The following warnings occurred:
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/printthread.php 16 require_once
Warning [2] Undefined array key "avatartype" - Line: 783 - File: global.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php 783 errorHandler->error
/printthread.php 16 require_once
Warning [2] Undefined variable $awaitingusers - Line: 34 - File: global.php(844) : eval()'d code PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/global.php(844) : eval()'d code 34 errorHandler->error
/global.php 844 eval
/printthread.php 16 require_once
Warning [2] Undefined array key "showimages" - Line: 160 - File: printthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/printthread.php 160 errorHandler->error
Warning [2] Undefined array key "showvideos" - Line: 165 - File: printthread.php PHP 8.0.30 (Linux)
File Line Function
/printthread.php 165 errorHandler->error



Forums
HANYOYI 52 DAKE KARAWA ZAMAN AURE MARTABA IDAN ANYI - Printable Version

+- Forums (http://contripeople.com)
+-- Forum: Retired Forums (http://contripeople.com/forumdisplay.php?fid=78)
+--- Forum: Retired Forums. Please Make Your Post Within The 3 Forums In General Discussion (http://contripeople.com/forumdisplay.php?fid=49)
+---- Forum: Hausa Language Forum (http://contripeople.com/forumdisplay.php?fid=40)
+---- Thread: HANYOYI 52 DAKE KARAWA ZAMAN AURE MARTABA IDAN ANYI (/showthread.php?tid=987)



HANYOYI 52 DAKE KARAWA ZAMAN AURE MARTABA IDAN ANYI - Gimbiya - 11-16-2017

HANYOYI 52 DAKE KARAWA ZAMAN AURE MARTABA IDAN ANYI
Laƙanoni 52 Na Mayar Da Mijinki ‘Mijin Tace’- Marigayi Sheikh Ja’afar Mahmud Adam
Da sunan ALLAH mai gamammiyar rahama, mai jinkai. Tsira da aminci su tabbata ga Annabin rahama, da alayansa, da sahabbansa, da duk wadanda suka bi tafarkinsu har ya zuwa ranar tashin al-kiyama.
[Image: husband_and_wife_by_babyjepux-d68tkhl-300x212.jpg]
Bayan haka, shakka babu, a wannan zamani ‘yan mata da zawarawa kai harma da matan aure suna cikin zullumi da tsoro da rashin kwanciyar hankali, saboda yadda aurensu yake yawan mutuwa, bayan kuma, an dauki dogon lokaci ana soyayya a tsakani.
 
Ga wasu Shawarwari wadan da idan mata suk ayi la’akari da su In shaa ALLAH za a samu kyautatuwar zaman aure. Muna addu’ar ALLAH ya bada ikon kiyayewa.
 
1- Aurenki ya zama domin neman yardar ALLAh ki ka yi ba don tara abin duniya ba.

2- Kada ki zama mai kwadayi wajen zaben mijin Aure.
 
3- Ki zabawa ‘ya’yanki uba ta hanyar auren wanda ki ka yarda da addininsa da dabi’unsa har ma da dangantakarsa.
 
4- Ki zama mai riko da addini a gidan mijinki.
 
5- kada ki zama mai kauracewa shimfidar mijinki.
 
6- Ki zama mai hakuri da halayyar mijinki.
 
7- Ki zama mai matukar biyayya ga mijinki.
 
8- Ki zama kwararriya wajen iya kwalliya kala-kala.
 
9- Ki zama kwararriya wajen iya girki kala-kala.
 
10- Ki zama kin iya barkwancin magana wajen baiwa mijinki dariya.
 
11- Kada ki zama mai rainuwa a cikin duk abinda mijinki ya baki.
 
12- Ki dinga wanke bakinki da safe da yamma da kuma lokacin kwanciya barci.
 
13- ki zama mai tsaftar jikinki, gidanki, abincinki, da sauransu.
 
14- Ki dinga girmama Iyayan mijinki da ‘yan uwansa da abokansa.
 
