shirya komai a Dining sannan na gyara kitchen din tare da kara gyara part din sosai.

   Bedroom na koma tare da fesa wanka na shirya cikin wata Atamfa cotton Orange riga da skert na Sha kyau sosai nayi kyau na gasken gaske,ina kamshi na hau Saman bed dinmu na kwanta ina hutawa 15mnt sai gashi ya shigo sanye cikin jallabiya fara yace muje Ku gaisa,na Mike haka nayi hanyar fita,
    Ya riko hannuna tare da juyo dani baya yace haka zaki fita? Nace mene to a nan?nayi waje abina a haka,da sauri ya jawo ni tare da cewa ki canja kaya bakiyi kyau ba kisa doguwar riga,banyi musu ba nasa Arabian Gown tare da mayafin kamar Balarabiya na fita har Palon da suke.


AsmaBaffa
Reply
#6
[1/19, 16:50] Sayyida Hauwa: ????
????

   KASUWANCI NA





             56-60







Official






By
AsmaBaffa






    SEEYAH IBRAHIM and UMMU SOPHIE ths page is for u tnx.








        A kunyace na Zauna a daya daga cikin kujerun palon nima sannan nace Ina yini kazo lfy,cike da fara'a ya amsa lafiya Alhmdllh Madam, daga mari kuma sai kuka koma Ma'aurata, murmushi nayi tare da cewa ai ka fini Sanin komai,dariya yayi yace gaskiya dai ai nasan watarana in kika ji labarin yanda na tsara sai kin bani gift ma,ya dai baka gift tunda Ku kuka San me kuka tsara,Aayan dai yana jinmu bai ce komai ba na Mike ina cewa ga abinci Fa yana Dining ko na kawo ma nan? Yace ai dole naci girkin Amarya guda kamar ma kin San yunwa nake ji,kai tashi Malam naje naci abinci.
   Mikewa sukayi har Dining suka zauna nayi Serving dinsu, Yarima sai murna yake yi abin cin da yake so ne,suka fara ci Lauma daya Yarima ya fara Santi uhmm kaga yar yarinya da iya girki shi yasa naga mutumin sai kiba yake yi da kyau, Dariya nayi wace tasa nayi wani mugun kyau.

    Tsaki muka ji ya ja tare da gasa min harara,shuru nayi tare da sadda kaina kasa,kallona yayi tare da cewa je bedroom ki dauko min wata paper saman Bed,ok nace tare da mikewa zan tashi kawai na bige flask din miya ta dan zubo min a hannu ga Zafi sosai,hannuna na yarfe tare da cije lips dina,da sauri ya Mike tsaye tare da rike hannun nawa yana min sannu ya tsotse min yatsun da miyar ta zuba yana hura min da bakinsa kuma fuskarsa ba alamar rahma Sam sai ma fushi da yakeyi,ni dai kallonsa kawai nakeyi har ya gama ya kalleni tare da cewa ba Zafi? Kai na daga tare da cewa yeah,jeki to ki kawo min.
   Ina tafiya Yarima ya dura masa ashar yana cewa amma kace min wani fada ma kukeyi munafuki,to me nayi na wani soyayya a nan? Ku fa bakwa ganewa Hausawa ba dama aga mace da namiji sunyi ko magana sai ace wani love ni zan iya kwana da mace same Bed naked ma ba abinda zai faru.

   Dariya Yarima ya dinga yi yace Allah ya taimakeka ba kyau ganin sirrin wani da sai an gwada na gani a gabana,kai har kana da bakin magana dan Iska da ban sanka bane sai ka fadawa wani abinda har wani Fyarfadiya kakeyi idan ta ciwo ka shine zaka zo kana min kuri,Dariya  Aayan yayi tare da lashe lips din kasa kamar an tuno masa wani dadi daya taba ji yace lfy ce yaro,Kai aka bawa wahala wlh tunda kana iya sha'awa amma baza ka iya aikata komai ba akwai wahala abin har tausayinka nake ji frnd,Aayan yace kama daina tausayina yaro ni ba abinda nake ji,suna ganin na fito sukayi shuru tare da canja hira basu San naji komai ba,mika masa nayi na zauna kusa dashi a Dining din nima harda leka cikin paper daya bude nace mu gani,miko min yayi sai da ya bari na karba yace to ki rike du tunda Sa'idon naki ya kai haka,Murmushi nayi  tare da mika masa nace amma da niyyar karantawa nayi tun a dakin zan tsaya na duba yanzu ma izininka nake nema,yace bazai karba ba Sam yayi fushi na masa shishigi, mikewa nayi da paper zan tafi ya jawo hannuna ta bayan kujerarsa na zagayo  tare da zuro kaina a hankali ta saitin kansa fuskata na daura a wuyansa nasa hannayena tare rungumesu ta kirjinsa sannan na rada masa a kunne ina dariya ga paper dinka Dan Daddy mene na fushi na daura saman table din na juya tare da barin wajen na shige Bedroom.

    Yarima yana ta dariya yanda yaga Aayan yana jin kunyarsa,yace ah to yarinyar nan naga Alama wise ce kai a boye kake yi kana mana karya gashi ita wlh ta birgeni baka taba auren ma irin wannan kalar ba sauran tsoronka suke ji magana basa iya yi maka,haka idan munzo basa iya zama a kusa da kai tare da bakinka lallai kana kwasar Harka wlh ga shawara ka fara tunanin fara Sex da wannan maybe ma ka warke kake batawa kanka lokaci, Allah kiyaye da wannan yarinyar karama ai sai na balla mata Hips cewar Aayan,  nan dai suke ta faman zancensu ban san me suke shiryawa ba sai tafawa suke suna dariya.

    Bayan kwana Uku muka shirya dasu Meenat mukaje tsohuwar unguwarmu tare da gaisawa da abokan arziki a dalleliyar mota,kowa mamaki yake,Nawwara ma yanda taga mun canja mun koma yan gayu ga hutu ya nuna a jikinmu ta dade tana mamaki, na bata Address na gidan mijina,Haka Uwaliya still suna zaune a gidanmu nace su zauna sai nan gaba zan gyara gidan.
    Mun shirya dasu Meenat idan anyi Hutu zasu je Maiduguri dangin babanmu tare da Rimin Gado dangin Ammah can zasuyi Hutu sabo da zumunci kuma muna kiransu a waya muna gaisawa.
   Tun daga Ranar da Aayan yayiwa Kwaja magana bai kara yiwa Meenat magana ba sai dai idan ya ganta a gefen gate ya fara lashe lips yana mata signa da ido ita kuwa sai tayi kamar bata gani ba.

    Ana haka wataranar Asabar sun dawo daga Islamiyya sai ga wani ya Parker a motar eban kaya wacce ake cewa yar Kurkura ya fito ya taresu a hanyar gida,wani dan Gajere daf da kasa kamar a kifeshi da kwando me kwalelen kai sai ka rantse baza a samu Hula size din kansa ba,harda sa wata barmemiyar suit tsohuwa tasha duniya,Handkerchief ya zaro tare da goge wani kwafjejen takalminsa ya kalli Meenat yace Hajiya Meenat ko? lfy Malam idan tambaya kakeyi kayi sauri muke,murmushi yayi tare da cewa yan mata kenan wato Allah ya zuba baiwa a nan wajen yana maganar yana watsa hannayensa kafta kafta yan gajeru dasu kutuf ,ya kara cewa Allah yayi Kudirarsa anan,baki ya rike yace kai Kudirar Allah kenan,harara Meenat ta maka masa,Maeesha ma taja tsaki yace ahh harda ke yar ficika? kema kin hadu har kinfi babbar ma naga kinji haushina ke ban yabeki ba mata akwai kishi to kema kina da kyau ai baki sani ba kinfi ma babbar kyau shike nan ko?

    Saura kadan Meenat tayi dariya kawai taja hannun Ma'eesha sukayi gaba,da gudu ya datse gabansu,in kina kaunar Allah ki saurareni in dai akan nace kanwarki ma me kyau ce to na janye dama dan kar ranta ya baci ne ace kamata bata ji yabo daga gareni ba naga tana kumbura shi yasa amma ai kin fita komai,kinga gaki fara,gaki doguwa yar tsakiya,ga sura,ga idanu,ga kamshi gaki me ilmi wayyo sai naji dama munyi aure,Meenat ta kara hade rai tace bamu hanya mu wuce,ya wani shagwabe fuska tare da canja murya kamar dan iska zan miki shagwaba Allah wayyo Baby,ai basu San sanda suka sheke da dariya ba,shi kuwa gani yake ai yaci gari ya birgesu,yace kin gani tun ba a je ko ina ba,ina me tabbatar miki zaki san Allah ya baki miji na gari,zan miki soyayya,zaki ji dadi,zan baki kulawa,zan miki duk wani abu wanda mace take so take nema a duniya komai,kawai ki bani dama,ki kula dani ki yarda dani zaki ji dadi,sai kinyi alfahari da wannan rana ta Asabar da muka hadu,da ace ana harba namiji sama ina tabbatar miki idan muka yi aure nasan sai kin harbani sabo da yanda zaki koma sona da ganin mutunci na,

   Bari kar na dameku da surutu sunana Nasuru ko kuma ki kirani da OPERA,amma a unguwarmu anfi kirana da Nasuru me Hali, yayi dariya ya kara goge rigarsa yace Business man ne ni ina da yara dasu ke ci a karkashina sanadiyar wannan motar da kika ganni da ita domin daya a yarana shike Jan wannan motar,mutum biyu kuma sune masu tayashi lodi da saukewa,ba inda basa kai kayan miya da fruits,irin su tomatoes,Kankana,ke in baki a takaice har yalo suke daukowa daga Sumaila zuwa Lagos Agege, da sauransu,Meenat taji baza ta iya ji ba ta figi hannun Ma'eesha suka barshi nan tsaye bakin gate,suna shiga suka hango Haneefa da Sajeeda sun labe ta jikin gate suna ta dariya da alama Nasuru Opera ma su suka turowa Meenat shi tunda sunga an kori Kwaja.
    Meenat ta hararesu su, sai kuma suka sheke da dariya Sajeeda tace a haka zaki kare in Allah yarda sai dai ki auri irin wannan wai ku masu kyau,anzo gidan daula za a ce sai me kudi zaku gani wlh nan gaba da kafarku zaku bar mana gida.

   Meenat tayi murmushi sannan tace masu gida manya gidan wasu dai har iyayen naku basu da gado a nan bare Ku,a haka zaku kare banzaye marasa class,tass Meenat taji saukar mari tana dagowa taga Mujaheed ne ya mareta gasu Ameer nan a tsaye suna huci,Ma'eesha tace Allah ya isar mana,aiko Mujaheed ba imani kato dashi ya zage ya dinga Marin Ma'eesha yar yarinya karama ya Ciro takalmi ya fara kwada mata ta ko ina tana ihu,Meenat bakin ciki yasa ta dauki wani dutse kato ta buga masa a kai nan take jini yayi tsartuwa a kansa ya fashe,ya Dafe wajen yayi baya Su Ameer sukayi kansa suka rikeshi,Kafin kace me gida ya dau Alert sai kowa ya fito harda Hajja,Su Meenat tuni sun arce part dinsu da gudu,lokacin Mufeeda ta fita shopping,Hajja Bala'i take zubarwa kawai a tsakar gida an kashe mata jika,haka Ma su Abbi sai gasu duk sun dawo da motocinsu gida,haka ma iyayen su Mujaheed mata har da kuka,aka daukeshi sai asibiti don tuni ya Sume,sabo da hauka gaba daya suka bisu asibiti kamar wani Gomna haka dukkan yan gidan,Matar Abbi da Hajja sai Haneefa su kadai ne a Compound suna jimami tare da shirin daukan fansa,suna cikin wannan Hali sai kicif ga Driver na mun dawo daga shopping tun daga yanayin da na gansu gabana ya fadi haka na daure na fito ban fito da kayan dana siyo ba sabo da nima cikin shirin ko ta kwana na fito,ina taku dai dai nasha wanka sosai,

Ban san me ya faru ba,ba zato naji sun rufeni da duka,sunfi karfina ma'aikata si hakuri suke basu amma suka ki ji musamman Hajja kamar mahaukaciya ta dinga dunkule hannu tana dukana,Haneefa da takalmi me tudu,Matar Abbi ma ta ko ina,har sai da Hanci na ya fara jini ina habo, ana haka matar Abbi ta kara dauko Wayar charger tace duk kowa ya kyaleta dani sai ta ramawa Danta haka ta dinga tsula min wayar nan  sai da suka min lilis,da kyar nake iya numfashi,sai lokacin hankalinsu ya kwanta suka koma can part dinsu suna murna.

    Ina kwance a wajen hancina na fitar da jini sai ga Aayan ya dawo ya iskeni haka,da sauri ya daukeni kamar Jaririya don shi yasan yan gidan ne suka min haka,kawai ya sani a bayan mota shima ya shiga gefena Driver yaja da sauri sai Hospital,a motar ya kwantar dani saman cinyarsa yana min sannu duk ya damu ya rude,Hadadden asibiti ya kaini,suka min allurai da karin ruwa sannan suka bamu magunguna ya siya,na danji sauki da karfin jikina,ina tsaye zamu tafi ina cije lips ya tsuguna a kasa yace hau baya na, na kaiki cikin mota,bayansa na hau na lumshe ido sakamakon wani dadi da sanyin Ni'ima naji ya ratsani shima bangarensa hakane,haka ya dinga taka Steps ana ta kallonmu har mota ya kawo ni ya sani ciki a hankali shima ya zaga ya shiga Driver yaja muka tafi,a hankali ya min magana ko zaki kwanta cike da shagwaba ina Hawaye nace ae zan kwanta da muryar Kuka,saman kirjinsa ya kwantar dani kaina yana kirjinsa ina shakar kamshinsa ina Kukana wanda ba iya na ciwo bane harda shagwaba ma ta samun waje, hannunsa naji a fuskata yana share min Hawaye tare da lallashina to kiyi shuru haka ya Isa Ok, kai na daga Amma ban daina Kukan ba,yasa harshensa cikin kunnena nan take na dauke wuta wani mugun azabar dadin da ban taba ji ba shi naji,da Sauri na kankameshi tare da cewa wayyo ka bari yanda nayi maganar kamar me rada,nan take jikinsa ya wani amsa yarr, a hankali na daura lips dina saman wuyansa ina ta shagwaba, yana lallashina kiyi shuru kinji zan rama miki,nace to ka rama min ka samu Haneefa ka zaneta a gabana, yace zanyi miki sai nan gaba idan ta manta tayi miki haka,dole zan rama miki kinji, nace to sosa min gashina, ba musu ya fara sosa min gashina ina lumshe ido. Muna karasawa gida nan ma ya goyani suna kallonmu don lokacin sun dawo daga asibiti suma,ba damar yi mana magana suna tsoron Aayan haka muka wucesu, muna shiga yace ebo kayanki tare da su Meenat kowa akwati daya daya Sauri ku fito,gabana ya fadi ko korarmu zaiyi Amma sai na shiga muna hada kaya suna bani labarin abinda ya faru tun farko nima na fada musu abinda suka yi min.

  Muna fitowa da akwatunanmu Uku shima muka ganshi ya sha wanka da trolley ya fito,duk muka kashe kayan wuta da komai sannan ya kira wasu ma'aikata suka zuba kayanmu a mota,yace muje wajen Daddy, muna zuwa muka gaishe da Daddy yana ta murna ya amsa yana tsokanar su Meenat,yace sai kun dawo Allah kiyaye hanya,ban san inda zamuje ba nace Ameen kawai na janye hannun su Meenat muka fito Sabo da mu basu waje suyi sirrinsu na yaro da Mahaifi.

    Muna palon kasa ya dan dade sannan ya fito yace muje,ni da shi muna mota daya,Meenat da Ma'eesha ma suna mota daya can wata unguwa muka nufa me shegen nisa gata ba wasu gidajen kirki,kalar gidajen kamar na yan mafiya ban taba sanin da irin wannan unguwa ba sai dai ta hadu karshe.
    Wani rantsatsen gida muka shiga idan na tsaya fada muku yanda tsaruwarsa take zaku sha mamaki ina kuma mamakin yanda Aayan zai dawo damu nan tunda Daddy yace Hajja baza ta bari ba zata iya tsine masa,ashe kuma Hajja ce da kanta ta sanarwa Daddy ta gaji da jarabata ta gaji da ganina a dauke mata mu daga gidanta zuwa wani dan lokacin da zata bukaci a dawo damu Family House Amma yanzu mun gallabi rayuwarsu a gidan,wanda ba kowa bane yayi wannan zugar Sai Ameer Sabo da yana wasu shirye shirye a kaina.

     Gidan da ma'aikata masu kula da komai babu wani gyara da zamuyi komai Neat,Daki daya na sama muka dauka shi kuma Aayan yana hawa na biyu,Meenat tace Sis shawarata anan dayace ki koma ku dinga kwana room daya da Mijinki ki rungumi abinki ki fara auren nan da gaske,kisan damuwarsa yasan taki,ki kula da abinki,tunda yana da lalura baki sani ba ko zai warke,amma wannan abinda kikeyi ba mafita bane,meenat ance miki so na yake? So kike na kai kaina ya wulakantani watarana,wlh bazai miki ba Sis ki duba yanda ba so tsakaninku Amma kalli yanda yake mana Gashi mutimin kirki karki bari wata ta kwace miki miji ki dage ki koya masa sonki Sis.

    Harara na watsa mata nace Allah ya kiyaye na zubar da class dina zan dai dinga zuwa ina tayashi hira iya abinda zan iya kenan 11pm na dawo muyi bacci tare daku,Meenat ta dinga rokona nace Bazan iya ba ni iya kacina tayashi hira idan baya bukata itama na ki zuwa,haka ta kyaleni.

    Da ruwan zafi nayi wanka Allah yasa habo kawai nayi basu fasa min jiki ba banyi rauni a jikina ba,kamar ma basu dakeni ba tunda Habo nayi sai ciwon jiki,Meenat kuwa sun fita kallon gida suna zagawa,na fito daga wanka Daure da guntun towel ya shigo tare da ajiye min ledojin take away har guda biyar yayi gaba ba tare da ya kalleni ba, sai da muka ci muka koshi sannan nayi brush na shirya cikin riga ta dan wuce gwiwa kadan,karatu mukayi sosai Amma Meenat ta dameni sai naje dakin Aayan wai ko hira na tayashi,Maeesha ma ce min kije pls Sis,na zura hijab zan fita ina cika ina batsewa,Meenat tace haba Mufeen Ammah kamar baki waye ba me yasa kike abu kamar yar wajen gari ne wai? Shi yasa akace akwai dan birni a kauye a birni akwai dan kauye, ai sai ya dinga raina ki yana ganinki a baki waye ba,ni kuma sai nace ae haka ne to ya zanyi kenan? Meenat ta mike tare da dauko wata yar Ficikar riga da wando wanda da kadan ya rufe mazaunai rigar ma iya mazaunai take me hannun siririn hannu ba sai da bra ba domin an mata abinta,ba karamin kyau nayi ba dama gasu green dasu, Meenat ta kara gyara min gashi tare da fuskata, kamar wata Baturiya haka na fito,dan girgiza Mazaunan naki mu gani,hararar wasa na balla mata sannan na shafa turaruka na sa Hijab dina har kasa na musu sai da safe Meenat tasa key a kofar su ni kuma nayi samansa.
    Koda na je ban san wanne Bedroom ne nasa ba haka nayi ta duba dakuna sai can na bude wani naga Hadadden Palo na gaske yasha kayan alatu kida na tashi sosai har tsakiyar kai da alama speaker ce a palon,a 3seater na hango shi kwance yayi wani dai dai dashi yana karanta Magazine,sallama nayi kusa dashi ya amsa ba tare da ya kalleni ba naji yace ya jikin? Nace da sauki,shiga kitchen gashi nan ki hado min Ginger tea,dama ban zauna ba na shiga kayataccen kitchen nasa na daura tukunya, wata waka ta Yan Nija ta ratsani sabo da shegen dadinta na cire Hijab din na ajiye gefe ba wata rawa na iya ba amma kidan wakar yaci ace ko kaine an girgiza mata,nan take na fara rawata nace in dai hakane zan koyi rawa kwanan nan, can na manta da wani tea saman gas ina ta shagalina a jikin fridge,har ya gaji da jirana ya nufo kitchen din da kansa sabo da so yake ya Sha ya kwanta bacci,yana zuwa yayi arba da shegiyar shigar dake jikina sai girgiza jiki nake ni dole sai na iya rawa,dariya abin ya bashi har wakar nake bi da bakina dan abinda naji suna cewa,saida ya gaji da kallo na kawai ya tako lokacin ina jikin gas din amma rawa ta nake,hannun mutum na gani ta gefe na yasa tare da kashe gas din ya dauke Pot din dake kai ba tare da yace min komai ba,ni kuwa kunya ce me tsanani ta kamani da sauri na maida Hijab dina ina kame kame kamar nayi karya,A kitchen din ya zuba sugar sannan ya dauki abinsa yayi waje ya barni a nan tsaye cike da kunya sai da na Dade sannan na fito Palo baya palon da alama yana Bedroom,Na dade a Palon daga karshe na Mike na kashe komai na nufi Bedroom dinsa,lokacin tuni yayi shirin baccinsa yana saman Bed amma ba bacci yake ba System ya kunna yana aiki, a jikin kofa na tsaya ya kalleni yace shugo mana ki kwanta ko ba a nan zaki kwana ba? Kunya ta rufeni na daure dai na karasa Saman Bed din tare da haurawa can sama,muryarsa naji yace ba a sa Hijab a saman Bed dina,a kunyace na cire tare da linkewa na Mike na saka cikin Sip sai kallona yake yanda kayan suka min tsantsan kyau.

     Dawowa nayi ta gabansa na koma saman Bed din kansa ya sosa ya dan tsaya da danna system din sai kuma naga yaci gaba abinsa, zo ki gani naji muryarsa a hankali na zauna a bayansa tare da leka kaina cikin System din wasu zanen gidaje guda uku yace wanne yafi kyau a nan na kalla nace wancan Blue din yafi,ashe kin iya Zabe yace,ina bayansa bai San na zo daf da shi ba ya juyo da niyyar yi min magana ai ko ya gogi kirjina da gadon bayansa,ban san sanda numfashi na yayi sama ya dawo ba,shima wani shock yaji kamar electricity da Sauri ya kashe Laptop din ya ajiyeta gefe, duf naga ya kashe light duhu dundum ya gauraye dakin sai kamshi da karar Ac ke tashi,gaba daya jikina ya mutu ji nake kamar na shige jikinsa ina wannan tunani naji shi kusa dani ya kwanta tare da cewa kwanta mana me kike tunani,nace ba komai na kwanta nima gaba daya rabinsa a jikina ya kwanta tare da daura kansa saman Boobs dina,ban san sanda na daura hannuna saman sumar Sa ba me uban yawa da laushi,a hankali nake wasa da ita,kara makaleni yayi sannan a hankali yace yau me kika yiwa su Hajja haka? Cin Zaline kawai na bashi labari har abinda ya hadasu dasu Meenat tare da dukan Ma'eesha da sukayi.
   Ransa ya baci yace Ok zanyi maganinsu so sorry for tht ya furta kamar me rada tsigar jikina ta tashi yarrrrrr nace ba komai ya wuce, yanda ya haye min jiki da Alama son jiki ne dashi kamar mage maimakon ni  ya daurani saman jikinsa sai dai shi ya hau nawa ya wani lafe yana narkewa.

       Gefen fuskarsa ya fara gogawa a tawa yana kara kankameni yana shidewa,ban san sanda na lalubi lips dinsa ba yana jin nawa saman lips dinsa da Sauri ya amshe ya fara tsotsar bakina kamar zai tauneshi ya huta,Wuyansa nake murzawa a hankali da hannuna,hannu yasa tare da zame rigata kasa,na
Tsorata Amma na tuna bashi da lfy bazai iya min komai ba sai Romancing shi yasa ban damu ba na saki jiki,Hannunsa naji a kirjina yana shafasu cike da Salo na kwarewa,na gama fita daga hayaccina dan ban san abin haka yake ba sai yau,taimaka masa na farayi sosai nima ina masa abubuwan da ban san a ina na koyesu ba,kokonto na fara yi anya kuwa wannan bashi da lfy? Gashi gaba daya gawurtaccen lafiyayye komai yana matsawa ace bashi da lfy,kai ban yarda ba,jikina na zame daga nasa ya kara shigar dani jikinsa gaba daya ya haukace kalaman da yake fada sun zarta hankalina ni nasan na karya ne dan kawai yana cikin mayen dadi ne,
   Ganin da gaske bana so sai ya hakura ya kyaleni Amma yana jikina ya hanani maida rigata daga mu sai dan wando wasa kawai yake da kirjina Salo daban daban wanda karfin hali kawai nakeyi ina daurewa Amma na kai karshe da zan kasa Control,a hankali murya na rawa yace Ki bari a gwada ko na warke pls,na fashe da kuka ni ban yarda ba, to mene abin kuka tunda bakya so Bazan miki dole ba,shuru nayi sai ya bani tausayi yanda ya dade yana shan wahalar mata data rayuwa kawai sai nace na yarda ka gwada tunda hakkinka ne, da zafi zafi yake sarrafani nima Sabo da abinda yake mun na kasa Control nima biye masa nayi bare nayi Control din kaina,tunda ya fara sucking mini Down na zauce na susuce na fara yabon halayensa, ina Common Baby u r so Sweet, ina kukan dadi iri iri wanda na kara birkita masa lissafi har nan take ya fara neman hanyarsa,amma gaba daya nan take ya dawo normal ya daina sha'awar ba tare da ya biya bukatarsa ba,naji ya kwanta a gefena kawai,nace lfy?Yace kawai i can't, wani tausayinsa ya kamani,nace dama haka kake? Yace hmm kin gani da idonki,shi yasa ban son aure Sabo da zan zalunci mace,amma Daddy yace na aureki,kiyi hakuri kar ki soni ni dama Bazan so wata ba Sabo da bata lokacina zanyi kawai wace zata zauna a haka dani,yana ta Surutai da gani cikin bacin rai yake,na koma jikinsa tare da shigewa kasansa nace kwanta ina lallabashi kamar kwai ya kuwa kwantar da kansa a kirjina yana tunani,ina shafa bayansa na Lallashi  nace zan zauna da kai haka,in dai akan wannan ne ni ban damu ba iya wannan romancing ya isheni,yarinya ce ke shi yasa kike ganin iya wannan ya isheki,kirjina na hada da nasa nace Allah zan iya kawai ka daina damuwa Insha'allah watarana sai lbr zaka warke yace Ameen tare da kara nutsar dani a jikinsa, yanzu me kike so na kara miki irin na dazu?, Nace ae amma Idan kaima kana so sai nayi maka cike da kunya nake maganar,shi kuwa murmushi yayi tare da cewa alright.
    Wannan ba ance sai ana son mutum ake masa ba? Yace me? Nace abunda mukayi dazu kuma ai mu ba soyayya muke ba,au haka ne fa? ya fada yana shafa wuyana zuwa kirjina, kwanciya yayi tare da kwantar dani a kirjinsa,a hankali nace a Sa min riga ta pls,Yace to ya dauko kuwa ya saka min a jikina,kina so mu rabu kika ce ko? Gaba na ya fadi sai naji bana son rabuwa dashi sam,dan kar ya gano ni sai nace taya zaka ce haka bayan ka gane min Tsaraici ka tabani,Murmushi ya saki tare da cewa ni fa da kika tabani? Nace tunda Business mukeyi sai ka biya kudi shike nan,nawa zan baki? Na tsaya na gama tunani nace tunda ka biya Sadaki an yafe maka wannan,dariya ya dinga yi tare da cewa Na taba na alakoro,No Sadaka na maka iya yau banda gobe,ni kuma wanne na baki? Ai ni banji komai ba,uhm karya ko kinga me kike min kuwa ko na fada kiji ya bude baki zai gwada yanda nayi masa da Sauri na Sa baki na saman nasa, murmushi yake tare da cewa yaushe kika iya abubuwan nan a ina kika koyi wannan abun bayan ke yar yarinya dake ba wayo ba? Dariya nayi tare da cewa ka bar ganina haka wannan ai ba sai an koyawa mutum ba kawai ji ake an iya,na iya da yawa ma da ace shiri mukeyi da kai ko Love to da sai na kwance ma kwakwalwa,Dariya yayi tare da cewa to mu fara shirin mana daga yau,ko love din ne sai ayi na kudi kullum zan biya mu fara Drama kamar film a gaban kowa kuma,amma a zuciyarmu mun san Business ne ko? Sabo da naki dadin abin sai na wayance irin zan masa wayo mu dinga shan dadi ,sai na karbi maganar nace to na yarda yanzu soyayyar wasa zamu dinga yi kuma itama cikin kudina na kasuwanci,a ransa yana tuna rashin wayona yana dariya yace lallai zaki sha kudi karfa ki karar min da kudi,dadi ya kamani zan masa wayo da yawa na dinga shan dadi na,nace karka damu kadan zan dinga amsa,yace to cikin kudinki gobe zamu fita shopping da kaina zan kaiki.

   Ai kuwa farin ciki ya kamani nace Allah ya kara budi Ranka ya dade,a hankali nace Yanlabai a Sa nayi bacci cikin kudina ka zame dubu Uku tunda na saka aiki nima,dariya abin ya bashi yace to shike nan cikin kudinki na Kasuwanci zan cire kudina tunda yanzu ke kika nema,nan ya fara min wasu Salo a kunne na yana lallabani kamar masoyan gaskiya,na kara yin wata mika yace har naci dubu biyu,nace a'a ai banyi bacci ba dubu daya da dari biyar kaci dai,Dariya yake ta min ni ko lokacin hankalina baya tare dani ban san sanda nayi bacci ba.

     Washe gari da Safe Hajja tayi shiri sosai ta je wajen Daddy yana kwance ta dinga zuba masa masifa da zage zage karshe tace wlh wannan yarinyar da kasa ya auro mana Sabo da mugun halinka Sabo da baka kaunar yan uwanka to wlh sai nayi fata fata dasu,ka fadawa Danka tunda ka Isa dashi tun wuri ya fara shirin sakin wannan matsiyaciyar ko kuma kai ka fuskanci fushina,kar ma kasa ya saketa kyaleshi da kaina zanyi maganin abin ka sanni kuma ba a taka ni a zauna lfy,haka Hajja tayi ta sambatu har da na mahaukata ma kamar sabon kamu,ficewa tayi a fusace sai wajen Matar Abbi nan ma tana takama da gadara tace Karimatu jiya wanne yan iskan ma'aikata ne suka dafa min cabbage soup dinn nan me bauri Maggi har saman kaina,ke kuma da yake shashasha ce kika bari suka kawo min Sabo da kun rainani,nice na Haifa muku Mazajen da kuke aure dai baku Isa kun canja musu Uwa ba yan iskan surukan Zamani mutum da yayansa ace za ayi maka iko dasu,matar Abbi da yake Hajja ta shanyeta haka ta durkusa tana ta bata hakuri,tsaki taja ta figi Jakarta tare da fadawa kitchen ta dinga cin uban yan aiki kamar zata yage bakinta sai da ta gaji tace ta canja dokar gidan taga cewar yan aiki suna nema a hada baki dasu a kasheta jiya an mata girki da farin Maggi me hawa kai dan ta kusa suma.
  Tana gama masifarta ta hau mota Driver ya kaita har Airport sai Taraba state can kauyensu zata je wajen bokayenta wanda take ganin kamar malamai ne na Allah ka h.



  
    





Bakwa Sharhi fans








AsmaBaffa
[1/19, 16:50] Sayyida Hauwa: ????
????

   KASUWANCI NA






          61-65






Official







By
AsmaBaffa









      Page nakine Zainabsanusi78 Allah ya bar kauna.


    Godiya da jinjina me tarin yawa TASKAR SURAYYARHMS na gode da Sharhi kuna kokari, haka ake son gp.







        Bata zarce ko ina ba sai wani kungurmin kauye wanda mota bata shiga sai dai ka sauka ka hau machine a karasa da kai wata hanyar ma sai dai ka karasa a kafa,wata yar bukkar kara ce kamar ta Fulani, daga kofa Hajja ta tsaya tare da cewa Gafara dai Malam,yace Allah ee Mana Hajiya kece tafe yau? Hajja tace ae Wlh Malam ta furta tare da shiga dan karamin dakin,gefe ta zauna suka gaisa yana ta faman washe baki,tsoho gashi wani mugun kazami bakinsa duk goro yana yauki,hakora Yellow dasu shar in banda wari ba abinda yakeyi, farcensa zako zako kamar na kanti duk dirty a ciki,suma duguzum da wani lalatattun kayansa,yace Hajiya da Alama wata rigima ta taso ko,Hajja tace kwarai kuwa abinda ya kawoni kenan da waya zan maka Amma zuwa da kai yafi Sako, ko ina a dakin wasu litattafan ne na  sunayen taurari da Alama taurari yake bautawa dasu yake aikin shirkarsa.

    Hajja tace Malam kasan idan aiki babba ne bana bukatar a duba min,bana bukatar a hango min meke akwai dan kar ma naji wata matsala,kawai aiki na kawo cikin Uku ayi daya,wannan takadarin jikan nawa Aayan,kasan yayi aure to matarsa naga tafi karfina irinsa ce bata da kirki,nan take yace ba sai kin karasa ba na san komai, tace to aikin da nake so shine ko Ya saketa har abada kar ta dawo hannunsa,idan bai yuwu ba ya kara aure ta koma baiwa,idan bai yuwu ba ya tsaneta inda take kar ya raba ko ita ta tsaneshi da kanta,Malam ya dago yace me sauki kenan Amma bari muji abinda su zasu ce ayi wato aljanun da yake aiki dasu kenan,littafin taurarinsa ya bude da carbi sai wata kwalabar turare yayi shuru yana kallon littafin sai daí kaga bakinsa na motsi yana magana shi kadai yana to..to...ae...yawwa...ae...uhum...uhum..suna bashi Umarni kenan.

  Sai da ya gama sannan ya dago yace Hajiya baki taba kawo aiki me wahalar wannan ba,da farko dai sunce jikanki kullum cikin addua yake baza su iya shiga jikinsa ba ko sun shiga wahala zasu sha,na biyu kafin ma su shiga jikin nasa zasu kwashe shekaru suna fakonsa sai ranar da ya shagala da duniya sannan su shiga,ko sun shiga din dole fita zasuyi da kansu, aikin kuma bazai yuwu ba sai dole an shiga jikinsa,sannan ita yarinyar idan an Sa ta bar gidan Jikanku shi zai sha wahala ta dalilinta zai iya rasa ransa ita kanta yarinyar ba a zaune take ba kullum Azkhar take ba fashi,kuma kin san asiri ma yana tadda hali wannan taurin zuciya ce dasu gaba daya idan ma anyi suna da karfin zuciya,amma abu daya za ayi shine a hanasu kwanciyar hankali da zaman lfy idan kin yarda idan kuma kina ganin bai miki ba to fa a wannan lokaci sai daí kije wajen wasu duk rashin Imani na wannan yaron yasha kaina,dama kuma nasha fada miki,Hajja ta nisa tace ita yarinyar a batar da ita ko a haukatata mana gaba daya in yaso Shi ya kashe kansa dan ubansa,Malam yayi dariya yace Hajiya har yau kina nan da Halin nan naki na mugunta Amma kije zamuyi iya kokarinmu,ni kuma har India zan kira manyana dole ko ta yaya ne sai an miki abinda kika ce kina so,tunda kin yarda ko mutuwa ma jikan naki yayi baki da damuwa, Nan Hajja tace da dai yafi a dage sosai ta zube masa makudan kudi ta bar wajen,tayi waya da malamai da dama duk akan aikin sannan taje wajen wasu ma sunfi biyar Sabo da a hada karfi da karfe kuma sun bata tabbacin ba matsala.

     Makara mukayi don har rana ta fito bamu sani ba muna manne da juna muna bacci,lokacin Meenat har ta hada Breakfast da komai,Maeesha kuwa gyaran gidan ta fara kasancewar yau Ba schl,ni na fara bude ido na da kyar na iya zare jikina cikin nasa sabo da gaba daya ya makalkaleni ta ko ina ko juyi bazan iya ba,wannan ne ya tashe shi daga bacci,muna hada Ido na runtse ido, kawai sabo da kunya,Murmushi ya saki har ina jin sautinsa da sauri na sauka daga Bed din na shige hadaddiyar toilet dinsa nayi Brush da wanka kana na dauro Alwala na fito dan guntun Towel dinsa na daura na fito ina goge gashina,yana Saman Bed ya tsaya sai kallo na yake sannan ya mike shima ya shiga wanka,kafin ya fito na idar da Sallah na shafa Lotion dinsa tare da turarukansa har gashina na gyara shi sosai ina haka naji muryarsa yace kawo min Towel dina ko ki bude Wardrop ki miko min new, wai dan kar a bata kaya da yawa nayi Sauri na dauko Jallabiyarsa fara nasa dan tight short dinsa na Sa Jallabiya ba karamin kyau nayi ba duk da tayi min yawa kowa ya kalleni yasan nayi kyau.

   Toilet din na nufa na manta kawai na murda Handle na shige gaba daya da Sauri ya juya min baya yana ta masifa ban kalleshi ko daya ba na fito da gudu nace kayi hakuri mantawa nayi wlh na kara dan tura kofar na dan tura hannu na tare da  mika masa ya karba ya zuba su a washing machine sannan yace miko min wasu ki bude part din karshe,da Sauri na bude na dauko tare da kara miko masa ya amsa ya daura sannan ya fito ina dariya nace na gani dai abin tsoro ma, murmushi yayi yace ke kika sani kuma,Wajensa na karasa kawo na tayaka Allah na iya ni nake shirya su Meenat ma fa, na zuba Lotion a hannuna nace to juyo mana ni ko dama wayo zan masa dan na taba masa jiki ne Sabo da yana birgeni,shafa to kiyi kuma Sauri sallah zanyi na fara murza masa Lotion ina ta murmushi dan fatarsa sai laushi kawai,nazo waist dinsa na tsokaneshi Sabo da naga baya so a kalle masa tsaraici nace kwance towel din nayi Sauri mana dariya yayi yace a'a ki kwance da kanki kai.

   Ina gamawa yace saura kaya to ya dauko wani Yadi shara shara fari me shegen kyau karamin dinki fitted na Maza yan gayu,da Singlet sai short ya miko min karasa aikinki, na karba kuwa ya dauka zan wani kasa sai ya karbe yasa Boxers dinsa,nasa masa singlet yasa wandon kayan na Sa masa rigar, da Sauri ya gyara sumarsa tare da fesa turaruka ya tayar da Sallah,ni kuma na fita tare da sauka kasa na duba na ga me su Meenat suka dafa idan basuyi ba nayi,tea suka sha da Doya da kwai kawai,sai farfesun kaji,na dinga masifa kun san dai bazan fito da wuri ba dan Iskanci sai kuyi wani Doya kawai da tea mijina yana ci ne? Ba sosai yake ci ba,Meenat tace au bamu birgeki ba a hakan? Ke da kika ce hira zaki je kuyi kawai ki dawo sai yanzu zaki fito duk hirar ce tun jiya? Shike nan bacci bazai kwasheni ba nama kwana din ina ruwanki ke zaki tsara min abinda ya dace nayi kece gaba dani ko nice gaba dake? Daga yau ma acan zan dinga kwana sai me kuma? Dariya Meenat tayi kawai tace ah mun gane, to gyaran gidan fa? Ya kika gani ya miki ko shima mijinki bazai masa kyau ba? Dubawa nayi nace wannan ai nasan kun iya dama kuma na gani kunyi kokari,bari to zo ki tayani muyi masa Kunun Gyada,da su muka shiga kitchen din suka taimaka min Dan danan muka shirya lafiyayyen kunun gyada,na fara soya dankali suka ce sun gaji su nace to kuje ku huta,suna fita sai ga Aayan ya shugo kitchen din a bayana ya tsaya kamar zai shige jikina ina jin kamshinsa a saitin kunne na yayi magana a hankali yunwa nake ji fa ki danyi Sauri,yana fadan haka ya fita ya barni nan ina jin jikina wani iri.