15- Kada ki zama mai satar kayan mijinki.
 
16- Kada ki zama mai satar fita unguwa.
 
17- Ki guji Leke a gidan mijinki, dan yana daga cikin abinda yake raba Aure a tsakanin Hausawa.
 
18- Ki dinga godewa mijinki a cikin abinda ya baki.
 
19- ki kiyaye abinda mijinki ya fi so.
 
20- ki kiyaye abinda mijinki ya fi sonci da safe, rana, dakuma dare.
 
21- Ki dinga yabawa mijinki kwalliyarsa.
 
22- Ki dinga yawan neman shawarar mijinki akan duk wani al’amari da zaki yi.
 
23- Ki yi kwalliya ki tsane tsaf kafin dawowar mijinki.
 
24- Ki dinga sanya turaren wuta a dakinki, kuma ki kasance mai sanya turare a jikinki a duk lokacin kwanciya.
 
25- Lallai ki yi kokarin gama aikace-aikacenki kafin dawowar mijinki.
 
26- Kada ki bari mijinki ya dawo ya sameki gaja-gaja, ki sani kazanta tana haifar da kiyayya.
 
27- Ki zama mai yawan canza zanen kunshin kafarki da kuma zanen kitso.
 
28- Kada ki ce mijinki sai ya saya miki abinda ba shida ikon saye.
 
29- Lallai ki yi amfani da ilimi wajen yanke dukkan wani hukunci.
 
30- Ki yi shiru a duk lokacin da mijinki yake yi miki fada ko Nasiha.
 
31- Kada ki zama Al-mubazzara mara tattali.
 
32- Kada ki tara kayan wanki da yawa a daki, naki ko na mijinki suna wari.
 
33- Ki tanadi kayan kwalliyar gida bayan na zuwa unguwa.
 
34- Ki kula da yanayin da zai nuna miki cewa mijinki yana cikin Nishadi ko Damuwa.
 
35- Kada ki ringa baiwa kawayanki labarin sirrin dake tsakaninki da mijinki.
 
36- Idan zaki yiwa mijinki magana kiyi masa da tattaunsan harshe, da murya mai karya zukata.
 
38- Ki zama kin iya kallo mai nuna alamun sha’awa ko soyayya.
 
39- Idan kika samu sabani da mijinki ki bashi hakuri ko da kuwa kece da gaskiya.
 
40- Ki zama mai tattali a cikin dukkan abinda kika mallaka a gidan mijinki.
 
41- Kada ki zama mai kwauron baiwa dangin mijinki abinda ya umarceki da a basu.
 
42- Kada ki zama mai yin dare wajan girki.
 
43- Kada ki zama uwar adashi ba tare da sanin mijinki ba.
 
44- kada ki zama mai yawan fada da makwabtanki.
 
45- Kada ki kasance mai yawan zagi ko Ashariya.
 
46- Kada ki ringa baiwa Iyayanki Labarin laifin da mijinki yake miki.
 
47- Ki zama mai hakuri da juriya da halayyar Iyayan mijinki da ‘yan uwansa.
 
48- Idan mijinki ya yi miki laifi kada ki nuna masa bacin ranki a gaban iyayanki ko ‘yan uwansa.
 
49- Kada ki ringa daga murya sama idan kuna sa-in-sa da mijinki.
 
50- Kada ki ringa baiwa ‘yan uwan mijinki labarin laifukansa.
 
51- kada ki ci wani abu da mijinki baya son warinsa misali tafarnuwa.
 
52- Ki dinga yiwa mahafiyar mijinki Ihsani da ‘yan uwansa.
 
Ga Amana nan mun baki/ka ka tura wa mata ko maza domin a isar zuwa ga ‘yan uwa mata.

http://mujallarmu.com/addini/karanta-kaji-hanyoyi-52-dake-karawa-zaman-aure-martaba-idan-anyi/