    Tunowa nayi da zan fara yanga ta na daina cin abinci a gabansa da yawa Sabo da kar ya rainani gashi kuma bana koshi da wuri sai na shirya dabarata yanzu duk girki sai na samu na zuba a kitchen din in ci abina na koshi sai na rage space kadan idan anzo ci a dining sai aga ina ta yanga naki cin abincin da yawa sai dai na dan ci kadan,
    Cikin rashin Sa'a yau nace zan fara tunda tare zamu ci a dining,na zauna na ebi chips din na zuba kunun gyada ta,farfesun kajin dasu Meenat sukayi nan ma na zuba Naja gefe ina cin abina a nutse,Kawai Aayan yazo zai shigo kitchen yaganni kicif ina cin abina,nan take ya gane me zanyi don Allah ya zuba masa basirar gane abu,dariyace ta kamashi me karfi ya danneta,ya juya palo dan kar na ganshi naji kunya.
   Saida na koshi sannan na sha ruwa na gyara lips dina na fito na shirya Dining na gyara kitchen din na fito,Aayan yana Dining yana jirana nazo na zuba masa ni kuma na zuba komai dan kadan kamar dan yaro ne zaici irin yar gayun nan, yaga ina ta wani juya cokali a ciki ina tsakura,shiko yana ta cin abinsa har farfesun,ya kalleni yace kici mana wannan dan abincin nufinki zaki ci? So kike ace bana baki abinci ko so kike ki rame? Baki na tabe ina yatsina fuska na ce ya isheni haka,ya kalleni tare da danne dariyarsa yace me yasa kika daina cin abinci ko baki da lfy? Na shagwabe fuska nace ni...yanzu bana son wani ciye ciye da yawa,yace to kiyi hakuri kici kinji yanda ya zage yana ta lallabani sai naci abinci ni kuma ina botsewa haba sai naji wani dadi nace lallai Aayan ya fara sona sosai ji yanda yake ta kula dani yana damuwa sai naci abinci,ni kuwa sai yanga nake wai ni a dole na masa wayo ban san shike min wayon ba.
   
   Kusa dani ya dawo yace Dole sai ya bani da kansa nafi ci na koshi yaga wasa nake da cikina so nake cuta ta kamani,nan take na Tsorata Sabo da na koshi taf cikina ya cika,ina ji ina gani ya zauna ya dinga dura min abinci da kansa,kamar zanyi amai Amma yaki saurara min,Dankali da Kunun gyada ya dinga danna min,ya dawo kan farfesu,tun ina dannewa nace dan Allah na koshi Amma dama Sabo da mugunta ya shirya min yace sai na cinye ya san ina da ci,Idona ya kawo Hawaye na fara kuka ina bashi hakuri Amma yaki yarda sai cusa min yake,sai da naci me uban yawa wanda kwakwaran motsi nayi sai nayi Amai,ya miko min yatsun Sa da ya bani farfesu dasu yace tsotse abinki,haka na tsotse yatsun tas shi kuma yanda nake tsotsar yatsun ne ya tayar masa da hankali nan take ya birkice,Sha'awarsa ta motsa da kyar ya dan danne yace ku shirya da yamma zamu fita zan dawo na daukeku,hararsa nayi nace to ina turo baki akan dura da yayi min.

    Ameer dasu Mujaheed ne zaune a katafaren Palonsu suna game suna hira,Mujaheed yace ni fa guys wlh ina son beb din nan kanwar matar Aayan Meenat take ko wa? Khaleel yace ai yarinyar tayi ne  ina fada ma gaba dayansu Allah ya zuba baiwa Barin ma matar Aayan gaskiya Ameer Banga laifinka ba,Ameer yayi dariya irin ta yan duniya sannan yace baza ma ku gane ba sai nan gaba,ni na hango abinda na hango,kullum da ita nake kwana nake tashi,Sajeeda dake gefensu taji haushi dan ita Ameer take so yanzu, rai bace tace haba Ya Ameer mene haka wannan cin fuska ne ina wajen fa wlh zan fadawa Abbi kasan dai yace Aure zai mana,Ameer ya kalleta shekeke ke dalla rufe min baki me zaki kaimin gidan nawa? Har daki kike bina muna aikata abubuwa zaki zo kice wani na aureki,Amma kasan dai ai kaine kace ba komai zaka aureni tunda kaine ka lalata ni,Mujaheed yace ko kunya bakwa ji ku rufe mana baki Hajja in ta dawo ku fada mata mana a fasa can da matsalarku,Cousins kenan dama haka akeyi ko mai ace cousin dina ne Kaza Kaza kullum kayi tunanin yan uwan ashe ana nan ana aikata masha'a tare,Mata har gidan kani ko wan babansu zaka ga sun tafi hutu an samu Cousin mace ko namiji ana ta shekewa,su kuma iyaye tunaninsu zumunci akeyi sai suyi ta jin dadi Allah kyauta.

    Hajja ce sanye da glass dinta na ido ta zauna a Cikin jikokinta nan Fa Sajeeda tana kuka tace Hajja kinji wai Ameer bazai aureni ba, Hajja ta gyara zama fatarta duk tayi yaushi tace shi din banza,ya Isa ma,shi waye shi wlh wlh Allah daya sai anyi wannan aure kwanan nan ma kuwa ko sama da kasa zata hade,waye kai? Ka Isa nayi magana nasa doka da hukunci ka tsallake ko Ubanka Mustapha bai Isa ba bare kai karamin shege,nan Hajja tayi masa tatas yayi shuru yana ji Amma ya rantse indai Sajeeda ta shiga gidansa sai ya kusa hallakata da muguntarsa ita kuwa Sajeeda murna takeyi don tun da ta taso a duniya take son Ameer sosai Sabo da ya hadu shima ba laifi.

     5:30 muka gama shirinmu tsaf mun hadu karshe yau kamar wata Sallah haka muka dau wanka,Aayan kuwa bamu san a inda ya shirya ba haka muka ganshi ya shigo cikin dakakkiyar shadda sea blue yanda yayi kyau ya zarta hankali ma,Maeesha ya kalla yana zuba kamshi yace kinfi kowa kyau yau,nan take naji haushi ni bai yabeni ba ai ni ya dace yace nayi kyau ba su ba,Meenat kuwa yace Yau kamar Queen haka kika koma nan take Meenat ta fara dariya tana tnx Yaya,Ma'eesha kuwa ta makale a jikinsa,ni da yau nafi kowa haduwa yanda nayi kyau har ya wuce misali Amma bai ce nayi kyau ba sai su Meenat,kasa danne fushina nayi sai kumbura nakeyi haka na karasa Sa sarka ta na dauki mayafi na da jaka nace muje Meenat da Ma'eesha suka yi waje ni kuma zan fito yana Bedroom din namu ya jawo hannuna na fisge abina,ya kara jawoni na fado jikinsa gaba daya,na sadda kaina kasa a saitin kirjinsa,hannaye biyu yasa ya dago da fuskata yana kallon lips dina tare da cewa wa kika sawa jambaki kuma? Nace masu sona na cikin gari idan mun fita nake Sa ran zasu kalla suji dadi, bakin ciki ne ya ziyarce shi me tsanani Amma sai ya danne ya hade bakina da nashi ya dinga sha,sai da ya shanye jambakin tas sannan ya dauki wipes a saman mudubi na dinga tsalle ina son guduwa amma ya rikeni tam da kansa ya goge min fuska tas ba abinda ya bari na kwalliya ta,hakan ma yaga baiyi ba sai ya jani toilet fuska ba walwala ya danna kaina a saman sink yasa soap ya wanke min fuskar tas ya goge min da towel nayi wani mugun Fresh jajayan lips dina suka fito natural sai na kara wani kyau kowa yasan Natural kyau na gaske nayi,ga kayan sun hau jikina,dankwalin dana kafa kamar gogoro ya zame ya jefa shi saman Bed ya dauki Hijab ya sa min duk da haka nayi kyau sosai sai ya cire Hijab din ma tare da cewa baki da kyau sam sam Bazan iya fita dake ba bari muje da kyawawana su Meenat,dama haushinshi nakeji ya bata min kwalliya kuma baice ina da kyau ba yanzu kuma wai ya fasa zuwa dani,ban san sanda na fashe da kuka ba me karfi, ba shiri yace taso taso mene haka wannan uban kuka zaki fasa min kunne,gyalena na dauka ina share Hawaye yace Sa Hijab na kara sakin kuka yace to yafa gyalen haka muje wannan masifa haka,ina dariya na yafa haka nabi bayansa,sai da na kara tsayawa a bayansa na zaro Powder a jakata muna tafiya bai San ina ta shafawa ba,na gama nasa jambakina red,kafin mu karasa mota har na gyara ribbom din gashina nayi acuci sosai na gyara mayafin aiko na dau kyau kowa ya ganni yaga yar gayu,nasa glass dina dan Brown nayi kyau ba a magana,yana juyowa sai da ya firgita kamar aljana kafin aje mota har na sake kwalliya yace zanyi maganinki a ransa tunda bakya jin magana dai dai  nake dake.

     Gaba na shiga Meenat da Ma'eesha suna baya  shike Driving yau,katafaren store muka tsaya Meenat sai jin dadi muke muma mun Zama yan gayu,sabo da neman suna sai da na karasa tare da rike Hannunsa muka jera sabo da naga Yan mata sai shige da fice suke a wajen ko wacce ta Sha wanka, hannuna ya rike yana murzasu muna tafiya duk inda muka keta sai an kallemu,Kayan sawa iri iri yace mu zaba,dana tashi sabo da tausayin kudi abinka da ba a saba ba kawai sai na zabo atamfofi dasu laces materials dasu Ready made duk ba na sama da Dubu biyar daka biyar sai kasa,gani nake na gama kure karyar kudi, yana duba kudin yace a maida su wannan ai wanke kudinka ne Hajiya,da kansa ya dinga jidar mana kaya masu matukar tsadar gaske komai latest,haka takalma  ma,bags ma ba a magana,har su cosmetics yana zabo me tsada muma muna daukan wanda muke so,har jewelries, muka je bangaren Inner wears yace su Meenat su zabi nasu aiko suka jida masu kyau iri iri,ya jani wani bangaren can daban na inner wears yace zabi size naki naga ko Bra kuwa kina sawa? kullum daga an dage miki riga direct ake tafiya can,Kunya naji na rufe ido nace Ina sawa mana amma a boye nake sawa na wanke a boye bana so ace kamata ina sa Bra,to mene a ciki dan kinsa yaja tsaki tare da cewa anya kuwa jinin birni ce ke? Nace a'a daga garinku nazo murmushi ya saki sannan yace mu bamu da dangi a Rimin Gado mu gaba da baya dan birni ne ni,muna ta Zaba iri iri masu kyau ya dauko min wata yar karama yace ga wata me kyau,Hararar wasa na masa nace kaima kasan sunfi haka wuce nan sai kace yarinya,muna dariya sai ga wata yar gayu tana kwas kwas da takalmi ga kamshi tana zubawa muryarta muka ji tace Aayan  kaine a nan we finally meet here ohh,Dagowa yayi tare da zuba mata idonsa me matukar kyau ya danyi murmushi kadan sannan yace Sameera kece How u?longest time,tace am great ina ta so mu hadu wlh amma ba dama tun aurenka na farko fa gaskiya mun dade.

     Wani kishi da bacin rai ya taso min na bata rai nayi kicin kicin na tashi hankalina gaba daya ina Harare harare,itace second wife din naka? Ina Yarima yana dariya yace yana lfy yar duniya kin buya amma dai kin sake aure yanzu ko? a'a aure ai sai na huta ina aiki ina samun kudina matsalar maza ta isheni baku da kirki Sam ni sai na huta zan yi Insha'allah,Jin bata da aure yasa na kara fusata na daure fuska na dawo gaban Aayan na juya bayana tare da kwantar da jikina a jikinsa muna facing juna da Sameera sai kallon Banza nake mata,Hannunsa na jawo guda biyun na sakalosu ta kafaduna ina wasa da yatsunsa,Murmushi Sameera tayi tare da cewa am sorry to say Aayan kasan bana boye abinda ke raina amma wannan tayi maka yarinya da yawa Aayan kamarka da auren kamar wannan da gani ma baza ta wuce 15yrs ba,ga mata a gari zunduma zunduma da ka fada mana ai da mun zabo maka manyan yara amma irin wannan ai kuruciya zaka sha baza kaji dadinsu ba.

   Dariya sukayi gaba daya tare da wani tafawa abinda ya bani haushi kenan ya kara kuleni mene nasa na tafawa da mace,nan take naga fa ta fada min baka zata barni da takaici  ban san sanda nace uhm Allah sarki kuma a hakan bashi da kamata dan ina masa abinda Babba bata isa tayi masa ba,tunda tsab nake daukeshi wanda nasan ko uwarki yafi karfin.....kafin na karasa yasa tafin hannunsa ya rufe min baki da karfi dan yasan sai na karasa ko za a mutu sai na rama,ina so na kwace baki na amma yaki Sakina ya toshe min da tafin hannunsa yana fada min a kunne kina magana wlh yau na lahira sai ya fiki jin dadi bakya jin magana ko ke ba a isa an miki abu kin hakura ba sai kice sai kin rama wannan wacce magana ce ta marasa kunya uwarta fa kika ce,Sameera ta kalleni sosai tace da Sameera kike zance yarinya zaki san kin zagi uwata,wlh sai kin San wa kika cewa haka,Allah ya taimakeki yanzu Kinci darajar Mijinki amma a sannu zan goge miki abinda ke kanki,Bakina na kwace nace Ba Sameera ba Allah yasa kece Sameeran Gaya? wlh nafi karfinki kina magana kina cijewa ke ga yar daba karewar Daba munga Amana ta Alim ma? Sameera dama irin Masu takama da yan daba ne har yara ne da ita yan daba,bata da kunya duk abinda taga dama haka zata fadawa mutum shi yasa ko zaman aure bata iya yi,sabo da ko yaushe a shirin daba take kana mata zata sa yara yan daba suyi ma kaca kaca tana takama da kudi sabo da ubanta ita kadai ya haifa ya rasu ya bar mata dukiya me tarin yawa,Tun kafin ya mutu ya raba gado yaba yan uwansa ya barwa yarsa komai,shi yasa take abinda taga dama,kuma bata San mutunci ba duk inda take da kai zata iya ci ma mutunci ta ko wanne hanya,Aayan kuwa Business ne ya hadasu tsakanin Company nata da nasa tun da dadewa.

    Ni kuwa nace komai dabancinki baza ki bude min ido ba kiyi duk abinda zakiyi nima baki San ko ni wace ba shi yasa har kike magana dani haka ina kyaleki,ki Bari watarana Business ya hadamu anan zaki gane true color dina,Tsaki taja ta bar wajen a fusace,Aayan yana ta kallon yanda nake tsiwa yar ficika dani gaban sangamemiya irin Sameera ko tsoro bana ji,na kalleshi nace girma ya fadi wlh ka ba dani ina ma kallon Ustaz har wani hannu kake hadawa da yan tasha,da gani wannan yar tasha ce gaka da fyallelliyar budurwa me zaka ji a hannun wannan me suffar mazan, kayi dacen mata amma baka godewa Allah kana wani rikewa wata hannu bayan ga hannun da zaka samu lada Allah kyauta ka daina irin wannan a gabana dan wlh ni bazan dauki a wulakantani ba dan baka darajani ba Sam,ka zubar min da mutunci ace Namiji yana da kamata yana rike hannun wata banza,wannan babban matsalace dole na tuntubi kaina Ashe ma ban kai mace ba.

    Yana jina ina ta masifa kamar uwarsa yana dariya a ransa,yace to yi hakuri masifaffiya tunda bakya so na daina,wai nice budurwa shi baya daukana a budurwa Sam,yace wai ke nan budurwa ce? Bacin rai ya kamani sai na danne a fili  nace a'a kwaila ce,a na dinga masa masifa ina zan rama zaka San ba budurwa bace ni daga yau na Canja salo again na fasa wannan Business din da mukace za muyi wani zanyi daban sai na sa kayi nadama har ni za a wulakanta dan anga ina biyayya ina cusa kaina ina kokari naga an zauna lfy shike nan za a gani,dariya yayi yace a'a dan Allah tsokanarki nakeyi fa muyi Business dinmu zan biya kudin,nace anki din sai na rama nima.

    Mun gama siyayyar komai yasa aka kai boot din mota ya biya muka fito kenan sai ga Ameer da Khaleel tare da wasu yan mata masu suffar karuwai sai chewgum suke taunawa su a dole manyan yara,na kalli Aayan na bata rai nace kalli Meenat a gabanmu tsaya kaga abinda sukeyi kalli,ya kuwa kalla sosai ni kuwa wai dan kar ya kalli yan mata nayi masa wayo,Muna zuwa Ameer sai kallona yakeyi zasu shiga mu kuma zamu fito na bi ta tsakiyar yan matan nan a hankali yanda zasu ji nace yan iska sun dauko yan iska su a dole yan mata ana yaye baki a titi na wuce fit na koma kusa da Aayan,Khaleel ya fusata kwarai da maganata haka yan matan ma,Ameer kuwa so yasa baya ganin laifina sai dai ma birgeshi da nakeyi aransa ma cewa yayi wannan gaskiya kika fada Mufeedata tabbas yan iska ne suka dauko yan iska Allah ya baki basira tare da saurin ganewa?

    Yan matan zasu zageni Ameer yace wlh duk wacce ta fadi ko bakar magana a kaina sai ya mata illa har fada suka so yi da Khaleel..
   Muna shiga mota na tuna zanyi girki kuma kayan miyarmu ya kare nace Aayan kayan miya na manta,Yace to mu koma store din nace a'a danyi gaba wajen yar kasuwar can zamu samu.
    Muna zuwa yayi parking nace sai ya fito munje tare,yace a'a nifa ban taba siyan abu a kasuwa ko gefen hanya ba a store nake siya,Na fara rokonsa dole haka ya fito muka karasa wajensu,sabo da tattalina da son kudi nace Malam kwano nawa nawa? Aayan yace nidai a zuba kawai mu tafi,nace a'a so kake ayi mana tsada bazai yuwu ba yo ni akan barkono kwano daya idan nazo sarowa Basai na yini a wajen ba ana ciniki ba kuma karshe kaga na siya arahar banza,Dariya Aayan yayi yace yini guda fa? Nace Cass ma kuwa, Agogon Dubu biyu ina siyoshi a Dari biyu da hamsim ni highest Dari biyar zan siyi shege,ka dinga zuwa dani siyayya kaga araha,Aayan kallona kawai yake yana dariya,Nace kai me kayan miya kwanon tattasan ne dari biyar a garin gaba gaba muke da zan siya haka,yace gaskiyar magana Dari hudu da hamsim baya tsada bana nawa kike so a siyar miki,Nace to ka rage,nafa San kan kasuwar nan,Aayan yace Haba Ke kuwa har kwano guda Dari hudu da hamsim kacal a kasa siya mene na tsada a nan? Harara na watsa masa tare da dan zungurinsa nayi masa magana a hankali bana son haka ba a yiwa yan kasuwa haka,zaka kashe min ciniki idan kasan haka zaka min ka koma mota yanzu duk ragi ai ragi ne,Aayan yace Malam zuba mana kwano biyar ga kudin ya zaro kudi ya mika,na fara rigima na cumimiye a jikinsa baza a biya ba kwano har Dari biyar gwara Ku tafi gida ni Ku barni a nan nayi cinikin ko Dari hudu na siya sai na samu Dari Dari ta Zama tawa,na dawo a taxi, ko kulani baiyi ba yace to tumatir fa,nace a tsaya ni zan Zaba da kaina,me kayan miya yana ta dariya yace kudi kudi ne ga gwalagwaje wanda ya gama lugwiguwicewa daf yake da rubewa kudinsa daban,ga masu kyau manya da kanana,nayi layin  marar kyau gwalagwajen nace duk tumatir tumatir ne tunda dafashi za ayi mu sharbe miya Malam ga me sauki ba sai anyi asarar kudin ba a bamu wannan,Aayan dariya ta kamashi ta gaske ya dinga yi yace wlh baki isa ba gwara da Allah ya kawoni na gani dama abinda kike sawa muna ci kenan? Nace to sau nawa ka shanye miyar sa kana Santi ai ni in kaga lafiyayyan tumatir a fridge to na cin salat ne,ai ko harda kwalla Aayan yake dariya ni kuwa ko a jikina,yace Allah na gode ma da na gani da Ido na shi yasa Ashe ba kya yarda a bawa kowa yayi cefane sai ke Ashe Guba kike bamu muna ci.

    Aayan yace Malam me kyau wanda yafi kowanne tsada zaka zuba, na hangame baki ina jimami shike nan za a ci kudinmu a banza,akan dan tumatir har yan Dubu Dubu na fitowa naji kamar na fisge kudin,na bata rai ina ta fushi nace ai gwara ni ka bani na dinga tara ma kudin watarana sai mu dakko a siyi abu me amfani dasu amma wlh wannan Almubazzaranci ne, mukaje layin Albasa nan ma dan yaga yanda zanyi yace zabi da hannunki one by one ki dinga zubawa a ledar mu gani,me Albasa yace ai kwano kwano muke saida wa,Aayan yace bari ta Zaba sai a auna zan biya ko nawa ne,aiko na fara Zaba sai na duba wacce ta tsage ko ta kusa lalacewa ko marar kyau sai na dauka na nunawa me kayan miya nace kaga dai wannan araha zata yi ehe,wannan ma ba me tsada bace,Aayan yana murmushi yace pick the nice one mana,na kai hannuna kan me kyau sai na koma na faki idonsa na jefa marar kyan a leda yana kallona yana dariya har na gama sannan yace to Malam juye wacce ta bari bata Zaba ba su zamu siya,haka aka auna ina gani kamar na fashe sabo da ni kudin da aka kashe kawai nake jin haushi da an tattala su ai sai a moresu watarana Rayuwar Manage na iya a haka na taso da ita na saba.

   Na dauko shima ya dauki wasu muka zuba a mota ina ta harararsa yana kallona ta gefen Ido yace daga yau tsinke baza ki kara siyowa da kanki ba da kaina zan siyo ko na bayar a siyo,nace girkin ma ba sai kayi abinka ba,wlh ya kamata ka koyi adani sabo da rayuwa ni gaskiya nake fada ma.Maeesha dama suna gani sun San halina sun San yanda nakeyi a kasuwa dariya suma sukeyi Meenat tace Yaya Aayan ya kaga mutuniyar taka ta iya Zabe ko?

   Dama kadan yake jira ya dinga dariya yace ai naga Zahiri yau Meenat,haka takeyi ko a gida Ammah ta dinga ta mata fada amma baza ta ji ba cewar Ma'eesha.
   Meenat tace ai baka San abin haushi bama shi yasa bama Rakata kasuwa watarana akan egusi da zamu siya wlh sai da muka yini a table din me egusi har fada sukayi ya koremu gaba daya,kai ai kadan ka sani, turmi ma ba a cin arziki a gidanmu ko daka wasu sukayi a ciki sai ka biya ashirin, haka gugan Rijiya ma ko kurar Ciro guga duk na haya ne hhhhh Aayan ya dinga dariya Meenat suna ta bashi labari suna min dariya,sai da na saki Kuka sannan sukayi shuru.
    Haka ma Ya Aayan watarana ta siyo min jakar makaranta me kyau ina ta murna wata kawarta Nawwara tace gaskiya jakar tayi kyau nima zan siyo aiko Mufee na jin haka tace Dari uku na siyo ta bani Uku da hamsim na siyar miki,ina kuka haka ta siyar da jakar nan taci ribar Hamsim,Aayan yana driving yana dariya.

     Malamin Hajja ya hado mata muggunan da za a sa min tare da Aayan a abinci,da sauran wasu iri iri na wajen Malamai shi yasa yanzu ta saka rigima wai Daddy ya fadawa Aayan a dawo damu ai muma jikokinta ne taga abinda tayi bai dace ba bata kyauta ba
   Daddy yasan ba gaskiya bane amma yasan Allah na nan ba matsala ya Sanarwa Aayan.









AsmaBaffa
Reply
#7
[1/20, 09:13] Sayyida Hauwa: ????
????

     KASUWANCI NA







            66-70






Official







By
AsmaBaffa







                JANNAT wannan page naki ne.


    Godiya gareku House of Hausa Noveld kun iya Sharhi.




















 Bayan yayi parking a cikin gidan fitowa mukayi tare da jidar kayan muna kaiwa muna dawowa har muka kwashe komai ya rufe motar  take away na abinci da ya siya mana na karba ina ta masa godiya da addua ya wuce abinsa nima na shiga Bedroom dinmu, Bayan munci mun koshi wanka nayi na shirya cikin sabuwar Nighty dina iya cinya me siririn hannu peach color na fito fes ina kamshi Meent ce ta shigo Sis kije inji Ya Aayan amma fa yana compound jikin motarsa da alama fita zaiyi,Hijab nasa har kasa kamar zai ja kasa na fita lokacin tuni munyi sallar Isha,saman Motar na ganshi a zaune cikin kana nan kaya ba karamin kyau yayi ba,wani abu ya tsirga min na tsinci kaina cikin wani yanayi na shauki wanda bazai misaltu ba wani dadi yana ratsani, kallona yake cike da tsantsan nishadi kwance a fuskarsa zuciyarsa cike take da farin ciki wani Sanyi na ratsashi.

     Ina murmushi na karasa tare da cewa au akace fita zakayi kuma naga ka zauna saman bayan mota,yana murmushi yace zance fa nazo kinyi sabon saurayi kuma kina wani cewa fita dariya nayi nace kaima dai baka rabo da tsokana a haka zubin mugaye gareka, am serious ni fa zance nazo dama gori kike min kece kullum kike zuwa zance,Dariya nayi nace to nan gaba idan zaka zo ka dinga bugo waya sabo da ai banyi kwalliyar zuwa wajen saurayi ba na fada kamar gaske, muryarsa naji yace duk fa cikin business ne ki daina tunanin da gaske ne kudi za a biya ki wannan fitowar ma da kikayi kin ci kudade masu yawa,dadi ya kamani nace an gama ko kalma daya ce duk kudi ne? Yace of course, murmushi nayi tare da gyara tsaiwata yana sama na matsa jikin kafafunsa, yace yan mata suna na Aayan duk da cewa baki tambaya ba,ban san lokacin dana fara dariya ba ni abin ma kunya ya bani amma na daure nace ai yanzu gashi ka fada, yaci gaba da tunda na ganki kika shiga raina naji bazan iya bari ki wuce ba batare da na miko Kokon Barata ba gareki, uhmm nace tare da tunani sannan nace kasan me ni ban iya so farar daya ba dole sai mun zauna da mutum idan naga halayensa sun min sai na yarda amma yanzu bazan amince ba, sama naji yayi dani ya daudarani saman motar nima kusa dashi jikinmu na gugan juna,baki na bude tare da cewa wannan saurayine ko dan Shan minti ne kawai,dariya yayi ai an daura mana aure da Budurwar kawai bata sona ne shine nake zuwa zance sabo da na lallabata.
   Murmushi nayi nace to naji game din tayi kyau back to our business nawa na samu? Yace ai Dari biyar kika samu sabo da kin kasa magana baki fadi kalamai masu sanyi ba taya zaki samu kudi.

   Masu Zafi zan fada yanzu ma kuwa na irin fuske ba wasa nace look in to my eye aiko ya kalla da mayun idonsa I was kidding u  but u I knew I love u,i wish I can show u how much I love u,i care for u,my heart is full wth ur love my Prince, yana murmushi yace proof what u have just said, nan take da gaske nakeyin kalamai na ni, bana karya bane amma a boye a raina nace na samu Damar jin dadi na sai na fake da kudin,a fili kuwa sai na ce ka tabbata  zan samu kudin nan da yawa,kai ya daga min tare da kara matsowa jikina sosai yatsunsa ya sarke da nawa tare da jawo ni jikinsa, hannayena na sakalo ta wuyansa a hankali na rungumeshi a jikina sannan na dago kaina tare da shigar da bakina cikin nasa ya fara tsotsa kamar ba gobe, tunawa nayi ko yan aiki na zirga zirga a wurin nace yan aiki fa?yace ai basa kwana a nan gidan da safe suke zuwa nemi kudinki na Business yarinya,dariya nayi a raina nace Ina ta masa wayo ya kasa ganewa,nace ni dai mu koma bedroom,lallai kudi zaki nemo da yawa karfa ki karar min da dukiyata,ina dariya nace hau dani baya wannan ni zan baka kudin cikin nawa ka cire Dubu guda,baki isa ba sai dai na daukeki,nace ni dai baya nake son hawa,ko baka da karfi ne? Hannu yasa ya daga ni sama sosai kamar ya dauki tsinke ya dauri a kafadarsa naga ya mai Dani bayansa kamar yar jaririya,nace kai karfinka yayi yawa amma a haka dan Lange Lange da kai, murmushi yake har bedroom dinsa karki cire Hijab din, why? Zaki gani ya furta yana dorani saman bed sannan yazo ya daga hijab din tare da shigewa ciki,dariya nayi yanda yake min abubuwa a ciki don tuni ya zare min rigata tare da kashe light, gaba daya ya gama haukatani ni kaina abinda nake masa ba a cikin hankalina nakeyi ba, ba komai a jikinmu haka muke murzar juna, kalamai yake sabo da sucking na fara masa ko gidan ubanwa na koya oho wannan abu kamar da Aljanu sai kaji ka iya kaima?
    Kukan dadi yakeyi yana zazzagar da kalamai amma ni bana yarda kawai dama na karya ne tunda nasan Business yace ayi,nice nakeyi da gaske a raina, boobs dina yake murzawa har shidewa nakeyi,kiss kuwa yau ina jin sai lips da tongue dina sun kumbura maybe dan sun tsotse a wajensa,yau wani abin mamaki sai ga Aayan yayi releasing sosai abinda Bai taba yi ba tunda yayi aure sai dai a mafarki, bai taba tunanin zaiyi ba Sam shi yasa ma bai yi tunanin sexing dina ba Sam, ya dinga bakin ciki yana jin haushi yace ya zubar da yaransa a banza,za a wankesu a ruwa,na dinga dariya nace yanzu haka ma yan biyu ne ko yan uku ma,ya kara Jin haushi yana kwance gefe,na ce yanzu haka akwai me Sunan Mommynka a ciki ko me Sunan Daddy, dariya yayi tare da cewa wlh ba a wanke Daddyna ba ai Me sunan Daddy yana nan zuwa nan gaba bakiyi abinda zai fito ba,sai Abbansa yaji dadi da yawan gaske sannan me Sunan Daddy zai yo waje,haka kace ko? Ya jawoni jikinsa tare da cewa tnx Baby kinci kudi me yawa yau mota sabuwa dal da dalleliyar waya me tsada kika samu,ni haushi ma ya bani maimakon murna bai San dadin dana ke ji ba na faranta masa burina na ganshi cikin Jin dadi amma shi tunani yake ma dan kudi nayi ni Sam yanzu ba kudin bane a gaba na ba so nake ya so ni kawai.
   Shuru yaga nayi bana murna kamar baya can,ko sunyi kadan a kara miki? Nace a'a na gode hakanma sun isa,murmushi yayi yana kallon yanayi na,nayi miki kema kiji dadi? Jin dadine yasa nayi murmushi nace ae,ya fara gwangwajeni da salonsa nima saida na ji zam zam,garin kuma sani naji dadi shima ya sake dawowa ruwa nan na kara masa abubuwan da kawai ya kara kawowa,kamar yayi kuka sabo da takaici yace next time kawai Sex zaiyi shi kam,ina ta tsokanarsa har bacci ya kwashe mu,tun daga Ranar kuma ko me zamu yi bai kara kawowa ba,dama kuma baice ma zaiyi xxx din ba.

    Ameer kullum shi yana wajen Hajja sabo da sun shaku sosai duk wani plan din ta ya sani,duk bai damu ba dadi ma yakeji shi za a sa Aayan ya sakeni,kawai sai yaji Hajja tana cewa za a sa min ciwon hauka ko kuma wata cuta ko wacce za a rabani da gidan su Aayan gaba daya,nan hankalin Ameer ya tashi ya za ayi a haukata masa Mufeedansa,shi da yake so ya Aureni yana kauna ta baya kaunar abinda zai cutar dani ko ya ganni cikin wani Hali,nan take yace dole na dau mataki kan Hajja na hanata aikata abinda take niyya,nan ya dinga sawa Hajja ido har ya gano magungun nan data ajiye tana jira na dawo ta aikata abinda bokayen suka ce mata,Ameer murna ta kamashi ya kwashesu gaba daya harda wata yar tukunya da wani ruwa a ciki,ya zubar da ruwan a tsorace,ya fasa tukunyar,garin maganin da ruwan rubutu duk ya samu jikin katangar gidan ya haka rami me zurfi jikin flowers yanda baza a gane ba ya zuba rubutun ciki garin maganin ya juye su daga ledar a cikin rami sannan ya maida kasar ya binne su sosai yanda ba za a gane ba ya kwashe ledojin ya zuba cikin Dustbin.

    Bayan kwana biyu Hajja ta duba taga ba komai,kamar me ciwon hauka haka ta fito tana ihu da masifa,ta tambayi kowa amma ba wanda yace ya gani,Ameer kuwa dama tasan na wajenta ne bazai ma dauka ba sai dai ya goya mata baya shi yasa dashi ake tambayar yan gidan yana masifa kamar gaske,Hajja ana sa masa albarka ga wanda ya gajeta,haka a gaban Ameer ta kara buga waya wasu malaman sunce baza su sake samun irinsa ba bare su bata,wasu kuma sunce ta koma ta karba,Ameer ya makale mata tace ai shi zai kaita ma su karbo,kafin su tafi ya tara yan iska ya biya su kudi kan a tare motarsu su kwace jakar Hajja kudin dake ciki nasu ne masu aiki sauran maganin da suka samu kuma su bashi a hannunsa zai nemesu,haka suka tafi gari gari har wanda a jirgi sukaje daga nan suka je na kauyukan kano duk suna jakar Hajja tana murna,Ameer yana Driving tana gaban mota suna ta hira tana fada masa tsare tsarenta wanda zata shiryawa Mufeeda,suna tafiya hanyar daji daji ba kowa sai ga yaran Ameer sun tare motarsu kamar gaske suka kwantar da Ameer a kasa Hajja kuma suka kwace jakarta tana rokonsu suna ganin makudan kudin da suke ciki suka dinga murna suna godewa Ameer a Ransu,suka kwashe kudin tas,magungunan kuma sukace wato gidan bokaye kuke zuwa ko? Kune masu hana mutane Zama lfy a duniya Allah ya tonaki tsohuwar banza ke da jikanki yau karshenku yazo,Hajja ta fara magiya tana rokon kar a taba mata jika sabo da tana son Ameer sosai ita tun asali tafi kaunar Ameer da kowa,Ameer ya kifta musu ido su kyaleta haka su kwashe komai su tafi,ai kuwa suka kwashe komai suka jefawa Hajja jakarta,Ameer ya tuna da rubutu jarka har biyu a gaban mota yana sani yace Hajja maganin sun kwashe Allah yasa muna da biyu a gaban mota,kamar gaske suka take mishi wuya sukace au harda wasu a mota kuka boye Allah ya Toni asirinka dauko mana su ko mu fedeka,Ameer ya tashi yana kunshe dariyarsa ya ebo yana kuyi hakuri gashi kuje dan Allah,sai dai suka kaiwa Hajja masga daya sannan suka kara gaba.

    Hajja jiki na rawa tana kyarma a firgice tace Allah ya isanmu kaga shegun yara wannan turosu akayi,Ameer yace sannu Sannu Hajja ta Allah ya saka mana muje muyi mu bar nan kar su dawo ko wasu kalar suzo su harbemu,Hajja tace iceko baka ji rauni ba Ameer dina naga sun take ma wuya,ai munyi arziki da basu taba min kai ba,yana Driving Hajja tace yanzu me zan cewa malaman nan? da wanne baki zance an kara sacewa? Ameer a ransa yace kai Allah yayi muguwa a nan wajen sai son kai amma bata son Mufeedata,a fili yace shawara ta ki Bari sai an kwashe kamar wata daya ko biyu ki koma muce mun aikata baiyi aiki ba Sam bamu ga canjin komai ba sai su bamu wasu kalar kinga me zafin ma zasuyi mana tunda sunji wannan baiyi ba,Hajja taji dadi tana dariya ta balli goronta tace hakane Jikana shi yasa nake sonka akwai dabara amma idan suka ce sun San karya ne fa?,kasan fa duba sukeyi sun San komai,Murmushi Ameer yayi yace karya ne Hajja ba wanda yasan gaibu duk raina muku hankali sukeyi idan kina so ki san karya ne kije da jakarki ba komai a ciki kice ya duba miki mene a ciki idan ya fada ki bude wlh bazai San mene ciki ba wani abin ma da zaki ji sun fada Aljanu ke fada musu wani karya wani gaskiya amma sai ku dinga yarda,ai kamar Hajja zata daki Ameer ya karyata malamanta tace Wannan sabo kakeyi Ameer malamai magada Annabawa kake fadawa suna karya,Ameer ya dinga dariyar Jahilci n Hajja dan sunyi Islamiyya sun San komai,amma ganin baza ta gane ba kawai ya canja zancen ya kyaleta,ita ko sai masifa take masa,har ya gaji yace Hajja ke dai baza ki gane karyar mutanen ba a hadisi  aka rawaitosu ko a Alqurani?, Salati Hajja ta saki tace yau naji dan iskan yaro to yi min Wa'azi Allah ya taimakeka kaine da Mujaheed ne ko Khaleel wlh yau da basu kwana a gidan mu ba,ka kiyayeni rakani kayi ba Wa'azi nace kazo ka min ba,kai din abin arziki kake aikatawa? Wanne iskanci ne baka yi,ai ni nasan wlh ba dan iska bane tunda ni bana bin mata duk a baki kike ji ina surutuna ko kin ganni da mata wlh ni ba zina nake ba,ban taba yi ba,ko kinji nace Ina son mace wlh da aure nake sonta ni bada iskanci ba,bana fata na ajiye mace don kawai naji dadi da ita sai dan na aureta gaba daya har karshen rayuwata,Hajja tace Sajeeda fa ai tace ba abinda bakayi da ita ba? Wlh sharri ta min don na aureta amma ni ban lalata mata rayuwa ba kuje asibiti a dubata,idan ma an ganta a lalace to wlh Allah wani ne ba ni ba,ke kin San ni ba irin Khaleel bane ko Mujaheed wanda basa fada sai dai aga sun aikata sune masu son ayi fasikanci da mata, Hajja tace uhm naga Alama ai nasan halinka Ameer kai dai a barka da masifa ga kawo shawara wajen iya hada tuggu,to amma mene hadinka da mata tunda gashi duk inda za a ganku da mata kuma Sajeeda nima ai ina ganinta a dakinka,Hajja kenan kina son Gulma,zan ci ubanka wlh karka kawo min raini,ayi hakuri Hajja mata da kika gani Allah daya dan rage Zafi nake dasu ina dan tabe tabe a jikinsu idan na danji sai na kyalesu,Sajeeda kuwa har room take Bina na kwanta da ita naki yarda,tace na aureta naki shine take talla da kanta ganinta hakan ne zai sa na sota ni kuwa kara tsanarta ma nayi wlh ba wacce na tsana sama da ita,kuma ban aikata komai da ita ba sharri take min,Hajja dan Allah kar a aura min ita wlh zan iya mutuwa,banza Hajja tayi dashi sai daga baya tace amma kasan tana sonka,ae amma ai badan Allah take so na ba cewa fa tayi don duk gidan nan ni kadai nake kama da Yaya Aayan daga Aayan sai ni a kyau na yan gidan nan shine fa dalilinta dama nasan Aayan take so ba ni ba,ba sai ku aurawa Aayan ya kara ta biyu da ita ba,Hajja tace halina da kai basira haka za ayi aure za a kara masa ta nan zamu samu Damar wulakanta Mufeeda,Ameer najin haka yace ai kuwa bazan bari a aura masa Sajeedar ba tunda za a taba min lafiyar Mufeedansa ta nan za a dinga kai maganin bokaye,wa ya sani ma ko Sajeeda ta dinga dukan Mufee dinsa kullum ina Sam da sake bazai yuwu ba dole ya canjawa Hajja shawara amma sai ya nutsu ya samo dabara.

    Washe gari naje schl na dawo wanka nayi na shirya cikin wando pencil brown  riga Maroon na gyara gashina kamar wata Baturiya ba karamin kyau nayi ba, zaune nake a kujerar dake kitchen ina yanka cabbage, kamshin Aayan naji kafin na juyo naji ya tsaya a bayana tare da dafa kafaduna da hannu biyu a hankali yayi Sallama na amsa tare da mikewa tsaye nace sannu da zuwa, na kwanta a jikinsa ba tare da na tallabeshi da hannayena ba sabo da akwai cabbage a jiki,kallona yakeyi sosai yanda nayi kyau amma Bai ce nayi kyau ba,lemon Fruits dana hada  yayi Sanyi na tsiyaya masa a glass cup na mika masa ya karba ya shanye na karbi Cup din shi kuma ya bar kitchen din ya haura samansa,na dan Dade a tsaye ina tunanin ko lfy? Dan naga kamar yana cikin bacin rai amma ya zan masa tunda baya iya fada min matsalarsa sabo da ba sona yake ba nice dai nake wahalar da kaina a raina nace wlh bazan iya ba kaje kayi ta fushinka da kaina kuma nayi wa kaina fada ni da nake so ya soni back kuma in Zama jigon rayuwarsa na tsaya wasa gwara idan na sace masa zuciya sai na shareshi yanda zaita wahala a kaina yessss na fada da karfi wlh haka za ayi yanzu bari na kwantar da kaina first yanda Meenat tace nan ma da karfi nace shegiya Meenat yarinya da fusaha,da sauri na ajiye aikin da nake na wanke hannuna na bishi samansa sabo da irin su Aayan son girma garesu suna bukatar biyayya sosai.

    Ina shiga na iske wanka yake sabo da na sanshi ya sanni don ba kaya ma muna romancing juna me yayi Saura kuma kawai Toilet din na Murda handle din sannan nace na shigo,shigo mana kinga na huta ma,Shiga nayi da towel a jikinsa ya shafa shaving cream a kirjinsa zai fara aski, na karbi a bar askin na jawo masa wata doguwar kujera ya zauna nace aske gashin kirjin zakayi harda shi gaba daya? yana kallon shiga ta wacce tayi matukar yi masa kyau yace kinyi kyau idonsa har ya canja nace tnx amma yanzu har kirjin zan aske? Kina so ne? Hmm in ina so ma ai baza ka barshi ba tunda baya cikin Business dinmu, murmushi ya saki yace sai a zame wasu kudin cikin naki tunda ke kike so kece zaki biyani kudin ajiye miki shi,kuma yana da tsada kin sani,nace a'a karka taba min kudi aske abinka na hakura,in kina so zan bar miki kyauta,to ina so a bar min,hanci ya lakace min Hajiyar kudi kenan,dariya nayi nace to an fasa askin ai sai kazo ayi wankan,jansa nayi yace ai baki isa ba yarinya sai dai ki tube muyi tare amma baza ki min wanka ki kalleni ba bazan yarda ba sai dai ayi 50-50,Dariya nayi nace a'a to mene na jin kunyata abinda nasan komai na kai hannu zan janye Towel din ya ja gefe da sauri tare da Jana ya tura ni bedroom ya kulle kofar yace je ki kawo min abinci kafin na fito,lallai Aayan yana da kunya wasu mazan kuwa ba ruwansu amma shi ya sanni na sanshi amma kunyar na kalleshi yake.

   Kafin ya fito na shirya masa komai a dakinsa ina zaman jiransa dama wankan sa dadewa yakeyi sosai yafi mata ma,yana fitowa nace nazo? Yana dariya yace a'a dan Allah zauna abinki zan yi da kaina nasan halinki kice zaki cire min towel,ina zaune ya gama shirinsa tsab cikin kaya marasa nauyi,nace Ohh kayi kyau shi kuma ya dawo inda nake zaune a kasan Carpet dake dan gefen bed na sa abinci gaba,ya wara kafafuna tare da Zama a gabana ya jingina bayansa a fuskata,kayi kato ai Sai kace wani yaro zaka zauna min a gabana kalli fa ta ya zan baka abincin kato da kai a gaban  karama haka ka fiye son jiki,ni a Sanina mace tafi Namiji son jiki sai gashi kai kafi macen ma,sauri ki bani abincin wajen Daddy zan je yanzu,nace da dare nan haka? Ae mana dan Allah kaje Dani pls kaji,Su Meenat fa? sai mu tafi dasu ko a barsu a gida,hmm ina tunanin ma fa Family House zamu koma again tunda naji abinda Daddy ke nufi kenan,Nan take hankalina ya tashi,raina ya baci,muna jin dadinmu shike nan amma ya za muyi ko dan sabo da Daddy sai mu koma,a fili kuwa ban nuna damuwata ba sai ma nace ah kace mu shirya kayanmu amma an gyara mana part ko tunda har almost 1wk bama ciki,yace an gyara komai neat amma ban san me yasa ba ban son komawa amma Kin San Hajja zata takurawa Daddy ne ta fara fushi dashi a kaina,abincin na fara bashi me shegen dadi fried rice tasha hadi da kaji sai fruits da sauran kayan ciye ciye,nace ba matsala karka damu zamu koma ko dan Daddy ba abinda zai faru,kin san ma mene? Nace sai ka fada yace Ameer shike zuga Hajja akan komai na tabbata ma yanzu shine yace sai an dawo daku gidan,nan take na kara Jin tsanar Ameer a raina,Aayan yace Ameer shi ya gaji Hajja a mugunta komai shike tsara mata da Alama ya tsaneki kamar haka nake gani,baki na tabe ta Allah ba tasa ba,ya zaiyi dani ai ni Duwawu ce dole a zauna dani,shegen dan iska,jaraba annamimi da fuska kamar yalo, dariya Aayan dinga yi yanda yaga sai zagin Ameer nakeyi ba ji ba gani yace zagin ma harda Raps Baby ba a tsayawa a huta,dariya nayi nima nace Allah dan iskan yaro sai iyayin jaraba yana gadara da takama sai kace shine Aayan,to ko shine Aayan ma ya isa ya min na kyaleshi,Dariya Aayan yake au nine ma me gadara da iyayi? Nace a'a misali nayi hhh,Allah mutuncinsa daya da yasa nake dan raga masa yanda kuke dan kama dashi kadai kuke kama a gidan nan ni ban san ma ya akayi yayi kyau ba matsiyaci,Nan take naga Aayan ya hade girar sama data kasa kamar zai dakeni,lfy? Allah Baka hakuri in dai akan na zagi dan uwanka ne,Allah dan kuna kama....Tsawa ya buga min rabon da naji irinta har na manta tun farkon haduwarmu dashi,masifa ya fara ni bama kama zaki ce yana da wani kyau baki da hankali idan sonshi kike ba sai kin fada min haka ba ya ja tsaki ya haura saman Bed abinsa.

   Firgita nayi kaina ya daure daga ana labari sai fushi kuma ni mene hadina da wani Ameer kuma,mikewa nayi nace kayi hakuri ba haka nake nufi ba ni,da sauri ya Zabura ya Mike hado kayanku a kaiku can sai ki dinga ganin Ameer me kyau,Ka fahimceni bafa nufina kenan ba wlh,mene abin fushi a nan ana lbr to kayi hakuri na furta cikin sanyi na,shekeke ya kalleni yace na rantse yau sai kun koma Family House Hajja bata isa tasa na Canja muku gida ba ra'ayina ne ganin damata ne dan kawai hankalinku ya kwanta muje kawai na rigada na rantse,gani nayi ina lallabashi yana wani kara hawa nace fine mu koma mana mene to, na fice na bar masa Bedroom din naga cikin fushi yake gaba daya yau.  

    Su Meenat suna shigowa na sanar musu su Kansu basu ji dadi ba,nace su hada mana kaf kayanmu,Meenat tace sis dazu naga wani wlh kamar Abbanmu a mota wani me kama dashi tsaki Naja tare da cewa sai me to dan kin ganshi tunda bai neme mu ba me zamuyi masa,Sis kamar fushi kikeyi lfy? Ko fada kukayi da mijinki? Nan take na fara hawaye ina sanarwa Meenat,Meenat tayi dariya tace Sonki yakeyi kishinki ne,ke komai kiyi fushi ai ba haka akeyi ba,ki daina cewa zaki rama abu ko dole sai kin maida martani kinji mene abin Kuka ai zaku shirya ne,idona na goge muka shirya,Sai ga Aayan ya leko fuska a tamke yace let's go,muka bishi har mota da kayanmu,Driver ne yaja mu har gidan sai da ya tsaya a inda ake siyar da wayoyi ya siyo guda biyu masu kyau da shegiyar tsada ya bani daya ya bawa Meenat daya,sai Meenat ce kadai tayi masa godia ni shuru nayi masa muka je har gidan,Ameer yana so zai fita da mota kawai ya hangoni wani farin ciki ya kamashi Bai San sanda ya tsaya ba ya fake da gaisawa da Aayan,Bro ya kk? Aayan yana fushi kamar zai tsage yace am ok,ya kalleni kawai yace Sis barka da zuwa ko kulashi banyi ba Meenat ce ta amsa,sai da ya kara yi min magana sannan na amsa da kyar ina fitowa da kayanmu,yace Bari na tayaku kaiwa ciki,Aayan yace no need jeka abinka,murmushi ya saki a ransa yana ko banza zan dinga kallonta ina jin dadi na.

   Hajja tana sama tana kallonmu sai murna takeyi burinta zai cika,Abbi bakin mugu yana kusa da ita yana tsara mata muggun nufi,matarsa ma haka tare da sauran  kannen Abbi,Ameer kuwa ganin na dawo sai ya fasa fita kawai ya koma part dinsu.

    Aayan sai fushi yakeyi nima haka aka shigar mana da kayanmu, komai Neat a gidan yasha gyara sai kamshi,muna Hutawa muka wuce bangaren Daddy har Meenat muka kwashi gaisuwa sai murna yake yana jin dadi tare da sa mana albarka,bamu zauna ba muka dawo part dinmu tare dasu muka fada kitchen kamshi ya fara tashi a bargarenmu,sai ga jaraba sun fara shigowa,Sajeeda da Haneefa sunzo harda lekowa kitchen suna tabe baki Sajeeda tace yara ana ta jagwalgwalon ne? kamshi na tashi kamar gaske a baki ba dadi bari yau zamu dan dana muji,Aayan yana jinsu basu San yazo sakkowa kasa ba,yace kafin nazo nan waje Ku tabbatar kun bace min a part Nonsense ya furta yana Jan tsaki,da sauri suka fice Sumi Sumi sai suka tafi wajen Hajja,tana ganinsu tace to fa Allah kawo mu jaraba ta dawo na shiga uku da kawo kara me tayi muku,nan suka shirya karya wai nice nasa Aayan ya zagesu kuma nace ya koresu,Hajja da kanta tace muje wajen nata na daina saurara mata.
    Suka taho Aayan ne ya bude musu kofa Hajja ta fara ta kansa kamar zata cire bakinta tana zagin Aayan,Haneefa tace daga munce idan ta gama girki ta sanmana sai zagi,Hajja da karfi tace ina makirar take tana shigowa kitchen tace gidan ubanki ne ko kayan abincin uwarki ce ta zuba mana,to dole suci idan naga dama ma part dinsu zaki je ki dafa musu abinda suke so,Aayan yace wlh basu isa ba ai ba baiwarsu bace ni na biya sadaki na aureta ba wanda zai sata ko ya hanata sai ni,Hajja ta fashe da kuka Wlh sai na fadawa ubanka yiiiiiiii,muna jinsu a kitchen tace ke dan uwarki wlh sai jikokina sunyi abinda suke so baza ki raba min kan zuria ba,matsiyatan bayi a gama a zuba musu suci,Meenat tace ga danye nan shine naku shi kuka siyo da kudinku wannan kuwa mun rigada mun dafa,kuma hakki ne a kan miji ya ci da matarsa muma tunda ba mutunci baza mu basu ba basu kai matsayin da zamu dafa musu abinci suci ba,Hajja tace iyeeeeee kana ji da girma na suke fada min haka? Yace ai Hajja kin dade da zubar da girmanki shi yasa suka take amma matata me tarbiya ce,Haneefa Hajja ta kiftawa ido tare da cewa Ku zubar da abincin uban kowa ya rasa,Aayan yace wlh duk wacce ta zubar sai gaba daya kun bar gidan nan yau ba gobe ba ai ba gidan ubanku bane,akan Mufee ba abinda bazan iya ba dama darajar Daddy kuke ci gaba daya zaku bar min gida wlh kunji na rantse,haba wani dadi ya kamani a kitchen mijina ya tare min fada ya nuna yana sona a gaban kowa,Muna haka sai ga Ameer da zureriyar wayar wuta,yace ke Sajeeda dan uwarku abin naku har ya kai kuzo kuna zagin matar Aayan,a ransa kuma matarsa yake nufi tunda sona yasa baya so ko sauro ya cijeni,Sajeeda zata masa rashin kunya ya fara tafkarsu son ransa sai da ya Zane musu jiki Hajja na tsine masa tana kuka.

   Gaba daya fadan ya koma kan Ameer Hajja ta sanarwa Abbi,nan fa Ameer aka hadu a kansa suka masa tatas,a ransa kuwa yace babu wanda zai taba Mufee na kyaleshi,ta nan bangaren soyayyar Ameer a gareni rahma ce sabo da shi ke Tsarawa Hajja komai baya bata me kyau a kanmu yanda zata ci mana mutunci,shi kadai ya samu Hajja ya lallasheta ta hakura yace Hajja Ku baku iya mugunta ba ai ba a nunawa mutum a fili ba a sonsa ta kasa zamu bullo musu ki daina bari ana musu a gabansu sai su dauki mataki suma fa suna zuwa gidan malamai nan Ameer yasa Hajja farin ciki ya gama tsarata tsab,yace Asiri muka yiwa Aayan yanzu abinda zasuyi a karya asirin dake jikinsa sai a dora sabon aiki,Hajja ta fara kiran malamai tana so a karya asirin dake jikin Aayan ko wanne iri ne,maganin tsari take so ayiwa Aayan sannan ta sake sabon kalar nata.
   Hajja ta manta Sam anyiwa Aayan asirin da bazai Haihu ba bazai iya komai ba,Kuma tace a karya komai dake jikin sa ko zai karye din oho?

  Abbi Kansu suna mamakin Ameer bai fiye shiga harkar su ta makircin da suke aikatawa ba sai jefi jefi amma kuma yanzu yafi kowa bawa Hajja shawara a kanmu,sai sukayi tunanin Ameer ya tsane mu ne da yawa shi yasa,suma murna sukayi za ayi maganinmu sunga muna nema mu canjawa Aayan zuciya kamarma ya fara sona tunda sunga yana bin umarnina sabanin wancan matan nasa na baya,amma Abbi yace shima dole ya shiga harkar nan dan ganin ya raba ni da Aayan.














AsmaBaffa
[1/20, 09:13] Sayyida Hauwa: ????
????

   KASUWANCI NA







          71-75











Official








By
AsmaBaffa










   Ina matukar Godiya ga masu Sharhi Allah ya bar Kauna,kuma Insha'allah daya bayan daya sai kunga sunanku a Novel din nan na Kasuwanci na,sai dai ko Halin mantuwa,ina ganin sharhin ko wacce kuma kuna cikin list dina,sai dai duk wacce taga kamar na manta da ita ta tuna min pls love u all❤❤

   Sai masu Sharhi wanda zasuyi watarana ban kula ba suga banyi musu reply ba kuma nayiwa wasu to ayi min Afwa ban kula bane, wacce taji ban kyauta mata ba kar tayi shuru tazo taci kwalata sannan ta tsige min dankwali ta wankeni tasssss???na baku dama.


   Ga page dinki ta gidana,Al albarka, masoyiya ta gaske me Sharhi kamar ruwa,kina birgeni KHADIJA A HAMZA



  Gaisuwa ta zuwa ga babbar me kaunata HANAN ta Gp na gata nan na Cillo ta ki cafketa.?









    Abbi cikin takaici ya ja Hajja bedroom dinta yana cewa Hajja munyi sake,wlh munyi sakaki,taya zamu bari mu rasa dukiya muna ji muna gani,kin san yaron nan ya fara son yarinyar nan shike nan wlh sai abinda tace dashi talaucewa zamuyi dan naga Alama yarinyar nan bata da imani ko kadan, nan Hajja ta fada masa tsarinsu da suka shirya ita da Ameer,Nan take Abbi ya Dafe kai,yace shike nan kun kashemu iceko baku aikata ba? Ya zaki biye wani Ameer ai Rusa mana aiki ne wannan kin San mene a jikin yaron?dama da kyar muka samu wannan ya zauna a jikinsa,Hajja tace mene abin yi? Abbi da yan uwansa sukace ki bar komai a hannunmu,Ameer yazo shigowa wajen Hajja ya dau wanka so yake yazo part dinmu na ga kwalliyarsa.

   Yana jin me su Hajja suke yi hankalinsa ya tashi tabbas yasan sai sunga bayan Mufee amma yace ina Sam ba a isa ba baza a Rusa masa farin ciki ba,Shiga Bedroom din yayi tare da Zama gefe yana jinsu suna ta tsare tsare dan kar su gano shi sai ya dinga kiftawa Hajja ido yana mata signa da ido,ko idan Abbi yace ga abinda za ayi sai Ameer ya makewa Hajja kafada wai kar ta yarda,Hajja kadai ke gane me yake nufi,su kuwa su Abbi basu sani ba,sai ji sukayi Hajja tace me kuka sani,me kuka iya,har nawa kuke a duniyar,ni na tsuguna na haifeku zaku zo kuce ni zaku canjawa tunani,to baku isa ba iyyeee wato Ku ga wayayu wayonku yafi nawa?Ni wato bani da tunani ban san me nake ba ko? Abbi cike da ladabi ya Dafe kai yana Oh Hajja ki saurara kiji,Ameer ya kara makale mata kafada yana mata signa,Sani Kanin Abbi yace kai dan ubanka me ya sameka ne ko kafadarka ke ciwo ko tabin hankali ka hadu dashi,Abbi yace Lfy? Yace gashi nan Ameer sai wani makale kafada yake yana wani farfari da Ido ko dan daudu ka dawo bamu sani ba,kaga dan iskan yaro to uban me kake yi, pink lips dinsa ya turo yace to ni me nayi daga abu ya cijeni sai ace bazan sosa ba,Abbi yace to zaka bar dakin nan dan uwarka,Hajja tayi gazal tace kar Ku Zagar min shi ba ruwanku yaron kirki irin Ameeru dan albarka,Abbi ya tabe baki yaci gaba Hajja ki Bari muyi tsarinmu,Hajja tace sam bazai yuwu ba ni zanyi haka kawai na zauna jiranku wankin hula ya kaimu dare komai naku na yan boko sai anyi lissafi an tace an rairaye sannan a aikata,mu kuwa sha yanzu magani yanzu,Abbi suna matukar yin biyayya ga Hajja basa tsallake maganarta haka suka kyaleta cewa tayi nata suma za suyi nasu,Ameer ya kara kallon Hajja ya makale mata kafada Hajja tace a'a  ban yarda ba Ku bari idan na gama kalar nawa Bai yi aiki ba sai na baku dama kuyi naku mu gani,a haka suka tsaya amma Abbi yace karta je a karya asirin jikin Aayan pls sabo da akwai shirinsu a jikinsa,A nan kawai Hajja ta yarda cewar ta fasa karyawa kawai zasu ci gaba da nasu,a nan Ameer bai hana ba tunda ya hana abubuwa da dama kar Hajja ta ganeshi ne kawai ya hakura.

    Direct part dinmu Ameer ya zarce irin dole fa naga wankansa wanda ni ban san me yake nufi ba, ya kuwa yi dace muna zaune tare da Aayan a Palo yana fushi dani tun kan maganar Ameer dan nace yana da kyau,yaki cin abinci yau fushi yakeyi,har yamma 5pm yazo ya zauna a Palo,kuma nasan yunwa yake ji sai chat yake a waya,har sabon girki na masa kala biyu yaki ci,Yanzu haka ma Kunun gyada na masa na Dade banyi masa ba sai kosai naga yana sonsa,wanka na fesa Malam kamar a London cikin Wando tight iya rabin cinya Maroon,sai rigata fara me arnen kyau gashi yasha gyara na sakeshi na danyi masa style a gaban goshi kadan,Allah tsine wanda zai ce ban hadu ba yau ko mutum dutse ne yau ya kalleni sai jini ya fara gudana a jikinsa.

    Sabo da haka ma na kalli Meenat da suka dawo daga Islamiyya nace to ku zauna a Bedroom kar naga yar iskar da fito palo Dariya Sukayi Meenat tace to kin manta zamuje birthday party din kawata yau ni da Ma'eesha zamu wuce ta palon, wanne which kind party ba inda zakuje kun San dai ko Ammah na da rai bata bari muje wani party,bafa wani party bane na kirki sis,Driver baya nan kun sani schl ma yau banje ba kun  sani dai wa zai kaiku,zamuje a napep,fine amma kafin Ku fita kuje Ku fadawa Aayan shine ke rike mu yanzu kamar yayanku ne ko ma uba idan ya yarda kuje idan yace no shike nan.
   Meenat tace uhm lallai Sis yanzu mun koma hannun mijinki ma? To kici da kanki kiwa kanki Sutura sannan ki zauna a gidanki Meenat,duk wannan shike mana ai ko dole baza muyi gaban kanmu ba,ni macece Allah ya rufa mana asiri mun samu me Kula damu shike nan kuma komai sai muyi ba saninsa?

    To fa wasu idan ana rikesu a gida ganin wanda ke rikesu ba shine ya haifesu ba,kuma suna tunanin in ya tsine musu ko ya musu baki baza ta kamasu ba,kana gani zaka ciyar da mutum,ka shayar dashi,tufatarwa ka bashi ilmi da sauran abubuwa wasu ma ko yayansu basa yiwa rikon da sukewa dan riko sabo da su kyautata sai kaga kuma wanda ake rikewa yafi ma dan gidan iko,gadara,da rashin mutunci a gida,ayi ta ganin laifin masu rikon da ka zauna a gidan zaka ga yaron Ashe kwallon shege ne,ba wanda ya isa ya fada masa yaji,abinda yaga dama shi yakeyi baka isa dashi ba,da ka takura ace ka zaluncesu,kana gani zaita abinda yaga dama karshe ma wasu kaji a gari suna zaginka suna kala ma sharri cewar baka musu kaza kaza gari ayi ta tsine ma,karshe ma wasu su dinga cewa marikan nasu iyayen banza,ko a gidan suyi ta shirya ma mugunta iri iri suna zalintarka baka sani ba,more especially ace matar me gidan ce ta dauko wani ko wata take rikewa,suna ganin kamar itace da gidan ma ko saurarar mijin nata basa yi bayan komai shike yi a gidan suna cin arziki,kawai matar zasu fadawa itace take rikesu itace yar uwarsu mijin nata ko gaisuwa sai sunga dama,itama kuma tana kallo gani take ma ita ke musu komai ba mijin ba,bayan da dama zaka ga komai shi za a fadawa yayi musu amma Bai isa dasu ba,wani ko aikene sai dai ya aiki nasa ko na waje,da yawa ana magana kan azzalumai masu rikon yara ko yayan kishiya ko na yan Uwa ba a fadar laifin yaran,duk da cewa akwai masu zalincin Amma ya kamata mata masu dauko rikon Yara ko mijin ya kawo miki a daure a nuna musu muhimmancin me rikon nasu.ba kawai ayi ta yin abinda aka dama ba ana ganin ba iyayen da suka Haifa bane me zasuyi ya bika.

    Fita nayi ina sheka uban Kamshi Aayan zaune a palo yana danna waya na karasa dauke da hadadden tire jere da abinci iri iri,gaba daya bana jin dadin fushinsa yau,duk sai naji duniyar tayi min zafi,tun kafin na karaso ya zuba min ido yana kallona kamar ya hadiyeni naji dadi a raina ko bai fada ba nasan ya yaba kuma nayi kyau,kafin na gama tunanina ya juya min baya a saman 3seater tafkekiya,ni dariya ma ya bani kamar yaro na fushi,
  Ranka ya dade ga abinci ka daure kaci kaji,dama ni na saba da lallashin mutum kan dole yaci abinci ji nakeyi kamar nice banci komai ba shi yasa nake nacin sai anci abinci,Muna haka muka ji bugun kofar Ameer,na manta shigar dake jikina nayi hanyar Door zan bude, muryar Aayan naji a hankali yace kuma a haka zaki fita again? Da sauri na koma daki na saka Katon Hijab sannan na fito na bude kofar,Ameer yasha wanka gaskiya ba karya yayi kyau cikin kana nan kaya,Murmushi yayi min na bashi hanya ya shugo,Aayan tunda yaga shine ya kara hade rai da kyar ya amsa masa gaisuwar tasa,Yau Ameer harda ce min Aunty ya gida,ganin da mutunci yazo da fara'a na amsa masa nima sannan na koma kusa da kafafun Aayan inda yake kwance na fara masa tafiyar tsutsa a kafafu ina wasa da yatsunsa,Ameer yana satar kallonmu ransa ya baci sai kishi yake taso masa Amma ya danne, Aayan yana kallon yanayin Ameer shi bai yarda dashi ba sam yayi kicin kicin.

    Cike da shagwaba nace Yanlabai Abincin pls,wani shock yaji a jikinsa yanda nayi maganar shi kanshi Ameer sai da yasha mamakina a haka yar yarinya dani sai iya shege fal ciki,Ameer a ransa cewa yake ina ma nine Aayan gaskiya ya dace wlh irin wannan kulawa haka ga shagwaba kai da sake,a fili kuwa kamar baya jinmu danna wayarsa yake ya hakimce a kujera,Damun Aayan nayi da pls kajiii har sai da ya gaji ya mike zaune tare da ajiye wayar gefe can yace Bani zanci,da murna na zuba masa tare da mika masa,kin karba yayi yace hannunki aikin me yake? Da Sauri na gyara zama kusa dashi,yace ba fa a dining bane bazanji dadin ci ba,Nace ya zanyi to? Ke kika damu naci ai sai kiyi yanda kika ga dama ya fada cike da gadara, cinyarsa kawai na zauna samanta sosai bai ce komai ba sai lumshe ido da yayi ma,

na fara bashi a baki da hannuna idan na bashi bazai ko hadiye ko taunawa ba sai nace to ka ci mana sannan zai fara taunawa yana yanga yana kumbura wai fushi yakeyi shi fa,Ameer Kamar Tv yake kallonmu ya wuce gaban a share abin,yanzu ma waya Aayan yake dannawa yaki dago kansa bare na bashi abinci nayi nayi lallashin ya dago yakiya,sai ma ya kara yin can gefe da kansa ina binsa da kyar na rike kan da hannu na biyu na saitashi nan kuma ya tsaya Kikam a haka yaki bude bakin,Sai da nasa daya hannuna na bude masa lips sai ya datse hakoran nasa kuma suma,Yatsu nasa na ware su da kyar ya hangame dan mitsilin bakin nasa ya barshi haka,Ai Ameer tagumi ya rafka tare da Sa mu gaba kamar Tv yana ta dariya, na Sa masa abincin yaki kulle bakin bare ya hadiye nan ma Hannu nasa na rufe na matse bakin sannan ya cinye, haka yake ta bani wahala idan nayi wannan sai nayi wancan duk ya gajiyar dani ni kuma kamar dole sai yaci.
   Ameer ganin gatan Aayan yayi yawa ma haushi da kishi ya dameshi gashi wani abin yana sashi dariya ma watarana Amma kishi ji yake kamar ya mutu ko Ya batar da Aayan ace yau shine ake masa haka ai da yafi.

    Muna zaune na zubawa Ameer nace gashi Ameer kana shan kunun Gyada na sani ko? Ga abinci ma ka zuba ai ko ba ya sha sai ya sha yau tunda ni nayi girkin kuma daga hannuna ya fito, ya karba yana sha ko kallon Aayan baya yi Sabo da haushinsa yake ji ya aure masa Mufee Amma ta wani fannin yana godewa Aayan dan ta silarsa ya sanni kuma zai kwace ni nan gaba.

       Muna zaune sai ga Meenat da Ma'eesha sun dau wankan Material dinsu na ankon Birthday da zasu je yanda suka sha kyau ba a magana,Kamar yanda nace haka suka zo gaban Aayan tare da durkusawa suka gaisheshi cike da Ladabi sannan sukace Yaya Zamuje Birthday din kawarmu ta schl a gidansu akeyi idan ka Amince,mamaki yayi sannan kuma yaji dadi ga Sis dinsu basu nemi izininta ba sai shi gaskiya suna da tarbiya sun san me sukeyi,da murmushi dauke a fuskarsa yace shine kuka sha kyau haka salon a dinga kalkemin matana gaskiya am gealous dariya mukayi gaba daya har Ameer,Ameer yace Wannan Ma'eesha ai tafi kyau ma wannan Meenat ta fiye iyayin tsiya wai ita me kwalliya shi yasa bana kulata ni,Dariya nayi nace Wannan ai tsokanace Ameer kana ganin Yan mata an hadu,Ameer ya tabe baki tare da cewa masifaffiya dai ta fasawa Khaleel kai rannan wannan ai Dukan mijinta zata yi watarana, shi yasa ma bata da saurayin kirki sai irin su Kwaja da Nasuru Opera,Aayan ya sheke da dariya Kai Ameer wanne Nasuru Ópera din kake nufi? Ameer yana dariya yace Opera daka sani wanda su Haneefa suke aikensa Sa ido wajen wanda suke fada ai Camera suke bawa Opera Sabo da shige shigensa ake ce masa Opera kaga ko ina ka shiga ta Opera kayi Searching,Dariya muka dinga yi banda Meenat da take son yin Kuka.

   Ma'eesha tace wlh mantawa nayi Sis ban fada muku ba rannan ma a hanyar schl wani ya dinga bin Meenat yace sunansa FELA me GALA wai shi dan rawar gala ne  a kasuwannin kauye baku ganshi ba kafafunsa kamar na sauro yasha wandonsa Fela kato sai uwar Kafada kamar ansa riga a hanger ,Ameer yana dariya yace baki da sa'a Meenat Allah yayi a cikinsu zaki samu miji wai ya akayi ke duk wankan naki da iyayinki kike karewa a yaran su Sajeeda,Nima nace dama Yaran su Haneefa ne? Ameer yace sosai ma ai Fela Gala shike sanar musu duk wani wajen chasu idan za ayi show Saturday sunday irin su Haneefa ai duk basa muamula da manyan Yara,ki kula ki gani duk wata yar duniya me ji da kanta zaki ga mace har mace ga kudi ga kyau Amma indai lalatacciya ce bata taba kula mazan kirki sai daí ki gansu da maza kazamai,garori,munana, tabbas zancen Ameer hakane na fada a raina duk haka yan bariki suke kuma mace na ji da kanta Amma in kaga wanda take kulawa suna harka sai ka kusa kuka.

   Aayan yana dariya ya kalli Meenat da ta hade kamar yar Minister ya kasa rike dariyarsa duk ya san yaran nasu Sajeeda,karku damar min mata Kunji na fada muku kai Ameer tashi ka kai min su Driver dinsu dama baya nan kaga kaima kaci wanka kuje ko zaka samu wata Operiya a can kaima, wannan yarinyar da bata da kunya zaka ce na kaisu,Magana nayi nace haba Ameer ka kaisu mana kuje ku dawo yanzu ko dan ni ka taimaka,Ameer yace  a ransa dole na kai tunda Umarninki ne Queen Mufee ta,Tunda zan faranta miki ai zan kaisu dole,A fili yace Sunci darajar Ya Aayan da ke  kuzo mu tafi kuma ku tabbatar takalminku fes yake kar a bata min mota,Meenat sai Harara take zuba masa har suka fita tare gaba daya,da Sauri ya wuce wajen Hajja yace ku je jikin mota ina zuwa,

yana Zuwa wajen Hajja tana ta faman kurbar kunu yace Hajja Albishirinki na samo babbar hanyar maganin matsiyatan nan,Hajja tace mene abinda ka samo fada min Dan Albarka, yace yanzu zan shiga jikinsu sosai zaku ga muna mutunci dasu sosai,zan kwantar da kaina a wajensu yanda zasu yarda dani kinga kafin mu karbo maganin da zamu Sa musu na kulla alaka dasu me karfi ni sai na shige na aikata komai da Komai ko Ya kika ce,amma in ba haka ba za a samu matsala wajen aikata abinda malamai suke so a kansu tunda basu yarda damu ba,don haka yanzu zan fara kullum zaki dinga ganina a part dinsu zamu dinga mu'amula har su yarda dani cikin kankanin lokaci sai kawai mu gama dasu,Wani farin ciki ya kama Hajja,tace haka za ayi yanzu ka kawo magana me kyau,amma da ubanka yazo min da maganar banza ba basira ba wayo a ciki,to Amma kana ganin zasu yarda ka shige musu jiki har su yarda dakai? Ameer yace har nayi nisa ma yanzu ma sun yarda dani gashi nan sunce na kai mata kannenta wani party na dawo dasu,Hajja ta mike tsaye da murna dan Manzon Allah fa? Ko wasa kake?Yace da gaske leka ta window zaki gansu shi yasa nazo na sanar miki kar a kawo miki gulmata ki yarda kin san muna tare ke nakewa aiki,Hajja tace yo wa Isa ya kawo min gulmarka dan Albarka ai kasan bana yarda da maganar su a kanka,dariya Ameer yayi a ransa yace tsohuwa kenan nima kaina nake gyarawa hanyar samun Mufeeda na aureta ina ruwana da wani kudirinku ke dasu Abbi can da yawarku,a fili yace Hajja me zan siyo miki? Hajja tace abinda ka saba siyo min kullum dan Albarka,Ameer yace ai yau ba Hantar Rago kadai zaki ci ba harda yan shila idan ma dawisu kike so shi zan kawo,Dariya Hajja ta saki tace Ko mene ma duk ina so tunda kaine dan Aljanna.Ameer ya fito ransa fes ya tsara Hajja Sabo da yasan ana ganinsa tare da Su Meenat za a kai gulmarsa wajen Hajja ta daina yarda dashi,yanzu kuwa ya kashe bakin tsanya.

    Yana fitowa ya harari Meenat ke zaki shiga baya Ma'eesha ta ce zata shiga gaba tafi kyau baza a ganni da mummana a gaban mota ba,Meenat tayi banza dashi ta shiga bayan felleliyar motar Ameer, Ma'eesha a gaba,Ameer shi irin yan Tsabtar nan ne da shegen iyayi shi a dole Saurayi wankan ma da yake irin na mawakan turai matasa irin su Justin Bieber etc kowa yaga Ameer zaiyi tunanin kwallon dan iska ne ko ta askinsa kawai ba sai an tambaya ba,wandunansa kansu na zamani samari masu ji da kansu,Duk da cewa duk matasan yan wanka ne a gidan su Ameer Amma Ameer shi mata ma rubibinsa suke gashi da wanka Tsabta ga kamshi kuma yana da kyau wanda ke jan yan mata Uwa Uba ga diri me kyau.

    Aayan ne kadai bazai já dashi ba dan Aayan shi halittarsa ce ba kakalowa yayi ba haka yake komai in yayi me kyau ne,shiga kuwa dama shi a turai yake kana gani komai a jikinsa yake ba wasu yan dabaru akayi ba zallar baiwa ce,Shi kuwa Ameer tsabar kakale kakale ne da jarabar son iyayi ace Babban yaro sai da ya tsatso kyansa ya fito fili,Su Mujaheed ma haka suke shegun duniya ne wajen gayu,Suna Tafiya a hanya Ameer ya daga waya wata cikin yan matansa ta kirashi yanda ya kanannade murya kamar Sardaunan Ramlat yana Rapping English kamar wani Dj khaleed,Baki Meenat ta tabe tana jin iyayin da yake faman Digawa,aranta tace wannan wlh irin mijin Sis ne har kusan Halinsu ma sai daí Aayan karshe ne a komai,bayan ya gama wayar ya wani rare kidan Nija kawai tashi yake kamar zai fasa mana kunne,Maeesha ce mayyar rawa har ta fara yi a motar tana ihu uhhhh tare da dage hannaye sama,Shi kuwa idan kida yayi kida sai daí kaga ya bugu sitiyarin yana juya kan mota komar ma motar yakewa rawar,yanayi da kansa gashi duk Baiti ya iya abinda suke cewa kamar shi ya rerata, dama ga motar tasha tint ta samarin zamani,Maeesha yin abinta take wata tana shigowa me dadi tace ohhh yeee taci gaba da yi tana bi itama shi kanshi Ameer ta bashi dariya,ya kalleta yace ashe dai ke yar gari ce kin waye,duk kin san wakokin nan haka Amma kin iya rawa? Ma'eesha tace sosai ma ai  wayar Sis Mufee nake sacewa naje schl da ita na turo latest a wayoyin classmate dina,duk wacce ta shigo bata wuceni har rawar,Ameer ya mika mata hannu suka tafa yace kin birgeni ta gidana,ai kawai a Shana,tace tunin ma ai Baza a barmu a baya ba ina jss3 fa going to ss1 ai dole aje damu,Ameer yace yessooooo Baby,

Meenat tana jinsu suna tayi sun cika motar ga kida ga surutu suna ta yi da baki gashi ana jin wakar ana bi kuma da baki ga rawa anayi a zaune gaba daya sun gigita motar.
     Meenat kuwa wayarta take latsawa wacce Aayan ya siya mana tare katuwar gaske.
    a wani karamin hole akeyi Amma ya tsaru sosai wajen sabo da yarinyar dangin masu kudi ne shi yasa aka tsara abin,ashe yarinyar Cousin din Sameera me yan daba ce,itama Sameera tana wajen itace ma ta hada mata Birthday party din,Yan mata irin su Meenat duk sune a wajen ansha wanka da samari na schl Yara tare da wasu kuma manya sai yan Uwa,Yarinyar  Husna tasha wanka ana ta pics wasu na rawa,su Meenat ma suka Parker a wajen,Ameer yace ki bari yarinya na kankaro miki girma yanzu,Harara Meenat ta watsa masa,yace ni da zan taimaka miki nayi featuring dinki a wajen,Maeesha tace muje tare Yaya Ameer ni kayi ft dina ko a pics din da za muyi,kina ja Baby kanki na kawo light muje,ya rikewa Ma'eeshah hannu Meenat na gabansu duk inda suka wuce sai an kallesu,abinda Meenat bata sani ba an san Ameer sosai shima yanda yake nuna kudi da kalar Naira yana karyar arziki,kusan dama Daddy na Aayan ya makalewa lokacin Aayan bai dawo Nigeria ba,Ameer yake likewa Daddy sai da yayi suna sosai,ko a Tv za a nuna Daddy zai bude Abu sai kaga Ameer a wajen tun yana karami yake son ace shi wani ne yayi suna duniya ta sanshi shi yasa da farko bashi da Kamar Daddy shi yake masa labadi,ganin haka su Abbi suka juyawa Ameer hankali da ya girma sosai sai ya daina Saurarar Daddy gaba daya yake bin iyayensa.

     Ai kuwa Meenat tasha mamaki yanda taga ana ta kallon Ameer ana girmamashi ,mata na rubibinsa,Har uwar gayya Sameera tazo wajensa suka gaisa tace Ina Aayan?Yace yana gida,ka gaisa min shi,wannan yaran fa?ta furta tana mana wani kallon Banza,tana ta kallonmu tace Amma wannan sunyi min kama da wata sosai,yawwa yarinyar da Aayan ke aure,Ameer yace kannenta ne,Sameera tace kai Amma yarinyar bata da kunya ko kadan ina nan zan gyarata soon,nan take Ameer ya canja fuska yace ban gane ba? Tace kwarai tayi min laifi wanda ni kuma sai na nuna mata duniya ba kowa ake tabawa a kwana lfy ba,Ameer ya fusata yace lallai kema kuwa da kin tabbata wani in ya tabaka ya taba banza kuma ba kowa ake tabawa ace za a iya ramawa ba,wani in ya taba har abada ba a iya daukan fansa a kansa,Sameera tayi murmushi tace ba irinmu ba wlh,Meenat ma tace to ke har wace da baza a miki ki hakura ba wata tsohuwa ma dake,Sameera tace duk sai kun maimaita abinda kuka ce,Ameer yace Sameera kin san Halina ke a yan daban naki kanana ne kawai kallonki ake ana tunanin kin wuce haka Amma baki kai ba,wlh wlh kika sake wani abu ya samu Mufeeda ki fara irga kanki cikin wanda suka sheka lahira kin san mu kin san Halina try me.Dariya Sameera tayi tace Ameer kenan ko Aayan da take matarsa bai ce min komai ba sai kai? Husna ce tazo ta janye su gaba daya tana kuzo muyi pics nan fa suka dinga daukan hotuna Har Ameer dan shishigi cewar Meenat,yan mata kuwa jikin Ameer suke faman mannewa ana daukansu,anyiwa Ameer  ma haka inaga Aayan uban kyawawa da daukan wanka Meenat ta fada a ranta.

    Tunda su Meenat suka tafi naci gaba da bawa Aayan abinci yana min yanga,Yana karba da kyar har na gaji na mike na barshi a nan yana fushinsa,Kwashe komai nayi na gyara ko ina aiki yana kallona har Magrib tayi na shiga kitchen zan mana Dinner,Ban san sanda yaje masallaci ba kuma bai dawo ba har bayan Isha sosai,

     Su Meenat Suna gamawa Ameer ya dawo dasu gida sai da ya tsaya ya siyo musu ice cream sai yace banda Meenat bata da biyayya nawa dana Ma'eesha ne,Meenat tace sanda zansha ma ka sani ne,kuma sai na sha sai dai ka mutu.
    Ina gama girkin na gyara komai na gidan nayi wanka nasa rigar bacci ta da turare na kaiwa Aayan abincinsa yana dakinsa ya dawo ina ajiyewa na juya na bar dakin,Bedroom naje tare muka ci abincin  mu dasu Meenat muka koshi bayan ina dafawa naci wani kitchen Sabo da tsaro ko Aayan zai ce muci tare sai yaga ina cin kadan irin yar gayu ni. 
    Muna gamawa mukayi Brush muka kwanta tare dasu kamar yanda mukeyi da,Meenat tace to yau kuma baza aje hirar ba?Nace ina ruwanki Sa ido,Meenat tana dariya tace a'a maida wukar bani na kar zomon ba,Sis yau ba jin dadi?Dan Allah da zafi ko dadi ne dashi nasan yanzu an gama kwashe ki,Dukan wasa na kai mata ina dariya nace zan ci uwarki wlh uban kwasheni akayi ki bari idan kinyi auren kyaji naki kalar, kwana nan zan fara zuwa gyaran jiki idan munyi hutun schl zan karbi kudi wajen Aayan Amma bazance gyaran jiki zanyi ba kar ma yayi tunanin shi zanwa ko sonsa nake,Meenat ta dinga dariya tace Sis wa zakiwa gyaran jikin to? Kyaji dashi can sai kizo nan ki tamana zancen da bashi kenan Ba can kuma da kinje ki zage ku sha love,oh karya nake miki kenan? Meenat tace to mu dai kiyi bacci dan Allah mun gaji da labarinki ke Sis sai za ayi bacci kice zaki bamu labari,ko tsakar dare ki tashe mu,

Nace Meenat kinfa rainani wlh tam,ai kuwa sunyi Baccinsu wurin 12 na kasa bacci sabo da tunanin Aayan Yamin yawa sai juyi nake ina tunano yanda muke murza juna ina murmushi ni kadai, na tuna da abinda nake so muyi shawara da Meenat Aiko ba bata lokaci na juya jikin Meenat dake shakar bacci nace Meenat ina girgizata tsaki ta ja  tana sosa gefen kunne,nace Meenat ki tashi mana na daka mata duka ta mike a firgice, nace mantawa nayi ban fada miki ba wai don Allah rannan kika ce kinga alamar Aayan kamar yana so na? 

    Wani takaici ya kashe Meenat tace yanzu akan wannan zaki tasheni kusan karfe dayan dare?Nace ae gwara na kara jin gaskiya,cikin magagin bacci Meenat tace baya Sonki ko kadan,yaaaa tsaneki ne Sis kin kasa ganewa bakya birgeshi ko kadan ta koma ta kwanta sai baccinta takeyi,ni kuwa gaba daya naji duniyar ta kife min.

    Nan danan zazzabi ya fara kamani me zafi ga bakin ciki Meenat ta gano Aayan baya sona bana birgeshi,nan nayi tunanin yes gaskiya ne tunda ko yabo na ba yayi bai cewa ina da kyau na hadu,wannan ya nuna ya tsaneni sosai ne kawai sai na fashe da kuka na dinga yi da karfi a saman Bed cikin bargo,duk na hana Ma'eesha da Meenat bacci da Kukana sai ma kara karfinsa da nayi,sai tsaki sukeyi suna juyi su fa sam basa kaunar bacci tare dani dama tun Asali tun Ammah na da rai Sabo da tashinsu nake na hanasu bacci,lokacin ina Sana'a a gida tare da da Ammah cikin dare zan tashe su nace sai munyi lissafin kudi ko na fara basu labarin ya za ayi a tara kudi,ko tattali,idan kuwa nayi Sana'a banci riba ba ko jarin ya karye to fa sunga ta kansu kwana zanyi ina kuka a kan gadon mu,Ammah watarana sai ta jawo sandarta ta kwandala min sannan nake shuru dan ni bacci bai dameni da yawa ba,na riga na saba da jarabar neman kudi ban fiye bacci me yawan gaske ba.

   Suna jina kalar Kukan da nake harda me jiniyar motar yan kwana kwana,Meenat tasa Hijab ta fice har saman Aayan dan ita ta manta ma tace Aayan bai sona,cikin magagi ta fada min,knocking tayiwa Aayan ya zata nice sai yaji muryar Meenat,a firgice ya bude tunaninsa wani abu ne ya sameni tace wlh Yaya mudai kazo ka tafi da ita ta damemu wlh sai kuka take ta hana mu bacci,ko ka canja mata dakinta ita kadai mu takura mana takeyi,me ya sameta? Ba komai mu bamu sani ba dama haka takeyi ko a gida idan ta fadi a Business ko jarinta ya karye to sai ta kwana tana uban kuka har sai tayi Zazzabi,Aayan yace akan kudin? Meenat tace sosai ma watarana akan Naira darinta ta fadi a kasuwa sai da ta kwana tana kuka karshe sai da aka mata Allurar zazzabi Sabo da kuka,Duk daren nan sai da Aayan ya dinga dariya,Meenat tace ranar da jarin Awarar ta ya karye aka rasa dubu daya mun zata wlh ta samu tabin kwakwalwa,ni dai kaje dan Allah ka daukota a can ta damemu mu,maeesha ma tana zaune ba bacci kuma gobe muna da Test a schl. 

   Meenat na gaba Aayan yana bayanta suka je har Bedroom din yanda nake haka nake ta barka kuka na,muryar Aayan dana ji ce tasa na kara ci gaba da kuka na yafi na da karfi ma,na cukwikwiye kaina a bargo ga uban gumi na hada,yace ke mene haka? Amma anyi girman banza babba dake to wa zai wa wani fada kenan? Na dauka ma lallashina yazo ya lallabani mu tafi dakinsa sai kawai naji ya rufe ni da bala'i, Kamar me Aljanu na dinga shure shure a Cikin bargon na kara ci gaba da kuka na,ina wayyo Marainiya ni,Zan mutu, Meenat tace baza fa tayi shuru ba wlh sai a kwana a haka da ita gwara ka dauketa kuje can in yaso ko zaneta ma kayi mu muyi baccin mu,Maeesha tace wai me akayi mata ne tana dariya tace wlh sis Mufee baza ta girma ba ko ni na fita wannan kuka dama ta saba abinta,Aayan yace Dan kune kawai zata hanaku bacci Amma da Bazan kalleta ba ta shekara tanayi,Meenat tace dan Allah ka rufa mana asiri ka dauketa muyi bacci,Aayan ya fara kokarin janye bargon dana ke ciki yana tsaki nace wlh tunda yayi tsaki Bazan je ba a barni nayi Kuka na,da karfi ya fisge bargon ya hau saman Bed din yanda nake kwacewa ina burburwa hannayena ya rike biyu na kasa motsi sai Kukana nake harda hawaye kwara kwara,ya samu bakina yasa yatsun hannunsa dan mugunta ya dinga dalla masa yatsansa kamar Harbin kunama ba shiri nayi shuru,tashi mu tafi yace, nace Bazan je ba,ai kuwa ya make min baki naji zafi ba shiri nace zanje wlh kayi hakuri,meenat sai dariya suke ya figeni yana jana fii yace kusha baccinku yau zata gane kurenta,Meenat ta rufe kofa tace wanne zata gane kurenta wai mu za awa wayo kuje dai ku sha iskancinku kuyi luf abinda shi kanshi kasa bacci yayi dama hakan yake so na ganeku.

   Ai kuwa kamar Meenat ta sani yana kaini Bedroom ya fara masifa yana min fada ke baki san kina shiga hakkinsu ba? Ba kyau takura rayuwar wani Yara suna so suyi bacci kuma a gabansu kannenki kike musu kuka,ai ba su akewa ba matan aure me gida sukewa kuka ba wani ba,idan shagwabarki kikeji kizo kiyi min ni zan dauketa ba su ba,nace to ni me nayi abinda fushi kake dani, yace ba dole nayi fushi ba muna Business dinmu kinzo kince Ameer yana da kyau ke yanzu zaki ji dadi nace Meenat ce me kyau ba ke ba,to ai nima sau nawa kace Meenat ta fini,wannan ai cin fuska ne,to ki kiyaye yanzu duk kinsa ma na fasa baki kudin Business sai an sake sabo,nima dadi naji zan masa wayo naji dadina nace to a sake sabon mana wa yake jin tsoro tunda kudi zan samu sai na samu wanda yafi na da ma.

   A ransa yace lallai Mufeeda yarinya ce yanzu ta yarda,nima a raina nace dadi a banza kuma a bani kudi nice da riba ka hadu da ni,Muryarsa naji yace to yanzu duk kukanki da shagwabarki Maza sauketa a kaina ki samu kudi kuwa da yawa yarinya,Nace ai ba sai kace ba yanzu zan nemo hanyar arzikina mota,gida da kasar waje ko da kafar katako,jikinsa ya jawoni muka fada saman Bed ba kunya na fara kuka na irin na dazu,shi kuwa lallabani ya farayi yana mene ne Pretty na? Na koma shagwaba kala kala yana biye min tare da fara sarrafani,a raina nace da haka kawai ina can zanyi kwanan kunci tunda hakane Meenat na gano yanda zan dinga baki aiki idan ta baci,Aayan kuwa a ransa dadi yake ji marar misaltuwa yana godewa Meenat dama ya kasa bacci ko kadan ni kawai yake bukata.










AsmaBaffa
Reply
#8
KASUWANCI NA


76-80


Official

By
AsmaBaffa

Ina mika dubun godiya ta gereku
MAMAN 2 KIDS
AUNTY SUMEE
MEENAL SIDI
MRS HAMZA
ADABIYA ISAH
SAMEERA AHMAD
JAMILA SULE
MAMAN MEENAT

    Sai manya manyana ina jinjina muku
MAMAN MEENAT
MUM SUHAIL
MAMAN HAIDAR
QUEENMERMU
MAMAN WALEEDA
JIDDER ZARIA
MARCYCOOL
PHERTIMARH
AUTA
FLOWER ina kike kwana biyu Allah yasa lfy?
BIBA
HEENDU
HUMAIRAH

Page naki ne AYSHATABDULLAHI Me hadarin Sharhi na gode.??

Kwance nake a jikinsa na lafe luf muna huce gajiyar harkoki da muka kwasa,kin taba soyayya Ne Mufeeda? Naji muryarsa yana tambayata,wow yanda ya furta Mufeeda kamar wasu Aljanu ne suka fada Sabo da dadin sunan ba a cewa komai, kamar gaske nace ae na taba yi,gabansa ya fadi sosai ya shiga damuwa har kishi ya cika shi ya daure yace da wa? KUDI nace ina na san wani so ni ban san komai ba ai ni imani na kudi,ni kudi ne masoyina,Dariya yayi a ransa yasan ban san ma kudin ba ban san dadinsu ba Amma ina kirarin nasan kudi,a fili kuwa yace yanzu idan na baki million daya a hannunki me zakiyi da ita? Yanzu duk kuna ci kuna sha da Sutura ga schl baku da matsala da ita,ta ya zaki kashe million daya fada min naji? Kwanciya ta na gyara a jikinsa tare da fadawa tunanin ta yanda zan kashe kudin da ya fada,na gama tunani na nace na dinga cin kayan dadi,na fantama na Sa kaya irin na matan shugaban kasa,na dinga zuwa wajen da ake gasa kaji ina ci,na siyi fili kato,da mota,dariya yayi yace to kuna da motar hawa duk wacce kuke so akwai,me kike so kici wanda babu a gidan nan?Sannan kuna cin na wajen ma ai ko? Ae to ni dai ina so ace nima ina da nawa na kaina ba na wani ba,sabo dame?kayan mijinki ai naki ne, a'a ba nawa bane kafin a baka ma sai kayi yar murya,ko kuma a dinga bata rai ko kasa mutum ke ebowa ya baka watarana sai ya gaji,sannan Maza dan suna ma abu sai suyi ta juya ka ana ma kallon wata shatara, matan Hausawa kenan kike nufi duk abinda yasa suke karatu da aikin Gomnati don kawai su samu kudi ba sai sun saurari na mijinsu ba,kuma most of them badan Allah suke so su samu kudin ba kawai biyayya ce basa so suyiwa mijinsu shi yasa suke neman kudin, ya fita kin fita,bai Isa ya saki kiyi ba,wani ma in kudinta yafi na namiji zai sha wulakanci dole shi zai kwantar da kai yana mata biyayya.

    Nace hakane ko Ilmi macen tafi namiji sai kaga ko kudin albashi ya dauka ita zai kawowa sai yanda tayi dashi,shi yasa Maza suke tsoron auren macen da ta fisu Ilmi ko ta fisu albashi,sabo da matan Hausawa basu iya samu ba,mace daga tana daukan dan Salary sai kuga ta fara wulakanci kowa taka shi takeyi ita me kudi,dan Allah mata mu gyara halayen mu,wasu gidansu kaje da kyar suke kallonka ma bare mutunci ya hadaku Sabo da tana daukan Salary,mazan sam basa jin dadinsu,ga jarabar son kudi da neman kudi aje nan aje nan ba hutu ba lokacin me gida kuma bai Isa yace komai ba tafi karfinsa sai abinda taga dama,idan ma kishiya zaiyi cewa zatayi ya kara me ya dameni suje can su karata da kudina me nake nema a wajensa ko Sakina yayi zan iya rike kaina da Yara na,abin haushin kuma da zasu rabu sai aga ta koma bin Maza kanana tana kashe musu kudin da ta kasa taimakon mijinta dasu.

    Mun dade muna hirarmu dashi yana wasa da dukiyar fulanina wani dadi na shigata na juyo ina facing dinsa tare da kara shigewa jikinsa,yace ya dai? Wani sonsa nakeji yana ratsani ta ko wacce gaba dake jikina,baki nasa ina lashe lips dinsa kamar mayya nan ma haka muka kara birkita kanmu mun dade muna farantawa juna rai,ni kam yanzu son Aayan ya gama ragargaza min zuciya,kwakwaran numfashi banayi sai da tunaninsa,komai nasa birgeni yakeyi,ji nake kamar a hademu na zauna cikin jikinsa har abada abin fa ya wuce gona da iri yanda nake jin son Aayan ya zarta hankali har mamaki nakeyi,bani da burin da ya wuce na ganni tare dashi ina jikinsa,kallon Aayan kadai idan ina yi a Cikin gidan gaba daya sai naji dadi da sanyi marar misaltuwa,nayiwa zuciyata fada abin yaci tura,ko schl naje ba komai nake ganewa ba kawai tunanin Aayan yafiye min komai a duniya.
     Kwanaki sun dan ja,Ameer ko yaushe yana part dinmu kusan kullum sai yazo,a nan yake cin lunch da Dinner haka kullum suke fada da Meenat,Ma'eesha ce kawarsa kullum suna tare suna danna waya da jin wakoki aikinsu kenan, Meenat bata da time yanzu karatun waec da Neco sukeyi,Ma'eesha kuwa za a shiga Ss1 kwana nan,ni kuma ina ss1 going to 2 Sabo da ya tsallakemin jss3 ban karasa ba aka sani a ss1 shi yasa Amma da Ma'eesha ma ta fini class.
   Ma'eesha ta zama yan mata Sabo da kansu daya da Meenat kusan ma tafi Meenat girma ta kamoni Sabo da dama tana da saurin girma tsayin kafa tayi sai ka rantse ma ba Meenat ce yayarta ba,Sabo da zama da suke yawan yi da Ameer Ma'eesha har ta fara son Ameer sosai Amma boyewa takeyi dan kar mu gane sai dai kullum bata da zance sai Na Ameer.
    Kudi masu yawa Aayan ya bamu muje mu sake uniform tare da schl bags da takalma amma sai yace yasan idan nice me araha zan siyo mu tafi tare da su Meenat Driver ya kaimu.

     Muna mota Driver zai kaimu store nace canja hanya Baba ka kaimu Kasuwar kofar Wambai yafi araha,Meenat tace wlh mu store za a kaimu masu tsada yace a siya mana,Baki na make mata tayi shuru,ya kaimu Kofar Wambai muna gaban table din masu takalma ina ta zabga cikiniki yaki daidaita,na daga wani baki nace nawa wannan Malam? Dubu uku yace,a garin ina za a siyi wannan dubu uku Malam Dubu daya da Dari biyar idan ka siyar, Ma'eesha ce ta matsa gefe tare da kiran Aayan a waya Hello Yaya taki kaimu store wlh muna kasuwar Kofar Wambai kuma a kasuwar ma table din masu araha wai dan Dubu daya da Dari biyar kuma suna ta Surutu da masu saida kayan dan Allah da aurenta fa Yaya.
    Mata masu zuwa kasuwa a zauna ayi ta Surutu da masu saida kaya,da aurenki zaka ga wasu har canja murya suke suna lankwasheta abinda basa yiwa mazajensu sai siyiwa yan kasuwa sabo da suna neman a rage musu ayi musu araha su siya a banza.

   Aayan kuwa kishi ne ya sokeshi da bacin rai wai yacewa yarinyar nan  suje Mall amma ta kaisu kasuwa cikin maza ana ta cakudewa yanzu haka ma wani ya gogar masa jikin matarsa nan take bai San sanda ya shiga mota ba ya bar Office driver ya ja suka tafi,a hanya ya kira Ma'eesha ta fada masa inda suke minti kadan sai ga Aayan ya danna musu Horn tare da sauke glass.
    Ina ganinsa hankalina ya tashi na rude ko ta kan me kaya banbi ba nayi sauri na isa motar mu na fada ciki,Meenat da Ma'eesha suka shiga bayan mota kusa da Aayan da Kansa ya kaisu Shopping ya siya musu wanda suke so masu tsadar gaske komai har ni ma suka siya min nawa,ni kuwa tuni nasa Baba Driver ya maidani gida.
     Da suka dawo da kyar na fito palo,Ranar da dare nasha warning wajen Aayan sai da ya min ba dadi ina bashi hakuri.

    Anyi mana hutun schl Meenat tana zana waec da Neco dinta,yau Sunday muna zaune a palo ina yankewa Aayan Farce,Ma'eesha na karatu a wayarta da Ameer ya siya mata me kyau,Meenat kuwa abinci take ci dawowarta daga schl kenan yamma lisss,wayar Aayan ce ta fara ruri,da hannuna na daga kiran naga ansa Bobo nasan Yarima ne na kara masa a kunne yace Hey frnd  ya kk,Yarima yace gani a gidanku fa bude min kofa, Ma'eesha yayiwa magana yace budewa Yarima kofa Angel dama haka yake cewa Ma'eesha,Meenat kuma yace mata Preety, ni kuma daga ke shike nan sai ta mugun baci zai ce Mufeeda ina takaicin wannan abun da yake min Amma ya na iya tunda ni ba a sona.

     Ma'eesha na bude kofa Yarima yayi arba da ita wow ya furta a ransa da gani ba sai an fada ba yasan ma kanwar matar Aayan ce Sabo da kama da muke kawai haske zan fisu kadan shima idan baka sanni sosai ba baza kace na fisu haske ba,ba wani me yawa bane,Maeesha akwai fara'a ta gaisheshi tana murmushi sai kallonta yake ta gama Tafiya da Imaninsa gaba daya, bashi da burin auren yarinya karama Amma akan wannan kuwa sai dai a mutu, da sallama dauke a bakinsa ya shigo,Gaskiya Yarima ya hadu Chocolate ne me haske karshen kyau yana da shi dan fulanin Asali ne,ga wanka iya wanka dama duk irin abokan su Aayan ai haka suke basa muamula da garori, Ma'eesha kuwa kunya ma taji irin yanda ya mata Kwarjini gashi ya hadu sai kuma irin kallon da yake mata.
    Yana zuwa ya mikawa Aayan hannu suka tafa shegen gari kwana biyu Aayan ko Saudiyya banga kaje Umrah ba last wk ina can ina ta jiranka kace zaka je har na dawo bamu hadu ba,Tabe baki Aayan yayi tare da cewa gwauro shike yawo lokacin da yaga dama,dariya Yarima yayi lallai Aayan ka canja,juyawa nayi muka gaisa dashi a mutunce yana tsokanata da Abokinsa yayi kiba ya kara kyau me nake bashi ne,Meenat kawo masa ruwa,Kallon wacce aka kira da Meenat yayi tana can Dining tana cin abincinta da alama bata San anyi bako ba,Yarima a ransa yace su wannan gaba daya kama sukeyi da juna amma Ma'eesha irin muryata ce da ita sak,Meenat ce muryarta tafi tamu siranta sabo da iyayinta ta maidata siririya,kayan sanyi ta kawo masa iri iri kana ta gaisheshi a ladafce ya amsa tare da cewa Mufeeda wannan duk kannenki ne? Ae mana wannan Ma'eesha wannan Meenat,yace ke kuma Mufeeda triple M kenan yeah Ma'eesha ta amsa muna dariya,Meenat yan mata uwar iyayi tana ji da yan matan ci sai girman kan tsiya watarana kamar wata yar sarki aka take komawa magana ma sai taga dama,watarana kuma ta zage ayi da ita,Muna zaune ana hira sai ga Ameer ya shugo an ci wanka yazo dan ya birgeni ni Mufeeda wacce ban san me yake bama,Maeesha har taji sanyi data ganshi kusa da ita ya zauna ta gaisar dashi,Yarima ya fara kishin Ameer ya zauna kusa da Ma'eesha kuma yaga Ma'eesha sai wani Fara'a take masa sun fara surutunsu da alama sun saba da juna,s hi kuwa Ameer gaba daya Hankalinsa na kaina yanda na hade cikin Lace riga da skert ba karamin kyau nayi ba,abinda ya bashi haushi ganin ina yankewa Aayan farce gashi kuma kafafun Aayan gaba daya saman cinyata ya dorasu yana kwance dan naji dadin yanke masa farcen.

    Muna zaune daf da Magrib wata yar aiki ta shigo wai Meenat tazo tayi bako,Meenat tace ita bata da bako baza taje ba,tun kafin ta fara magana Ameer ya fara dariya,haka Aayan ma,nima na gane me suke nufi ko irin su Kwaja ne suka zo,Yarima yace mene haka daga ana kiran yarinya zaku fara mata dariya bai dace ba,Yar aikin tace a wata fyallelliyar mota yazo Hajiya da gani dan wanine,Nace mu ai bamu damu da wani me mota ba ko talakane indai yana da aikin yi,halaye masu kyau to alhmdllh zamu bashi ba wani sai me mota ko kudi etc,Aayan yace Pretty jeki kiji idan Bai miki ba ki dawo,kawai sabo da Aayan ne yace shi yasa ta figi Hijab tana fushi zata fita,nace ba kwalliya haka za a je? Kallona tayi kamar zatayi kuka ta fita abinta haka, taga mota iya mota tana jira taga wani Handsome ya fito sai taga Fela Gala da gani ba motarsa bace arota yayi, fitowa yayi tare da tsayawa yasa Hannu a aljihu harda Harde kafafu ya basar a jikin mota sai yanzu ma ta gane Ashe Motar tana ganin su Haneefa a cikinta,wato sune suka bashi aro azo a raina mata hankali.

   Ko saurarar Fela batayi ba tayi gaba abinta sai gata ta shugo kamar zata fashe tana wa Aayan magana dan Allah Yaya ka ganshi can ya biyo ni har gida wlh dan Allah ka koreshi sune suka kara turoshi, Ma'eesha tace Fela Gala ne wlh tun daga sunan Yarima shima ya fara dariya bai Sha dariya ba sai da ya leka ya ganewa idonsa harda rike ciki sabo da dariya,Ameer kuwa ba a magana,Aayan ne ya fita ba shiri yayiwa Nasuru fata fata da gudu ya fice daga gidan ya bar motar dama ta gidan ce.
   Meenat ta kalli Ameer tare da zuba masa Harara ta wuce Bedroom ta barsu suna bawa Yarima labari duk kwalliya da iyayin Meenat irin su Nasuru Fela ke zuwa wajenta,Yarima ya kalli Ma'eesha tare da cewa to ke yar ficika wanne kala ne naki? Dariya sukayi Sabo da Fela Gala ne yace mata Yar ficika,Maeesha tace ni yarinya ce ba yanzu ba,wani dadi Yarima yaji a ransa,Maeesha kuwa a ranta cewa take insha'allah Ameer ne ma,Shi ko Ameer tunani ma yake yaushene zai mallaki Mufeedansa,Ni kuwa ina nan zuciyata dankare take da son Mijina Aayan wanda naga Sam bai damu dani ba.
    Sallah sukaje masallaci har Isha basu dawo ba,lokacin na tattara su Meenat muna kitchen muna karasa abincin da muke,suna dawowa na fito da ludayi a hannuna ni ga uwar girki na manta ma da Ludayin juya miyar na fito,Ameer yace ina zaki abun miya kuma? Nace na manta sauri nake nasan Babyna yanzu wanka zaiyi,Ameer nan take mood dinsa ya canja amma ni ban gane ba nace bari ka gani na koma kitchen na ajiye ludayin na fito naji muryar Ameer yace mu dai ki koma ki karasa mana abincinmu yaran nan jagwalgwalo zasuyi mana,murmushi nayi nace sun iya sosai ba matsala,ya kara magana pls Aunty kije ki karasa da kanki,nufin Ameer dan kar naje wajen Aayan shine ya hada min wayo wanda ban sani ba ni kuma sai na koma kitchen din,n a tayasu muka karasa komai na barsu su gyara kitchen tare da shirya Dining,dana fito nace Ameer ina Aayan fa? Baki ya tabe yace suna wancen palon shi da Yarima,palon da ya fada min na nufa

    Direct naje shiga palon naki muryar Aayan yana cewa kyaleta ai wahalar da kanta takeyi bari nayi ta gama shiga hannu zata ga wulakanci,sai suka tafa da Yarima,nan take naji jikina ya dauki rawar sanyi,tsoro da fargaba tare da bakin ciki ya dirar min,ban san wa suke nufi ba,ban san akan me suke maganar ba sai na fassara maganar da naji kawai ba bincike ban tsaya naji dalili ba ko da wa yake nufi kawai sai na yanke hukunci cewar ni suke nufi dani suke,wato ni ya gano ina sonsa wahalar da kaina nakeyi,ya bari na shugo hannu ya wulakantani,ni zai wulakanta ma tab lallai dan Adam,duk abinda nakeyi Ashe baya gani a banza sai ma mugunta da yake hada min,nan take na fara tunano tun farkon haduwarmu irin tsanar da ya nuna min,Ammah ta da suka kashe min tunda sune suka jawo duk so yasa na manta,har aurenmu irin abinda ya dinga min a farko na wulakanci ina ta binsa,so yasa na manne masa nake kai kaina har dakinsa na sakar masa jiki,nasa yaji dadi,na godewa Allah da yasa ba ayi sex ba.
    Mata da dama suna irin wannan daga jin magana bata kai ta kawo ba,basu san ma akan me akeyin ta ba,amma da yake kullum a zargin mazajensu suke irin ko sun daina sonsu,ko suna kula wata,musamman ace suna da kishiya ko zai kara aure,ko wani dalili yasa dai taga mijin ya dan canja to zargi zata kasance a ciki iri iri,komai yayi laifi ne a wajenta,magana idan ta ji ko da abokinsa sai ta fassarata ta koma tashin hankali Babba,wata ma har abokin zata daina kulawa,ko ta masa rashin mutunci,miji na neman aure abokin dole shine a gaba wai dan me zaiyi nan fa zata kulla masa wata ma sai ta rabasu sun bata sun daina abotar,wata kuma duk abokansa ta daina kulawa ko ta ci musu mutunci wai sune suke zuga mijinta,duk da cewa ana samun masu hakan amma mata mu daure mu daina zargi tare da saurin yanke hukunci,ko magana akayi sai a dinga fassara ta bai bai sabo da ba a son zaman lfy.

     Ni dai ina tsaye naji kamar ma zazzabi zan fara sabo da yanda nake son Aayan ko kaina ban so haka,bani da burin da ya wuce naga ya soni back amma sai gashi abinda naji ma daga bakinsa,Hawaye na share na daure na shiga palon fuskata ba walwala nayi Sallama suka amsa,Nan take Aayan ya kafeni da idonsa yana ganin yanda lokaci kadan na fita daga hayyacina,dazu lfy lfy muke,kamar ma kuka nayi,ganin yana kallona nayi kasa da kaina,tunaninsa ko yan gidansu ne suka yi min rashin mutunci ya tabbatar idan kuwa sune suka sa na dawo haka yau sai anyi yaki a gidan nan,baya son a taba masa ni yanzu ko kadan, kasa jurewa yayi yace ina zuwa Yarima yaja hannuna mukayi waje dashi muna fitowa a jikin kofar yasa yatsansa tare da dago da fuskata yana kallona sannan a hankali yace lfy? Me akayi miki? Nayi shuru,Hajja ce? Su Haneefa nan ma shuru sai Hawaye dake biyo min a kumatuna a raina ina kara cewa yanzu wannan zankadeden rabuwa zaiyi dani,shike nan baya sona? Yace am asking u me suka miki ya fada da tsawa,duk ya shiga damuwa lokaci guda ya rude Allah sarki So,so banza ne kawai sai ya bani tausayi kuma na batawa wanda nake so rai,har bana ganin laifinsa sai nawa sabo da Aayan baya laifi a wajena so hana ganin laifi,tunowa da maganarsu dana jine yasa na kara birkicewa,kawai nace ni ba wanda ya min komai kawai ji nayi bana son auren Kasuwancin nan ko nawa zan samu,ko yanke talauci ne wlh bana sonsa dan Allah ka sakeni na tafi, wani dum yaji maganar a bazata to ko dai itama sun mata wani asirin ne ko kuma sun sa mata wani abu taci ai ko wlh bazai iya sakinta ba har abada sai dai duk inda zata je da aurensa,jikin Bango ya Dafe kawai yayi shuru yana Innalillahi kawai yake maimaitawa duk zarginsa tunaninsa Su Hajja ne ko asiri ko kuma wani abu suka mata wanda baza ta iya zama ba, da kyar ya dago muka hada Ido sai da na rumtse Idona yanda bazan iya kallonsa ba ya Zama wani iri idonsa yayi jajir,Hannu na ya figa kamar zai tashi sama ya jani muka Haura samansa har Bedroom ni dai kawai binsa nakeyi,a ciki ya tsaya tare da rike kugunsa da hannu biyu kansa ya daga sama yana danne lips dinsa na kasa da Hakoransa yama rasa ta ina zai fara, maganarsa naji a hankali yace Mufeeda! na kalleshi tare da sadda kaina kasa,yace ki fada min me ya faru dake me kike ji me yake damunki ko kuma a gidan ne wasu suka ce miki wani abu ni dai nasan ban miki komai ba,ko kema sabo da bamuyi Xxx ba zaki tafi? Da sauri nace a'a wlh ba haka bane,yana kallona yace to ko bana Haihuwa kike nufi? Nan ma kafin ya rufe baki nace wlh ba wannan bane,to mene tell me,karki rufeni ko ki cuci kanki just tell me what's is going on? Ina Hawayena nace ni kawai na gaji da auren ne Bana son kudin yanzu,Wait bafa Business muke ba wannan wasa ne kema kin san aure ne na sunna aka yishi ba wai akan kudi ba,nace ae na sani kawai bana son auren ne nace ma ni bazan zauna ba kawai,ok yace ko gidan nan ne bakya so? Fada min sai na Canja muku gida,kai na girgiza a'a, yace ko Wacce kasa kike so fada min wlh zamu koma can indai kina so,a raina nace jibeshi kamar gaske salon ya kara mallake min zuciya yaji dadin wulakantani da kyau to bazan je ba,nace bazanje ba ni a fili,Abuja fa?nace ko villa ne banso,to kiyi Hakuri idan wani abu aka yi miki addua akeyi akan komai ba fushi ba haba yan mata nan ya dinga lallashina,sai nayi kamar zan Yarda naji tausayinsa sai kuma na fasa nace nifa bazan zauna ba.

   Yana gajiya ya tamke fuska ba mutunci yanda na sanshi tun farko,nan take naji tsoronsa jikina ya fara rawa, tahowa yayi kamar zai makeni na fara ja da baya yana Huci yace bari kiji bude kannenki wallah kinji na rantse har uku bazan sakeki ba kuma ba inda zakije idan kika fita ma ko gate ne bada izinina ba sai munyi Shari'a dake a gaban Allah ban yafe miki ba,kiji ni da kyau ba wani Business auren za ayi as from today ni kuma duk Hakkin ki daga yau zan fara baki,yana gama fadin haka ya kwanta a saman Bed yana Dafe kansa dake Sarawa, tausayi kuma ya bani sosai yanda ya nuna ya damu a kaina gaba daya sai na tsani kaina me yasa nayi haka,amma dai zuciyata ta hanani na hakura,ido ya rufe sosai still yana Dafe da kansa ya rike sosai da alama ciwo yake masa da yawa,Hankalina ya tashi nima,mikewa yayi tsaye kamar wanda yasha giya yana maye da tangadi,haba ban san sanda tausayinsa ya gama rufeni ba gaba daya naga ya fini shiga damuwa yazo ya ratsa ta gefen zai wuce ya fita tuni na damko hannunsa ya tsaya cak tare da juyo da fuskarsa ya kalleni gabansa na koma tare da fadawa jikinsa na rungumeshi kam kam sosai da sosai kamar za a kwace min shi, baiyi hugging dina back ba,da kaina cikin kunnensa na rada masa Rug me back am so sorry, bai kulani ba babu zato naji bakinsa cikin nawa ya fara tsotsa ya rabani da kasa dan dagani yayi sama yanda tsayinmu zaizo dai dai ba sai yasha wahalar sunkuyoba,haka muke tsotse bakin juna kamar mun samu wani kayan dadi na tsotsa,wannan kiss din yafi na kullum dadi,gardi,tare da nishadi,yanda nakeji  ya zarce na fada muku,muna ta yi ba ji ba gani kamar zamu cinye kanmu ko nayi kamar zan kwace bakina sai ya kara rikeni kam ya hanani sai da muka dauki dogon zango a haka sannan da kyar na zare jikina daga nasa,amma duk da haka kara jawoni yayi jikinsa tare da fara lashe min wuya,tsigar jikina tashi take kawai gaba daya ya gama kara min sonsa a zuciyata, da kyar nake iya tsaiwa da kafaguna shima haka,ya fara kokarin cire min kaya na tuna yayi maganar hakki dazu da sauri na rike masa hannu tare da cewa abinci still dai ban saki raina ba bana wani nishadi kamar dazu,kyaleni shima yayi fuska ba walwala yace let's go,sai da muka saita kanmu sannan muka sauka kasa,Gaba dayansu Har Yarima da Ameer suna Dining suna ta cin abincinsu muka sakko duk kayanmu ya nuna da gani anyi yamutse yamutse,ga T-shirt din Aayan Fara kar ce duk jambakina red da Powder a jiki duk na shafa masa ba tare da mun sani ba sabo da murzar juna,Yarima da Ameer duk sun gane me akayi,Meenat ma ta gane gani ba jambaki a bakina sannan duk ga wani nan a bata gefen bakina,Aayan harda digon jambakin a hancinsa duk sai yanzu ma muka kula da hakan,Yarima sai dariya yake kunshewa yana kallon Aayan, dan Iska wlh zaka bar gidan nan banza munafiki Cewar Aayan,Yarima yace to me nayi kuma? Bayan ka shanyani,Ameer kishi ya hanashi kallon kowa kawai tura abincinsa yakeyi,Aayan har yau yana cikin damuwa ya kasa cin abincin kuma yunwa yake ji,ni kuwa bakin ciki baya hanani cin abinci ko cuta nake sai naci na koshi haka nake bare kuma kafin naji Maganar da su Aayan sukeyi tun a kitchen muna girkin na cika tumbina, ganin ya kasa ci na Mike tare da Zama kujerar dake kusa da tashi zan bashi da kaina,kafin na fara Ameer ya ajiye spoon yace ina zuwa bari nayi waya ya fice da sauri zuwa part dinsu,Yarima yace nima tafiya zanyi Ma'eesha zo ki rakani mota nan yayi mana Sallama suka fita,Aayan yace sai nazo zanyi maganinka ya furta da alama kawai danne bacin ransa yakeyi,Meenat ma tuni tayi Bedroom zata fara karatu,daga ni sai shi ya Dafe kai tare da rafka tagumi da gani yana cikin damuwa me yawa.

     Hannun da yayi tagumi na janye a hankali ba tare da nace komai ba na ebo abincin a spoon na fara bashi da kaina yanda yake ci zaka San baya jin dadinsa ko kadan,kamar kurame haka muke har yace ya koshi nace ko spoon biyar baka ci ba fa? Zan fara masa magiya ya Mike kawai ya haura sama ya barni a nan,ban damu ba na tattara komai na kai kitchen tare da gyara komai na shiga Bedroom dinmu nayi wanka da duk wani abu da zanyi nayi nasa Night gown dina da kawata Sayyah ta bani wai inji mamanta kala Uku hadaddu amma basu fiye tsaraici ba nasa light blue din masha Allah nayi gaskiya karshe na daura ta samanta na fita lokacin Ma'eesha ta dawo daga wajen Yarima tana nuna min chocolate masu Uban yawa da kudi masu yawa wai a bani inji shi,na karba nayi godiya nace bari na nunawa Aayan kafin Ku fara sha nayi waje zuwa Bedroom dinsa,gefen Bed na hangoshi a zaune yayi shuru kawai yana kallon sama da alama tunani yakeyi yaji Sallama ta,amsamin yayi kawai tare da kwanciyarsa saman Bed ya barni a tsaye,banji dadi ba ni kaina muna zamanmu lfy na jawo bacin rai kuma shi dama kafin a lallasheshi aikine.

    Haneefa ce Zaune tare da Mommynsu suna hira,Mommy tace Ameer naga fa kamar kwanan nan ya Mannewa wajen yan iskan can a part dinsu ban san ko Hajja tasan labarin ba,Haneefa tace Mommy ki barshi ai da alama bata sani ba gwara ma da kika tuna min bari naje na fesa mata tayi maganinsa ya daina zuwa na tsani Su Mufeedan nan Shegu wai su masu kyau,Mommy baki ta tabe tare da cewa je ki sanarwa Hajja ni ma yau zan fadawa Abbi abin na Ameer yayi yawa, da sauri Haneefa ta tafi part din Hajja,ta samu Hajja sai Mulki take zubawa tana wani takama da isa tare da bawa yan aiki umarni.

     Haneefa ta zauna gefenta tare da cewa Hajja wani labari na kawo miki marar dadi so sad wlh abin kunya ma,Ina jinki Hajja ta furta tana gadara,Haneefa ta gyara Zama tare da sanarwa Hajja yanda Ameer ya koma bangarensu Mufeeda.
   Hajja da masifa tace to azukwi uwar munafunci me yasa kuke takurawa Ameeru ne,ina ruwanki Algunguma to nasan da zuwansa aikina yake ni na turashi,kinzo da guntun munafuncinki ai zai shigo ne zan fada masa me kika ce ya farfasa miki jiki,Haneefa ta fara bata hakuri daga fadar gaskiya sai a lullubeni da fada to daga yau bazan kara fada ba ko mene zai faru ya faru,Hajja ta dakko yar sandarta ta karfe tayi kan Haneefa da gudu ta fice ta bar Hajja na Masifa ta gaji da Gulmar Ameeru da akeyi a gidan nan.


AsmaBaffa 
    Loves u all ❤?
Reply


Possibly Related Threads...
Thread Author Replies Views Last Post
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA Gimbiya 1 32,229 03-26-2019, 10:46 AM
Last Post: Gimbiya
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA Gimbiya 4 120,151 02-22-2019, 08:04 AM
Last Post: Gimbiya
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA Gimbiya 0 7,552 01-18-2019, 09:17 AM
Last Post: Gimbiya
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA 0 2,511 Less than 1 minute ago
Last Post:
  *KASUWANCI NA* by ASMABAFFA 0 3,072 Less than 1 minute ago
Last Post:



Users browsing this thread: 1 Guest(s)